.
by @nkds
___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ_
"Daddy.!
Daddy!!
Daddy!!!
Ka tsaya a'iya matsayinka na mahaifi a gareni, kar kayi yunƙurin shiga abin da bai shafe ka ba, domin kuwa wannan Rayuwa Ta ce dan haka ka barni nayi ta yadda naga dama, kuma da kake maganar sanadina mutane biyu suka rasa rayukansu, kai wani kalar mutum ne, da baisan tsautsayi ba. Sanadin tsautsayi komai ya faru, kullum cikin dana sani nake na zama na gynaecologist a matsayina na cikakken likitan mata wanda na kwashe tsawon shekaru ina karatu na kasa taimakon ta na kasa taimakon IKRAM, a kullum da ko yaushe cikin tuna kalamanta na ƙarshe a gareni nake, a lokacin faɗi take."
''Dr. Ka taimaka ka cece rayuwata a gurin surgery nan ina tsoro na mutu Burina bai cika ba, please Dr. Save my life please pleased Dr. I'm beg you.''
''Kullum irin wannan maganar nata su suke min kuwa cikin kunne cikin dare su hanani bacci, da rana kuma su hana ni sukuni duka sanadin tsautsayi da kuma ƙaddara komai ya faru..."
Tunda Maleek ya fara magana babu abin da Alhaji Abubakar. Yake yi sai faman gyaɗa kai Maleek ɗin har yakai ƙarshen maganganun nasa sannan Yace.
"It's okay Wato ma haka zancen yake, wato dai har rogonka tayi ka ceci Rayuwar ta, amma saboda kaiɗin cikakken idiot ne, sai dai babu komai daga yau kaɗauka cewa ni Alhaji Abubakar Sameer Lamiɗo bani ba kai, ka ɗauka cewa baka taɓa mahaifi ba a
Duniya..."🥵
Katse sa Maleek Ya yi cikin tafi Raf-Raf sannan yana faɗin
"Wow, Amazing, please Mister Mai Kyau, da gaske kake, oh Lord so nice, it's amazingly fa. Yaudai wannan Ranar da nake jira tazo, bani babu wannan tsangwama da takurawa yanzu zanyi Rayuwata Normalcy irin na cikakkun mutane, oh my pride..."
Habba nan aka fara cacar baki tsakanin Alhaji Abubakar Mai Kyau da Ɗan nasa Maleek kowa cikin mugun zafin rai dana zuciya yake furta duk wani abu da yazo bakinsa.
Gaba ɗaya Yaran in banda kuka babu abin da suke yi ganin wannan tashin Hankalin da yake faruwa cikin gidan su.
Afeefah kuwa wacca kwata kwata ta tsana hashin hankali ko ya ya yake jikinta har wani rawa yake yi, na tashin hankali, Yayin da ita kuwa Momy Rafi'at baza'a iya faɗin ga irin yanayin halin da take ciki ba, amma dai kana kallon ta kasan ta fita hayyacinta. Yayin da ita kuma Zaynerb ta ƙarisa da gudu ta riƙe ƙafar mahaifin nasu tana basa haƙuri jin irin zafafan kalmomin da suke fitowa daga bakin sa.
Da ƙarfin gaske Maleek ya buga hannun sa saman glass center table dake tsakiyar palon, aikuwa nan jini ya fara tsatata kamar ambuɗe famfo bai damu da jinin dake zuba a hannun sa ba, saboda tsananin fusatar da yake ciki ya nufa staircases wanda kai tsaye zai sadashi da part nasa, ya fara taka steps cikin sauri sauri in twin's.
Gaba ɗaya suka bisa da kallon mamaki. Yayin da Alhaji Abubakar ya koma saman sofa ya zauna daɓasd, gaba ɗaya jikin su ya yi mugun sanyi an rasa mai magana.
*After some minutes*
Sai ga shi yana saukowa daga saman benen janye da akwati harya ƙarisa saukowa ko tsayawa bai yi ba, ya nufa ƙofar palon zai fita.🤕
Aikuwa da gudu ƙanin nasa su duka harda Momy Rafi'at suka bisa suna kiran sunan sa.
A guje Nainarh ta ƙarisa wurin sa ta riƙo akwatin hannun sa sannan cikin kuka take faɗin
"Buddy, ka taimaka karka tafi, please karabu da wannan unwarranted and unwanted tunanin, please Buddy na roƙeka karka tafi, ka duba Halin da Daddyn da Momyn dama mu ƙannin ka gaba ɗaya zamu shiga idan ka tafi pleased..."
Ganin Ya yi shiru baice komai bane yasa su duka suka ƙarisa wurin suka yi kamar yadda ita ma Nainarh tayi cikin kuka suke basa haƙuri, hadda Momy Rafi'at a kan karya tafi.
Abin dai babu daɗin faɗa gunin ban Tausayi gaba ɗaya suke _-_Lamarin it's heart touch obaaaaa_-_🔥
Kallon mahaifiyar su Maleek Ya yi sannan Yace
"Momy ki dena kuka kinji, ki dena zubar da hawayenki a kan wannan ƙaramin tashin hankalin, ba dai gida bane, to zan barmasa gidan sa."
Cikin kuka xixi ta katse shi da cewa "Haba Buddy ka taimaka ka tsaya, indai kana so Momy ta dena zubar da Hawayen ta..."
Haɗuwa suka yi gaba ɗaya suna basa haƙuri, sai dai duk da irin haƙurin da Suke basa, haka ya tsallake suna ji suna gani yasa ƙafa yabar gidan ko waywayensu bayyi ba, wayyo Allah.😭
Gaba ɗaya ranar cikin ɓaƙin ciki da wani kalar yanayi gunin ban tausayi suka wuni, jigum jigum a palon kaf cikin su babu wanda ya iya tashi tun tafiyar Maleek har yanzu da aka kwashe kusan awanni biyu da tafiyar sa.
Tun ɗazu wayar tarho dake tsakiyar palon take ƙara, sai dai saboda yanayin da suke ciki, an rasa wanda zai je domin ɗauka.
