KANA NAKA BOOK 1.
KANA NAKA..!
1
LITTAFIN
JAMILA UMAR
(JANAFTY)
***.
***.
SHEKARAR RUBUTU:2023.
SADAUKARWA.
Gabadaya Littafin KANA NAKA, Sadaukarwa ne ga iyayena guda biyu. ALHAJI UMAR MUHAMMAD MAILOKI, tare da mshaifiyata albar alfaharina HADIZA MUHAMMAD BA'ARE. Allah ya saka muku da gidan Aljannah Firdausi. Allah ya sa ku gama da Duniya lafiya Ameen.
TUKWAICI.
KANA NAKA. Tukwici ne zuwa ga re ku Anty Sis(My Anty), Surraya Dahiru gwaram(Kawata), Aisha muhammad Alto,(Sisinah), Halima Yusuf gwarzo(Besty), Khadija Salisu yusuf(Ummina).
Ina kaunar ku Allah ya had'amu a Aljannah.
KUNA RAINA.
Daukacin JANAF, Fatima Umar(Fatina),Sci.Jamilu Umar(Ya jay), Hafsah Mustapha Hafnan(Sahibatu), Zainab Muhammad Chubado, tare da Daukancin Ahalin gidan Baba mailoki.
GARGAD'I.
Ban yarda a sarrafa wannan labarin ta kowace siga batare da izinina ba. Karantawa a wata kafar sada zumunta batare da izinina ba, ya saba ma hakkin mallakata.
TSOKACI.
Labarin KANA NAKA, kirkirarren labari ne, ganin abunda ya yi daidai da na suna,gari ko Hallaya. To an sa ne domin arashin labari ba da niyyar cin zarafin wani ko nu ni da rayuwar wasu ba.
*Shimfid'a.*
Katsina.
Area:Layout.
Karfe Tara ya shigo gidan nasa kamar yadda ya saba duk da yau yayi dare agidan mama chan kofar soro tunda tachan ya fara sauka bayan isowarsa Dazu da mangariba dagachan inda yake aiki a birnin Abuja.
Da kansa ya Tuko kansa Daga Abuja wannan Satin sakamakon Direbansa mallan iliya,mahaifinsa ba Lafiya ya tafi garinsu ya Dubasa bayan ya mai izini..shiyasa gabadaya agajiye yake gabobinsa gabadaya sun sake suna Bukatar Ruwa mai zafi tare da Tattausan Hannun wajen kwantar dasu su koma Daidai kuma Gajiyarsa ta Hada harda Dadewar da yayi mai baiyi Dogon Tuki ba ko Chan karofi zai Tafi Mallam Iliya ke tukasa Abu ne mai Wahala ka gansa yana Tuki da karan kansa.
Cikin muryansa mai Cike da Zati kamar ko yaushe yayi sallama bayan ya shigo Kyakyawan falon gidan nasa,wanda yara duk sun bata Fentin da Rubutu da Maker da Pencil,sun gama Lalata kyakyawan fentin Dake cikin Falon da ba'a sabuntasu ba Sannan ga kujerun nan duk sun ji jiki,sun fara yagewa Kushin din zaman duk yayi kasa,ya yamushe,shi kanshi Cafet din Tsakar Dakin ya fita Hayyacinsa Duk yayi Wusu wusu sannan yayi Datti Sosai.
Sau tari irin wad'anan abubuwan ke saka yayi zamansa Abuja baya kaunar ya shigo Katsina ya Shigo Gidansa yaci karo da yanayin yadda MATAR gidan ta bar yara suka barnata komai na gidam kamar gidan wata mai Saida Kuli kuli Tsabar yadda gidan ya fita Hayyacinsa.
Cikin yanayin kallonsa ya kare ma Falon kallo karamin Tsaki yaja ganin harda Takardun yaran duk sun yaga sun gama Haukata Falon bai nemi kowa ba sanin ba Sautin dawowarsa zataji ba Wacce ko agabanta kake sai kayi mgana kana Faman maimaici take iya jinka.
Yana Sarsarfa zuwa Bangaransa,wanda ke Rufe sai in ya Dawo ne yake budesa da kansa kamar Daga sama yaji Daga bayansa ance"Sannu da zuwa Yaya ISHAQ.."
Cak ya tsaya kafin ya juyo lokaci D'aya yana kara rike yar Jakar Laptop din dake Hannunsa,Girman Idonsa ya kara na ganinta domin har ya koma wanchan Satin bata agidan kenan bayan Tafiyarsa ne tazo gidan kenan..?
Bai damu ba illah baki Daya mele kafin ya ce"Sannu da gida.."
Ta amsa mai tana kokarin Tattara kayan yaran da suka gama Bidirinsu yanzu afalon kafin Yaya Fa'iza ta ja su ciki Domin su yi Fitsari su kwanta.
Bata Damu da yanayin da ya amsa mata ba inda Sabo ta saba tun tasowarta bata Taba ganin Fara'ar Ya Ishaq acikin gidan yayarta ba sai dai in chan gidan Mama kofar soro ce ko kuma yana Tare da yan'uwansa su a Gare su mutum ne mai wahalan mu'amala.."
Agabanta ya Bude kofar Shashensa ya shige ya rufo kofa ta bisa da kallo ta jinjina kai Gaskiyan Anty Binta batagwara ce Data Dad'e tana Fadin ban da Kaddaran aure ta ina Yaya FA'IZA ta Dace da Ya Ishaq..?Ya Ishaq Dogo ne Farin Buzu tas dashi Domin Mama kofar soro Buzuwar Yamai ce,Sannan Baba Kabiru marigayi Cikakken batsine daya fito Daga Korofin katsina Sai dai kaf ya'yan mama ita suka Dauko Wajen kyau da Nasaba Domin har yau da shekaru suka ja kyanta bai Zube ba Tanan nan mai kyau da ita.
Kuma yanayin Tsahon sa ya biyo na Dangin su Baba ne dake Karofi suma Dagayen katsinawa ne marasa Lalaci sannnan sai ya Hada da Hancin Mama da Sirantar ka ta yasa Ishaq ya zama mai kyau kuma mai aji sannan mai Tarin Ilimi Addini dana Zamani Wanda Duniya ta san sa kuma take ji dashi,Ayanzu haka Babban ma'aikaci ne A Hukumar Tattara Haraji na kasa reshen Abuja(FIRS)Federal Inland revenue Services,Ya dade yana aiki a wajen shekaru hudu da suka gabata da farko a reshen su na Jahar katsina ya fara aiki da su shekara uku kafin ya samu karin matsayi sai aka yi Transfer dinsa ya koma babban Ofishin su na Abuja,sosai yake jin dadin aiki a abuja musamman ma da samun Adalin Shugaba irin Dr. Lawal bako da yakasance shine Shugaba a ofishin su na Abuja kuma Uba garesa ko nace wanda ke shirin zama Surukinsa nan da Lokaci kad'an.
Yaya FA'IZA kuwa iyakarta primary School,primary di'n ma ba ta gama ba,a karatun Boko kenan na addini kam Saukakkiyace ta wannan Fanni sannan ta karanci sauran littafan addini iya abunda ya sauwaka ammh Duba da wannan Zamanin da muke cike domin kina da karatun muhammadiya ke bakowan kowa bace in baki Hada Fukafukan Ilimin Boko ba,Bama wannan ba Yaya Fa'iza ba irin Zabin Ya Ishaq ba ce ba cin haka ma Tana dq Laluran rashin ji,Bata iya jin mgana ahankali sai an mata da karfi take ji Dashi aka Haifeta Laluran TaMADINA ce ya shafeta Tunda ita din BEBIYA ce da shi aka Haifeta ba ciwo bane.
Tana wannan Tunanin tana Faman gyara Falon acikin ranta Tana Tunanin Yaya Fa'iza batasan ya Ishaq zai dawo yau ba domim kwata kwata bataji tayi zencen ba sannan basu da abinci agidan Taliyace ta Dafa ma su AMIR da Daddaren nan kuma D'ayace duka suka cinyeta ba Saura.
Kayan yaran ta kwashe ta tattara Takardun da suka yanka suka Zubar ta kai waje ta kofar Kitchen ta fita ta zubar a Abunda suke tara shara kafin ta Dawo Cikin Falon Dakin yaran ta Nufa inda yayar tata take domin ta shaida mata Dawowar Mijinta nata.
Da sallama ta shiga duk tasan ba lalle ta jita ba Amir Dake kwance ne ya amsa mata,Anum kuma har tayi barci mustapah musty Tuni har yayi barci,Ahmad ne a Hannunta tana Faman kiciniyar sanya mai pampers alamun wanka ta sake mai.
Karisowa shigowa Dakin yaran tayi mai Dauke da ciki Daya da karamin Tiolet,Adakin akwai gado guda uku kanana na yara,Daya na babban yaya ne Amir D'aya na Anun ce sai d'ayan na Mustpaha ne Ahmad na shan Nono Fa'iza bata yayesa ba wajenta yake kwana
Akwai Drowers na yaran guda uku acikin Dakin,inda suke ijiye kayansu na makaranta Dana gida,Har HAFSATU ta kariso ta zauna gefen Gadon Amir Fa'iza bata san ta shigo ba Hankalinta na kan saka ma Ahmad pampers ganin haka yasa Hafsatun watsa ma Amir Harara tana Fadin"Wai sau nawa zan maka Fad'an watsar da kayan ku duk inda kuka samu ne.?
Cikin muryan yarinta yace"Na Dauke nawa nasu Anum ne fa.."
Kayan ta Daga tana Fadin"Ai kai ne babba in suka bata sai ka gyara Amir din Umma.."
Jin Abunda tace ne yasa yayi mirmishi kafin yace"To Anty Hafsatu.."
Yafada Lokaci Daya yana kallon Fa'iza wacce har alokacin bata san Hafsatu na Cikin Dakin ba,Har sai da ta mike ta Zube kayan cikin kwandon da yaran ke tara kayan wanki Amir D'an kimanin shekaru Shidda da wani abu aduniya yace"Anty Hafsatu..Umma fa bata san kin shigo ba, kiyi mata mgana."
Hafsatu tace"Zan mata ka kwanta kayi barci.."
Kai Tsaye yace"Umma nake jira ta gama shirya Ahmad ta mana Addu'an kwanciya barci.."
Hafsatu ta juyo Daidai Lokacin da Fa'iza ta Dago bayan ta gama saka ma Ahmad saukakkam kaya tunda zasu kwanta ne taci karo da idon kanwar nata akanta Cikin Sanyinta da yanayin mganarta Tace"Hafsatu..yau..she kika shigo..?
Ta Fada tana kokarin Daukan Ahmad.
Hafsatu ta zauna gefen gadon Amir tana Fadin"na da'n jima da shigowa.Amir oya bude Hannu muyi addu'an barci."
Ba musu ya Bude hannu itama ta Bude suna karanta addu'ar Barcin da Annabi ya koyar da karfi ita dashi zaku mamakin yadda yaron yake karantowa Tiryan Tiryan wannan kuma kokarin Fa'iza ne bata bari wannan Ilimin nata ya tashi a banza ba Tana kokarin Rabashi ita da ya'yanta.
Fa'iza kuma Ficewa tayi Daga Dakin ganin suna addu'ar Barci Bedroom din Dake kallon Shashen Ishaq ta Shiga ta Shimfide Ahmad a kan gadonta na Royal bed sai dai ya kwana Biyu duk yaji jiki.
Dakin shima dai kadahan kadahan,Wardrope ne babba adakin ssi kofar Tiolet,daga ganin yanayin Dakin shi kanshi Shirgi yayi masa yawa Sannan uwa uba Cafet din Daya malale bedroom din shima duk ya kode yaji Duniya Duk da karfinsa na Italiyan Cafet..
Ta kwantar da Ahmad din kenan zata Fito Daga Dakin suka kusa cin karo da Hafsatu daya sa ta koma da baya tana Fadin"Ban san zaki shigo ba.."
Hafsatu ta bi ta da kallon Tsausayi kafin tace"Yaya Fa'iza kinsan ya Ishaq zai dawo yau..?
Ta fada da dan karfi Saboda ta jita Da Sauri Fa'izan tace"Eh..Me kika ce..?
Tafada Cikin yanayin sanyinta da mganarta Hafsatu ta kara matsowa kusa da ita da dan karfi tace"Ya Ishaq ya dawo nace.."
Fa'iza ta zaro ido kafin tace"Yaushe..?
Wlh bansani ba..?
Hafsatu tace"Dazu ina falo kafin na shiga Dakin su Amir.."
Fa'iza ta kama Hanyar barin Dakin Tana Fadin"Yana bangaransa ne..?
Da karfi Hafsatu tace"Eh..!
Har ta fice tana binta da kallo ganin yadda take tafe tana kokarin Daidaita Hannun Rigar jikinta na Atamfa Daya dan mata yawa yana dan Fado mata.
Kitchen naa fara isa na Bude Fridge na Dauko mai lemu da ruwa na D'ora saman wani karamin Faranti na kuma Dora Kofuna guda biyu na fito lokaci d'aya na nufi bangaran Megidan.
Kofar shashen nashi yana Bude ne ta Tura ta shiga da sallamanta duk da tasan ba lalle yana Falon ba,Agidan kaf bangaransa ne ke da Falo da Bedroom har guda biyu ne,Kuma bangaransa ne yafi ko'ina kyau domin ayanzu ma kyakyawan Falo ne Dake Dauke da Manyan kujeru na alfarma masu ruwan zuma gabadaya Falon Ruwan zuma ne,harta da Labulayen kalansu ruwan zuma da Hadadden Tattausan Cafet din Dake Falon wani Sihirittacen kamshi na tashi na Irin Turaran da Ya Ishaq ke yawan amfani dashi ne..
Akan Center Table din dake falon na Sauke Farantin Hannuna kafin na karisa D'aya daga cikin Bedroom din Dake bangaran inda na san Ishaq din yana ciki.
Da sallama na Tura kofar na shiga yana Tsaye gaban madubi ya gama saka kayan barcinsa masu Taushi Farare,riga da wando,waya ce a Hannunsa yana mgana cikin Sanyi da Tattausawa.
Ganin haka yasa Fa'iza ta juya zata fita har ta kai jikin kofa Hannunta kan marikin kofar ba zato taji muryansa Cikin Kaushinsa akoda yaushe ya Kirata.
"FA'IZA.."
dayake da karfi yayi mganar na jisa Da Sauri nq juyo inaa gyara wuyar riga ta kallon da yake min ne ya sanyaya min Jiki D'aya sa na kariso gabansa Jikina na rawa ko kafin nq samu Zarafin mgana ya D'aga min hannu Cikin Fushi yana Fadin"Je ki ma kawai domin ganin ki karin Takaici ne a wajena.."
Yafada kai tsaye Lokaci D'aya yana kauda kai Dauke da matsanancin Takaicin daya Dade yana cinsa tun shekaru Takwas da suka gabata.
Duk da ba duka tna jisa ba nasan ransa ya baci sai na Durkusa kan gwiwiyoyina Cikin yanayina nace"Ka..kayi hakuri.."
Kamar na watsa ma Fushinsa Fetir haka ya taso min yana Fadin"An ki ayi Hakurin..?
Nace bazan hakuran ba..?
Aikin banza ni zaki raina haka Fa'iza..?In shigo gidan nan tund'azu kiyi banza Dani kamar wani kashi sannan kin ga Dama kin shigo bangarena kuma kin gan ina waya ki Tsaya in gama ki gaisheni ne ki ke ke jin asara ko..?
Har da juyawa ko kunya zaki Fice ga Dan iska ko..?
To tashi ki Ficemin Daga Daki bana son ganinki..Domin ganinki ba komai Cikin sa sai karin Takaici da bakinciki..wlh har gobe bazan Daina cewa Hajiyar Karofi da Baba sun cutar dani ba..Cuta ta har Abada da suka Hada aure na Dake FA'IZA.."
Ya karishe Fad'a yana nuna min babban yatsansa Lokaci Da'ya da wani banzan kallo dayake bina dashi kaina na kasa ko motsin kirkin na kasa yi daga inda nake durkushe Domin indai ana Sabo da Tozarci da Mganangun Cin mutimci to ni na gama Sabo indai Daga bangaran Yaya Ishaq ne.
Baya ya juya min yana Faman kokuwa da bacin ransa yana jina Cikin yanayin mganata ina kara Fadin.
"Kaayi hakuri don Allah..Ban ji shigowarka bane ina chan ina ma su Anum shirin barci sai yanzu Hafsatu ke shaidamin dawowarka..!
Sannu da zuwa.."
Kyaci yayi kamar wani maciji shifa ba Domin Ya Binta ta Kira sa akan yazo yaga kayan lefensa da ya bata kwangilar hadawa ba,da babu abunda zai kawosa katsina cikin wannan Satin ballatana har yazo ya shaki wannan Bakinciki.
Juyowa yayi yana kallona Lokaci d'aya kawai ya tsaya yana kara kare ma Fa'iza kallo akasan ransa yana kara Tambayan kansa da gaske FA'IZA matar sace?
Fuskarta ya kara kalla yana jin Shima Tunda yake bai taba ganin mai baki,bakin Fuska irin Fa'iza ba, zai iya Rantsuwa ga Allah kaf ajikinta banda Hakoranta ba inda yake da Haske bakace ta kwantance irin bakin nan mai Duhu da Dususu,Sannan mummuna ce bata da kyau a ganinsa sannan bata da Tsaho wanda Hausawa suke cewa mai cike Girman kyan y'a mace Gajera ce,da Fadin Fuskarta kamar Fanteka,Da guntun Hancinta da bakinta mai Fadi shima,Abu daya ne zai ce mai kyau a wajen Fa'iza shine tana da Kirar mata Wannan kam masha Allah Dirarriyace Kirjinta da kugunta suna cike da Fasali ya mace ko ayanzu Data Haifi ya'ya Hudu bata Sauya ba Ta na nan da Jikinta mai Fasali daidai misali bata da kiba sai dai Haihuwa ta d'an Budata.
Sai kuma bangaran Ni'imar jikinta ta wannan bangaran bai da ta cewa ya san Fa'iza fiye da yadda ya san kanshi Fa'iza bata shan kayan mata ko wani abun da zai kara mata Ni'ima duk abunda yaji in yazo tarayya da ita shine Hallitarta wanda Ubangiji ya yi mata,bazai kusheta ta wannan bangaran ba,abu daya ne ke masa cikas baya sonta sannan tun farko komai nata a wajensa bamai kyau ba ne shiyasa ta wannan bangaran ya gaza sakin jikinsa to ya saki jiki a wajen Fa'iza yaji me..?Matar da bata iya komai ba,Shiyasa ba kasafai ya cika Raba'arta ba.
Kayan jikinta ya kara bi da kallo,sai da Ransa ya baci har gobe yana jin Mamakin yadda Fa'iza bata taba saka kayan da yayi mata Daidai ba ko Rigar da hannu yayi yawa ko Sikat kagansa kamar Buhu in yayi mata mgana sai tace itake son haka kada watarana su mata Kad'an,Yau ma din riga da Zani ne ajikinta Rigar Hannun dai bai zama ya na yi ya na Sabule mata Jan Bra dinta Data sanya tana bayyana Saman kafad'anta.
