SARAUNIYAR KYAU (Book 1)

.

by @nkds

*SARAUNIYAR KYAU.*


*£nd Of Takun Farko*




~Last Free Page's~😸


*And*


🔚σϝ ϝιɾʂƚ ɱιԃԃʅҽ🔚


Zaune take saman ɗaya daga cikin kujerun Dining da aka ƙawata kitchen ɗin dasu. Yayin da take cin breakfast ɗin ta wanda kaiwa da komowa a cikin gidan Bai Bari ta samu taci ba sai Yanzu.


Hannunta kuwa wayarta ne yayinda gaba ɗaya hankalinta yake akan wayar nata tana karanta littafin Mrs Aysib mai suna ZAN JIRA KA.


Message ne ya shigo wayar nata hakan ne yasa ta fita daga whatsApp da take ciki sannan ta buɗe, message da taga lambar Afeefah ne.


Waro ido tayi cike da mamaki tana tunanin anya kuwa ita ce, bawai mistake Afeefah tayi ba, idan ba haka ba mai zai sa Afeefah ta turo ma ta har 500k.


Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta buɗe message na farko da Afeefah ɗin ta haɗo ma ta dashi kamar haka.


"Hi, Ummi ga waɗannan kuɗaɗen nasan dai ba zaki rasa hidimar da zakiyi dasu ba, please bana son ki watsa min ƙasa a ido wurin cewa a'a, Afeefah ce."


Wani murmushin jindaɗi Ummi tayi a fili take faɗin


"Aikuwa Afeefah nagode sosai, kamar kuwa kin san kuɗi nake nema ruwa a jallo."


Cikin sauri ta lalubo lambar ƙanwar ta Ummu Salma, tana ɗagawa ba tare da Ummi ta jira tayi wata magana ba ta ce 


"Ummu Salma, Allah ya Rufa mana asiri Yanzun nan wata budurwar da nake aiki a gidan su ta turomin da 500k, saboda haka yanzun nan ba anjima ba, ki turomin lambar account naki domin na taro miki kuɗaɗen saboda a samu ayi ma Ummu Shaheedah aikin ƙarin da ya fito ma ta kinji ummu Salma?.

Yanzun nan fa zaki turomin."


Ajiyar zuciya ta ɗayan ɓangaren wacca Ummi ta kira da Ummu Salma ta sauke sannan ta amsa da faɗin


"Toh Auntie Ummi amma please ba dai roƙonta kika yi ba koh?."


Ɗan murmushi Ummi tayi tana bawa ƙanwar nata amsa da cewa 


"A'a ko ɗaya ban roƙeta ba, ha sali ma ko faɗa ma ta ina cikin matsalar kuɗi, banyi ba, kawai dai ina zaune naga anyi min alert na 500k, Yanzu dai ya jikin ita Ummu Shaheedah ɗin ne?."


Ummi ta tambaya domin kawar da wancan maganar.


Kallon ƙanwar tasu, dake kwance saman gado irin na marasa lafiya, Ummu Salma tayi ta ɓangaren ta sannan ta bata amsa da faɗin


"Lafiya Alhamdulillah Yanzu ma ta sama Bacci ne, kuma ita Oumm Sun tafi Gida, domin suyi wanka ita dasu Uzair da Usman Sai kuma Ummu Shahuda da tazo duba lafiyar Ummu Shaheedah ɗin."


"Okay,👌


Haka ake so yanzu Abin da nakeso dake, kiyi sauri ki turomin lambar account ɗin naki kinji ko?."


Cewar Ummi sannan ta kashe wayar bayan Ummu Salma ta amsa ma ta.


Ajiyar zuciya ta kuma saukewa tana tunanin Ahalinta da irin Halin da Suke ciki.

A gaskiya ba ƙaramin taimakon ta Afeefah tayi ba, wannan turo ma ta kuɗin da tayi. Sai taji ta kuma ba Afeefah wani muhimmanci a Rayuwa.


Buɗe ɗayan message ɗin da Afeefah ta haɗo ma ta dashi, tayi sannan ta fara karanta.


"Assalamu Alaikum, Ummi Ni ce feefah mai kyau, please kai tsaye maganar dama ita ce ki daure kiyi tunani akan Yaya mah'fuz ɗina, domin kuwa ƙaunar ki yake yi da gaskiya, shiyasa ma kika ga Yana miki wannan kallon ɗazun nan, please karki masa wani mummunar fahimta domin kuwa Yaya mah'fuz mutumin kirki ne shi, zai riƙe da amana Bayan Aure, saboda Haka ki daure kiyi tunani kafin nanda two days zamu dawo daga kano State, sai ki faɗamin abin da kika yanke, kinga ae sai ah haɗa bikin naku kawai dana Yaya Maleek shida Husnee.