Lailah da ƙarar wayar ya isheta ta miƙe cike da masifa ta nufa wayar ta kara a kunne cike da Bala'i ta buɗe baki zata yi magana.
Kawai sai gani suka yi wayar tarhon dake hannunta ta faɗi ƙasa. Yayin da ita kuma ta zube ƙasan kamar wacca ta fita hayyacinta.
Da gudu gaba ɗaya suka mimmiƙe sukai kanta suna tambayar ta abin da aka faɗa ma ta, ganin yadda take faman Hawaye.
A hankali ta buɗe bakinta cikin sarƙaƙƙiyar murya irin na wanda tasha kuka ta ƙoshi Ta ce
"Hajiya Zuwairiya ce Allah ya yi ma ta Rasuwa, shi ne aka kira aka faɗa yanzu."
Cak gaba ɗaya suka tsaya tamkar waɗanda wutan lantarki taja, saboda tsananin kiɗima da tashin hankalin da maganar ya ƙara musu akan wanda suke ciki.
Qarar faɗin mutum da suka ji a ta bayan su ne, yasa gaba ɗaya suka juya harda Alhaji Abubakar wanda ba'a gane yanayin da yake ciki ba.
Afeefah ce kwance ta faɗi a sume ashe ciwon ta ne ya tashi.🤧
*Tashin sense*
A taƙaicen taƙai tawa dai faɗi ko rubuta irin tashin hankalin da gaba ɗaya Ahalin Alhaji Sameer Lamiɗo suka shiga, bazai yiwu ba, saboda yanayin ba daɗi ko kaɗan, domin kuwa Afeefah ciwon tane ya tashi kuma yazo da matsala highly.
Domin kuwa sai da ta kwashe tsawon watanni huɗu a hospital na ƙasar Hindi tana jinya, kamar ba za ta Rayuwa ba, domin har an cire rai da ita.
Sannan aka samu ta dawo normal nata Sannan kuma Rayuwa ta ci gaba da tafiya babu daɗi domin kuwa duk irin neman da aka yiwa Maleek ƙasa, ƙasa ba'a ganshi ba, haka suka haƙura aka ci gaba da gunadanar da Rayuwar.
____*_💅
Nainarh Abubakar Mai Kyau.
Nainarh, ta kasance kyakyawar mace ce ita, son kowa ƙin mara sa'a, domin kuwa kyakyawa ce sosai, ita ɗin ta kasance mace ce mara haƙuri gashi bata ɗaukar raini ko kaɗan gata akwai son girma kamar me, gata tanada wani hali na riƙe abu arai ko ya ya yake, sai dai kuma duk da rashin mutuncinta tanason Ƴan uwanta sosai kamar yadda suma suke ƙaunar ta.
Yayin da ita kuma Biyuninta Nailah Abubakar Mai Kyau.
Nailah, ta kasance mace mai yawan sanyin hali da kuma maida abu ba abu ba, sannan kuma ita ma ɗin kyakyawar mace ce mai ji da ƙuruciya ga kyau da Naira.
Nailah ta kasance mace mai matuƙar tsoron tsiya, domin kuwa ko kyanwa tsoranta take yi, kamar mutuwar ta sannan ita ma ɗin macecce mai matuƙar ƙaunar Ƴan uwanta da Ahalinta.
Haleesat Abubakar Mai Kyau.
Haleesat, ita ma ta kasance miskilar gaske ce na bugawa a mujalla, domin kuwa komai miskilanci ka idan ka haɗu da ita, sai ka sara ma ta
To shigarta University ne ta rage miskilancin kaɗan, amma fah kaɗan ɗin. Sanadin haɗuwarta da Manyan mata masu fariya da dukiyar iyayen su, idonta ya kuma buɗewa sosai sosai. Sanadin shigarta University kuma a can tayi ƙawaye har uku domin kuwa a baya ko ƙawa ɗaya bata da ita.
Ƙawayen da tayi a University su ne, Zuree, Feenah sai kuma Jenny waɗanda Sanadin haɗuwarta dasu ne ma ta fara zuwa mashaya, amma fah a ɓoye, sannan kuma Haleesat ta kasance cikakkiyar kyakyawar mace ce ita ta nunawa a tv, gata ta iya ɗaukar wanka na manyan yara gata tana masifar kama da wannan shahararriyar Jarumar indian nan wannan kyakyawar wato 'Krithi Shetty'.
Zaynerb Abubakar Mai Kyau.
Zaynerb, ta kasance cikakkiyar mace ce mai ji da kyau na musamman gata wayayyiyar mace ce ta nunawa sa'a, sannan akwai ta da shiga shara babu shanu wasu lokutan, domin kuwa akwai ta da surutu babu laifi sannan kuma tanada kirki dai dai ita, gata akwai wayau domin idonta a buɗe yake kar, gata tana masifar ƙaunar ƙanwar ta Afeefah, kamar Rayuwar ta domin kuwa Afeefah ita ce Raunin Zaynerb a komai, sai dai kuma ita ma tanada wani hali ɗaya shi ne, akwaita da mugun zuciya kamar me, sannan kuma bata iya so ba, domin idan zata so abu son gaba ɗaaya take masa, haka ma idan zataƙi abu tofa ƙin gaba ɗaya take masa, ita haka take a rayuwar ta, Zaynerb ta kasance suna masifar kama da wannan Turkish actress Cemre Baysel, Yanayin gashin nasu ma kala ɗaya suna kama obaaaaa, highly highly.🤩
Sannan, Kuma...!
*Afeefah Abubakar Mai Kyau.*
Afeefah *SARAUNIYAR KYAU* ke nan kyakyawa ce wacca idan aka ce kyau. Tofa ana zuwa kanta an rufe ƙofa. 💋
Afeefah ta kasance cikakkiyar mace mai son mutane kamar me, domin kuwa kowa nata ne, dukiyar mahaifin ta bai rufe ma ta ido ba sam ko kaɗan, gata akwai kirki kamar mene.