Wani mololoon abu ya tsaya mai yaki wucewa a makogwaronsa Saboda Bakinciki kamar shi ISHAQ KABIR KAROFI kamar shi Ace wannan abar ce Matarsa Uwar ya'yansa..?
In ya kalli FA'IZA sai yaji Fiye da madaukacin Takaicin daya ke ji in ya tuna itace yau MATAR SA..Fa"iza ba mafarkin sa bace a irin Rayuwar ISHAQ KABIR KARAFI..Sam Fa'iza bata dace ko kadan da Tsarin Rayuwarsa ba kowa yasan Ishaq dan gayu ne mai ilimi ne,kyakyawa ne dan Fafane d'an Alfahari ne Duniya tasan da zamansa mai Burin Auran mace FARA mai kyau mai Tarin kwalayen matakan karatun Zamani SAI DAI KASH"
Hakan bai samu ba..Sakamakon kutse da Fa'iza tayi cikin Rayuwarsa ta Ruguza Mafarkinsa har Abada bazai daina Hango FA'IZA a matsayin Nakasun Mafarkinsa ba.
Sannan karin bakin cikinsa yana da Burin kullum in ya Dawo aiki kyakyawan matarsa ta tarbesa ita da yan Gudi gudin ya'yansu Farare masu kyau kamar ya'yan Turaawa tun yana yaronsa yasha yin wannan mafarkin sai dai ina Hajiyar Karofi da Baba sun Saka almakashi sun Datse wannan Mafarkin nashi,Gabadaya ya'yan da suka Haifa da Fa'iza Shekara Takwas da auransu duka ita suka Biyo acikin su ba wanda ya Dauko ko da Hasken Fatansa ne sai Baki irin na uwarsu,Yana Tsananin kaunar yaransa ammh wani Lokacin yana kunyar nuna su ga Duniya Saboda a yanayin Tsarin Rayuwarsa bai kamata Tsarin Iyalansa su zama haka ba.
Duk da irin barnan kudin dayake yi a kansu Fa'iza bata da wannan Tattalin komai sai ta barshi su lalata shiyasa ya gaji ya barta ta karaci muguntarta sai dai yaci ta ita kadai.
Gefen gadon Dake Dakin nasa ya koma ya zauna yana Kad'a Fararan kafafunsa masu cike da gargasa yana kara kallon Fa'iza Dake duke har Lokacin kanta na kasa kamar tamai Sujjada,Kai ya girgiza yana Tunanin yadda yaso ya Dakile ma Fa'iza Haihuwa sai dai ina kana naka ne Allah na nashi,Kowani Tsarin iyali bai karbeta ba,da an saka mata lokaci kadan' sai ya bata matsala na karshe ma da aka saka mata yar Ashanan da jini ya Tsinke mata Dakyar ta sha Ashe Rabon Ahmad ne,Haihuwa take yi akai akai ita ko gajiya batayi da Hidiman yara da Haihuwa kamar akuya..?
Tsakani ga Allah ya'ya indai ta Bangaran Fa'iza ne shifa ya kai makuran Hakura da hakan.
Shi kadai kawai ya saki Tsaki"Mtse***"
Kallonta ya sake yi kai Tsaye kafin yace"Where is my Childreen.?
Yafada da dan karfi ta Dago tana Kallonsa Kafin tace"Eh me kace..?
Wani Tsakin yaja Kafin yace"Na manta ba Turanci..Ina yarana na nace..?
Mutum yayi ta wage baki yana mgana har sai makota sun gama jinsa ke ko Sirri ne bamai yi Dake domin kafin ki gama gane abunda mutum ke nufi Duniya ta gama jin Halin Dayake ciki..Mtswwwsss.."
Yana gama Fadin haka ya mike ya Tsallaketa ya fice Daga Dakin,Kaina na kasa na saka hannuna na share guntun Hawayena kafin na mike Salau Salau nabi bayansa saman D'aya Daga Cikin kujerun falon na samesa ya kunna kallo remot a Hannunsa yana Sarrafawa.
Jikina na rawa na karisa inda na ijiye Farantin dana shigo dashi na Tsiyaya mai ruwa mai sanyi nataso nazo gabansa na Duka ina Fadin"Kayi hakuri..Ga ruwa kasha.."
Sai da ya ga Dama sannan ya kalleni kafin ya amshi ruwan kadan yasha ya maida mata yana Fadin"Da ruwa kadai kika iya tarban mijin ki da yayi kwana Goma baya nan..?
Ya fada yana mai Tsurata mata ido Fa"iza bata ji farkon mganarsa ba sai karshe yasa tace"Kwana goma..?
Tafada Cikin alamun Tambaya kai kawai ya Dafe kafin yace"Innalillahi..Gaskiya an gama Dani..Ishaq ka gama aiki kawai.."
Yafada kamar yayi kuka kafin ya kalleta yana Fadin"Ahmad yayi barci ne..?
Tana kallonsa ya kara ware murya yana Fadin"Eh nace Ahmad yayi barci ne..?
Da Sauri tace"Dukaa sun yi barci.."
Kai ya girgiza kafin yace"Ruwa k'adai ne kuke dashi agidan..?
Yafada muryansa asama kusan fa Fa'iza ta fara maida shi Sama sama ko ba da ita yake mgana ba ya yi mugun Sabon da sai ya Daga murya.
Cikin Ladabina nace"Taliya Hafsatu ta Dafa ma su Amir ina jin ta kare ma..Sai dai bari da sauri nayi maka ko Faten Dankali ne..
Dayake bansan kana Hanya ba."
Komawa yayi ya jingina jikin kujeran dayake kai yana maida Hankalinsa kan Tashar Mbc action din Daya sanya Reastling din da ake yi ya Fara Daukan Hankalinsa ganin haka yasa na Mike jikina na rawa na kwashi Farantin Dana shigo dashi na Fice ya Bita da kallo kamar ya saka kuka ai bazai ce A'a ba inda kuma bazai Zagi Fa'iza ba kenan ta iya girki,girkinta ba inda baza'a Kaisa ba,Shi kadai ne abu mai kyau a rayuwar Fa'iza ban dashi shi dai bai gani ba ya Dade yana ganin mutane marasa sa'a a rayuwarsa ammh Rashin Sa'ar Fa'iza na musamman ne ta rasa wasu abubuwa masu Muhimmanci a Rayuwarta Rashin Sa'arta ne ma ya shafesa shima Gabadaya Rayuwarsa na neman komawa irin tata ba Domin Mama na Tsaye kansa ba, da Shima ya koma Dangin KURAME kamar yadda Zama da Kaddara ya Hadasa da Fa'iza.
Minti Talatin da wani abu na Sake Dawowa Dauke da Voul cike da Faten Dankali da Hanta sai maltina mai Sanyi Dana Hado mai dashi bai yi Tsaya mgana ba Domin yunwa yake ji Gidan Mama Tuwo sukayi shi kuma na Cimarsa bane abaya dai yaci banda yanzu Dayake cin guminsa.
Kasa ya Sauko ya tankwashe kafa ya sha Fantansa sosai,ya Dora da ruwa Maltina,Yayi gyatsa Lokaci D'aya da Hamdala Duk Fa'iza na gefensa yana Gamawa Jikina har rawa yake yi wajen kwashe kayan daya yayi amfani da su, na maida Kitchen adaran nan na wankesu domin Fa'iza in akwai abunda ta tsana kwano ya kwanar mata akitchen ba'a wanke ba.
Ita dai barta da barin shirgin yara da Rashin Shiga mai Fasali ammh ita da ya'yanta basu da kazanta ko yaya ne wanka ne Safe da yammah ita da yaran Duk Ranar duniya har sun saba suma.
Sai da nagama na kara leka Dakin na wajen Ahmad in sauri ban tsaya na Tofe shi da addu'a ba yasa na bata Lokaci Wajen Yimai addu'a Hafsatu bata Dakin kila tana Dakin datake sauka in tazo Gidan.
Dayake nayi wanka Dazu da mangariba ban yi Tunanin Sake wani wankan ba na Sauya kayana zuwa wata Dogouwar Riga ta barci mai Taushi mai gajeren hannu,Duk da ina na da masu wando basa Burgeni nafi son Dogayen masu rufe min Har Cinyoyina Fa'iza ta Tsani ta saka kaya taga sun kamata ko sun nuna Tsiraicinta.
Ina cikin Daure gashin kaina Da na Tsefe shi yau da Safe,Hafsatu ce zata min Kitso yau bata samu Dama ba Karfanfan gashina tun na Virgin Dakyar yake Haduwa cika garesa bai da Tsawo inaa Hakin kamasa na Daure cikin Ribbon baji muryan ISHAQ asama yana Faman kiran sunana kamar yadda ya saba.
"FA'IZA.."
"FA'IZA.."
Da sauri na bar abunda nake yi lokaci daya na Rarumi Hulata ta barci na Saka ina niyar fitowa Daga Dakin ya shigo,ganinsa Tsaye a gaban ba Kikam da irin kallon Dayake min yasa nq rankwafa da Sauri ina Fadin"Gani ina..ina..!
Ban karisa ba ya Daga min Hannu Lokaci Daya yana Fadin"FA"IZA hala baki sam zan kara aure bane..?
Yafada yana Tsareni da manyan Idanuwansa.
Gabanna ya Fadi Ras! Sai na Daburce Da yanayin da yayi mganar,ba da karfi bane sai dai ai mganar auran nasa na Haddace ta akaina shiyasa nq karancin Bakinsa.
Cikin Fusata yace"Wai bada ke nake mgana bane kikamin banza..?
Da Sauri nace"Eh..Eh..Na sani..Mamakofar soro ta fadamin..Sannan sannan.."
Daka min tsawa yayi yana Fadin"Sannan me..?
Kinsan bana son wannan sanyin naki in muna mgana ko..?
Mgana bata kai ta kawo ba kiyi ta uban Rabata kamar wani abun arziki zaki Fada.."
Kokarim Boye Raunina nayi Cikin Dakewa nace"Anty Binta batagwara ta Fadamin wanchan satin da muka Hadu gidan Mama."
Wata Uwar Harara ya jefa min kafin yace"Kin sani ammh ko Fatan Alheri bazaki min ba Fa"iza..?
Kina bakinciki ne saboda zan kara aure..?
Da Sauri nace"Ahah.Naga baka nan ne,Shiyasa.."
Takaici ya kamasa kafin yace"Baki da waya ne..?
Ko lambatace baki da ita..?
Koda yake ke ai ba matar kiran jin Lafiyan miji bace za dai ki kira in wata Bukatarki ta taso miki."
Ya karishe Fada yana kallona Cikin Doguwar Rigar Barcin dana sanya kadan ya Rage bai yi Dariya ba.
Dariyan Takaichi wai zaki kwana da Miji ki saka wannan abu kamar kullib goro.
Karamin Tsaki yaja kafin yace"Na zata kina Bakinciki ne nace kin so kanki Fa'iza Shekara Takwas nayi ina Zaune Dake ban kara aure ba..Tsakaninki ga Allah ban miki alfarma da Mutumci ba Fa"iza..?
Fadamin da bakin ki na yi miki adalci ko ban yi miki ba..?
Ya fada da karfi yadda Zan jisa jikina na rawa nace"kaayi min..sosai kayi min adalci.."
Naso na Daure ammh ina Raunina ya bada ni sai kuka hawaye sharr Tsayawa yayi yana kallon na kafin ya Tabe baki yace"Naji Dadi da kika Fahimci haka..Kada Goggon karofi da yan'uwanki su tasaki suna Faman tambayanki kice musu ban yi miki adalci ba kiga yadda zamu kwashe.."
Malama ki kuma cire min wannan bargon Dake jikin ki wlh matukar wajena zaki kwana na Haramta miki kara sakamin wadanan Rigunan ai ba Cinikaya zamu yi ba..Ke kinga ma sha ma Zamanki ana tabaki Ke mai cikin Haihuwa Zan D'aure nan da Wata D'aya ne kamar gobe ne.."
Yafad'a Lokaci D'aya ya juya zai Fice Daga Dakin na Bisa da kallo ina D'igar kwallah duk da ba Duka mganarsa na ji ba ammh nasan yana kushe ni ne kamar yadda ya saba.
Har ya fita Daga Dakin ni kuma har na juya kawai naji dawowarsa da kara Kiran sunana da yayi da karfi.
"FA'IZA..!
Da Sauri na Juyo Cikin muryata Data Fara sauyawa saboda kuka nace"Na'am..!
Kallona ya tsaya yanayi lokaci d'aya yana rike da Kofar Cikin Mamaki na yace"Kuka..?
Na Dake ki ne..?
Da Sauri na Share hawayena ina Fadin"A"ah kamar wani abu ne ya Fadamim a ido na..!"
Bai Damu ba Kafad'a ya Zakud'a kafin yace"Mama ta fada miki gidana na Abuja Zeey zata zauna..?
Kai na gyada mai bai bani Damar mgana ba yacigaba da Fadin"Fa'iza kinga barin yaran nan suna bata gidan nan Duka duka yaushe muka tare acikinsa ammh kalli yadda suka maidasa..?
Komai naki ba kula ba Lura..?
Ko da yake ke kanki abar akula Dake ne bama ki kula da wani ba Anyway dai tunda kuka lalata gidan in ma mugunta ce ke zata ci..Sai da Safe.."
Daga haka ya Sakar min kofa ya fice na Bisa da kallo hawayena na kara cika Idanuwana ina jinsa ya Bude kofa ya shiga D'akin yaransa ya Dade kafin naji ya Fito ya Tafi bangaransa.
Kamar wacce aka Mangara kawai sai na fashe da kuka wiwi,Sai kuma nahau Rufe Bakina,lokaci D'aya da wayata Dake samam madubin dakin ta D'auki Karan neman agaji.
Da Sauri na mike na nufi wayar kirar Kamfanin Itel karama Tunda Anum tataba Fasa min Sreen din Samsumg din da Ya Ishaq ya siya min bai kara siya min wata babbar wayar ba ya Had'ani da karama acewarsa ba amfanin ma Siyan min Shafa shafan tunda ba iyawa nayi ba, ta bakinsa Fa'iza ba turanci.
Gabana sai da ya amsa ganin wacce ke Kirana Maman Naja ce Yaya ASIYA,Sunan d'iyarta ta fari ce wacce ta rasu Naja'atu ammh dayake sunan ya riga ya bita da Maman naja ake kiranta.
Da sauri na share Hawayena nayi kokarin daidaita yanayina domin ni Fa'iza ko Uwar data Haife ni bana kaunar taga raunina ballatana yan'uwana da kullum suke kallona abar Tausayi wacce batayi dacen Gidan aure ba acewar su.
Saboda yanayin Raunin ji na, in aka kirani a waya a speaker nake saka ta wato amsa kuwwa yanzu din ma haka nayi na Daga kiran sannan na saka a speaker daidai Lokacin da naji muryan Ya Asiya na kiran sunana na amsa mata cikin dan D'aga murya.
Dagachan bangaran Ya Asiya tace"Fa'iza Ashe Yaya Ishaq zai kara aure bamu sani ba..?
Fa'iza tayi wani mirmishin yak'e kafin tace"Eh Yaya Asiya zai kaara aure.."
Ya Asiya tace"Shi ne baki Fadamin ba, kuma baki fada ma Mariya ba ko..?
Fa'iza tayi shuru batayi mgana ba Ya Asiya Haushi ya kamata ta fara Fada Tana Fadin"Kila ma baki sani ba..?
Domin sai ma an Dauke ka da Daraja da kima ne ake sanar dakai wani abun."
Da Sauri nace"Aaha nasani fa..Wlh na sani Mama ta fadamin sannan Anty Binta batagarawa itama ta fadamin."
Ya Asiya Dagachan bangaran ta jimjina kai kafin tace"Shi Uban gayyar bai Samu Fada miki ba kenan..?
Sai a bakin Uwarsa da yayarsa kike ji kenan..?
Anya Fa'iza wannan Rayuwar zata tafi ahaka kuwa..?
Shekara Takwas ai ba kwanaki Takwas bane."
Fa'iza ta share hawayenta da suka zubo mata kafin tace"Ai shima ya fadamin yau daya dawo.."
Ya Asiya tace"Umhh..!
Saboda takaici ma ta kasa mgana,Fa'iza kuma Daman ba ma'abociya mgana bace Ya Asiya Tagaji da shurun Fa'iza yasa ta katse mganar da cewa"Goggon Karofi ke Fadamin Zai yi aure yanzu muka gama waya da ita..Ita kema Fadamin Hafsatu tazo wajen ki shekaran jiya."
Fa'iza tace"Eh tazo shekaran jiya..tazo..."
Sai ta saki wanchan mganar Saboda bata son tayi Tsawo ita kanta Ya Asiya ai ta sani Fa'iza bata kaunar mganar Data Danganci Ishaq da Danginsa in ma ka matsa sai ta saka maka kuka Ajiyar rai ta sauke kafin tace"Yaushe ne Bikin..?
Fa"iza tace"Bansani ba.."
Ya Asiya tace"Allah ya kyauta zan shigo katsinar nima In nazo Duba Tamadina hala ba ma kiji bata ji Dadi ba..?
Ciwon kafafu take fama dashi."
Fa'iza tace"Naji Da Hafsatu tazo ta Fadamim."
Ya Asiya tace"Yaushe zaki leka ki Dubata ke da ke kusa ma Fa'iza yaushe Rabon ki da Dutsenmah Tun Sanda Ta madina ta kwanta asibiti an kusa shekara fa"
Fa'iza tayi shuru ta kasa mgana Saboda bata da tacewa Ishaq ne baya barinta tana son zuwa inda Mahaifiyarta take sai yace me zataje yi tana gidan wani..?
Ya'yansa bazasu je gidan wani suna Rab'e Rab'e ba.
Ya Asiya tayi shuru yasa ta kyaleta sai ta shigo da mganar"Ina yaran nan..?
Hala sun yi barci..?
Ta amsa mata Ya Asiya tace"Shikenan Sai mun shigo zamu karisawa Tattauna ki kara Hakuri Fa'iza kowani bawa da irin tasa kaddaran..Mu Tamu kaddaran Rasuwar Baba ne itace silar Shigar mu duk Halin da muka shiga."
Fa'iza tace"Haka ne Daman ai KANA NAKA ne Allah na nashi ne..Sannan na Allah ne Daidai."
Ya Asiya na jinjina kai tana Fadin"Hakane Fa'iza Allah ya mana mai kyau..Mu kwana Lafiya.
Fa'iza ta rakata da Fadin ta gaida yaranta Daga haka sukayi sallama Sannan na ijiye wayar nq koma gefen gado na zauna ina mai kura ma Madubi Ido duk da ance ba kyau kallon kai a madubi in Duhu ya shiga ammh ni sai ta samu kaina da kare ma Jikinna kallo.
Tare da Fuskata ina Ayyana adadin Lokuta nawa ya Ishaq ya kalleni ya yab'a min..?