Idan kina buƙatar lambar wayansa ba saikin nemeni ba, domin kuwa ga lambar nan ta ƙasa. Good Luck, Feefah Mai Kyau ce. Bye bye."😇


Ta karanta wannan message yafi sau goma, tana ƙarawa da dai ta gaji ne, ta tsaya dan kanta.


Murmushi tayi sannan a fili take faɗin "Afeefah ke nan ƴar Gidan Babanta. Yanzu haka ake rubuto kalaman huɗubar saurayi a garin ku Abuja?. Wannan saiki saka naji ya gundureni fa."


Murmushin ta kuma saki tuno drama ɗin ta dashi na Safe, a lokacin sai da Auntie Yusra matar uncle Yusuf da ta ƙariso wurin ta tarar da abin da ke faruwa, ta saka Baki sannan ya haqura Yaci abincin.


"Ikon Allah shi kuma irin na shi salon ƙaunar ke nan?, amma fah hakan ya tafi da Ummu Sulaym highly highly, ae Afeefah Mai Kyau, karki damu ranki, domin kuwa tuni mah'fuz Ya yi nisa cikin heart na Ummu Sulaym tun kallon Farko Ya sace heart ɗina." 👩‍❤️‍👨💃


*KANO STATE*


Misalin ƙarfe 2:00 na rana Jirgin su Ya yi Landing a babban Filin Saukar Jirgin sama na garin Kano.


Aikuwa batare da da ɓata lokaci ba, gaba ɗaya suka shishshiga motocin Gidan Uncle Sagir, da Yazo ɗaukarsu shida kansa.

Nan suka Bar Filin Saukar Jirgin suka nufi Katafaren Gidan Uncle Sagir dake nan New Life Kano State.


Da Isar su Katafaren Gidan na Uncle Sagir Sameer Lamiɗo. Nan securities da Suke tsaron ƙaton wagameman gate na gidan Suka buɗe musu gate ɗin cikin sauri.


A Jere sannan kuma a tare tsadaddun motocin guda Bakwai suka yi parking a wangameman Filin ajiye motoci dake Katafaren Gidan.


Sannan gaba ɗaya Suka fiffito a tare, to da yake tare da matar Gidan Suke shiyasa basu tsaya ɓata Lokaci ba.


Gaba ɗaya suka nufa cikin Ainihin Gidan, da Shigar su Katafaren daular duniya ƙaton palon Gidan Uncle Sagir. Wanda yasha ya gaji da shan kayan Mo re Rayuwa Ba'a magana, gaba ɗayan su zama su kayi saman Royal sofa's da aka ƙawata ƙaton palon dasu.


Yayin da mutanen gaba ɗaya waɗanda akazo dasu tun daga kan Mah'eesha, Haseeya, da kuma mahaifiyar su Auntie Suwaiba suka shiga kitchen domin Bawa masu aiki umarnin haɗa lunch Wanda Baƙi zasu ci. Yayinda mah'fuz shi da Yasir ɗan Uncle Yusuf kuwa ko tsayawa a Palon basu yi ba. Kai tsaye ɓangaren mazan Gidan suka wuce domin sauke gajiya.😘


Shima dai Uncle Yusuf da shigowar sa Gidan tuni ɓangaren da Amma wato Hajiya Raheemah take ya nufa tare da Uncle Sagir domin gaisheta da kuma duba lafiyar ta.


Sai ya kasance gaba ɗaya mutanen palon su Afeefah ne da kuma yaran Uncle Yusuf ma ta sai kuma Auntie Yusra matar sa da tabi Auntie Suwaiba kitchen domin tayata wasu ayyukan.


Tunda suka shigo wannan Katafaren Gidan har ƙuka ƙariso palon Suka zazzauna Deejarh tana maƙale da Afeefah. Yayin da take ƙarewa ƙaton palon wanda komai Ya yi zam zam domin kuwa ba ƙaramin kuɗaɗe aka zuba ba, sai dai kuma ita haryanzu bai kai kyan Gidan Mister mai kyau ba, mahaifin su Afeefah ba a wurinta, domin kuwa shi wannan Gidan part's part's ne da yawa gare shi. Tundaga kan na yara ma ta da kuma na maza sai kuma na Amma sai kuma na Uncle Sagir sai wannan wanda Suke ciki da ya kasance na Auntie Suwaiba matar Uncle Sagir.