Afeefah ta kasance tana masifar ƙaunar Labari na *SOYAYYA* dama duk wani Abu daya shafi soyayya.
A lura da kyau Labarin soyayya nace Afeefah take ƙauna bawai soyayyar ba, domin kuwa bata taɓa soyayya ba, ita ɗin haka take, gata akwai ta da matuƙar kaifin basira da tunani sannan kuma Afeefah tana ƙaunar Ƴan uwanta sosai sosai obaaaaa.
Sannan kuma akwai ta da wani kyakyawan hali wanda shi ne kana ma ta Abu yanzu tofa yanzun zata manta, ita sam bata da riƙo ko kaɗan, sai dai kuma fah. A Lura kyau Afeefah ta kasance mace ce wacca tasan haƙin gayu obaaaaa.
Sannan duk da kirkinta bata ɗaukar raini ko kaɗan bata da girman kai amma fah akwai class highly highly. Sannan kuma ta kasance tana ƙaunar ayi surprisingly nata a komai. 💞
Lailah Abubakar Mai Kyau.
Lailah, ta kasance mace ce ita mai matuƙar tsafta da kyankyami kamar me, sannan kuma akwai ta da mugun rashin mutunci ba kaɗan ba, dan ma haɗuwarta da Afeefah ne ta raƙe wasu abubuwan.
Sannan kuma ita Lailah bata damu da harkar kowa ba, sai dai nata sannan kuma ita ba mace bace wacca ta iya gulma, sam bata iya gulma ko ƙarya ba, kai tsaye take harkar ta.
Amma fah akwai ɗan karan surutu, sannan kuma ita Lailah sam bata soyayya, ace warta ma soyayya ɓata lokaci ne kawai da shirme, amma fah a fahimtar ta ke nan.😂
Lailah tanason Afeefah sosai fi ye da son da take yi ma kanta. *_-_kunji masuyi Don Allah _-_*💫💫
Sannan Ita ma dai tana da kirkinta dai dai ita sai dai hali kawai irin na ɗan Adam.
Zinaru Abubakar Mai Kyau.
Xixi ke nan ƴar kwalisa da iya ado ga tsafta kamar me, gata ita ma akwai ɗan banzan iya yi da son asan da zamanta, ta wani ɓangaren halinta yazo ɗaya dana Zaynerb wajen iya shiga shara babu shanu, gata faɗi ba'a tambayeki ba ke nan.
Akwai surutun tsiya sannan Ita ma irin Afeefah ce, ta wani fannin domin tanason mutane babu laifi sannan kuma Abin hannunta sam baya rufe ma ta ido eheee.🌝🌚
*Wannan ke nan, Kaɗan daga cikin Halayen Ƴaƴan Mister Mai Kyau...*💅
___***
To Haka dai Rayuwar nasu ta ci gaba da lulawa ba wani farin ciki gunin ban Tausayi ta kowani ɓangare watanni tara da barin Maleek Gida aka yi bikin Nainarh da Nailah.
Yayin da ita Nainarh ta Aura wani haifaffen ƙasar Eritrea. Wanda haɗuwar social media ce, harta kaisu ga Aure.
Duk da dai kafin Auren sai da aka sha fama da Momy Rafi'at domin taƙi yadda ne.
To daga baya haka ta haƙura aka yi ba yadda ta iya.
Yayin da ita ma Nailah ta Aura wani ɗan ƙasa Nigeria haifaffen Nasarawa State, mazaunin Lagos duk da Ita ma da farko Alhaji Abubakar Mai Kyau.
Yaso ya bada matsala, ace war sa bai amince da mijin da Nailah ɗin zata aura ba, saboda Yanayin sana'ar sa, amma daga baya haka komai ya wuce aka sha shagalin biki.
- _-
Rayuwa ta ci gaba da gangarawa ta kowani ɓangare yau daɗi gobe babu, dama haka abin yake ba kullum ake cikin enjoying komai ba.
Shekarun Maleek Biyu da Barin Gida ba ko wai waye.
A lokacin ne kuma xixi ta kammala secondary school nata. Sannan ta ce ita a ƙasar france wurin Uncle Yunus take so ta ci gaba da karatunta, a can tare da Labiba ɗiyar sa wacca suke sa'anni ace war ta gaba ɗaya Gidan nasu babu daɗi tun Barin Buddy nasu.
To koda ta sama mahaifin su Alhaji Abubakar, da maganar da farko ƙin Yarda Ya yi saboda a tunanin sa Sanadin karatu a Abroad Babban ɗan sa Abdulmaleek Tarbiyar sa ta sama matsala.
Ita ma zaynerb kuma sanadin haka ta sama matsalar soyayya. Wanda nan gaba zamuji ainihin abin da ya faru da ita acan Amsterdam ɗin.
A lokacin ba ƙaramin wani hali xixi ta shiga ba, dalilin hana ta zuwa faransa domin ɗaura karatun ta na degree.
A lokacin har rashin Lafiyar ƙarya ta kwanta dan dai kawai a barta ta tafi, aikuwa daga baya Alhaji Abubakar Mai Kyau, da yaga babu sarki sai Allah, haka ya barta ta tattare ya nata ya nata ta koma faransa. Wajen Uncle Yunus ta fara sabuwar Rayuwa. Yayin da gefe guda ita da ɗiyar Uncle Yunus Labiba suka fara karatun anan wata hamshaƙiyar jami'a na ƙasar faransa.
Yayinda suke karantar course ɗaya.
Nigeria kuwa Rayuwar Ahalin Alhaji Abubakar Mai Kyau, ta ci gaba da tafiya salin alin. Yayin da aka kwashe tsawon shekaru uku hadda watanni da Maleek Yabar gida sai wannan karon ya dawo...💃💃
*Masu karatu idan nace zan ci gaba da tafiya cikin ainihin abin da ya faru a baya*.
To gaskiya ina ga har mu kammala wannan novel baza'a dawo cikin ainihin Labarin ba, saboda haka anyi min afuwa mu koma cikin ainihin Labari.