Koda yaushe cikin kusheni yake yi an samu ma bayan sun fara Tara zuru'a ya Daina jifana da kalmar Mummuna ammh kalmar Baka sai dai in yan Cin mutumcinsa basa kusa ni na sani Tazaran Dake tsakanina da Ya Ishaq kamar Tazaran kasa da Sama ne ko abaya ban taba mafarkim auran miji kamarsa ba Domin ba Tsarana ba ne, sannan ba kuma Had'i shi kanshi na san ni ba irin wacce ta Dace dashi bane Mama kofar soro kullum tana Fada min hakama Anty Binta batagarawa,To ammh Ba kai kake Tsarama kanka Rayuwa ba Allah ne Kana naka ne yana nashi kuma Tsarinsa ne akan gaba.
Na tabbata ba Domin kakkausan Bakin Baba kan Ya Ishaq ba, da Tuni bayan kasa ta shafe idonsa ya rabu dani ya samu salama kamar yadda yake Fadi sai dai ina Ya Ishaq bazai iya Tsallaken mganar Baba ba Shiyasa har yanzu muke tare ina D'aukan dukkan cin kashi da Tozarcinsa
Bani da wani gata nan Duniya sai Ishaq shine uwaa na shine Ubana da Duniya ta Tamadina ga yanayin yadda Rayuwa tazo mata sauran yan'uwanna ba waje daya muka tashi ba Bayan Rasuwar mahaifinmu Raba mu akayi ni a karofi na fara Rayuwata Kafin dalili ya yanke zamanna achan Baba Kabiru ya maido ni katsina ya Damkani Hannun Mama.
Hawaye na haka suke faman zuba ban iya saka Hannuna domin na tare su ba Saboda ko na goge su wasu ne zasu kara fitowa a irin wannam Lokacin nake samun Fitar da abunda ya dade yana Damuna,Ba bakinciki nake yi Saboda Ishaq zai kara aure ba,A'a ai daman na sani yafi shekaru yana ikararin zai auri Zab'insa Daidai da Ra'ayinsa tun kafin ma yakai haka zama a rayuwa ballatana yanzu dayake jin kansa ashi wani ne.
Sai dai abu D'aya na sani zuwan Amarya nan tozarcin danake sha sai ya Ninka wanda nake sha abaya abu daya ne naake gudu wulakanci ina tsoro da firgicin Amaryan tazo tasan duka labarina tazo tana ganina a wulakance ta goraanta min Kamar yadda Shima yasha Fadi Fa'iza ba kyau ba Turanci komai nata Total zer0 ne. ammh a raina bana mai Bakinciki don zai kara aure ai yayi ma kokari da muka kwarari wad'anan shekaru bai kara ba,sai yanzu na kuma ji Dadi da matar zatayi nesa damu ko Bakomai kazantar da baka gani ba Tsabtace akasan chan raina kuma ina da kishi Domin ina son mijina so irin wanda Duk Macetagari zata nuna ma uban ya'yanta,duk da tarin Nakasun da auran mu ya kunsa, duk da ko shi din' bai taba sona ba.
sai dai bazan barsa yayi wani Tasiri a kaina ba tunda inda Son ke da muhalli baza'a martabasa ba, zan iya Rantsuwa ko Kaffara bazan yi baa Ya Ishaq baya sona karfin Biyayyar Baba ce take Rike da igiyar auranmu.
Naso na sauya Rigar Jikina kamar yadda yace sai dai kuma Tunda yace na bar shi nasan ko da na bisa Shashensa sai ya koreni shiyasa ban bata ma kaina Lokaci ba na Haura kan gadona naa jawo Ahmad jiki na,na Rumgume sa Abu D'aya ke sanyayamin Rai ya'ya na Domin duk duniya bayan Ishaq bani da kamarsu basa san iya adadin Lokacin Dana Dauka inaa kuka ba ammh nasan Har barci ya kwasheni kukana bai Tsaya ba.
Kiran Sallar Farko na tashi kamar yadda ya zame min Jiki Fa'iza bata barcin Rana sannan karfe Hudun Asuba take tashi sai kuma wani Dare.
Fita nayi naje Dakin yaran na Tashi Amir da Mustapha zasu bi Babansu masallaci Bayan sun tashi na fita zuwa Dakin Hafsatu na isketa ta tashi har ta Shiga Tiolet sai na Fice su Amir ta Tsaya akansu sukayi alwala Daidai Sanda Ishaq ya fito Daga bangaransa Sanye da Jallabiya baka da Carbi Kofar Dakin yaran ya Coge duk Fadan sa bai isa yayi ma Fa'iza Fadan rashin Tarbiya da kula da yaransa ba wannan in bai Gode mata ba ai bazai Zageta ba.
Amir ne ya karisa ga Baban yana Fadin"Oyoyo Daada sannu da zuwa.."
Yafada yana rumgumesa rike sa yayi yana Shafa kansa kafin yace"Jiya na dawo lokacin kun yi barci.."
Ina musty..?
Yafada yana kallonsa Fa'iza na kiciniyar saka mai wata riga bayan ta cire mai na barci sai faman mutsike ido yake yi alamun barcin bai sake sa ba.
Dariya yayi yana kallonsa kafin ya Bude Hannunsa yana Fadin"Oya come Here..!"
Da gudu yaron ya nufessa ya Fada jikinsa yana Fadin"Daada.."
Shafa kansa yake yana jin Farimciki acikin ransa Fa'iza ya kalla Dake tashin Anum da dan karfi yace"Kyaleta mana.."
Fa'iza ta Dago tana Fadin"Suna da Hadda yau."
Yana rike hannun su Amir yace"Ai da Sauran lokaci ke komai naki na Hanzari ne karfe Biyar din Asuban ne zasu tafi Haddar..?
Bada karfi yayi mganar ba saboda Haka ban ma jisa ba nadai san yayi mgana kuma nasan bai wuce Fada ne irin nasa Daya saba ba, shiyasa har yaja su Amir suka fice ban kara mgana ba..
Suna Fitan nayi kokarin tashin Anum Saboda tayi sallah ta wartsake kafin su Dawo Daki na muka koma Tare nima na Dauro alwala mukayi sallah Tare da Anum muna idarwa Ahmad ya tashi na Daukesa naga ya bata pampers dinsa,sai na mike na Goyasa na shiga Kitchen bayan na gargadi Anum kada ta koma barci ta zauna tayi azkar din Safe wanda yaran duk sun Haddace..
Ruwan Zafi na fara sakawa saboda nayi ma Ahmad wanka kafin sauran yaran su Dawo Sai kuma na fara kokarin Fere Doya saboda na soya musu na Tafiya dashi makaranta sai ga Hafsah ta shigo Kitchen din da Hijabinta.
Fa'iza Hankalinta na wajen aiki bata san Hafsatun ta shigo ba sai da ta tabata sannan ta dago tana kallonta kafin tace"Kin fito Hafsah..?
Da yanayin mganarta Hafsah tace"Eh Ina kwana.."
Da dan daga Sauti Saboda Fa"izan ta jita sosai.
Ta amsa mata Cikin Sakewarta Hafsah tace"Bari na amshe ki."
Fa"iza tace"A"a barin min wanan aiki..Ga dai ruwa nan na saka in ya Tafasa ki juyo ki yima Ahmad da Anum wanka kafin su Amir su dawo."
Tafada cikin yanayin Raba mganarta Hafsah ta amsa mata da Toh,ba Dadewa ruwan ya Tafasa ta Dauko wani Karamin baho ta juyo ruwan ta kai Tiolet din Dakin Fa'iza da suna da Shower na wanka ya lalace kuma ya Ishaq yace da gan gane saboda haka bazai gyara ba.
Dawowa tayi ta karbi Ahmad ta je ta fara mai wanka ta shiryasa sannan tayi ma Anum nata wanka alokacin har su Amir sun Dawo masallaci suna Falo Tare da Ya Ishaq Sanda Hafsat ta fito Dauke da Ahmad daya fara Rigima ne Fa'iza ta fito Daga Kitchen din tana gaida Ishaq ya amsa mata bai ko kalleta ba Hankalinsa na wajen Amir Dake bashi Labarin abunda ya Faru a makarantasu jiya shi kuma Musty bai da Hayaniya yana Lafe jikin Uban..
Hafsah ma tabi ayarin yar'uwanta ta gaisheshi ya amsa yana Dubanta ganinta Dauke da Ahmad yasa yace"Ina zaki kaishi..?
Hafsah tace"Kuka yake yi zan kai shi ta bashi Nono ne."
Hannu ya mika mata yana Fadin"A kitchen din zaki kai mata shi..?
Wato salon ta jefa shi Cikin wani abu kin santa bata da kula."
Hafsah dai batace komai ba ta mikamai D'ansa ya Cafe shi yana Daga sa sama cikin Fara"a Hafsah bata damu ba ta karisa kitchen din Domin kama ma yayar nata aikin itama gobe zata koma Daman Hutun Midterm break Aka basu a makaranta yasa Goggo ta barta ta taho itama tana Karofi ne wajen Hajiya Indo da suke kira Goggon Karofi ita take rikonta tun bayan da ta karbota wajen mahaifiyarsu Ta madina.
Suna Kitchen din suna aiki Hafsah taji Sanda Anum ta fito ganin babanta yasa ta nufesa cikin murna tana Fadin"Daada yaushe ka dawo..?
Daman Anum akwai kirniya da Rashin jin mgana Yana ganinta itama ya Tarbeta yana Fadin"Anum dina jiya da Daddare na dawo kun yi barci."
Kai Tsaye tace mai ina Tsarabanta yace sai an juma in ya sake fita Hafsah ce ke Sauraran Hiransa da ya"yansa banda Fa'iza da baji take yi Sosai ba sannan Hankalinta na wajen Soya Doya bata ma san Abunda suke ciki ba.
Kafin bakwai na Safe tayi Fa'iza ta gama komai sai ta bar Hafsah a kitchen din tana karisawa,ni kuma sai naje na Shiryan yaran saboda suna da Hadda Tahfiz ne tun Safe sai shida suke Dawowa Allah ya taimake ni Ahmad na wajen Ya Ishaq ya shiga Dashi Shashensa.
Koda bakwai da Rabi tayi sun karya sun shirya Tsab Cikin kayan makarantarsu Ga Basket din kowanne an shiryamai da soyayyar doya da miyar kwai,Sai lemu da ruwa Fa'iza na kokarin Tura Hafsah ta leka tayi ma wani wani makotanci Haruna mgana mai Tuka adaidaita shi ke kai yaran makaramtar Hadda da Boko a wata Ya Ishaq na Biyansa Saboda abaya motace har da Direba ya Daukan musu tunda Anum ta taba koke motar Mama ta sa ya bama Jamal kaninsa motar tana chan gidanta Kofar soro in ya Dawo Hutu Daga Kano inda yake karatunsa na Engeering yake amfani da ita su kuma Ishaq ya Daukam ma yaran mai adaidaita a cewarsa Tunda bata iya Tattali ba shi ba asararrre bane sannan kuma yace Mota bata Dace da ni ba,irin mu yawo acikin Adaidatan yafi Dacewa damu,ni Dayake ban Damu ba, ba fita take yi sosai ba Daga Gidan Mama sai gidan Anty Binta shima na da'n Rage zuwa tunda ba maraba suke da zuwana ba Karofi kuma sai dai in an yi Rasuwa muje Gabadaya ammh ni kad'ai Ya Ishaq cewa yake bai yarda da ni ba zanje ne na Had'u da yan'uwana azagesa shiyasa ban ma Damu da Fitan ba nima.
Ina shirin aika Hafsah ne sai ga Ya Ishaq din ya fito yace shi zai kai su,jin Haka yaran suka fara Murna sosai,Tare da Ahmad suka tafi har Lokacin bai koma barci ba shima ai yasam Ishaq saboda gaskiya in yana Gida yana bama yaransa Lokacinsa nice dai bani da wannan matsayin.
Har sun fita naa bisu Haraban gidan ina kwalama Amir kira ya juyo yana Fadin"Umma menene..?
Ina Sosa gashin idona nace"Kada ku manta ku karanta addu'ar fita Daga gida."
Da Karfi Anum ta fara karantawa Amir na Binta shi da mustpaha suna gamawa nabisu da mirmishi ina Daga musu Hannu Ishaq dai Tuni ya Shige mota yana Dauke da Ahmad irin wad'anan Hallayar na Fa'iza ba wani Burgesa suke yi ba,Sai dai kuma a kasan Ranta yasan Tarbiya ce mai kyau shiyasa wani lokacin baya mgana.
Ganin ya shiga motar bai bude get ba yasa na karisa na Budemai motarsa ta Fice Daga gidan sannan na maida na Rufe,abaya munq da megadi wani Dattijo,Tunda lokacin da Yaya Ishaq yaga ina basa Abinci yace don me..?
Ai yana Biyansa duk wata ba wata mgana kawai sai ji nayi ya sallamesa Daganan kuma bai kara Daukan mana wani megadi ba yace Tunda Zan iya na yi Hidiman get din da kaina
Sai da suka tafi naje nayi wanka na Sauya kaya zuwa wata Doguwar Rigar Shadda Dinkin zamani kan na gama Shiryawa Hafsah ta gyara Falon ta share in da yaran suka bata sannan ta gyaro Dakin yaran suma ganin haka yasa nayi mata sannu da aiki ni sai na shiga Shashen Ishaq na gyara duk da ba sosai yayi Datti ba na Cika shi da Turaran kamshin Daki sanin sa mai son kamshi ne.
Kafin ya Dawo na jera mai kayan karinsa,na koma Falo muka karya ni da Hafsah muna yi muna Taba Hira duk da Hiran Daga Hafsah ne ita Fa'iza nata Eh ne ko A'a sai mganar da batayi Tsawo ba.
Har muka gama karyawan bai shigo ba,Hafsah tatafi tayi wanka ni kuma na kwashe komai nakai kitchen na Fara kimtsa wajen,Bayan na gama nayi wanke wanke,ina cikin goge gogen kitchen din naji Sallama atsakar Falon Sai na leko da Towel din gogogogen a Hannuna,Baki na washe ina fadin" BADARIYA.."
Cikin bayyana Murna ta ganin wacce aka Kira da Badariya na Tsaye da katuwar leda a Hannunta yar matashiya doguwa Fara Fuska kamar ta Ishaq sai dai ta fisa Haske saboda ita macece Autansu ce Badariya Kabir Karofi.
Karisowa tayi Cikin Falon Tana Fadin"Anty Fa'iza yunwa nake ji wlh..akwai sauran abun kari kuwa..?
Tafada tana wanchalar da gyalen Hannunta Lokaci Daya da ledan Data shigo da ita.
Bata ma saurari Fa'izan Dake faman mata gaisuwan yasu Mama ba
Ta Shiga kitchen din tana Dube Dube ta samu Doya a kula da Miyar Kwai ta Dauko ta Fito Tana Fadin"Anty Fa'iza adana gaisuwarki sai naci na koshi Tukunna."
Dariya nayi mata bance komai ba na koma kitchen din na Cigaba da goge gogen da na fara ina mai jin Dadin zuwan Badariya din duk cikin ya"yan Mama Ita kadai ce ke sona sai Jamal shi kuma bai da alkibla yau ya min Mutumci gobe kuma akasasin sa shidai baka gane ina ya Dosa,Ammh yana zuwa gidan nan wajen su Amir sannan yana zuwa cin abinci ba wacce tafi Tsanata Daman Tun zamana wajen Mama irin Anty Binta batagwara ita da Ya Ishaq daman basu so zamana agidansu ba Sun gama Dora min karan Tsana wanda har yafi ma wanda Mama take min tun ina da karanci shekaru kafin ma aure ya shiga tsakani da ya Ishaq
Sai da nagama aikin na Sannan ta sake Fitowa Falon na iske su Tare da Hafsah wacce tayi Rashe Rashe kasan Cafet tana Bude kayan da Badariya ta shigo Dasu ita kuma Badariya na kan kujera ta cin Doyarta suna mgana da Hafsah.
Ina Shigowa Hafsah tace"Anty Fa'iza kinga ankon Bikin ya Ishaq.."
Jin Shuru yasa Badariya tace"Bafa ta jiki ba..Anty Fa'iza ga ankon Ya Ishaq..kin gani..?
Sai alokacin najisu nabi Kayan Dake Hannun Hafsah da kallo sai na kasa mgana Badariya da Hafsah suka kalleni Cikin wani yanayi kafin Hafsah tace"Kilama bata san da ankon ba.."
Badariya tace"Anya..?Anty Binta ta Dauko fa..Ranar agabana da tazo gidan Mama ta Kira ya Ishaq din tace zata Daukan ma Anty Fa'iza ,Anum kuma zata Hadasu dasu Hibba ne.
Hafsah tace"To ba mamaki."
Badariya tace"Wannan da kike Dagawa naki D'aya nawa daya..Yanzu Daga wajen tela nake bai Dinka Less din ba.."
Hafsah ta zaro ido tana Fadin"Wai nawa..?
Badariya ta mata Dariya ai sai tatashi ta Daga Tsalle tana murna ta Rumgume Fa'iza Dake Tsaye tana kallonsu tana Mirmishi Cikin Fara"a tace"Kinga Anty Fa'iza Badariya ta Dinka mana..!"
Fa"iza ta karbi Atamfan tana gani kafin tace"Sun yi kyau.."
Hafsah ta isa ga Badariya ta Rumgumeta tana Fadin"Nagode sister..Allah ya bar zumumci."
Badariya tace"Ameen ammh bani Zaki ma Godiya ba Ya Ishaq ne shi ya siya mana.."
Hafsah bata wani ji mamaki ba,Saboda in yayi Niyya yana da Alheri sosai tana ta godiya tana Santin kayan.
Badariya tace"Za dai kizo bikin ko..?
Nima yanzu aBakin Ya Ishaq nake jin kinzo Daga kai yara makaranta wajen Mama ya biya."
Hafsah tace"Zan zo tunda weekend ne."
Badariya tace"in Goggon Korofin ta bar ki ba..Domin ita kanta ban Tabbatar da zata zo ba..Naji suna waya da Mama tana Fadan Ya Ishaq bai Fada musu zencen auran nasa ba"
Hafsah dai batace komai ba Badariya ce tacigaba da Fadin"To waya fadamawa..?
Daga shi sai Mama sai Anty Binta suke abinsu Amaryan ma suna waya da Anty Binta tunda ita ta Hada lefen.
Hafsah tace"To yaushe ne ma Bikin..?
Badariya ta tabe baki Tana kallon Fa"iza dake zaune gefe tana kallonsu kafin tace"Anty Fa"iza ta san Lokacin Bikin..?
Hafsah tace"Anya..? Batamin mgana ba."
Badariya tace"Karshen wata ne sauran Sati uku."
Hafsah tace"Allah ya kaimu nan za"a kawo Amaryan..?
Badariya tace"A"a chan Abuja zata zauna..Ai itama yar Abujan ce,mahaifinta shugaban ya ishaq ne a wajen aiki,Itama ai ma'aikaciya ce tana aiki da wani kamfani ban dai san ko na menene ba nima
Haka naji Anty Binta na fada ma mama cikin Hirarsu."