Yayin da shi kuma Gidan su Afeefah a haɗe ginin yake kuma a tsare yake.


Kallon Afeefah Deejarh tayi sannan ta raɗa Mata magana a kunne Muryar ta rawa.


Da sauri Afeefah ta kalle ta, amma bata ce komai ba, ita kuma Deejarh ta Ma ta alama da ido, wai zata fita, miƙefwa Afeefah tayi sannan ta kamo hannun Deejarh suka bar palon.


Sai da suka fita daga palon sannan Afeefah ta saki hannun Deejarh da ta riƙe, kallon ta tayi tana faɗin


"Da gaske kike yi wai?."


Tayi maganar tana ƙarewa Deejarh ɗin kallo, ko zataga alama.

Rau Rau Deejarh tayi da idanunta kamar zatayi kuka ta ce 


"Allah Balarabiyar India haka kawai naji jikina kamar Ruwa yana tsiyaya. Nifa tsoro nake ji ƙilama saboda nahau Jirgine, shiyasa nake zubar da jini ta da yawa kuma."


Ta ƙarishe maganar tana shirin fashewa da kuka.


Ganin Haka yasa Afeefah ta kamo hannunta sannan suka nufa wani ɓangare daban ba wanda suka fito daga ciki ba.


Kwankwasa ƙofar palon da suka tsaya gaban sa, Afeefah tayi sannan kuma har lokacin hannunta yana cikin na Deejarh wacca gaba ɗaya ta gama tsurewa, saboda tsoron wani Abu kamar Ruwa da take ji yana ma ta Yawo a jiki. 😲


Wata kyakyawar Budurwa ce ta buɗe musu ƙofar palon, jikin ta sanye da kayan bacci, da alama daga Baccin ta farka.

Ganin Afeefah tsaye yasa budurwar sakin ihun murna sannan ta ƙarisa da sauri ta Rungumo Afeefah tana faɗin


"Feefah mai kyau kece, Yaushe ku ka zo, ah ah ina su Haseeya da Mah'eesha ɗin ne, waima ya ya banji ƙarar shigowar motocin ku ba, saida fah na faɗa wa Dad idan zai tafi Airport ɗauko ku yayi min magana shi ne yaƙi ko?."


Budurwar ta ƙarishe maganar cike da Rashin jindaɗin ɗaukosu Afeefah da bata sama Damar yi ba.


"Oh My Auntie Hameeda zaki ɓallani fah."


Afeefah tayi maganar cikin murmushi, ita ma Hameeda murmushi tayi sannan ta saki Afeefah daga Rungumar da tayi ma ta tana kallon Deejarh, cikin murmushi ta ce 


"Feefah wannan kyakyawar fa, daga ina kuka samo ta?."


"Wai Deejarh bari zan faɗa miki, yanzu dai Bari mu shiga ciki."


 Afeefah tayi maganar tana kamo hannun Deejarh Sannan suka yi cikin palon.


Ita ma Hameeda ta mara musu baya, a tsakiyar palon suka tsaya.


Cire mayafin kanta Afeefah tayi sannan ta a je saman sofa, kallon Hameeda tayi tana cewa


"Please Auntie Hameeda Bari muyi amfani da bathroom na bedroom ɗin ki Abin is urgently."


"Okay babu damuwa ku Shiga ciki."


Hameeda ta bata amsa sannan Afeefah da Deejarh suka nufa wani bedroom dake cikin palon. Yayin da ita kuma Hameeda ta zauna saman 2sieter.


Suna Shiga bedroom ɗin sai da Afeefah ta mayar da ƙofar ta rufe, sannan ta juyo tana kallon Deejarh kana ta ce 


"Oya cire doguwar gown dake jikin ki mu gani."


Da sauri Deejarh ta kalla Afeefah cikin mamaki ta ce


"Balarabiyar India in cire riga na fa kika ce, mai zakimin?."


"Oh Deejarh ina nufin ki cire muga jinin da kike zubar ne fa."


Cewar Afeefah.


Ae jin Afeefah ta ambaci jini kawai sai Deejarh ta fashe da kuka faɗi take 

"Shikenan zan haihu, waiyo gwaggo na ki taimake ni zan haihu, daga zuwa Birni na shiga ukuna ni Deeje."