Yanzu dai kunji ainihin dalilin abin da Ya saka Maleek ya bar Gidan su tsawon shekaru uku da watanni sai wannan Lokaci ya dawo.
Kuma kunji dalilin da yasa Momy Rafi'at bata ƙaunar su Afeefah, saboda wai mahaifiyar su ta Aure mata miji.
Sannan kuma munji wani abu daga cikin ainihin dalilin da yasa Haleesat ta fara zuwa mashaya, wato Sanadin haɗuwarta dasu Zuree da Feenah da kuma Jenny.
Sannan again munji ainihin dalilin da Yasa Zaynerb ta dawo Nigeria.
Bayan kuma a Amsterdam ta fara karatu, wato dai Sanadin soyayya, kamar yadda nayi Alƙawari nan gaba zamu ji ainihin abin da ya faru da Zaynerb a can ƙasar NETH Babban Birnin ƙasar wato Amsterdam.
Haka ma Lailah munji wasu daga cikin silly. 😜 dalilanta da suka saka ta tsani soyayya, har ma da maza😕
Sannan kuma munji irin ciwon dake damun Jarumar mu.
To shin akwai maganin wannan ciwo nata ko kuma babu kudai kawai ku Biyo alƙalamin Nainarh Kd domin jin wannan ƙayataccen Novel Na musamman Wanda sai da a tsaya a Ta ce sannan kuma a tsaya aka zuba Basira wajen Taho muku dashi Labari mai Cike da sinqi sinqin chakwakiya_🤩_Cin Amana🤣_Yaudara😏_Zamba cikin Aminci🤕_Ban dariya obaaaaaaaaaa😆_Rikita Rikita🥴_____
Nishaɗantarwa🤪_Game da wa'azantarwa 😜_Buri💫_Fansa_makirci🤮_Hargitsi🤥_____
Game da Tsananin Zazzafar Soyayya Mai Ban sha'awa da Burgewa, da kuma tsindima mutum cikin Shauƙi ba tare da Da ya shirya ba. Labari Mai suna SARAUNIYAR KYAU 💋💋💋__THE GLAM QUEEN 👑💕🌹
💓💓ƚԋҽ ϝαʂԋισɳ ʂԋσɯ.💓💓
*PR£S£NT*
*Ci gaban Labari*
*_-_Masu Karatu, Ina Fatan Dai Baku Manta Ta Wajajen Da Muka Tsaya Ba, To Yanzu Dai Zamu Ɗaura_-_*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Bayan sun shishshiga ƙayataccen palon, Gaba ɗayan su iyayen suka zazzauna saman Royal sofa's dake zagaye da ƙaton palon, Yayin da su kuma gaba ɗaya yaran suka zazzauna a ƙasa tsakiyar palon harda Maleek wanda kansa yake ƙasa cike da yasa nin komai da ya faru baya.
Yayin da ita kuma Afeefah wacca har zuwa lokacin bata farfaɗo ba, aka ɗaurata saman doguwar kujera 3sieter Yayin da Momy Rafi'at ta zauna kusa da ita tana ma ta firfita sama sama.
Gaba ɗaya palon shiru ya ɗauka tamkar babu wani hallita mai rai ciki, sai da aka shafe kusan mintuna goma, a haka sannan Uncle Yusuf da ya kasance mutum ne shi mai bala'in sauƙin kai da kuma ƙaunar peaceble.
Gyaran murya Ya yi sannan ya kuma buɗewa da addu'a bayan ya kammala suka shafa sannan ya kalla Maleek cike da kulawa ya fara magana kamar haka.
"Yanzu kai Maleek ka dawo gida Bayan ɗaukar tsawon shekaru baka nan, shin zaka iya faɗa mana duniyar da kaje ko kuma wurin da ka tafiya ko waiwaye babu?."
Gaba ɗaya mutanen palon ne suka mayar da hankulan su kan Maleek suna jira suji amsar da zai bawa Uncle Yusuf da ya yi masa tambayar.
Shikuwa Alhaji Abubakar, babu abin da yake sai faman sauke huci kurum yana kallon Ɗiyarsa dake kwance bata ko numfashi.
Shiru Maleek ya yi tsawon mintuna uku sannan ya yi gyaran murya yana gyara Yanayin zaman sa ya fara magana cikin murya wacca dai Yanayin ta sai as low.
"Da Farko dai Bayan na Bar Gidan nan kai tsaye Airport na wuce nabi jirgin ƙasar Rasha, to koda na isa Rasha Ban tsaya komai ba. Kai tsaye na fara aiki a Babban asibiti dake ƙasar tsawon shekara ɗaya, sannan kuma na fahimci wani abu, cewar shi baturen mutum kwata kwata bashi da alƙawari.
Wato abin dai da ya faru shi ne, ina gabatar da aiki cikin gaskiya a ƙasar cikin Babban asibitin ƙasar, sai wata Rana ɗaya daga cikin manyan likitocin asibitin da yake ba musulmi bane, shiyasa bama wani jituwa dashi, daɗi da kari kuma na fahimci baya da wani hali na KIRKI..."
Katse sa Alhaji Abubakar Ya yi cikin sauri
"Okay ke nan kai ɗin wani Halin kirki ne dakai. Yanzu kaine har zaka ce wani bashi da Halin kirki?."
Da sauri Uncle Yusuf ya katse Alhaji Abubakar cikin sanyin murya Yace
"Ina ga da kayi shiru mun gama jin abin da yake so ya faɗa mana."
Alhaji Abubakar bai tsaya sauraron maganar da Uncle Yusuf Yake ba, Ya kalla Maleek cikin daka tsawa yace "Yanzu me kake nufi?, kana nufin kace ka dawo Gidan nan ne, to a matsayin wane ke nan?, ni dai nasan bani da wani Yaro na miji duka Yarana mata ne, kuma ina ƙaunar su duka."