Hafsah tayi shuru jikinta yayi sanyi Tana kallon yar'uwanta wani Tsausayinta ya kamata sai taji Badariya na Fadin"Ya Ishaq ya samu Cikar Burinsa Mace mai kyau Fara Doguwa mai kwalayen zamani ga Kudi da Nasaba..Allah yasa a wanye Lafiya."
Hafsah ta amsa mata da Ameen kawai Domin bata da tacewa,Fa'iza ce ta dan Daga Sautinta tana Fadin"Badariya ya mama..?
Badariya tace da karfi"Tana lafiya..Tana chan tare da D'anta na barsu na fito amso dinki nan sanan kuma yunwa ce ta koroni."
Mirmishi kawai nayi ban ce komai ba ni kowa yasanni bani dayawan mgnaa Saboda yanayina
Sai Hirar ta koma Tsakanin Hafsah da Badariya da Daman kawaye ne suna Hirar Hajiya Fatima wacce suke kira da Hajiyar Dala tana chan kano tana auran wani Babba a soja.
Hafsah ke tambayan su Suwaiba sun san Bikin ya Ishaq din..?
Badariya ta tabe baki tace"Ke share su basa min mgana ko achart kuma suna da Layina..Naji dai mama na Fadin Hajiyar dalar bata nan ta Raka megidanta India Cheekup,Kinsan ta bata Damu da zumunci ba.
Hafsah tace"Haka naji Goggo na Korafi kinsan zuwanta na karshe kaca kaca suka Rabu da Goggon.."
Badariya ta tabe baki tace"Shiyasa sau Daya na taba zuwa gidanta.
Hafsah tace"Ni ai ban ma taba zuwa ba.Yaya Asiya da ta zauna awajenta in tanaa baki Labari sai kin sha mamakinta."
Badariya tace"Shiyasa tasu tazo daya da Mama fa."
Dariya kawai Hafsah tayi suna ma Hirar Fa'iza ta koma Dakinta tana gyarawa,Hankalinta na kan aikinta duk yadda Tunani ke mukurkusanna naki bashi muhalli,na gyara Dakin Tas sai dai abu daya ne Fa"iza bata iya gyarashi ba shirgi bata iya yadda Zata kakkanta ko'ina yayi kyau ba,Sai dai ta gyara ko'ina ta kuma ta maida shirgin waje D'aya.
Mata kala kala ne, kuma kowacce da yanayin yadda ta iya gyaran waje,Ita fa'iza haka Allah ya yi ta tana da Tsafta jiki da na zuciya sai dai bata san yadda zata gyara komai a bisa muhallinsa ba.
Tunani nake yi anjuma zan yi wanki kayan yaran hade da Uniform dinsu Tunda Anum ta lalata injimin wankin su na koma yi da kaina domin duk abunda yara suka Lalata Laifin a kai na Ishaq ke dorashi.
Kayan Ahmad masu Datti nake fitowa Dashi Sanda Hafsah ta shigo ta kawo min Ahmad,alokacin nasan ya Ishaq ya shigo gidan ganin na riga ta kai mai abun karinsa yasa na zauna ina Bashi Nono,ko kafin ya gama sha yayi barci naa koma na shimfidar dashi,na kwashe kayan Ahmad da na Anum data cire dasafe zuwa Dakin yaran na wuce Badariya da Hafsah a Falo suna Hira Dayake Tv Din dake falon yara sun Lalata kuma Ishaq bai Damu daya gyara ba.
Sai da na gama Hada kayan waje daya na kullesu cikin wani Dankwali Sannan na fito ta nufi Shashen Ishaq.
Afalo na sameshi zaune kan kujera mai zaman mutum Daya ya lafe ni ban ma san waya yake yi ba Saboda ba Karfin ji gareni baa.
Kayan daya gama kari dasu na kwashe na kai Kitchen kuma ban baro kitchen din ba sai da na wankesu,koda ma fito ta iske Badariya zata tafi mukayi sallama Hafsah ta fita domin ta taka mata...Shashen megidam na koma naji ko akwai abunda yake so saboda karamin abu laifi ne a wajensa..Ina Shiga Har Lokacin bai gama wayarsa Daga yanayin yadda yake mgana zaka san yana bama wayar Muhimmanci kayan Haushi Fa'iza bata ma jin me yake Fadi shi da Zeey tana mai shagwaban jiya Daga Tahowarsa har tayi kewarsa.
Ganin yadda Fa'iza tamai zaune agabansa ne yasa yace ma Zeey ta bashi Minti biyar sannan ya datse kiran..
Fa"iza ya kura ma ido yana kallonta hankalinta na ma kan Tv dake aiki afalon cikin Tashar Mbc3 cartoon suke yi Ahmad ya kunna ma D'azu da Safe kafin fitarsu.
Mirmishi takaici yayi kafin ya Kirani a Kaushashe kamar yadda ya Saba.
"FA'IZA..!"
Firgigit nayi na Dago ina kallonsa Lokaci daya ina amsawa da Na"am
Kallonta ya karayi yana Nazarina domin Idanuwanta sun kumbura sai kuma ya waske cikin yanayinsa yace"Kin tasani agaba ina waya wani abu ne..?
Dayake a sama yayi mganar na jisa sai nace da Sauri"Kayi hakuuri..Daman nazo naji ko kana Bukatar wani abu ne..?
Karamin Tsaki yaja kafin yace"In ma ina bukata ai zam miki mgana ko..?
Tashi kije abunki ban cika son kina yawan zama a inda nake ba Fa"iza Allah Nagani."
Tsam na mike zan fice dagaa Shashen nasa, lokaci daya kuma ina daga rigata Daga kasa saboda tsawon yamin yawa kallo ya Bini dashi To ai Daman yasan Tunda wuyan yayi mata Daidai Daga kasan Rigar sai ta bata mtsala.
Har zan fice ya Kira sunana da karfi na juyo ina amsawa da hannu yayi min alaman na Dawo da Hanzari na na Dawo na Duka agabansa sai da ya sha Iskarsa sannan ya Tashi ya shiga cikin Dakinsa minti kad'an ya fito Hannunsa Dauke da wani Hoto ya zauna Lokaci Daya yana mika min Hoton na sa ka Hannu biyu na karb'a Fuskata da mamaki da neman karin bayani.
Ya Dora kafa d'aya kan D'aya kafin ya kalleni yana Fadin"Duba ta da kyau ki gani Fa'iza.."
Sannan ki Fadamin ya kika ganta..?
Fa'iza tabi Hoton Dake hannunta da kallo Wata kyakyawan Hallita nagani kamar ita tayi kanta wajen kyau Doguwa mai Dogon Fuska da Hanci har Baka Farace tss mai ja ja ja,Sannan tana da lobawar Kumatu,Wato Dimple Gashinta Har gadon bayanta yake,ga Diri na Cikar ya mace duk da Abaya ne ajkinta Shape dinta ya bayyana sannan tana da Wushirya hakoranta data Bude sun bayyana Farare masu Tsari ga Kunshinta ja ne ya fito akan Fararan Hannayenta masu kyau da sheki Fa'iza tana ganin Ya Ishaq mai kyau ne sai dai dataga wannan sai taga ai shi bamai kyau bane.
Ganin yadda ta bada Zuciyarta wajen kallon Hoton yasa ya Karbe Hoton batare data shirya ba na Dago ina kallonsa ya Daga Hoton yana Fadin"Ya kika ganta..?
Fa'iza cikin yanayin mganarta tace"Tana da kyau..!"
Ishaq yace"Eh ban ji me kikace ba..?
Fa'iza tace"Tana..tana da kyau sosai.."
Ishaq yayi wani irin Dariya kafin yace"Bayan kyau fa..?
Baki Fahimci ta mallaki komai na Kyau da Zatin ya' mace ba..?
Fa'iza tayi shuru batayi mgana ba Ishaq ya kalli Hoton na wani Lokaci kafin yace"Kinsan wacece wannan..?
Fa'iza ta girgiza kai kafin Ishaq ya Cigaba da Fadin"Matar da zan aura ce..Zabi na ce Fa'iza Zainab lawal Bako kenan..Mace ce mai kyau Kamar yadda kika ganni Mai tarin ilimin Zamani Tana da Degree Biyu sannan tana Shirin komawa Phd dinta,Iyayanta masu Kudi ne da Nasaba ta mallaki Duka Burina na nan duniya nan da Sati uku zata zama matata zata cika min gurbin mafarkina da kika Tarwartsa Fa'iza.
Shiyasa na yanke shawaran zaki Dakatar da Haihuwa hakanan ki bar mai wuri tazo ta fara Haifamin kyawawan ya'yan da nike Mafarki.Yanzu ne zan san ni Ishaq nayi aure,abaya ina jin kunyar nuna ki a matsayin Matata ammh ayanzu banda Haufin Duniya taga Zeey a matsayin Matata ina Rokon ki Fa'iza nayi miki komai a Rayuwar ki yi Free d'ina ki barni naji D'adin Rayuwata ni da Matar data dace dani."
Ya karishe fada ya na kallon Fa'iza da kanta ke kasa ta kasa gane ina mganganunsa ya Dosa Cikin wani yanayi na Dago ina Fadin"Bangane ba..?
Kai Tsaye yace"Zamu jingine AURAN mu ne Fa'iza..Wlh in nace ashekara Takwas din da mukayi da aure ban cutu da auranki ba nayi karya kiyi ma kanki adalci kiyi min adalci nima"
Gaskiya ya Fada Tabbas gaskiya ya Fada Fa'iza ta fada acikin aranta.
Cikin wani karfin gwiwa na kallesa kafin nace"Jingina kamar ya..?
Kai Tsaye yace"Jingina ina nufin ba Saduwar aure tsskanimu a matsayin miji da mata ba wata mu'alama ta aure ba Raba kwana Tsakaninki da Zeey..Sai dai zan cigaba da kula Dake saboda Darajan ya'yan dake tsakanin mu Kada ki manta ba Mu'alaman miji da mata Tsakanina Dake..Kawai zan kula Dake ne Saboda ya'yana kawai"
Har ya gama mganansa kallonsa nake yi Hawaye sun gama wanke min Fuskata ga mamakinsa sai kawai yaga nayi Mirmishi,mirmishin da zai iya rantsuwa bai taba ganin Fa'iza tayi irin sa ba.
Cikin wata irin muryan da baisan ina da ita ba yaji nace
"Na Amince.."
Farinciki ya kamasa ya kalleni yana Fadin"Nagode Fa'iza ko bakomai kin yi sakayyah ga Alherin Baba agareki."
Ko kara Sauraransa ban yi ba na mike Zan fice ya Kira sunana na waigo Cikin Kaushinsa yace"I ya ni da ke..Ban yarda wani yaji wannan mganar ba kina jina..?
Kai na gyadamai ina sharan Hawaye, muryata na rawa nace"Insha Allahu ba wanda zai ji sai indan kai kaso hakan"
Daga haka na fice da Sauri Saura kadan Rigar jikina ta Hardeni na Fadi bai Damu ba Murna yake zai samu Salama Shekara Takwas yana cikin kurkuku sai yanzu yaji sa kamar yana Shakan iskar yanci.
Har na karisa Dakina kuka nakeyi bana ko ganin gabana sosai,kan gadona na Fad'a gefen Ahmad ina wani gunjin kuka Dake fitowa Daga kasan Raina Hasbunallahu wani'imal wakeel shin ni na Tsara ma kaina Rayuwata a haka..?
Allah ne yayi ni baka mummuna Allah ne ya so ya ganni afasalin daya ijiyeni meyasa ya Ishaq bazai gane haka ba..?
Yau ni Ya Ishaq ke mganar zai jingine auranmu Saboda wata.? Na tabbata ba Domin mganar Baba ba da tuni aurane da Ishaq ya kare to ai yanzu ma ba Maraba..?
Zai jingine ne kawai saboda mganar Baba ba Domin Ra'ayinsa ba,sai kuma domin kuma ya'yansa Ba laifi na bane domin na fito a mummuna ba, kuma ba Laifina bane domin na fito daga jikin Bebiya ba, ba Laifina bane domin na kasance an Haifeni da Laluran rashin ji sosai da yanayin mgana taba, ba Laifi na bane Allah ne ya Tsara min Rayuwata Daki Daki.
Sannan ba Laifi na bane domin ban zama mai ilimin zamani ba Domin duk yadda ka kai ga Tsara rayuwarka To KANA NAKA ne Allah na nashi kuma na Allah shine daidai kuma Tsari mai kyau.
Ina cikin wannan halin bansan sanda na fara jin tunanin yadda yanayin rayuwata ya fara dawomin acikin kaina ba,tundaga farko har zuwa yau din da Ishaq yace zai jingine aure na saboda wata.
Nafara da Tunano yadda yanayin Rayuwata ta fara ne cikin Farinciki Tun mahaifinmu ALHAJI SIDI KAROFI na raye.
Asalin kakanmu wanda ya haifi iyayan mu maza ni da Yaya ishaq bakatsine ne wanda ya fito daga Tsatson katsinawan Karofi.
Karofi kamar Anguwa ce ko wata alkarya dake cikin Garin karamar hukumar Dutsenmah ta Jahar katsina.
Tunda ga Dutsenmah,Katsina Kankara,malumfashi bakori,mahuta da Sauran kananan hukumomin dake zagaye da Garin katsina ba wanda bai san Waye Alhaji Sulaiman Karofi ba,Saboda tun lokacin yana Raye shekaru sama Hamsin da wani abu da suka gabata an yi Attijirin mai kudi,Domin kaf yankin nan ba inda ake siyan Siminti sai a wajensa manyan manyan Store yake kama haya ana cikamai su da Siminti tun yana matashinsa da wannan sana'ar ya fara kuma alhamdulillah ita ta Daukakesa har kuma Allah ya Dauki Rayuwarsa bai sauya sana'a ba.
A yadda Babanmu ya bamu labari Lokacin yana raye Saboda muma ko da mukazo Lokacin Allah ya karbi Ran Alhaji Sulaiman sai dai mun sha Labarin kirkinsa da Dattakonsa bakin Babanmu.
Ya sanar damu cewa Alhaji Sulaiman Kamfani kamfani na Siminti Mota mota ke shigowa Karofi Domin saukemai Siminti kuma ba'a sati duk sai ya kare bayan manyan yan kasuwa yana saida ma marasa karfi da masu siyan daidai misali sannan karin Daukakarsa baya tsawwalla kudi i ya abunda Allah yasa ya samu sai ya sanya musu albarka.
Mutum ne akace nagari kamili mai sanin Darajan dan adam da Dattako,da kowa yake yabonsa Daga uwa har uba duka haifaffun karofi ne,Kenan ba shi da wani garin da ya wuce mai Karofi alokacin.
Yana da matar auransa Daya Hajiya Suwaiba(Hajiyar karofi) ita ta Haifamai manyan ya'yansa guda Uku Hajiya Fatima ce Babba(Hajiyar Dala) sai Hajiya Aisha(Goggon karofi)
Sai karamin su Alhaji Kabiru(Baban katsina)
Sai Autan su Alhaji Sidi( Babanmu)
Wanda rabonsa ne yasa aure ya kullu Tsakanin Mahaifiyarsa Asiya da Alhaji Sulaiman Karofi.
Alokacin baya in aka auro mace daga wani waje ta shigo inda bata san kowa ba,to akan samu a makotan da aka kawo ki kina samu yar D'aki da zata rika shigowa tana tayaki zama da yan aikece aikece to haka ne ya faru da Hajiya Suwaiba ita din yar cikin garin Dutsemah ce kuma auran Soyayya ne ya kulla Tsakanin su mai karfi kafin ta kai su ga aure.
Yadda na samu Labari Hajiya tun tana matashiyarta macece mai kirki da Sanin ya kamata sai dai akan mijinta bata da kauda kai tana son shi Shiyasa take bala'in kishinsa.
Tun sanda aka kawota garin gidan da Alhaji Sulaiman ya gina gefen katangar gidan su Asiya ne, wanda garun gidan Alhaji Sulaiman shi ne garin gidan su Asiya talaakawa ne Futuk,mahaifinta mallan Haruna ya rasu bayan doguwar jinyar da yayi a baya masarin bishiya ne an ce Tun wani Sare wata bishiya da yayi shikenan bai kara lafiya ba har ya rasu Daga Asiya sai mahaifiyarta Atika suke Fafutukar Rayuwa to lokacin da aka kawo Hajiya Suwaiba Asiya ta kan shiga ta taimaka mata da yan aike ce aike ce tunda daman Asiya bata da kiywuya Lokaci kadan suka saba da Hajiya tun balle data fahimci suna cikin Halin matsi ita ke taimaka musu da abinci suturu har kuma ta saka Alhaji Sulaiman shima ya tallafa musu.
Cikin lokaci kadan Asiya ta zama yar Dakin Hajiya Suwaiba duk wanda yasanta yasanta da Asiya,Suna tare ta yi goyon cikin Fatima ta haifeta kowa yaga Asiya sai yaba da kokarinta da Himmanta Hajiya kuwa har ga Allah ta ke tare da Asiya bata taba jin wani abu aranta game da ita ba..
Ana haka har ta sake haihuwan Aisha,lokacin ne Alhaji Sulaiman yazo mata da mganar da ta kusa girgizata wai zai auri Asiya saboda yayi jihadi sannan ta zama abokiyar zamanta na Har Abada.
Ance a lokacin Hajiya Suwaiba tayi tashin Hankali har sai da ta koma gida Ma'ana tayi yaji kuma hakan baisan an fasa ba sai dai ta Dawo ta iske ya gyara ma Asiya dakin dake kusa da nata har an yi biki Asiya ta tare,Ance sillar wannan gabar daga wannan auran ne Hajiya ta kullaci Asiya da Mahaifiyarta Atika akan sun yi auran cin Amana ita kuwa Asiya bata mgana sai kuka ba Laifinta ba ne,Ita batace tana son Alhaji ba shi yace yana sonta batare da sun sani ba ya je ya gabatar da kansa wajen Dangin babanta su kuma sun ga Alhaji ga kudi ga Dattako nan da nan suka basa da Atika tayi mgana suka Rufeta da fada dole tayi shuru.
Sanadin wannan auran ne komai ya fara ko nace shine sillar komai bazan ce Hajiyar karofi ta fara assasan wutar kiyayyar ba Tunda kafin ta Mutu ta yi Tuba tuba irin na Taubatul nasuha.
Zan iya cewa Tsantsan Rabo ne kawai ya kawo mahaifin mu wannan Duniyan,Asalin sunansa ba Sidi ba ne Sidik ne Asiya ce ke kiransa da Sidi har ya bisa zuwa girmansa.
Kusan Lokaci daya Asiya da Hajiya suka yi goyan yaransu ita tana goyan Babanmu ita kuma Hajiya na goyan Baban katsina.
Hajiya ita ta ke zaunar da ya'yanta tana fada musu auran cin Amana mahaifinsu yayi da Asiya har aka samu Sidi saboda haka shi ba Dan'uwan su ba ne bare ne tunda auran cin Amana ne to ba d'an Sunna ba ne shege ne, mgana fa har ta fita Domin ba inda Hajiya bata yada mgana gidan biki ko suna har yakai ga Asiya ko Atika suka daina fita Saboda kananun mganganu.