Ganin zata tara ma ta jama'a ne yasa Afeefah saurin kamota kai tsaye ta shiga bathroom da ita. Yayin da har zuwa lokacin Deejarh bata yi shiru ba.


"Ke deejarth kiyi shiru kiji abin da zan faɗa miki mana, kina kuka taya zakiji please my Deejarh wiping your tears okay."


Hannu takai ta sha re hawayen sannan tac e nayi.


Murmushi Afeefah tayi sannan ta ce ''Yauwa ina ce dai kin san wannan abun da ma ta suke yi duk ƙarshen wata ko?."


"A'a bansan shi ba. Menene shi haka?."


Deejarh ta tambaya. Afeefah ta bata amsa da cewa


"Wannan abun fah wanda idan mace takai shekaru goma sha huɗu ko fi ye da Haka ko kuma ƙasa da Hakan. Idan ta fara yi sai ace ta girma, wai bakisan shi ba?."


Da sauri Deejarh ta ce


"Nasan shi mana shi ne ma wanda Deluwa ta taɓayi a kasuwan garin mu, mutane suna ta kallon ta."


"Okay to shi ne fah yazo miki yanzu ae baki gane ba."


Afeefah ta faɗa hakan da son fahimtar da ita.


Zaro ido Deejarh tayi cike da tashin Hankali ta buɗe Baki ta ce


"Lah Balarabiyar India.!"


Shiru tayi tana zare ido domin kuwa bata san abin da zata ce ba.


Murmushi Afeefah tayi sannan ta ce "Yanzu dai kin fahimci komai ko?."


Da sauri Deejarh ta girgiza kai alamar e,


"Yauwa yanzu bari na fita na barki kiyi abin da zaki iya."


Afeefah tayi maganar sannan ta buɗe ƙofar bathroom ɗin ta fita.


Ganin haka yasa Deejarh cikin sauri sauri ta cire doguwar gown na atamfa dake jikin ta sannan tayi hanging nata Jikin ƙarfen shower curtain, sannan ta wanke duka inda jinin ya ɓata ta sannan tayi wanka gaba ɗaya bayan tayi na tsarki.


Knocking ɗin ƙofar bathroom ɗin da taji ana yi ne yasa tayi saurin ɗaukar orange towel dake saman bathtub ta ɗaura, sannan ta ƙarisa ta buɗe ƙofar Afeefah ce tsaye hannunta riqe da sanitary pads.


Miƙa ma ta tayi "Ga wannan ki saka ina fatan kinyi wankan tsarki?."


"Eh Nayi, amma Balarabiyar India a'ina kika sama wannan abin?."


"Oh wannan Hameeda ce ta bani ae, akwai matsala ne?."


Zaro ido Deejarh tayi tana furta "Shikenan kuma tasani ko?."🥺


Wata dariya ce ta kusa kwace wa Afeefah ganin yadda Deejarh ta zaro ido tana tambaya, danne wa tayi sannan ta bata amsa da faɗin


"Deejarh ni banma san abin da zan faɗa miki ba, ga wannan kawai."


Tayi maganar tana miƙa ma ta sanitary pad ɗin.


Karɓa tayi, har Afeefah ta juya zata fita, sai kuma ta juyo kallon ta tayi sannan ta ce

"Rigar ta ɓaci ne?."


Da sauri Deejarh ta ce "A'a bata ɓaci ba, amma dai dogon wandon ya ɓaci sosai, da kuma pant ɗin."


"Okay to a cikin wannan ledar na hannun ki akwai pant sai kiyi amfani dashi, sannan kuma idan kin fito."


Ta nuna ma ta wardrobe sannan ta ci gaba da cewa


"Ki buɗe ki ɗauki leggings wanda zai miki ki saka, kinji ko?."


"Toh Balarabiyar India na gode highly da kulawarki a gareni."


Murmushi Afeefah tayi sai dai bata ce komai ba, ta buɗe ƙofar bedroom ɗin ta fita.


Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta koma cikin bathroom ɗin.


"Yane feefah bai dai zo ma ta da ciro bah koh?."


Hameeda dake tsaye bakin ƙofar ta tambaya.

Afeefah ta ce "Eh bai zo ma ta da komai ba an goda Allah."


Komawa suka yi Palo sannan suka zauna, Hameeda saman 3sieter Yayin da Afeefah ta zauna saman 2, tana faɗin.


"Auntie Hameeda jiya fa, naga ɗaukar firan da kika yi da wannan budurwa da tayi rashin nasara wajen gasar SARAUNIYAR KYAU matakin jahar Kano na shekaran jiya."