Jin abin da mahaifin nasu yake faɗa ne yasa gaba ɗaya yaran nasa suka ɗago suna kallon sa, cike da tsananin tashin hankali.
Cike da nadama Maleek ya rarrafa kusa da mahaifin nasu ya kamo ƙafafunsa yana basa haƙuri kamar zayyi hauka cike da tsantsan nadama.
Yayin da shi kuma Alhaji Abubakar yake ture shi cikin tsananin fushi yana tuna duka abubuwan da suka faru baya tamkar yaune suke faruwa.
Maleek faɗi Yake yi "Please Daddy ka yafe min, wallahi na tuba, bazan kuma ba, domin nayi nadama highly."
Gaba ɗaya yaran kuka suke bama kamar Zaynerb da Nailah har wani shiɗewa suke yi saboda tsananin tashin hankali, tsoro suke karfa tarihi ya kuma maimaita kansa.
Ajiyar zuciya Alhaji Abubakar Mai Kyau, ya sauke a karo na babu a dadi yana kallon gaba ɗaya Yaran sa yadda suke kuka, shi uba ne dole yaji babu daɗi da ƙari ƙin yafewa Maleek da Ya yi bawai yana nufin baya ƙaunar sa bane ko kuma wani abun, kawai dai yanaso ya fahimci shin da gaske ya tuba ko kuwa.
Kallon Maleek dake hawaye kamar zararre, Uncle Yusuf Ya yi sannan ya masa umarni da ya koma ya zauna.
Komawa Maleek Ya yi kusa da ƙafafun mahaifin sa ya zauna dan Bala'i.🥵
Kallon gaba ɗaya mutanen palon Uncle Yusuf ya kuma yi sannan ya ƙara mayar da kallon sa, kan Alhaji Abubakar yana masa kallon nutsuwa, daga ƙarshe dai ya sauke idanun sa a kan Maleek.
Kiran sunan Abdulmaleek Ya yi har sau uku, yana amsawa sannan ya ci gaba da cewa.
"Yanzu dai mu a je maganar wurin da kaje gefe, a gaskiya gaba ɗaya Ahali ba muji daɗin barin Gida da kayi ba, a kan wani dalili wanda bai kai ya kawo ba, sannan kuma yanzu da ka dawo, ka dawo ka ci gaba da Rayuwa da Ahalin ka ne, ko kuwa dai akwai wani nufi a tare dakai?."
Uncle Yusuf Ya yi masa tambayar yana kallon Maleek ɗinda ya yi shiru kansa a ƙasa.
"Please Uncle ayi min haƙuri na duka abin da ya faru baya, sharrin shaiɗan ne sannan kuma na dawo gida ne saboda na ci gaba da Rayuwa cikin Ahalina kamar kowa."
Wani ƙayataccen murmushi Mister Mai Kyau. Ya yi amma fah na iya gefan fuska, domin kuwa idan ba ƙura masa ido kayi ba, to ba zaka fahimci Ya yi murmushin ba, daga yadda fuskar sa take a tsume, wani sanyi yaji cikin zuciyar sa jin abin da Maleek yake faɗa, a fili kuwa kallon Maleek dake kallon sa. Ya yi sannan yana faɗin
"Indai kanaso na manta komai da ya faru a baya, na bari ka dawo ka ci gaba da Rayuwa cikin mu. Tofa sai dai idan ka amince zaka fito da matar Aure. Idan kuma baka da budurwa ka zaɓa cikin Ƴan matan dangi, duk wacca tayi maka."
Duk wannan maganar Alhaji Abubakar ya yima Maleek ne cikin kakkausar murya da kuma bada zaɓi.
Murmushin enjoying da kalaman ɗan uwan nasa Uncle Yusuf Ya yi sannan Ya mayar da kallon sa a kan Maleek ɗin.
"Ka dai ji da kunnen ka, abin da mahaifin ka ya faɗa, saboda haka yanzu zaɓi ya rage naka."
Shima Uncle Yusuf Ya yi maganar cikin gimtse fuska alamar dai babu wasa cikin maganar.
Haka ma gaba ɗaya mutanen palon suka mayar da hankulan su kan sa hadda Momy Rafi'at da tun ganin Yaron nata bata ce komai ba.
Kai harda Afeefah wacca farfaɗowarta ke nan taji zancen Uncle Yusuf a sama, sannan kuma babu wanda ya lura ta farfaɗo domin kuwa bata nuna alama ba.
Ajiyar zuciya Maleek ya sauke yana tariyo gaba ɗaya girlfriend's da ya taɓayi kaf cikin su, baiga wacca suke tare yanzu ba, gaba ɗaya basa tare domin kuwa tunda daɗewa yabar kalar Rayuwar sa ta baya, shi dai yanzu iya tunanin sa baiga macen da zaice ya taɓa ma ta kallon so ba, ko kuma ya ma ta kallon wani abun ban da ƙawance, ɗagowa Ya yi Yana kallon gaba ɗaya mutanen palon, kamar yadda suma shi Suke kallo.
Murmushi Ya yi kaɗan kana ya buɗe muryar yadda gaba ɗaya zasuji yana faɗin
"Husnee ce wacca na zaɓa..." 💞💞
Gaba ɗaya palon dariya suka saka ganin yadda Husnee ta ɗago a firgice tana kallon sa hankali tashe.
Uncle Yusuf kuwa babu abin da yake faɗi sai
"Masha Allah dama haka ake so, lamari ya yi daɗi."
Nan kuma palon ya ɗauki hayaniyar murna da jindaɗi.
Sai da suka sama nutsuwa gaba ɗaya suka yi shiru sannan Uncle Yusuf ya kalla Husnee cikin maganar irin na manya yake tambayar ta
"Husnee Ɗiyata kin amince zaki Aura Yayanki Abdulmaleek kamar yadda shima yace keya zaɓa?."
Kallon jama'ar palon Husnee tayi kamar yadda suma suka zubo ma ta na mujiya suna kallo.😅
Cikin gimtse kyakyawar fuskar ta take faɗin
"Uncle Yusuf a bani mintuna biyar zanje yanzun nan nayi shawara na dawo."