Har sai da Alhaji Sulaiman yaji ya tsawarta mata ya kuma ja kunnenta da sai ya iya Rabuwa da ita Saboda haka ance ta sha kuka Ranar Asiya tasha zagi da gorin ita ta zama gatan taa ammh Daga karshe ta saka mata da Auran mijinta.
Adalilin irin wada'nan kalaman na bakin Hajiya suka yi tasiri a zuciyar Babbar yarta Hajiya Fatima(Hajiyar Dala) wanda har mahaifin mu ya koma ga Allah bata kaunace sa ba Duk da kuwa an ce Kafin Asiya ta bar gidan Duniya sai da ta rika rokon Hajiya gafara ammh taki yafe mata sai daga bayan ta jima ita da Atika a kushewarsu sannan Hajiyar Karofi ta gane kuskuranta ta gyara alokacin kuma komai ya kure mata.
Babbar Bakincikim Hajiya ganin da tayi Sidi da Kabiru sun taso kan su daya sannan komai Alhaji Sulaiman zai yi musu tare ne,ita kuma bata so har ko yaushe a shege take kallon Sidi Tunda auran cin Amana ne..azaba da ukuba ba wanda Sidi bai shata a hannun Hajiya ba ko kasheshi Hajiya zatayi Asiya ko Tarin ta bamai ji a Tsakar gida tana da hakuri da kawaici sannan ga Ladabi da Biyayya ko da ta auri Alhaji bata daina yi ma Hajiya bauta ba sai dai bata gani Laifinta daya meyasa ta auran mata miji..?
Babanmu ya fada mana yana d'an Shekara goma sha uku a duniya Mahaifiyarsa Asiya ta rasu da tsohom ciki ta fito daga makewayi jirin Hawan jini ya fardar da ita kwananta Daya asibiti tace ga garin ku nan da Farko Mutuwar ta daki Hajiya ammh Daga baya sai ta saketa.
An yi tashe tashen hankula Har sai da iyaye suka shiga ciki kan zaman babbanmu a wajen Hajiya kememe ko tace bazata rika dan shege d'an cin Amana ba sai Atika aka kai mashi ta rikesa Gefe D'aya Alhaji Sulaiman na kula dashi sai dai duk yadda Hajiya taso ta raba Kabiru da Sidi ta kasa wannan jinin na yawo ajikinsu..sannan Fatima ce kadai ta ke bayanta Aisha kuma babu ruwanta bata Cika Daukan mganarta ba..
Babanmu ya d'anda'na gudarsa a Hannun Hajiya tun da duka bai Rufe shekara biyu a hannun Atika ba,ta rasu sakamakon amai da guduwa shi kuma Alhaji Sulaiman yace hajiya bata isa ba Sidi zai zauna agidan nan tunda shima gidan ubansa ne kamar sauran ya'yanta wannan dalilin ya kawo babban baraka tsakanin ma'auratan,In yana gidan Sidi zai zauna cikin salama ammh da zarar ya fita sai abunda Allah yayi ukuba ba irin wacce bai gani ba,Hajiya ta taba Cire masa riga ta zane shi da wayar radio mai karfi kawai saboda sun fita shi da Kabir suka dawo jikinsu duk kasa shine ta rufesa da dukan meyasa yake jan Kabiru ai ba Daya suke ba shi da'n Shege ne Kabiru kuma yaron sunna ne da sahihin aure ya samar dashi Ance sanadin dukan har sai da Sidi ya suma saboda azaba wannan dalilin yasa Alhaji Sulaiman ya saki Hajiya saki daya sakin daya girgizata ta Dade bata gidan ta kuma kwashe ya'yanta duka ta tafi dasu shi kuma sai ya kyaleta iyayenta sun shiga ciki ammh ba'a samu daidaito ba Saboda Hajiya ta riga ta kara hawa dokin naki kan bazata rike Sidi ba shi kuma Alhaji Sulaima yace ba inda zai kai shi in bazata rikesa ba to ta barshi kusan shekara daya Alhaji sulaiman shi ya Dinga wahala da Sadi komai shi ke yi mai Hajiya kuma ta Dauka Alhaji Sulaiman zai sauko yazo ya bata Hakuri sai taga ba haka ba ne ga su kabiru suna ta Damunta da Babansu shi kuma tunda haka ta faru bai taba Takawa wajenta ba ai yace ba shi yace tatafi da ya'ya ba ita taga dama Saboda haka ba zai bisu ba in har ya'yansa ne zasu nemesa.
Ganin Ba riba ne yasa da Umarnin Iyayanta Hajiya ta dawo gidan Alhaji Sulaiman ammh an yi musi tsakani da Sidi ba ruwanta da shi,Shi dai yana bata girmanta domin kamar uwa ya Dauketa ita kuwa ta tsani ma ta Bude ido ta gansa don dai bata da yarda zatayi.
Cikin wannan Halin Rayuwa ta rika ganganrawa Alhaji sulaiman bai tara dukiya ya rika siyan kaddarori ba sai dai ya gina ya'yansa ya basu kyakyawan ilimin zamani,Matan daga Sakandiri yake aurar da su,Ammh dukkansu sai da ya kai su Hajji suka sauke Farali Hajiya fatima Soja ta aura dan kano ne chan aka kaita,ammh daga baya an sauya mai wajen aiki ya koma Kudu,Kafin zuwa yanzu sun zauna garuruwa da dama kafin ya yi ta samun karin girma har ya kawo matsayin da ya kai a yanzu.
Sai Hajiya Aisha da ita kuma d'an karofi ta aura kuma kamar aboki yake wajen Alhaji Sulaiman sai dai tun alokacin ba'annin juna ba ne..
Alhaji sulaiman bai bar gidan duniya ba sai da ya gina ya'yansa sannan ya aurar da su bayan mata ma har da mazan har kuma ya bar duniya bai ga Nadamar Hajiya suwaiba(karofi),kan Asiya da zuru'ar ta ba,har alokacin bata ganin duk wani daya shafi zuru'ar Asiya da Atika da Daraja saboda abunda ya faru.
Daga kabiru har Sidi sai da suka fara samun Takardan Education kafin su Dora degree din su,Baba kabiru fanni Biology ya karanta,shi kuma Babanmu sai ya karanta Fanni Kasuwanci Business admistration.
Bayan kamallah karatun su dukkansu sun samu aiki Kabiru ya fara koyarwa a wata makaranta gwamnati dake Karofi shi kuma Sidi sai ya samu aiki a wani ma'aikatan littafai dake katsina chan ya tattara ma ya koma Saboda gidan baya mai dadin zama Hajiya ko zai gaisheta sau dubu bazata amsa ba sai tayi kamar bata gansa ba,Sai dai yana bata girmanta a matsayinta na uwa bai taba riketa aransa ba kuma kullun haka Alhaji Sulaiman ke gaya masa Hajiya uwa ce garesa komai zatayi mai kada ya Daukesa a wani abu ya Dauka ajizanci ne na D'an adam.
Shiyasa bai taba kallonta da wani abu ba,Balle da suka taso kamar uwa daya uba daya shi da Kabiru in ba mutun bai sani ba zai dauka uwar su daya ubansu daya sai an fada maka ne zaka san ba Uwa dayace ta haifesu ba ammh suna Diban kama Dukkan su Dogayen katsinawa ne marasa Lalaci Sannan shi kabiru yafi Sidi haske Saboda Hajiya farace,Sakamakon ita Asiya baka ce shiyasa sai hasken sa ya zama mai Duhuwa..
Yana shigowa karofi duk bayan Sati hudu kuma duk alherin da zai yi ma Dangin Mahaifiyarsa,zai yi ma Hajiya sai dai bata karba yana sauke ledan zata Dauka ta kone daga baya sai ta Daina konawa Tunda Alhaji Sulaiman ya ja mata kunnen tana albuzuranci da Dukiya da kaya watarana zanin Daurawa sai ya gagareta sai ta tsorata ta Daina Konawa sai dai ta Sadakar da su.
Kabiru ya riga Sidi aure saboda shi Daga baya shima katsinan ya koma da koyarwa a wata babbar sakandiri,Achan ya hadu da Saudatu ita din buzuwar yamai ce Kasuwanci ke shigo da su Katsina ta Jibiya anan suka Hadu Allah ya hada kauna Tsakaninsu har ta kai su ga aure Saudatu(Mama kofar soro) farace Doguwa kyakyawa kin kowa kin wanda ya rasa ga gashinta har gadon Baya Hajiya tayi alfahari da wannan auran ganin kamar Kabiru ya kece sa'a cikin maza zai auri buzuwa,Barin ma Hajiya Aisha da itace kamar makwafin Hajiyar tafi kowa Fi'ili da karairata Ita Hajiya Fatima babu ruwanta ita datake ma kusa.
Har chan yamai akaje aka nema ma Kabiru auran Saudatu,suka kuma Tare a gidan su dake karofi inda Alhaji Sulaiman ya gina musu barayi guda biyu,Na kabiru da Sidi shima sai da Hajiya ta rika yada mganar ai shi ba Dan gida ba ne bashi da gadon Alhaji shi dai bai kulata ba sai dai yayi mata addu'an shiriya tunda ganin Shekaru sun fara ja Hajiya bata Sauya ba,bai tunanin zata iya sauyawa sai dai shiriyan Allah kawai.
Tun zaman Saudatu karofi taga gata wajen Hajiya kamar ta lasheta barin ma har zuwa ake yi ganinta Saboda kyanta da gashinta,sai taji dadin haka Domin daman tana bakincikin Sidi na aikin kamfani Kabiru kuma ya zama malamin makaranta in tayi mai korafin haka dariya yakan yi kafin yace"Hajiya kenan ko wani bawa da kika gani yana tafe da kaddaransa arzikinsa da aurensa da Haihuwarsa da Mutuwarsa'"
In yace mata haka sai dai ta kallesa ta Harareshi kafin tayi kyafci Sai tace"Ai daman haka zakace Yaron nan Sidi ya gama dakai kai da Aisha Fati ce kadai tasan ciwo na"
Sun riga sun Saba da Halinta shiyasa suke Lallabata su rabu lafiya,yana katsina sai sati sati yake zuwa ganin gida Tun auran su daman Hajiya ta gama karanta ma Saudatu kaf Waye Sidi da auran cin amanan da Asiya tayi da mijinta,Sannan ta fadamata Sidi ba dan sunna ba ne An haifesa da cin Amana ne,shi yasa ta tsane shi duk da ta Lura Kabiru na bala'in ji da kaunar Sidi shiyasa ranar da ya fara kawo mata shi kadahan kadahan ta karbesu sai faman tab'e baki take yi Sidi na lura da ita bai yi mamaki ba Daman yasan za'a rina shiyasa baya fatan in yayi aure ya kawo matarsa wannan gidan yasan ta zama Nama.
Sai da Kabiru da Saudatu suka Haifi Diyar su ta farko Fatima suna kiran ta Binta sunan Hajiyar Dala taci.
Ashekaran Sidi yayi aure auran da Hajiya taji dadinsa tunda ba auran kece sa'a ba ne,Sidi yar'uwansa ya aura da kakansa na wurin uwa da kuma kakan TAMADINA na wajen Uwa itama sun hada iyaye daya,su biyu kadai mahaifinsu ya haifa kafin ya rasu Tamadina da Usman kuma ba uwarsu daya ba kowanne da Tsatson sa Ita ta Madina mahaifiyarta haifaffiyar karofi ce ita kuma mahaifiyar Usman yar karaye ne dake kano Lokacin data gama Takaba ta roki alfarman Tafiya da Usman garinsu aka bata Tun yana da Shekaru goma aduniya ya bar Karofi.
Hafsatu(Tamadina) shine ainihin sunanta,kuma ta samo sunan ne tun tana karama tun da bakinta ya bude duk wanda yayi mata mgana sai tace madina zata tafi shikenan Hafsatu ya bace sai dai tamadina,sannan Tamadina Bebiya ce kuma ba Ciwo bane da shi aka Haifeta mganar ta baya fita Sosai sannan bata ji sosai,ahaka taso cikin rashin gata tunda kaf zuru'ar su Asiya ba wani mai arziki sai Buga buga kawai.
Tamadina baka ce kuma gajera shiyasa duk wanda yasan Tamadina ya ganni ni Fa'iza zai san kammaninta da suffanta duka na Dauko sakamakon su ya Asiya sun Dauko Tsawon babbanmu da Hasken Fatarsa ni kuma hatta bakin Tamadina ni na Dauko shi har da gadon Rashin ji, na duk daga wajenta na gaje shi.
Ba auran Tausayi Sidi yayi da tamadina ba shi ya ganta yaji yana sonta kuma manya suka shiga ciki,Musamman Alhaji Sulaiman da ya shige ma Sidi gaba,har akayi auran da farko yaso ya tafi da ita Katsina ne sai Alhaji Sulaiman ya hana yace ya barta agida kamar yadda Dan'uwansa yayi shi kuma bazai iya yi mai gaddama ba sai ya bar Tamadina a gidan karkashin Hajiyar Karofi da Saudatu(Mama kofar soro)
Ba iya ni na wahala da Mama ba Mahaifiyata ma taci wuyarta ita da Hajiya suka maidata kamar jaka gashi Tana da lalura sai su yi ta zaginta bataji,Gashi ba daman tayi mgana sai Hajiya ta hantareta tana fadin"Ta fi chan Dangin maciya Amana..Dangin bakake munana kawai masu bakincikin munafunci"
Kalaman tun tamadina bata gane su har ta fara ganesu ta kuma Haddace su,In Sidi na nan ne take samun salama sannan tana jin dadin zama da Uban mijinta Alhaji Sulaiman.
Da kuma Hajiya Aisha(Goggon karofi),Sai Kabiru wanda shima ba ruwan shi ammh Hajiyar Dala sai abunda ta manta cin mutumci in tazo gidan nan Tamadina sai tayi kuka Taruwa suke yi su yi ta cin mata Mutumci wani Lokacin batama jinsu har Jin dadi take yi da Allah yasa bebiyace ita da ta kunshi bakinciki.
Bayan Haihuwar Saudatu in da ta Haifi ISHAQ Bayan Haihuwar Saudatu,Tamadina ta haifi yarta mace Aka saka mata suna Asiya sunan mahaifiyar Sidi taci,Shekara shida tsakaninsu an yi sunanta ba jimawa Alhaji Sulaiman ya kwanta jinya ciwon sugar da bai tashi ba Gabadaya duk abunda ya tara sai da ya kare wajen neman mgani daga karshe bai tashi ba ya koma ga Allah.
Rasuwar sa itace silar Wargajewar komai an yi ta rigima wajen raban gado,Domin Hajiya ta yi tsaye tace Sidi bai da gadon Alhaji Saboda shi din d'an cin Amana ne ganin rigiman tayi girma sidi ya tattara matarsa suka koma katsina ya kama Hayar Daki biyu da Tsarkar gida sai kitchen,Ya kuma ce ya yafe gadon har Abada aka rasa rai ma aka Hakura ballatana Duniya tun faruwar lamarin yasan Hajiya bazata taba kaunarsa ba kawai sai ya Hakura wanda ya hada ya raba,Tundaga Lokacin sai ya Dade bai je karofi ba Sai dai suna mgana ta waya da Kabiru da Aisha tunda su kam basu yar da Zumunci ba..
Ko shekara basu shafe a katsina ba ya samu aiki a wani kamfanin Sarrafa leda dake malunfashi sun basa matsayi mai girma da gidan zama ya tattara tamadina suka koma malumfashi da zama
Acikin shekarun da suka gabata abubuwa dadama sun faru ciki har da Sauyin rayuwar da kowa ya samu Sannan da Nadamar Hajiya,Rana daya ta rika kuka tana a kira mata Sidi ta nemi afuwarsa dayake ita kadai ce agidan yanzu Kabiru shima ya Tattara sun koma cikin katsina da zama Tunda ya zama principal bayan yaje ya karo karatunsa
Sidi yayi matukar mamakin nadamar Hajiya daman bai taba riketa ba ya riketa yana share mata hawaye tare da Fadin bai taba riketa acikin Ransa ba kowa yaji dadin wannan al'amarin ban da Hajiyar Dala domin har Abada bazata kaunaci Sidi da zuru'arsa ba.
Hakama Saudatu(Mama kofar soro) itama ta tsani Sidi da zuru"arsa ganin tafi TaMadina komai na bangaran kyau da Nasaba ammh a bangaran jin dadin gidan miji,Sai dai su goga domin bata fita komai na inganta Rayuwa ba, Sidi na yima Iyalansa komai sun gado Halin Dattako wajen mahaifin su Alhaji Sulaiman
*****
Shekaru goma da suka gabata.
A cikin wad'anan shekarun goman,komai ya faru kuma ya kare,mun fara samun ingantattaciyar Rayuwa a malunfashi,Bayan haihuwar Ya Asiya sai Yaya mariya sai ni Fa'iza da aka Haifeni da Laluran Raunin ji sai autarmu dataci sunan Tamadina Hafsatu ita an haifeta ma ne Babanmu na cikin Tsananin jinya shima Ciwon sugar yayi gado wajen mahaifin su Alhaji Sulaiman shima kamar shi din sai da komai ya kare tas wajen neman mgani kafin rasuwarsa sai da aka yanke mai kafa Da Hannu bazan taba mantawa ba ina Aji hudu na matakin primary a asibitin gwammatin garin Malunfashi Babanmu ya rasu a hannun Alhaji Kabiru(Baban katsina) da Tamadina Mutuwar da Sanadinta ta gama gigita Rayuwarmu gabadaya sanadinta muka san halin Rayuwa muka san maraici da rashin gata.
Da gidan da muke ciki kadai muka Tsira shima da aka saida shi duk a bashi ya tafi tunda jinya yayi kusan shekara uku sai da komai ya kare aka koma cin bashi duk da Baban katsina na Tallafa mana shi da Hajiyar Karofi.
Mutuwar Babanmu shine Silar Barowarmu Malumfashi muka koma Karofi daga Lokacin kuma komai na Cigabaman mu ya tsaya,Tamadina tana gama Takaba gidan su ta koma,mu kuma ta barmu gaban Hajiya da Farko da nan aka barmu da mun samu Rayuwa mai inganci saboda Hajiya tana kaunarmu kwatankwacin kaunar da take yi ma Sauran jokokinta.
Ammh sai hakan bai samu ba Baban katsina ya tara su Hajiyar Dala yace zasu rabamu a Tsakaninsu Saboda Rage ma Hajiya Dawainiya,Shi farko Yaya Asiya yace zai dauka Ita kuma Goggon Karofi tace zata Dauki Yaya mariya ta hadata cikin ya'yanta ta rike Tsakani ga Allah.
Shi kuma Baban Katsina sai yace Hajiyar Dala ta Dauke ni Tunda Hajiya ta maida ma Tamadina Hafsatu tunda tana karama ne Lokacin sosai tace ta riketa tukunna har sai ta yi wayo sosai.