Murmushi Hameeda tayi ta ce


"Oho Juwairiya Jabir Bici, ae ina faɗa miki Afeefah Yarinyar ba ƙaramin tausayi ta bani ba, shiyasa ma saida Nasan Yadda nayi Dad yamin Hanya Nayi fira da ita cikin asibitin."


"Aikuwa abin dai akwai tausayi domin saida na kusa ma ta kuka a lokacin da naji labarin ta fa."


Cewar Afeefah, Hameeda ta ce "Ae shi ne ma Babban dalilin da yasa nayi fira da ita, domin ƙara wayar da kan mutane, yanzu kamar ita Juwairiya kaf Gidan su fa, wai YaYanta ne kawai yake mara ma ta Baya, ni banga amfanin mahaifiyar su ba Wallahi, menene amfanin uwan da ba za ta tsaya taji matsalar Yaranta ba, ae babu yanzu da Abin yazo da tsautsayi fa, duk da ba fata ake ba, ace ita Juwairiya ɗin wannan faɗin da tayi ta sama cardiology ko kuma wani ƙaton ciwon fah?.

Da sai dai uwan tayi kukan nadama only."


Ajiyar zuciya Afeefah ta sauke tana faɗin

"Please Auntie Hameeda idan kin san Gidan su, please Gobe zaki rakani, domin kuwa Haka kawai naji ina so naga Yarinyar face to face."


Murmushi Hameeda Tayi sannan ta amsa ma ta da cewa


"Sosai ma nasan Gidan su, dama nima gobe ina shirin zuwa duba ta, saboda Yanayin aikina bai bari naje duba ta ba kinga sai muje tare."


Hmmm wannan Aiki naki ma, ae kina ƙoƙari highly highly domin kuwa idan ni ce, wallah Bana iyawa."


Cewar Afeefah cikin kyaɓe fuska


"Kin ji ki feefah da wani zance, ae gwara aikin jarida akan wannan aikin da kike karanta na likitanci amma fa ganina?."


 Cewar Hameeda.


"Duk da haka aikin jarida kamar zai fi wahala fa."

Afeefah ta kuma faɗa, taɓe baki Hameeda tayi

"Kyaji dashi dai don nidai duk da haka nafi son aikina domin kuwa yana bani nishaɗi obaaa."


"Wani lokacin kuma ya na sakaki kuka ko?."


Afeefah ta kuma maganar.


"Ke feefah rabu dani haka kinji domin kuwa aikine a gabana, na tsaya fira dake zuwa anjima zan fita nida wata Abokiyar aikina Humaira, za muje wani company ne, da ake zargi ana safaran mata da ƙananan Yara a ciki."


Waro Manyan idanunta tayi tana kallon Hameeda da tayi maganar hankali kwance, buɗe baki tayi zatayi magana, sai ga Deejarh ta fito daga bedroom ɗin da take ciki.


Ajiyar zuciya Afeefah ta sauke bata ce komai ba, saima kallon Deejarh da tayi cikin murmushi ta ce 


"My Deejarh kin gama ke nan?."


"Eh Balarabiyar India, na kammala."


"Okay yanzu ni wurin Amma zani zaki rakani ne, ko kuwa na tafi nika ɗai ke zaki tsaya anan?."


Afeefah ta Tambaya Deejarh ɗin tana kallon ta.


"Eh zan rakaki wurin Amma ɗin kawai."


Deejarh ta bata amsa. Miƙewa Afeefah tayi sannan ta kalla Hameeda tana cewa


"Auntie Hameeda bari muyi wajen Amma wata ƙila ma karki fita ba zaki gammu mun dawo ba."


Miƙewa tsaye ita ma Hameeda tayi tana faɗin 


"Bari nima nabi ku wurin Amma ɗin domin kuwa yau kwata kwata bamu gaisa ba, saboda makaran da nayi."


Gaba ɗaya ɗunguma suka yi suka fita a tare, daga palon kai tsaye suka nufa Hanyar da zata sadasu da part na Amma.


Buɗe ƙofar palon Hameeda tayi sannan suka shiga ciki, aikuwa nan suka Hango ta sanye cikin shiga ta alfarma tana zaune saman tattausar carpet. Yayin da gabanta kuwa Littafai ne kala kala wasu na Addini wasu kuma na Likitoci.

Idanun ta cikin medical glass white color.

Ɗagowa tayi tana amsa sallamar da suka yi, sannan suka ƙariso kusa da ita, gaba ɗaya suma suka zazzauna a ƙasan carpet suna gaisheta, amsawa tayi tana ƙare musu kallo.