Tayi maganar fuska ba rahama, dariya suka saka baki ɗaya, sannan Uncle Yusuf yace cikin dariyar shima
"Kinji jeki Ɗiyata ki ɗauki iya a dadin lokacin da kike so domin duka naki ne."🥰
Miƙewa tayi sannan ta zagaya ta bayan kujeru ta wuce kai tsaye bedroom ɗin Lailah, ta wuce tana shiga ta rufe ƙofar harda murza key, sannan ta dawo ta ƙarisa can gaban madubi tana kallon kanta.
Cire mayafin da tayi rolling kanta dashi tayi kana ta daka tsalle tana faɗin
"Yes, Yes, sai ni Husnee, wallahi sai ni Husnee, a gaskiya na cire tuta cikin ma ta niɗin ma mai sa'a ce cikin masu Nasara, inba hakan ba wannan Diamond boyfriend guda kamar Yaya Maleek Yace Yanaso Ya Aureni.
Haba duk inda aka ji maganar Aure ansan da akwai soyayya, Yasin sai ni Husnee, lallai dawowar Buddy Gida ba kowa Ya yi ma amfani ba sai ni, kai dole ma nayi waƙa, oh toni wata kalar waƙa ma, na iya?..."
Tayi maganar tana zama gefan bed cike da matsanancin nishaɗi highly highly,
Murmushi tayi sannan Ta ce "Yeah Wallahi na tuna."💃💃
Buɗe daddaɗar muryar ta Ta yi sannan ta fara Raira waƙa cike da enjoying Mood da take ciki rairawa take yi kamar haka.
"I'm coming home😌 I'm coming home. Tell the world, I'am coming home, 🙂 Let the rain Wash away..☔🌈 All.. the pain of yesterday😥😊 I know my kingdom awaits 💕💕 and... They've forgive my mistake"🤗💝 I'm coming home, I'm coming home Tell the world I'am coming home... { home is not a place it's feeling. }."
Murmushi tayi Bayan ta kai haka a waƙar nata sannan ta ɗauki mayafinta, wannan karon yafashi tayi saman kafaɗarta, sannan ta buɗe ƙofar ta fito bayan ta kuma gimtse kyakyawar fuskar ta.💝
Husnee ta kasance Ɗiyace ta uku wajen Hajiya Jawaheer.
Husnee, kyakyawar matashiyar budurwa ce wankan tarwatsa, doguwa ga hanci, ba zata Haura shekaru ashirin da ɗaya zuwa da biyu ba a duniya, sa'ar su Afeefah ce, ta kammala karatun degree nata anan Babbar University dake Jigawa State ta Karanci fannin Agriculture, Husnee akwai ta da san barkwanci kamar mene, gata akwai kirki da sauƙin kai, sai dai abin da ba'a rasa ba domin kuwa ɗan Adam ajizine. 😸
Komawa tayi ta zauna kusa da su Ƙarama da Mah'eesha saɓanin ɗazun da take kusa da Lailah da kuma Fateemah da Zakiyya.
Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta kalla Uncle Yusuf Ta ce
"Eh Uncle na amince nima."
Tayi maganar tana rufe fuska wai kunya.🤓
Gaba ɗaya fuskokin mutanen wurin idan ka kalla zaka fahimci bawai iya farin cikin dake bayyane a fuskar su bane, harda zuciyoyin su ma.
Murmushi Uncle Yusuf Ya yi sannan Yace
"hakan ake so. Yanzu sai a fara tunanin saka rana ko?."
Zuruf Husnee ta ce "Ah ai Uncle ina ga kawai tunda Already na kammala karatu na, a saka nan da one month kawai, kaga Lokacin Ya yi dai dai da lokacin da za'a kuma gasar SARAUNIYAR KYAU matakin ƙasa ko?."
Tayi maganar iya gaskiyar ta kuma har zuciyarta.
Fashewa da dariya gaba ɗaya mutanen palon, suka yi cike da nishaɗi.
Lailah da bata gani bata tanka ba, ta ce
"Oh oh ikon God sai Look. Wato yanzu ke Husnee ko kunya babu kike wannan zance gaban mu ko?."
Tayi maganar cikin dariya, muryar da basu yi tsammanin jinta bane, suka ji tana faɗin
"Oh ke kuma Lailah sarkin surutu zaki ba, My Aunty to be, kunya cikin society ko?."
Cewar Afeefah tana saukowa daga saman doguwar kujerar da aka kwantar da ita.
Murmushi Husnee tayi sannan ta ce "Batta kawai dai dai nake da ita nima ae, ko tayi tunanin zanji kunyar tane?."
Gaba ɗaya dariya suka kuma yi habba daga haka kuma fira ta kuma shiga tsakani cike da nishaɗi.
Shidai Maleek shiru ya yi yana kallon Ahalin nasa gaba ɗaya sun canza sosai. Jinsa yake tamkar wani sabo cikin su, sai yaji yau ya kuma yarda da wannan maganar da ake cewa 'Duk Wanda Yabar gida, Tofa Tabbas Gida Ya barsa'. Home is not a place it's feeling for All people.💞
*KANO*
Wannan karon da tsananin mamaki ya kuma kallon mahaifiyar tasa jin abin da take faɗi, shifa sam kansa ya ɗaure ya kasa fahimtar komai yadda ya kamata.
Murmushi tayi sannan ta ci gaba da cewa
"Umarni nake baka, akan kaje ka nema soyayyar Jiddarh saboda sai da hakan burina na tsawon shekaru fi ye da ashirin zai cika, idan kuma ba haka ba, zan san abin yi."
Murya na ɗan rawa Yace
"Ni nifa ina da wacca nakeso kuma zan Aura, sannan kuma da kike maganar na nema soyayyar jiddarh nifa matsayin ƙanwa na ɗauke ta sannan kuma..."