Ai Hajiyar Dala agaban kowa da kowa ta Daka tsalle tace bazata Daukeni ba takai gidanta ban ko ji sosai ta Daukan ma kanta Lalura ita bazata iya ba har Hajiyar karofi sai da tayi mata mgana tace bazata Dauki kowa ba,Sai aka kyaleta Baban katsina da ya fara fada Hajiya ta hanasa tace ita zata rikeni shi ya tafi da Ya Asiyan kawai ita zata rikeni Hajiyar Dala najin haka sai tace sai dai ta Dauki Yaya Asiya tunda ita Lafiyarta kalau Baban katsina yaso ya hana sai Hajiya tace abata,wannan shine Dalilin Rarrabuwarmu Yaya Asiya a kano ta tashi Ta samu tayi karatunta har Sakandiri ita kuma Yaya mariya ta taso Hannun Goggon karofi itama tayo karatunta ita kam har matakin N.C.E,Sai Hafsatu wanda Baban katsina yace in ta kara girma shi zai Dauketa Tunda ni Hajiyar karofi zata rikeni ammh duka Dawaniyata Na hannunsu.
Naji dadin barina a karofi da akayi Saboda Tamadina da Hafsatu sai kuma Yaya Mariya dake kusa Damu ko da yaushe suna gidan Hajiya tare damu Ni dai Dakyar Hajiyar Karofi ta bari na gama nakai aji Biyar na matakin primary domin na rubuta jarabawar fita ba sai fada take yi Me zan ji a makaranta ko me zan gane Tunda ba ji nake yi sosai ba,Baban Katsina ya so nayi karatu ammh sai yaga bayan Hajiya Nima bana so Saboda ina shan Dariya da Wulakanci a makaranta wajen Sa'annina Saboda yanayin mganata da raunin ji na sannan kuma ni bakace bani da kyau shiyasa sai karatun ya ficemin Daga raina na,na saka araina sai mai gata ko mara Lalura yake zama mai ilimi bani da na ke nakasashiya ba.
Ammh Hajiyar karofi bata bari nayi Sakaci da na addina ba,Ta sakani Islamiya da Hadda da Makarantar allo ta Safe da Dare,Shi kam ban yi sakaci ba Kuma dayake karatun Qur'ani ne da Liffafan addini ina ganewa sannan Hajiya bata hanani ba shima na Bokon bazata iya juran dawowa da nike da kuka bane Saboda har waka ake yi min bebiya mamarta ma Bebiya sai nake jin guilt din abun acikin raina da yasa naji na Tsani bokon gabadaya sai Hajiyar Karofi ta maramin baya domin gatan Duniya ba wanda bata nuna min ba.
Rikon Hafsa ya koma Hannun Goggon Karofi Saboda Tamadina tayi aure a Dutsenmah ta auri wani magini ne matan sa Biyu itace ta uku,Sai Baban katsina yaso ya karbi Hafsah Mama kofar soro ta daka tsalle tace bazata rike zuru'ar Tamadina ba dangin Maciya Amana da Bebaye ba Hajiya tayi kuka kamar ranta zai fita tasan duk abunda ta Shuka ne take gani ta zaunar da Mama da Hajiyar Dala ta gaya musu komai ta kuma yi kokarin cire musu wannan Tunanin ammh batayi nasara ba Dole ta zuba musu ido ganin abun na neman ya lalace Sai Goggon Karofi ta raba Gardama ta Dauketa kawai ni da Farko ban san matsala ko matsin Rayuwa ba, sai da sanadin ciwon Hajiya ya wujijjiga Rayuwata. sannan na kara Fahimtar bamu da gata sannan maraici ya gama Lullube rayuwarmu tun a baya na Fad'a muku ita kanta Tamadina ba su da wani gata balle mu yi Tunanin samun gatan ta barayinta gatanmu kenan Dangin Babanmu su kuma k'alilan din su ke son mu da Kaunarmu.
Bazan taba mantawa da wata rana na Dawo daga allon Safe ina shiga Dakin Hajiya na ganta kwance ba yadda take ni na Ruga na je na kira Goggon Karofi tazo ta gani,aka kwashi Hajiya sai asibiti ashe Faduwa tayi ta samu shanyewar barin jiki,ta koma sai dai a kwantar a tayas,ganin haka yasa Goggon Karofi suka yi shawara da Baban katsina ta maida Hajiya da ni gidanta tana kula Damu gabadayamu,Ko wata uku Hajiya batayi tana jnya ba,jikinta ya kara Rikicewa ga nauyi yayi ma Goggo yawa Mijinta ma'aikacin gwamnati ne ammh kuma akwai Dawainiya shi kuma Baban katsina Lokacin ya na matsayin Daractan Ilimi ne na Katsina gabadaya ya samu Rufin asiri sosai.
Shiyasa Saboda ya rage mata nauyi yace zai daukeni alokacin cikin Fargaba ta kallesa kafin tace"Abban Ishaq kana ganin ba matsala..?
Ajiyar rai ya sauke tabbas akwai matsala yasan Halin Saudatu ammh kuma ai gidansa ne kuma shi ke auranta Dole Fa'iza ta zauna karkashin kulawarsa shiyasa cikin karfin Hali yace"Kada ki damu ba wata matsala ta had'a kayanta da zarar na tashi da ita zan wuce"
Nayi kuka kamar zan mutu da naji Goggo tace na shirya nabi Baban Katsina gidansa Yaya mariya ne da Goggo suka rika Lallashina ni nasan gidan bamai kaunata,Daga maman har Anty Binta da Ya Ishaq wanda in dai suka yi Hutun Makaranta yakan Biyo Baban katsina ya gaida Hajiya wlh baya kallona bazan taba mantawa da Ranar da ya fara ganina agidan Hajiyar karofi ba kallon Sama da kasa yayi min kafin ya kauda kai ya yamutsa Fuska ya kalli Hajiya yana Fadin"Hajiya wacece wannan mummunar bakar yarinyar..?
Hajiya cikin yar Dariya tace"Baka gane ta ba ko..?
Fa'iza ce yar wajen Marigayi Babanka Sidi"
Ina kallo ya kara kallona ya yamutsa Fuska kamar yaga kashi kafin yace"Hajiya bata da kyau Sannan ban taba ganin baki irin bakinta ba kamar ta shafa shuni"
Yafad'a cikin Sigar Tozarci ita ko Hajiya Dariya tayi kafin tace"Kuma kai nayi ma kamu ba"
Agaba na ya Tofar da yawu kafin yace"Allah ya tsareni Hajiya ai ni Matata bata zo duniya ba tukunnah"
Alokacin Hajiya bata Dauka wani abu ba ammh ni da na taso cikin wannan yanayin nasan tozarci ne nayi kuka Sosai.
Ina kuka ina komai Baban katsina ya sakani a mota yana bani baki sai Katsina Hajiyar karofi kuma bata mgana Sosai jikinta yayi zafi,sai dai bin mutane da ido kawai sai hawaye bata mgana.
Tana kallona zan tafi na rike hannunta ta gyadamin kai ina kuka tana Hawaye itama a mota ma kukan na Dinga sharba sai da Baban katsina ya jawoni jikinsa yana Lallahina Fadi yake yi"Kwantar da Hankalinki Fa'iza zan kula dake kwantacin yadda sidi zai kula da dake in yana raye"
Lokacin ba jinsa nayi ba ammh nasan Lallashina yake yi.
Sai dare muka isa katsina anguwar Kofar soro Makeken gidan da Baban katsina ya gina Tun ranar da na saka kafata acikin gidan nan ban kara farinciki ba har fita ta zuwa gidan Ishaq babu abunda ya Sauya.
Nasan dai Baba na gaba ina Binsa a baya da jakar kayana ina kalle kalle har Babban Falon gidan in da mama ke zaune ita da Yaya Ishaq sai Anty Binta da tayi aure ammh acikin garin katsina Sai Jamal wanda ke bi ma Yaya ishaq sai Karamar su Badariya.
Dukkansu Baban suka zuba ma Ido da farko Mama ta fara mai lale bata ganni ba sai da ya juya yana kallona kafin yace"Saudatu ga Fa'iza ta Dawo Hannuna da zama har na aurar da ita ki kaita Dakin yaran nan ta yi wanka ta Huta"
Ai ranar naga tashin Hankali agabanmu Mama ta dinga Bala'i tana fadin bazan zauna mata agida ba Dangin munana maciya amana Dangin kurame me zatayi dani ban da akara mata wahala Fada dai sosai tana Fad'a Baban katsina na Fad'a har yakai ga Baba ya kusa saka ma Mama Hannu sai da su Ya Ishaq suka Shiga Tsakani ita kuma tayi shewa tace da ya sa ke ya mareta wlh bazan zauna mata agida ba.
Ranar a falo na kwana rakub'e ina rawan sanyi da tsoro,Duk naji mganganun Mama Saboda da karfi take mganarta Tunda Baba ya shige Ciki itama ta shige a Fusace ban kara ganin kowa ba Badariya ce tazo wajena Anty Binta tajata suka tafi gidanta saboda Kada ta rabe ni Jamal kuma daman ba wani babba ba ne alokacin tashi yayi ya shige Dakinsa ko ajikinsa Ya Ishaq ne ya taso yazo gabana yana min kallon Tsana da kaskanci kafin yace"Dama kece Kurman nan..?
Ko Bebiya ma zan ce..?
Ban ji sa ba shiyasa na kura masa ido kauda kai yayi ya wuce yana fadin"Abubuwan sun yi miki yawa..ga baki ga Muni ga maraici ga Ki kurma"
Daga haka shima ya Tsallake ashe wasa farin girki wani kukan Rahma ne Duk yadda Baban katsina yaso ya inganta Rayuwata ya kasa Domin Mama tafi karfinsa bashi da yarda zai yi da ita,Tunda nazo gidan ta sallami Duka yan aikinta a shekaruna sha Uku a duniya na bautu da aikin Wahala nau'i Dabam Dabam,in na tashi Tun asuba bana komawa sai wani Daran abinci kuma sai an rage nake samun naci Tun ban iya girki ba har na iya aiki kuwa ba wanda ban iya ba In Baba yayi mgana sai tace zata koreni.
Nayi wahala da Mama da ya'yanta sannan nayi wahala da Anty Binta da Ya'yanta Ya Ishaq ko ta gabansa na Gifta sai ya Hantare ni da Mummuna,baka,Tun bana Fahimtarsa har na fara gane hantara ce da Tsana shi da Anty Binta sun ce basa son kallon Fuskata baki na da muni na yayi yawa.
Baba yaso ya maidani makaranta Mama tace zai yi asaran kudin sa ne Tunda baji nake yi ba Sai yace zai maidani islamiya Dakyar ta amince ina zuwa ta Lasar zuwa shidda na yammah ammh sai nagama duka aikina sannan zan fita,anan na samu na Sauke alqur'ani daman kum na d'an yi nisa a karofi,sannan nayi karatun Sauran Littafan Addini da wannan zan iya cewa na Tsira a zamana a gidan Baban katsina.
Sai kuma girken girken zamani da na gargajiya da na koya a iya zamana agidan mama shima ba wai ita ta koyamin ba,Ni na koya da kaina Saboda ina da karambani Mama bata taba Damuwa dani ba tsakani na da ita sai Harara da hantara,tana ganina a matsayin wata aba mara gata da galishu wuya ce da wahala yasa tun ban iya komai ba har na koya.
Na yarda ina da nakasun rashin ji ammh bani da nakasun wani abun Hallita ajikina ina da rai na da lafiyata to zan yin komai,Na iya wasu girken girken a tashar arewa24 na shirin su Akushi da Rufi wani Lokacin Tibin ita kad'ai afalo tayi ta babatu in nagama aikina sai na Lallabo nazo na zauna Duk da bana jin yadda suke koyar da girken girken ina bin yanayin yadda suke Hada komai ina ganewa.
Sannan da kuma Anty Mamah babbar Diyar mijin Anty Binta ce mahaifiyarta ta rasu ne dalilin da yasa ma ya auri Anty Binta kenan.
Tana aure acikin asibitin Kashi wato Othorpedic na katsina mijinta Likita ne tana da Yan biyu wato Twins,Mama na yawan Tura ni gidanta Saboda reno Yaran nata duka mazane Hassan da Husaini masu Rigima ne Anty Mahma ba kamar Anty Binta take ba,bata da mugunta sai dai akwai saka aiki,Kuma tana da kyauta sannan bata kyamatata ko tayi min fada, in naje gidanta kamar jaka har gwara ma gidan mama ina Hutawa sai dai ita bambamcin su bana girki da kaina ita da kanta take shiga kitchen tayi abunta ammh nakan shiga na taimaka mata da yanke yanke da miko miko to da haka nake zura ido ina Fahimtar wasu abubuwan nasan bani da gatan da zan yi karatu ko ina dashi ina jin tsoro zuwa makaranta saboda kada akusheni ko ayi ma Nakasuna Dariya shiyasa na kan kasa ido da raunannun kunnuwana ina duba wasu abubuwan da jin wasu abubuwan iya abunda zan iya ji na kuma d'auka.
Sannan agidan Anty Binta ma na koya su Snaks saboda Diyar Anty Binta ta farko mai suna Halisa zamu iya zama tsaran juna tunda Anty binta tayi aure tana da kananun shekaru alokacin to ita ke sana'ar yin Snaks in naje gidan nakan kasa idanuwana ina lura da abubuwan da take yi a hakan na nake daukan wasu abubuwan.
Da yake ita Halisa tana da bambamci da su ba kasafai take nuna kyama gareni ba sai dai bata shigemin sau tari nakan taya ta aikin Snaks din ta in an kawo mata dayake sana'arta ne tayi suna tunda tana amfani da Social media alokacin.
Tun ina da shekaru goma sha Hudu a duniya jikina ya gogu da aiki babu aikin da zai gagareni komai yawansa agidan Mama tun karfe Hudu nake tashi Daga barci naje kitchen na kintsa Sannan na Dora abun kari sai naje na tada Badariya bayan na saka mata Heater na wanka Saboda zuwa makaranta Domin dokar da Mama ta kwafanin kafin bakwai na Safe na gama komai kada ta fito bata iske abinci a saman dining ba,ko kuma taji kafafunta na taka Datti acikin Falonta Shiyasa ina yin abun kari wani Lokacin ina Share sharen dakuna hatta Dakin Jamal ni nake gyaramai in suka tafi makaramta Saukin ta ma shi bai cika mgana ba barshi da waya a Hannunsa irin su ba kasafai ake gane inda suka dosa ba.
Ya ishaq kuma baya gida sai an yi Hutu yake zuwa yana ABU Zaria inda yake Masters di'nsa nima abakin Anty Binta naji sunan karatun nasa har na iya rikewa,Hatta da kayan Jamal da na Badariya da na Mama ni nake wankewa ammh Baba bai sani ba Saboda yasan duk wata baya fashin bada kudin mai wanki da guga Tunda Mama ta sameni take soke yan kud'ade'nta,in wankin ya taru tun safe in naje baya na fara sai yammah watarana ma bana ko samin zuwa islamiya,Washegari kuma Baba na fita zan dasa guga har sai bayana ya kage ba ci ba sha sai na gama in kuma nace zan tashi ko sallah in yi sai Mama ta kai min duka tana Fadin"Me kika sani a karatun sallar..?Ni fa jin baban su kawai nake in yana Fadin kina da ilimin addini ke da kike Bebiya gaki ba kyau ba fasalin y'a mace ai bautar da ta dace da irin ku kenan.."
In ta fadi haka bana damuwa sai naga gaskiya ta fada domin na fahimci in baka da kyau ko Asali da gata ko kana da wani nakasun Hallita baka da wani amfani Domin wad'anda suka fi kusanci dakai sune suka fi kowa kyamatarka to inaga na waje wad'anda basu san ka ba, mu'alama ce zata hadaku..?
Ina tuna Lokacin muna Malumfashi Iyayena sun san ina da Lalura ammh ko sau daya basu taba nuna gazawar su ba sun min dukkan gata a malumfashi makarantan da aka kaini ina gane karatu tunda ana yimin yadda zan gane sannan bamai kyamatata Saboda ina da gata alokacin ammh daga Lokacin da gata na ya kare sai nima nake fama da guilt din shiga cikin Mutane ina ganin ban kai ko wani matsayi ba sannan na aminta da mganar Mama iri iren mata irina Bautace ta Dace damu..
Shiyasa duk wahalan da nike sha bana Damuwa ina ganin ahakan ma ni kila nafi wasu ma ire irena,Baba duk baya sanin wasu abubuwan tun da in ya fita tun Safe sai Dare,in kuma ya Dawo yayi sallah yaci abinci zai kirani falo yayi ta kokarin na bayyana mai abunda nake bukata ko nake so ammh bana iya mgana Saboda Mama ina bala'in jin tsoronta kamar wata mala'ikar Mutuwa.
Baban katsina irin mazan nan ne marasa Bibiyan al'umuran gidansu shiyasa Mama ta samu dama tana Damawarta,Komai na Cefane Mama yake bamawa,Duk watan Duniya ita kuma sai ta samu nata aciki Mama tasan kan kasuwanci,Tana saida dikkakun kayan mata da maza anan ake dinka mata tana aika ma yan'uwanta dake yamai suna Siyar mata kuma har anan tana samun ciniki sosai tana harka da manyan mata bayan dikakku har Tamfofi da Lesuna tana saidawa da takalma Shiyasa take da tarin kawaye da Mutanen arziki da ke shiga suna Fita agidan,Shiyasa ko Sutura ita Baba ke bama kudin ko na Mutanen karofi ne kuma baya Bibiya,Shiyasa sai wanda taga dama ta bawa,ba kuma wanda ya isa yayi mgana duk sallah har da su Yaya Asiya Baban katsina ke yi ma Dinki adadin yadda yayi ma Badariya dani ammh ni ko Sabo daya Mama bata bani na saka sai tace Mace irina da kwance ta dace ni kuma sai mganarta ta zaunamin kayan alfarma masu kyau sai ajikin kyawawan mata wad'anda basu da wani nakasu Mata kuma irina da kwance muka Dace yawancin kayan yaran kawayen Mama nake sakawa Domin na badariya bazai min ba Na girmeta sosai alokacin,Su Yaya Asiya kuwa Kala dai'dai take jifan su dashi Yaya mariya bata da matsala ita da Hafsatu Goggo macece mai Tsayawa akanta ita da iyalanta Yaya Asiya kuma tace duk mugunta Hajiyar Dala tana barinta da Suturu Saboda ita yar gayu ce sannan mijinta Soja ne ya'yanta fes suke itama haka saboda haka Itama Yaya Asiya badai a ganta da kama mara kyau ba.
Ni dai ko da yaushe cikin Tsumma da Ragga In Baba ya gani yayi mgana Mama ta lawayance zance ni kuma bana iya karyatata agabansa,bazan taba mantawa da wata sallah ba,Sallah da na fara yinta a gidan Baban katsina Lokacin na kwashe wajen wata Tara a katsina,kuma tunda nazo ko Karofi kafata bata kara takawa ba Ga Hajiya na raina in Baba zai tafi gaisheta sai naji kamar na bisa,tunda duk karshen wata yake zuwa wani Lokacin shi da Mama suke zuwa wani lokacin shi kadai da Direba ko shi da Jamal.