Katse sa tayi cikin tsananin ɓacin rai sannan cikin tsawa da ɗan ɗaga murya ta fara magana
"Heesham, indai ni ce mahaifiyar da ta haife ka ina baka umarni da kaje ka nema soyayyar wannan yarinya jiddarh, domin sai da hakan Burina zai cika."
Sai kuma ta ɗan sassauta murya tana tambayarsa da cewa
"Menene sunan ita yarinyar da kakeso ka Aura ɗin?."
Wannan karon cikin sanyin murya ya fara maganar domin kuwa mahaifiyar tasa a maimakon mamakin ta da ya faraji, tofa yanzu tsoro ta fara bashi, ganin yadda take maganar cikin kakkausar murya.
"Sunanta Bilkisu ne."
"Bilkisu. Bilkisu.."
Auntie ta maimaita tana ya mutsa fuskar ta, wacca ta ɓaci da Bleaching ta gode Allah.
"Ita ɗin Ƴar ina ce haka?".
"Katsina ne mahaifarta."
Ya bata amsa cikin sauri sauri, wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sauke, jin ba wacca take tunanin ba ce, sannan ta ce
"Babu damuwa ita ma zaka iya Aurenta, amma fah Bayan ka Aura Ƴar uwarka Jiddarh. Zuwa lokacin Burina na tsayin shekaru ya cika sannan...."
Gyara zaman sa Ya yi saman swivel chair da yake kai sannan ya kira ta da sunan da sukafi kiranta dashi.
"Auntie."
Ta amsa sannan ya ci gaba da cewa
"Shin zan iya sannin wannan Burina naki da kike cewa har saina Aura Jiddarh shi ne zai cika?."
Murmushi tayi kalar na cikakkun wayayyun Mata tana kaɗa ido ta amsa masa da faɗin
"Oh no Heesham har yanzu kai yaro ne ba zaka fahimci komai ba, koda na faɗa maka."
"Kai, Auntie ni ne Yaron? nafa Haura Twenty five highly fa."
Cewar Heesham yana zare ido jin an kira shi da Yaro.
Still it's her cheek have clear smile, shiru tayi sannan ta kuma cewa
"Habba My first Born, just chill Boss, mana daga wasa to na yadda kai ɗin, ba yaro bane, Kocin ne."🥳
Tayi maganar tana ƴar dariya sannan ta ci gaba da cewa
"Wato Heesham misali kai ne kana da wata Riga wacca wannan Riga ta kasance tana da wani masifar kyau da tsada, kowa sonta yake kaima hakan, kana masifar ƙaunar ta, sai kuma ya kasance ita wannan Riga daga ka ɗaukota ka saka ta a jikinka zata dinga yi maka ƙaiƙayi ta ko wanne ɓangare na jikin ka har sai ka cire ta, ka ƙona ta da wuta da fetur ta zama babu ɓurɓushinta sannan zata dena wahalar da kai shin idan kai ne ya zaka yi da wannan haɗaɗɗiyar Riga da kake masifar ƙauna?, shin zaka a jeta ne gefe ka dinga kallo kanajin daɗi, ko kuwa zaka ƙonata ne ka huta saboda bata da wani amfani?..."
Murmushi Heesham Ya yi Yana nazarin maganar ta, tabbas idan ya fahimta wato dai Hausa take masa cikin Hausa, sai dai kuma daga maganar ta bai fahimci komai ba, saima ɗaure masa kai da maganganun nata suka yi, ajiyar zuciya ya sauke yana kallon ta, sannan ya bata amsa da cewa
"Gaskiya idan ni ne mutum mai wannan Rigar tunda ina ƙaunar ta sosai, kawai zan saƙaleta ne na dunga kallon ta kullum tunda saka ta bazai Yiwu ba."
"Oh Heesham wannan maganar naka is not a efficacy, bazai yiwu ba, kawai kabar zancen nan, domin kuwa yafi ƙarfin tunanin ka."
Heesham zayyi magana yaji Alamar za'a shigo Bedroom ɗin, hakan ne Yasa sa fasa faɗar abin da zai ce, sannan ya mayar da kallon sa kan ƙofar.
A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga jikin ta sanye cikin Elegant Beauty Dress doguwar gown c.green color, wacca daga gaban gown ɗin Anyi ado da wasu stones sky green masu shaining, gown ɗin mara hannu ce, gashi ta matse ta gam gam, kanta babu hula sai gashinta Wanda Yasha gyara ta mishi style in braid.
"Oh Jiddarh lafiya kuwa naga kina faman dafe kan ki haka?."
Cewar Auntie a ɗan ruɗe, ƙari sawa wurin ta Jiddarh tayi sannan ta zauna kusa da ita, ta jingina kanta da Headboard na gadon da Auntie take zaune saman sa, tana faɗin
"Auntie kaina ciwo yake min kamar zai tsage gida biyar, haka nake ji."
"Oh sannu fah, kin sha magani kuwa?."
Auntie ta tambaya tana kamo ta jikin ta, ganin hankalin mahaifiyar tashi ya koma kan Jiddarh ne. Yasa shi tashi da sauri yabar bedroom ɗin, kai tsaye staircases ya nufa yana taka steps ya lalubo wata lamba kana ya dan na ma ta kira.
"Oh no Way gaskiya Auntie kema kin san bama shiri da magani ko kaɗan, kawai dai Yanayin hayaniyar dana shiga Yaune Ya ka womin Headache, amma nasan zuwa anjima zan dawo Normal nawa fa."
Cewar Jiddarh tana kyaɓe Beauty face nata. Domin ta tsani magani sama da komai.
*ABUJA*
*Wuraren Ƙarfe Biyar Da Rabi Na Yamma*
Gaba ɗayansu Ahalin Gidan suna tsai tsai ye a parking lot na gidan. Tun daga kan Daddy Mister Mai Kyau, da kuma Momy Rafi'at sai Nainarh, Nailah, Haleesat, Zaynerb, Afeefah, Lailah sai Deejarh sai kuma sauran baƙi.
Suna yiwa su Mamy Zuwaira da kuma Mamy Jawaheer, da Sakeenah harda Jummai waɗannda a yau zasu koma Jigawa State. Yayin da sauran kuma sai zuwa gobe zasu wuce ta Kano sannan su wuce States nasu.
Sai faman waige waigen ta inda zata hangosa take amma bata hango kowa ba, tayi mamakin Rashin ganin sa cikin mutane.
Kamar ance ta ɗaga kanta wajajen part nasa, aikuwa ta hango sa tsaye yana leƙen su ta ƙaton glass window dake palon sa. Yana sanye cikin Black t-shirt and short white color hannun sa riƙe da coffee cup yana sipping a hankali.
Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta masa alama da hannunta cikin iska wai zasu Tafi fah, baizo Ya yi mata bye bye bah 👋.
Murmushi ya yi daga inda yake tsaye sannan shima Ya yi ma ta Bye bye daga inda yake tsaye.
Maƙe kafaɗa tayi wai a'a, sannan ta kuma yi masa alama da tafiso Yazo.
shima maƙe ma ta kafaɗar Ya yi sannan Ya koma saman Royal sofa nasa ya zauna kana ya ɗauki remote control ya danna curtains na wurin suka koma suka Rufe.
Murmushi Tayi sannan cike da nishaɗi ta shige cikin tsadaddiyar motar su cikin zuciyarta kuwa faɗi take
"Oh my God wallahi Yaya Maleek is so adorable highly, nidai wannan zuwa Gidan Uncle Mai kyau gaba ta kaini tunda na sama dami a kala."
Murmushi kawai Afeefah dake lura da Love drama tsakanin Buddy nasu da Husnee take yi cikin zuciyarta faɗi take
"Ah Yaya Maleek kaga ta kanka indai Husnee ce wallahi."
Sai da suka ga ficewar motocin kaf daga gate na gidan nasu sannan suka juya suka yi ciki. Bayan sun shiga ƙayataccen palon ga tsananin maɗaukakin mamakin su part na Maleek suka ga Daddy mahaifin su Mister Mai Kyau. Ya nufa.😸
Ganin haka shima Uncle Yusuf da sai gobe zai koma Mai duguri da iyalansa yabi bayan sa.
_+_🥴🥴Oh Oh Malam Mai Kyau Yada Sauri Hakan?..🥴🥴_-_
Gaba ɗaya murmushi suka yi harda Momy Rafi'at sannan Ita ma ta nufa staircases tana taka steps tana qwalawa Haleesat dake zaune saman 2sieter kira, tashi ita ma Haleesat tayi kana tabi Bayan Momyn nata.
Yayin da gaba ɗaya suka zazzauna saman Royal sofa's dake Palon suka dasa sabon fira tsakanin su.
Afeefah da kuma Auntie Yusra matar Uncle Yusuf da Yaranta waɗanda suka zo da kuma Auntie Suwaiba matar Uncle Sagir da Yaranta wa'inda suma sai gobe zasu wuce Kano tare da su Zaynerb.
A hankali Deejarh takai fresh hand nata cikin pocket na gown dake jikin ta ta ciro wata siririyar chain, bata zinare bace sannan kuma bata diamond bace, kawai dai normal chain ne, amma fah Kalar wannan chain ne wacca bata komai.
Murmushi tayi sannan ta kuma mayarwa cikin pocket gown nata.
Kallon Afeefah dake zaune gefanta tana latsa waya tayi, kana ta ce
"Balarabiyar India kin san Menene kuwa?, a'a sai kin faɗa."
Cewar Afeefah.
"Toki Rufe idon ki."
Deejarh ta faɗa lokacin da ta miƙe tsaye ta koma tana fuskan tar Afeefah ɗin. murmushin da ya bayyana dimples tayi sannan tana faɗin
"Oh My Deejarh, Menene zakimin Idan na Rufe?."
"Kedai kawai ki Rufe."
"Okay."
Jin haka Yasa Afeefah ta Rufe idanunta tana jiran taji abin da Deejarh zatayi gaba.
Dariya Deejarth tayi sannan tasa hannunta cikin gown pocket dake jikin ta, ta ciro wannan Ƴar siririyar chain mai ɗaukar ido Like a diamond, sannan ta ce
"Yanzu ki buɗe, a hankali ta buɗe manyan dara daran kyawawan idanunta, aikuwa taci karo da wannan haɗaɗɗiyar siririyar chain mai tsananin ɗaukar ido.
Dariya Deejarh tayi sannan ta miƙawa Afeefah ɗin chain ɗin tana faɗin
"Wannan ita ce kyauta na ta musamman a gareki."🤗
Fashewa gaba ɗaya mutanen palon suka yi da dariya, Zaynerb na faɗi
"A gaskiya anyi son kai wannan haɗaɗɗiyar chain a rasa wacca za'a ba sai Afeefah Bayan Wanda ta samu Wajen gasa."
Haseeya da take ɗiya wurin Uncle Sagir ta ce "Ah ta cancanta ne, shiyasa kika ga ta bata."
Ita kuwa Afeefah bakinta yaƙi rufuwa tsaban farin ciki, a Rayuwar ta tanaso ayi ma ta kyautar Abu, kamar dai sarƙa ko zobe kodai dangin waɗannan babu abin da take yi sai faman juya sarƙar a hannunta.
Kallon Deejarh tayi fuskarta ɗauke da matsanancin farin ciki ta ce
"Oh my Deejarh a gaskiya naji daɗin wannan special gift da kika bani highly."
Dariya ita ma Deejarh take yi sannan ta ams da,
"Haka nakeso Balarabiyar India kullum ki kasance ciki farin ciki sosai."
Komawa tayi ta zauna sannan ta ci gaba da cewa
"Nima kalar ta guda biyu nake da su, duka Babana ne ya bani da yake sana'ar sa ke nan siya da siyarwa na sarƙoƙi."
"Aikuwa na gode highly, da kika zaɓeni matsayin wacca zaki bawa wannan haɗaɗɗiyar chain."