Hajiya na rai na ita da su Yaya Asiya musamman Hasfatu kewar Tamadina kuwa har na cire sa araina tunda ba samun ganinta zan yi ba Tun bayan dawowata Ko mutum daya Daga karofi bai leko mu ba na dai ga Hajiyar Dala da suka taba zuwa Bikin Dangin mijinta ta sauka anan kawaye ne ita da Mama sai muguntar su tazo daya sai dai ita tafi mama ji da kai da nuna ita din watace.
Sallar azumi ne Dama da azumi duk na Rame na kara lalacewa,Ni bansan gayu ba, bansan komai mai kyau ba ni na dauka abu mai kyau a wajen mata masu kyau ake samun sa,Wani Riga da Sikat na saka cikin kwancen kayan ya'yan kawayen Da mama ke bani ne wuyan zamemin yake haka ma Sikat din yayi min yawa sai da na saka Tsumma na Taresa ajikina Hijabi ne kadai Sabo Shima Anty Mahma ce ta dinkamin domin jiya gidanta na wuni na tayata soyan Nama da aikin cinci Sai Dare ita da mijinta suka maidoni gida ita ta na da kyauta in nayi mata wahala tana min alheri takalmin kafata na Roba ne shima din Na jamal ne da ya daina amfani da shi na Dauka
Da farko Mama bata so aje dani Sallar idi ba,Sai Baba yace dani za'a tafi Ya Ishaq ya dawo agida yayi azuminsa Shi na lura kamar baya ma san kallo na shiyasa ban cika giftawa ta gabansa ba.
Lokacin da na fito Kofar gida Baba ya ganni sai da yaji kwallah ta cikamai ido,Ya kalli Badariya ta kure adaka ita da Mama,Jamal da Ya ishaq sun ci Fararan Shaddodi sai Faman sheke suke ni kuma bazar bazar kamar mahaukaciya wata yar aikin ma tafini kyan gani ni kuwa bakina kamar zai Tsage Saboda murna zan fita masallaci naga jama'a Tun kafin Baba yayi mgana Mama ta rigasa da fadin"Ke Fa'iza meyasa kika saka wadanan kayan..? Ina naki irin na Badariya..?
Sai na kasa mgana Saboda ni dai bansan da wani kaya ba,ba'a bani ba ganin Baba ya saussauto yana kallonta yasa ta kara karya murya tana Fadim"Bansan meke damun Yarinyar nan ba Abban Ishaq ko da yaushe bata da aiki sai saka Tsumman kaya nama ce ta hada su in zaka Karofi ka tafi da su arabama mabukata"
Ban yi mamakin kalaman Mama ba Domin tun zuwana gidan ba Dadewa,Ta daina Fada da Baba akaina sai ta koma aiki da Kissa shima shawaran wata kanwartace daga Yamai hure ita tace mata in tana so taci Ribar Rayuwa to ta daina tada Hankali ta yi amfani da kiss,kuma Tabbas kissanta tana Tasiri wajen Baba don nan take ya kalleni kafin yace"Haba Fa'iza ya zaki saka wadanan kaya..? Baki ga sauran yan'uwanki ba ne.?maza je ki sauya kaya mu tafi kada mu makara'"
Da Sauri Mama tace"Zamu bata Lokaci Alhaji muje in mun dawo sai ta sauya"
Sanin Halinsa na rashin bincike kan al'umura yasa tace haka,Haka muka tafi su kamar zara cikin wata ni kuma kamar yar aikin su Shikenan ko da muka Dawo Baba yayi baki yana falon waje har Dare bai kara bi ta kaina ba,Sai da Washegarin Sallah da kwana Biyu mukaje Karofi ranar dai Mama ta bani Sabon kaya na saka ta kuma ja kunnena in taji wata mgana sai na Raina kaina ni ko araina nace wazan gayamawa.?bata san ina da zurfin ciki ba ba tun yau ba,bakomai ake jinsa bakina ba.
Duk da Sabon kayane ammh da na sanya kamar wata Dussa komai ba Tsari ni kaina nasan ba kyakyawa bace ban mallaki komai na mata masu sa'a da gata ba,Kusan daman Hausawa kan ce in kana da kyau ka kara da wanka to ni bani da kyau din sannan ban iya wankan ba ballatana na kara dashi,Wani Lokacin sai Dare nake samun Damar yin wankan Tunda Dakin da nake ciki akwai karamin Tiolet to iya wankan ne ko shi ba don kyau nake yi ba Komai bazar bazar ne bansan iyakarsa ba.
Da mukaje karofi na hadu da su Ya Asiya har sai da sukace har baki na kara na rame sun yi tambayan Duniyan nan kan wani irin rayuwa nake yi agidan Baban katsina naki ce musu komai sai dai in kallesu ina mirmishi naji dadin ganinsu haka barin ma Hafsatu da ta zama kamar ba ita ba ta kara wayau da girma.
Ina jin su a tsakaninsu suna tattauna yadda Rayuwa ta jefa su a inda suke ni dai bana ce musu komai nadai san na Tambayesu tamadina suka fadamin tana Lafiya Yaya mariya na zuwa Dubata ita da Goggon Karofi sukace In Baba ya barni gobe sai muje na ganta.
Ganin Goggon Korofi yasa Mama batayi mgana ba,Baba kuma ya amince washegari chan muka wuni sai yammah muka dawo ita kanta Tamadina ta na cikin wahala gida cike da yara,wahalar tayi mata yawa sai dai ba yadda zatayi ne kwanan mu biyu muka koma Katsina,Na koma da Tausayin Hajiyar Karofi ganin jikinta duk ya kara rikicewa yanzu ma dayan barin shima ya Daina aiki Goggon Karofi da ya'yanta suna matukar kokari kan Hajiya.
Haka rayuwata ta cigaba da tafiya a gidan Baban katsina duk da irin azaban da nike sha achan ban taba jin na gaza ba sai ma nake ganin Sun yi min komai tunda zan ci na sha na kuma samu wajen barci Baba na jin Takaicin rashin Karatu na ko da yaushe naje gaishe shi da Safe sai ya kalleni yace min"Fa'iza kin k'i makaranta ko..?
Baki san ilimin zamani ginshiki ne ga rayuwar ya'mace ba..?
Ni kuma bana iya mgana sai dai na Dukar da kaina cikin Tausasawarsa yake cigaba da Fadin"Da kin Daure Fa'iza ai kina jin mgana zaki gane komai sannan zan yi ma malaman ku bayani kamar yadda nayi ma malamanki na islamiya bayanin Laluran ki"
Ina Dagowa muka Hada ido da Mama ta Sakar min harara sai jikina ya fara rawa cikin yanayin mgana ta nace"Baba shi na addinin ba Ilimi ba ne..?
Sannan shi ba Ginshiki ba ne ga rayuwar mu ba..?
Baba ya jinjina mganata kafin yace"Ginshiki ne Fa'iza babban ginshiki ba kuwa..Sai dai ka hada duka fufukan guda biyu sai ka samu na zaman duniya da Lahira"
Alokacin sai nace ma Baba"Baba ka barni haka..na islamiyan kadai ya isheni"
Zai matsamin sai Mama ta taresa tana nuna mai Tunda ban so to ya kyaleni,Shi kuma bai da Zafi sai ya Rabu dani ammh ko da yaushe kalamansa akaina na alheri ne har ya bar duniya ko kallona yayi sai yace"Fa'iza Allah yayi miki albarka In sha Allahi bazaki Taggyara ba..Ina ji ajikina kina da wata baiwar da Sanadinta zaki Daukaka watarana"
In naji haka sai nayi Dariya araina Domin bana hango ma kaina hakan
Na amince Baban Katsina ya karbo ni Hannun Goggo karofi ne domin ya inganta Rayuwa ta,sai dai bashi da Mafita ne Mama ta fi karfinsa ammh har yau bazan manta kokarinsa akaina ba.
Shi ya fadama malaman islamiyan da nake zuwa yanayina suke bani kyakyawan horo ko an gama karatu gabadaya sai an kara min bita ni kadai,Bani da wata kawa shiyasa ni kadai nake zama iyakata da kowa Mirmishi ko Sannu nasan ana mgamata ammh da yake bana ma ji Sosai ban cika Damuwa da su ba.
A farkon zuwa na gidan Mama cikin kasuwar katsina take zuwa siyayyarta ammh sai Kawarta Hajiya Barira irin masu son kudin nan ne ita ta bata shawaran ta rika zuwa kano kwantin kwari tana saro kaya alokacin Mama sai tace"Kai Barira ya yi nisa ni kinsan ban san wahala"
Hajiya barira ta rika nuna mata yanayin komai tare da fadin nachan sun fi sauki sannan zata hadata da yan kasuwar chan tunda itama tana siyayya achan har sai da Maama ta amince bazan manta ba na zo kawo ma Hajiya Barira abinci na juya naji tana ce ma Mama"ko wannan bakar yarinyar kika tara sai kuje tare ta rika Daukan miki kaya"
Mama ta kalleta kafin tace"Ko Hajiya barira"?
Tace to zauna Daman meye amfanin irin su in ba aikin wahala ba.
Da wannan shawaran Mama ta zauna tana fadama Baba ya amince tunda shi ba mutum ne mai Takura ga iyalansa ba.kuma da tace dani zata bai yi gaddama ba domin nuna mai tayi ina kokari zata nuna min komai Domin tana Tunanin nan gaba ko ban yi karatu ba zan yi kasuwanci to ai Daman haka take fadamai ko na wahalan da nake yi ne,Girki ma Baba yace nayi kankanta Mama tayi Karaf tace gwara na koya Saboda gaba gidan wani zani Daganan Baba bai kara mgana ba.
Daman tun anan ni nake kaimata Dinki chan batagwara kusa da gidan Anty binta,in ba'a gama ba sai na zauna an gama Wani Lokaci anan nake wuni buhu ne shake da kaya zam Dauko akai zuwa bakin Titi na samu Daidaita sannan in na Dawo na Hau ware ma masu kayan nasu,wad'anda za'a tafi da su yamai kuma duk ni ke shirya su Mama na gefe tana lissafin komai ban isa nace nagaji ba.
Ranar da muka fara zuwa kano sai da na raina kaina Wuni guda acikin kasuwa kuma bata Dauki dan dako ba ni ke daukan mata kaya akai kamar mahaukaciya ga yunwa ga kishi Takalmi a Hannu hijabi a hannu Wlh ko abinci bata siyamin ba Da muka Dawo sai da nayi rashin Lafiya Saboda na Jigata matuka alokacin Mama fada ta Dinga min akan na fara zama mai son jiki to in zam mike tun wuri gwara na mike Bani da wani amfani in ba Bauta ba.
Ni ba kyau ba,Ba ilimi ba,Ba ji ba,ba komai na inganci rayuwa ba,bai kamata na rika nuna gazawata ba tabbas gaskiya ta fada ba ni da wani gata a Duniya Bautar dai da ta Fada shine ya fi dacewa da mata marasa galihu ire irena
zuwa Lokacin da na shafe shekaru Shidda Cif a wajen Baban katsina bazan iya fadin irin bautar da nayi ba abu daya na sani ni Fa'iza ban sauya ba Sai dai na kara girma ammh ba Domin na sauya Daga yadda nake ba Ina nan a mai raunannan ji,Mara gata baka Mummuna mara sa'an rayuwa in ji ya Ishaq in ya ganni yakan ce Bai taba ganin mace mara sa'a ba irina komai Total zero ne a bangarena ba wani abun so ko sha'awa tare dani nima nasan haka ko badariya dake tasowa mai kyau ce sannan yar gayu kuma yar gata ni kuwa ban ma san me ake kira da gayun ba,Ni dai kawai nayi wanka na suturta jikina mganar gyaran jiki da Tsaftan jiki ban san shi ba Ba kuma wanda ya ke zaunar dani ya koyamin Ko kitso sai ni nagaji da kaina na tsefe shi kitso kuma sai in Mama taga dama zata bani kudi naje,ayi min.
Zuwa Lokacin rayuwa ta Daga,Sosai ba kamar baya ba,kawayen Mama da suka sani tun abaya in suka gani sai like sai suka rika ce ma Mama Daman wannan mummunar dangin mijin naki na nan baki aurar da ita ba.?
Mama kan basu amsa da cewa wazai kwashi Baki da muni da bebanci sannan uwa uba ba ilimi sai su yi ta Dariya suna cema Mama shikenan ta samu yar aiki to ai daman ba marabata da mai aiki maraban mu daya in da Daukoni akayi da sunan aiki za'a rika biyana albashi,Shine kawai bambamcina da mai aiki acikin wannan gidan.
Su Yaya Asiya duk sun yi aure ita da Yaya Mariya Ya Asiya acikin garin kano tayi aure wani malamin makaranta ne yana da mata da yara,Mai karamin karfi ita kuma Yaya Mariya A karofi tayi aurenta wani dan kasuwa ta aura mai rufin asiri.
Kusan tare akayi Bikin su sai dai na Ya Asiya aka fara yi ,Duka naje bikin su ammh na Ya Asiya sai da Goggon Karofi ta kira Baba ta mai mgana domin tasan Halin Mama munje kano mun yi kwanaki Tunda Bikin tare da manyan ya'yan Hajiyar Dala babansu ya Hada, da Asiya harta duka kudin siyayyan kayan Daki tare ya bada ammh Mama ta zuga Hajiyar Dala akan su ya'yanta suna da gata Asiya kuma ayi mata na Daidai da ita Daga karshe ma ita taci kudin domin duka Dawaniyar Yaya Asiya Baban katsina yayi mata shi,Duk ciki ita kadai ta auri mai karamin karfi gidan falo daya ne sai Dakuma nata da na uwargidan Ba Shakka Baba yayi mata kokari sosai,Bangaran Yaya mariya Goggo da Mijinta sukayi komai ita gidanta ita kadai wannan bikin ne har Tamadina tazo,na Yaya Asiya ne bata je ba, in naga yadda Rayuwar Mahaifiyarmu ta koma sai na kara tabbatarwa lalle bamu da gata gatanmu ya fadi tun Lokacin Rasuwar Baba.
Da ace Hajiyar Karofi na Da lafiyanta da kila abubuwa sun sauya ammh kuma tana kwance sai dai a kwantar a tayar bama wanda ya zata kai haka araye,ana zuwa gida ana Dubata har yau tana nan jiya iyau bata ko mgana Sai wanda ya kara kunnensa yake ji me take fadi in naje Hajiya ta rika kallona kenan na rike hannunta ina Fadin"Allah zai baki lafiya Hajiya"
Sai dai kaga Hawaye na Bin gefen fuskarta Hajiya na bani Tausayi sosai shekaru kusan bakwai tana jinya tana kwance waje daya,Gidan su na karofi Babban Yaron Goggo Yaya Isa ya gyara da yayi aure yake zaune da matarsa kada abar gidan ba kowa ya mutu Baba ya matsa sai ya zauna da Farko Goggon Karofi bata so hakan ba gudun Rigiman zumunci.
Ya Ishaq ya dawo gida ya gama karatu har ya samu aiki a Hukumar Tattara Haraji na kasa reshen jahar katsina,Shekaru uku da suka gabata,Sai dai baya zaman gidan in ya fita tun safe sai dare in kuma ya Dawo yana Dakinsa na fada muku tun a baya shi baima son ganina shiyasa bamu cika Haduwa ba, bana zama inda nasan zai ganni Saboda yafi kowa iya kallon wulakanci da kaskanci.
Akwai watarana tana cikin cikin Ranakun da bazan manta da su ba acikin kaddarorina ba,Muna gabda Riskan kaddaran auren mu ni da Ya Ishaq al'amarin ya faru watarana ya kira Mama a waya yace yana son abincin Mutum hudu abokansa zasu zo su yi Dinner anan biki sukayi na wani abokin aikinsu.
Nan da nan Mama ta tasoni na shiga Kirchen daman na fada muku a bangaran girki ni Fa'iza bani da makusa,Harta Mama yanzu in ba girki na ba bata iya cin abinci,Shi ko Baba kullum Mama yake godemawa yana ganin ita ta tallafamin na iya girken girken zamani zuwa kuma Lokacin na rage wasu walwahalun,Saboda Mama ta daina aike na ta samu yaron aike bangaran kasuwancinta kuma komai ta waya ne sai dai a saka mata a mota a aiko mata dashi,sannan ta dauki masu wanki da guga da kuma mai wanke wanke na koma gyaran gida da girki.
Jin baki ya ishaq zai zo da su na Zage nayi musu girki mai rai da lafiya fatan pototo,da Hanta sai white rice da Miyar kifi,Sai nayi musu lemun Abarba Sai na hada musu da na Gwangwani kafin ya kariso Mama ta sani na je na shirya komai afalon Baba,na koma kitchen na Dora abincin dare na gida har bakin suka zo ni bansani ba Na gama girkin Dare doya da Miya Mama tace ayi naje nayi sallar mangariba ina zaune saman sallaya Jamal ya shigo Dakin da nake mai karamar katifa sai tarkace yace min Ya Ishaq na kirana afalon Baba sai da gabana ya fadi ban cire Hijabin jikina ba yamin yawa yana neman gadani na nufi Falon Baba
Ina shiga da sallama gabadaya zaratan mazan dake falon suka Dago suna kallona ni ban iya kallon su ba,Saboda yadda jikina ke kyarma,ina ji Ya Ishaq ya dakamin Tsawa yana Fadin in kariso,Ni dai nasan nazo gabansa na durkusa kaina na kasa ina ji yace musu"To ga wacce tayi girkin nan da kuka matsu ku ganta"
Ya fada cikin sigar Dariya da karfi yayi mganar yasa naji abunda yace gabadaya shuru sukayi kafin naji sun kaure da Dariya gabadayansu sai naji na muzanta matuka muzantan da ban taba yi ba suna ta mganganu wasu ina ji wasu kuma bana ji nadai ji sanda Ya Ishaq yace"Kai ka yi mata da Hausa No Turanci..Sannan Ears."
Gabadaya suka gwalalo ido kafin ya kalleni yace"Yes..sai kunyi mgana da karfi zata jiku Bebiya ce"
Na kusa dani ne ya matso saitin kunnena yana Fadin"What is your Name.?
Aoh Sorry ya sunanki..?
Na dago idanuwana sun cika da kwallah nace"Fa'iza"
Cikin yanayin mganata gabadaya sai suka sheke Da Dariya har suna Tafawa da junansu Sai naji na kara raina kaina Nasan ni ba bebiyace ba ce ina dai da Raunin ji ammh ba Kurma bace ni Mutane ne suka kara Raunana jina da kushe da Tsangwaman su akaina,Ninasan inaji sai dai sai an yi mgana da karfi Sannan mganata tana da Tsami Tsami Kuma ina Rabe ta kamar ina in ina kuma saboda Raunin ji na ina karantar bakin mutum in yana mgana Ko Tamadina ba Kurma bace tana mgana sai dai mganata tafi nata fita sannan na fita karfin ji.
Ammh yadda suke kankanba Bebanci na abun bai kai haka ba.
Ban taba jin guilt irin wanda naji ba Ranar hawaye suna bin fuskata na mike zan fita Ya Ishaq ya dakamin tsawa yana fadan sun sallameni ne..?sai na Dawo kawai na Durkusa ina jin Ya Ishaq na fadin bai taba ganin baki da muni ba sai a wajena su ma abokan irin sa ne suna ta Dariya na kamar sun ga abun dariya ajikina ko acikin Abunda suke ma Dariya aciki akwai wanda na bama kaina ba Allah ya bani ba? abun da nake sakawa araina kenan ina jin wani irin abu a kasan raina.
Sun dade suna kallona suna Dariya kafin Ya Ishaq yace na kauce daga gabansa na mike idona ya rufe bana ko gani,bansani ba na ture Teburin dake gaban su jug din lemu ya fado ya zube Lemun ya fallatsa a jikin abokan nasa dashi kanshi har ga Allah ban lura ba,ba karfi ji ne dani ba shiyasa ban ji karar faduwar wani abu ba,ba ma haka ba yanayin da nake ciki gabadaya ji na sa ganina ne suka Dauke a lokaci d'aya.
Na dai san kafata ta bigi wani abu ammh yanayin da nake ciki bai sa na Tsaya Dubawa ba.
Sai ji kawai nayi an dawo dani baya an yarfar dani akasa ya Ishaq ya Daga Hannu ya wankeni da mari acikin kalmominsa na tsinci kalmar"Banza Jaka,Mummuna useless har na isa na wulakanta abokansa ko akwai sa,a na acikin su ne..?
Ina dafe da kuncina na bisu da Kallo ya fadi gaskiya ba sa'a na acikin su kamar yadda yake kyakyawan gaye haka suke suma,jikina na rawa na fara bashi Hakuri sai yace sai na juya na basu hakuri haka na Durkushe ina basu Hakuri sai da sukace sun hakura ya bi ni da Hambari ina Rarrafe na bar Falon ranar kwana nayi ina kuka har na fara neman nayi Sabo sai na zauna nace meyasa Allah bai yo ni mai kyau kamar kowa ba..?
Ko dai da gasken ne bani da Sa'a..?
Washegari Da Mama taji Labari Allah ya kara tayi har da fadin da ya fada mata Tun jiya sai ta karamin da Duka.
Ina Falon ina goge goge ne alokacin naji sanda Jamal yace"Kai ma Bro meyasa ka kirata cikin abokan ka.?
Sai da yayi tsaki mai karfi kafin yace"Su suka matsa sai sun ga wacce tayi abincin"
Daganan ban ji meya ke fad'i daga karshe ba,Saboda ya Rage murya Ranar ina aiki ina kuka abaya bana Damuwa in an kusheni ammh yanzu sai naji kamar da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a
Ashe abunda Ya Ishaq bai sani ba Matarsa ya Tozarta,Agaban abokansa Domin ko sati ba'ayi ba Baba ya tafi Karofi Sakamakon kiran da Goggo tayi mai kan cewa jikin Hajiyar ya tashi Abun mamaki tana ta kiran sunan sa shi da Mama da ya Ishaq suka tafi suna chan ne nima ina gida Hankalina nakan Hajiya ban san me ya faru ba, ni dai nasan sun Dawo gidan cikin Hargitsi da Rashin kwanciyar Hankali mama sai kuka take yi tana Fadin bamai hada mata zuru'a da Dangin munana da kurame.
Washegari fada ita da Baba har Falo alokacin naji Baba yace"ko bayan Ransa sai auran Fa'iza da Ishaq ya kulli sai dai ta mutu"
Dayake da karfi yayi mganar naji sa ni kaina sai da na gigice ana haka sai ga Ya jamal yazo yana fadin Ya Ishaq ya kwashe kayansa ya bar gida Mama ta fadi kasa Hannunta akai tana kururuwam ta shiga uku ta Lalace
Haka Baba ya tsallake ya barta ban bari kowa ya ganni ba na koma Daki ina rawan jiki mai nake ji,Wai ni Ya Ishaq zai aura.?
Tirkashi ni kaina na hango tashin Hankali acikin lamarin ranar har Anty Binta tazo ita da Anty Mahma da kawayen Mama na kusa,sai mganganu suke ni,ni ina Daki baji nake yi sosai ba, ranar ko girkin ban iya yi ba kuma ba wanda ya nemeni.
Nima Badariya ta shigo take fadamin Wai Hajiyar Karofi tace a hada aurena da Ya Ishaq,ance Dakyar ma aka gane me take nufi Saboda Harshenta ya karye.
Ba Ya Ishaq kadai Hajiyar Karofi ta cuta ba wlh har dani ina ni ina Ya Ishaq ai tazaran ma mai yawa ne.ranar kafin Baba ya Dawo Mama da su Anty Binta suka kirani Falo suka min Fata fata zagi da gori ba wanda ba su yi min ba har da gorin mu dangin maciya Amana ne to wanda ma naji kenan wanda kuma ban ji bansa me suka fada ba,Dayake da karfi suke mganar Anty Binta ko har tana Hadamin da dunguri Mama taci kuka har ta godema Allah idanuwanta sun kala sun yi jajir Ita damuwarta Ishaq ba bawanda yasan inda ya tafi ya kuma kashe duka wayoyinsa Mama taja kunnina da cewa in Baba ya Kirani ya tambaaye ni in na amsa mganar auran nan sai na gwammace rashin amsawata Domin bata fatan Had'a zuru'a dani Har gaban Abada.
*KANA NAKA..!*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*
*🅿️05*
Lokacin da Baban katsina ya kirani Falonsa adaran da su Mama suka ja kunne ne ammh na kasa iya d'ago ido na kalli Baba ballatana nayi mai gaddama kan lamarin da yazo min dashi cikin wani yanayi na roko da Tausasawa Baba ya sanar dani Umarnin Hajiya na had'a aurena tsakani na da Ya Ishaq shi Uba ne gareni zai iya aurar dani ko da ban sani ba addini ya basa wannan damar ammh bai yi haka ba, sai ya zabi da ya kirani yana Roko na na amince don ya samu damar da zai cika Muradin Hajiya..
Ina kallonsa da kumburarrun idanuwana da suka tasa saboda kuka Da damuwa Hawaye suna Biyo Fuska ta wasu na korar wasu Baba nake kallo wani Mutum da nake gani Da kima da Daraja mutumin da nake ganin shi Kad'ai ne ya ragemin gata na aduniya ta ya ya zan iya bude baki nayi mai gaddama.? Amsa masa kuma Daidai yake da Fadawa Ukuba kamar yadda Mama ta shaidamin ita da su Anty Binta..
Na bude baki da niyar nayi mgana kalmar
" Baba.."
Kad'ai ya iya fita a bakina sai kawai na saka ma Baba kuka shi kuma bai duba yanayi na ba ya shiga sakamin albarka da Fatan gamawa da Duniya Lafiya sai harshe na yayi nauyin da har Baba ya sallame ni na kasa Furta ko kalma d'aya ammh a kasan raina nasan wannan auran bai kamata ya tabbata ba Domin babu had'i ko gami acikin sa gabad'aya.
Ranar nasha kuka kamar raina zai fita Tun cikin Dare Mama da Baba suke Rigima da karfi suke mganar Shiyasa nake jiyo su sama sama Tunda Baba ya fita sallar asuba bai Dawo ba Mama ta rude ta shiga tashin Hankali Saboda rashin Sanin inda Ya Ishaq ya shiga Tunda yaji mganar auran mu
Ni dai ban san ya akayi ba ina kwance sai ji nayi an rufeni da duka kota ko'ina,ina kuka ina ihu ammh Mama bata Tausayamin ba kuka take yi tana Dukana fadi take yi"Dangin jaraba dangin masifa Saboda ke Abban Ishaq yace zai iya rabuwa dani...?Saboda ke Ishaq ya bar gida ban san ina ya shiga ba..? Kuma ahaka zan amince na hada Zuru'a dake..?wlh sai dai ki mutu ammh ni Saudatu bazan taba Hada zuru'ata da b'ara gurbi irin ki ba Shegiya ya'yan shegu dangin maciya amana Mummuna dake D'ana yafi karfin ki"
Da karfi take mgana shiyasa na ke jinta ina ta bata Hakuri bata jini ba Badariya na gefe tana kuka tana rokon Mama ta kyaleni ammh bata tanka ta ba Jamal kuwa yana Tsaye shima Fadi yake yi"Mama duka wayoyin ya Ishaq suna kashe ne sannan na kira abokan sa na kusa sun sanar dani bai zo ba kuma bai kira su ba..Gaskiya Baba shima bai yi Tunani ba Ta ina Ya Ishaq ya Dace da Fa'iza..?
Ina ji Mama ta wurgoni Falo tana Fadin"Ai yadda ta saka ya bar gidan nan nayi Rantsuwa bazan yi kaffara ba itama ta gama zama a wannan gidan yau ba sai gobe ba sai ta bar min gidana"
Da duka da gori da Tsinuwa Mama ta rakani waje ta maida kofa ta Rufe,Dagani sai rigar jikina ta atamfa sai dankwali shima tana Dukana na Rarumeshi na rike a hannuna kafata ba Takalmi Mama ta koreni nan na rakube jikin gidan ina ta kuka na Duba gabas da yammah kudu da arewa bani da wani gata a garin katsina kuma Mama Tunda tayi Rantsuwa to da gaske take Dankwalina na warware na yane kaina Dashi gidan Anty Mamah ya fadomin tana da Sauki Sauki kila ita zata iya taimakamin da kudin motan da zan koma karofi domin chan ne gata na anan duniya..
Da kafata Tun daga Kofar soro har Cikin asibitin kashi,A kafata ina tafe ina kuka kamar zararriya,ban gaji ba Domin halin da nike ciki gajiya bata da Muhalli a wajena Sai dai Anty Mahma ta ganni kwatsam kamar Daga sama tayi matukar kad'uwa da na zube ina bata labarin korar da Mama tayi min Kai ta girgiza kafin tace"Kai Mama meyasa bata bin abu a Hankali ne..?
Bari na kirata.."
Da Sauri na rike mata Hannu naji tana mgana ban ji me tace ba sai dai Yanayin mganarta da wayarta data Dauka sai Tunani na ya bani Mama zata kira ko Anty Binta ni kuma na shiga Tsaka mai wuya acikin wannan Halin Karofi nake son zuwa na Durkushe gaban Hajiya na Roketa ta janye wannan mganar in tana so na cigaba da Rayuwata yadda Allah ya Tsaramin in bata so ta kara jefa Rayuwata cikin wani Sabon kangi.
Dakyar Anty Mamah ta amince da Rokona ta bani kudin mota ta Daukeni a motar ta da kanta ta kaini Tasha ta sakani a motar Karofi ina ta kuka ta Tausayamin ta Dafa kaina Dake cikin Sabon Hijabin data bani da Takalmi tace"Ki daina kuka Fa'iza ba matsala in sha Allahu Mama zata Sauko"
Har na kai karofi kuka nake yi sai da Muryata ta dishe kukan rashin gata da kuma Tunanin yadda yanayin Rayuwata ya fara na fara jin kamshin gaskiya kila bani da sa'a ne komai nawa ba mai kyau ba ne irin na kowa rayuwata ba Daidai take da Sauran mata ba.
Sai dai Goggon Karofi ta ganni yarkace yarkace kafin na fadamata abunda ya faru sai ta nemi dukana sannan na Zayyane mata komai bazan manta ba sai da ta share kwallah ta kamani ta Rumgume tana Fadin"Abunda Saudatu ta aikata miki kenan..? Daina kuka Fa'iza watarana sai Saudatu tayi kuka idanuwanta akan abunda ta aika miki akwai Allah"
Araina ban taba Hango hakan ba ni kuwa wani matsayi zan taka da Mama zatayi kuka Saboda ni..?
A daran ta Kira Baban katsina ta fadamai Halin da ake ciki yace da Safe zai shigo garin ni kuwa Lallashina Goggo ta dinga yi Hatta Hafsatu dake da karancin shekaru ta shiga Damuwa ganina cikin wannan Halin Hajiyar karofi kuwa tana kwance sai bina da kallo take na kasa na mata wata mgana domin sai naji bakina yayi nauyi ganin yanayin datake ciki Goggo tace tun ranar da Baba ya bar nan jikin Hajiya ya kara rikicewa.
Washegari Baba yazo sun kai ta ba dadi da goggo ta nuna mai ya janye mganar auran nan ita zata rikeni Allah ya bani wani mai sona in yi aurena ammh ba Ishaq d'an Saudatu ba shi kuma Baba yace indai yana Raye sannan shi ne Uba ga Ishaq kamar ya aureni ya gama ina Durkushe gabansu suka rika wannan Hayaniyar ad'akin da Hajiya take jinya itama tana kwance bata iya mgana ba sai gyad'a kai hawaye na bin gefe da gefen Fuskarta.
Baban katsina ya tafi ko sallama bai yi ma goggo ba Allahu akbar adaran Hajiya ta amsa kiran Mahallacinta,Tun daga Lokacin da naji goggon na Salatun mutuwar HaJiya da kaina ya amsa Dum! Har gobe in na Tuna da mutuwar Hajiya sai yanayin ya Dawomin da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a?
Meyasa duk wad'anda suka Tsayamin suke tafiya su barni Farko Babanmu Sannan ga Hajiya itama har aka kai Hajiya kushewarta bana cikin Hayyacina gida ya cika Har Hajiyar Dala da duka zuru'arta suna nan Hadda Mama da su Anty Binta su Ya Asiya sun Dauka mutuwar Hajiya ce ta tab'ani basu san abunda ke Faruwa ba har kuma lokacin ba'a san ina ya Ishaq ya shiga ba.
Ranar da bazan manta ba,Itace Ranar da aure ya kulli tsakani da Wanda bai Taba sona ba har ko yau da muka Tara zuru'a dashi aurena da Ya Ishaq wanda yau har gobe Mama bata daina aibatani da zuru'aar maciya Amana Dangin Tsiya ba,Ranar addu'ar bakwai din Hajiyar Karofi Baba ya tara Mutane ya Biya Sadaki aka Daura aure na ba wanda ya sani sai da aka Daura Gidan mutuwa sai ya koma Gidan Fad'a da Hayaniya domin Mama kaina tayi tana fadin sai taga bayana Goggon Karofi ta shiga Tsakani Ranar ba iya ni kad'ai ba hadda Mahaifin mu dake kasa yasha zagi Taamadina na gidan sulalewa tayi ta koma gidansu tana kuka,kukan maraici da Tausayin ya'yanta.
Sai alokacin kowa yasan Halin da ake ciki Goggon Karofi ce kad'ai da ya'yanta ke tare dani ban da Hajiyar Dala data mara ma Mama baya,Aranar Mama ta koma katsina ta sha alwashin sai taga yadda auran nan zai Tabbata shi kuma Baba yace sai dai in ba shi ya Haifi Ishaq ba.
Ya Asiya da Yaya Mariya sun koma Gidajen su da Tunanina aransu da Tausayina su kan su sun hango Yadda rayuwa da kaddara suka kara gangarawa dani.
Kwana Ashirin da Rasuwar Hajiyar Karofi Sai ga Baba ya zo shi da Ya ishaaq,wanda ya gama gudun nasa ya Dawo jiya da Daddare ya samu labarin An daura masa aure dani Ya Ishaq ya kasa katabus domin Baba ya Daga mai murya yace in har yaki karb'ata a matsayin mata to sai dai ya chanza wani uban ba shi ba.
Wannan mganar shine Sarka na Farko da ya fara kulle aurena da ya ishaq,Baba ya bama Goggo kudi ta yi min siyayya sannan ya kama mana Haya a katsina cikin gari in da zamu zauna ni da Ya Ishaq,har suka tafi ban gansa ba shima bai nemi ba,Tun kuma Daga Lokacin Baba ya fara shirin Tarewata Mama kuwa tayi Kukan har tagaji ta Saduda ganin Da gasken Baban bazai fasa ba.
Kafin Ranar arba'in din Hajiya karofi hatta jere na Goggon Karofi da ya'yanta da Yan'uwana sun gama min komai Domin Baba yace ranar addu'ar arba'in Zan tare agidana Yaya Mariya ita takaini gidanta ta tsifemin kai ta wanke ta kaini akayi min kitso da Kunshi Ina ta ce mata ta barshi kunshi da gyaran jiki sai Mata masu kyau ba irina ba ban taba manta kalamanta alokacin Kaina ta Dafa kafin tace"Kema kina da kyan ki Fa'iza sai dai in ba'a gansa yanzu ba ne..Ammh na tabbatar miki nan gaba zasu ga abunda nake gayamiki"
Alokacin mirmishi nayi mata Domin nasan ta fada ne ni kaina nasan bani da kyau sannan ina da nakasu ta bangaran Ji na da mganata
Aranar da Hajiya ta cika kwana arba'in a kushewarta ranar na Tare agidan Ya ishaq aurena ba irin na mata masu kyau da gata ba ne,Daga ni sai kayana da Goggo ta d'inkamin Sabbi ita da Baba domin da Goggo Taso su yi min Rakiya sai ya Ishaq yace baya Bukata dagani sai shi a mota sai Baba da Direbansa.
Daga Mama har ya'yanta ba wanda ya Leko karofi,Baba da kansa ya shiga Dani karamin flat din da ya kama mana mai Falo da Dakuna Biyu sai kitchen da Tsakar gida,Shi ya damka Amanata Hannun ya Ishaq da karin wasu manya manya sarkunan da Tun abaya na fada muku su suke rike da wannan auran namu yau har da nike baku wannan Labarin,Domin cikin kaukkausan murya yace mai"Ishaq ga Fa'iza nan na baka auranta ba Domin ta rasa me son ta ba sai domin cika Muradin mahaifiyata..Wlh tallahi ko da Rana daya in ka zalunce ta ban yafe maka ba Ishaq..Kuma ko da rana d'aya kabi Hudubar mahaifiyarka ka Tozarta Fa'iza shima nace ban yafe ba..Daga karshe matarka ce ta sunna ka Kula da ita kuma in ka Danne mata Hakki Allah na kallon ka sannan nima bazan yafe maka ba Sannan kasani Ranar gobe kiyama bazaka Rabauta ba Ishaq in dai ka saba ma Umarnina.."
Kafin ya tafi sai da ya kara Jadaddamai in ya danne min hakkina na aure ko guda d'aya ya sani bazai kara samun albarkarsa ba,ya tafi bayan yayi min nasiha hakuri sannan ya sanar dani na zauna nayi ma aure Biyayya bazan taba Tabewa ba Duniya da Lahira Tabbas wannan Biyayyar da Baba ya Rokeni har bayan mutuwarsa ban sauka daga kanta ba,nima ita ke rike dani acikin rayuwar aure na da Ya Ishaq.
Warware tarin kalubalen da na Fuskata a zama na da Ya Ishaq abu …