Ganin dai kamar yau tsufan nata ya motsa ne, yasa Hameeda faɗin

"Amma Afeefah ce fa, kodai baki gane ta bane?."


Murmushi Amma tayi sannan ta ce "Au au ohoo Afeefah ta Wajen Abubakari ke nan. Na gane ta mana sosai ma, sai dai kuma wannan ta kusa da ita." Ta nuna Deejarh "Ita ce ban gane ba."


"Okay wai wannan sunanta Khadeejah fa, ita ma ɗiyar Uncle Mai Kyau ce fa, sai dai idan kece baki gane ta ba."


Cewar Hameeda tana kwashewa su Afeefah ido.


"Ke Hameeda ja'irar Yarinya, an faɗa miki niɗin na makance ne ko kuwa?, wannan kyakyawar Yarinyar da ganinta ba ɗiyar Abubakar bace, ɗiyar Yarona Mai Kyau ne da gani."


Gaba ɗaya fashewa da dariya suka yi na jin abin da ta faɗa wato ba ɗiyar Abubakar bane, ɗiyar Mai Kyau ce. 🤣😂😅


"Kai Amma idan aka ce kin tsufa, sai kice a'a. Yanzu in banda rikicin tsufa, wanene Abubakar?, sannan kuma wanene Mai Kyau?, ae duk mutum ɗaya ko?."


Cewar Hameeda still fuskar ta ƙayataccen murmushi ce saman ta.


"Ae kyaji dashi ja'irar Yarinya ni dai nasan wannan Yarinya ɗiyar Yaro na Mai Kyau ce ehe."


Cewar Amma tana ci gaba da duba littafan gabanta.


Dariya Afeefah tayi tana faɗin "Kai Amma wato dai har Yanzu baki manta Baya ba, kina nan da wannan karance karance naki na littafan Addini da na ɓangaren ki ko wato Likitanci, to nima dai bari na gani ko akwai wanda zan iya karantawa a ciki."


Afeefah tayi maganar tana duba tilin littafan dake gaban Amma kamar wata professor.


Murmushi Hameeda tayi sannan ta miƙe tsaye ta nafa saman sofa ta kwanta a saman 3sieter tana faɗin 


"Ae sai kiyi karatu da kyau da kyau ni dai nayi nan."🏃


Kallon Deejarh Afeefah tayi ganin kamar ba ita ba, duk ta nutsu, a Hankali ta kira sunan ta.


"Deejarh."


"Na'am Balarabiyar India."


Ita ma ta amsa, Murmushi tayi sannan ta ce

"Karfa kice zaki sakawa kanki damuwa, domin kuwa da haka aka fara gaba ɗaya, ba kanki fa rau ba."


Deejarth ta ce "Amma Balarabiyar India lokacin da kika fara yi, ya kikayi sannan kuma ya kikaji ne dan Allah?."


Deejarh tayi ma Afeefah tambayar tana dariya.


Sai da tayi tambayar kuma tayi saurin rufe baki, mana kallon Amma, dariya Afeefah tayi ta ce


"Ae indai Amma ce batama san kinayi ba, saboda haka saki jikin ki mutumiyar."


Washe baki Deejarh tayi jin abin da Afeefah ta ce sannan ta kuma cewa 


"Ya kikaji ke a lokacin kuma kina ina ne?."


Wani murmushin tuno baya Afeefah tayi tana lumshe ido ta ce 


"A Lokacin wai. Eh toh a Lokacin muna ƙasar Jamus ne, ni da Zaynerb da kuma Daddyn.

Ae deejarth ina faɗa miki bazan taɓa mantawa da lokacin ba, tsawon rayuwata, wato dai abin da ya faru shi ne.


Wata Ranar Monday na dawo daga school goye da Backpack ɗita, na fito daga cikin Bus na makarantar mu, wacca ta saukeni a ƙofar gate na gidan mu.

Kamar ance na kalla ƙasa, a lokacin kawai na tsinci kaina da durƙusawa ina kallon white socks dake ƙafafuna, aikuwa me zan gani?.👺

Nan fah naga wani abu kamar jini, kamar manja yana ɗigowa duk yabi ya ɓatamin safa ta, ina faɗa miki bansan Lokacin dana rintima a guje ba, ko tsayawa kula Baturen mai gadi, banyi ba, tunda Allah ya bani sa'a na shiga cikin gidan na dangana da Palo, aikuwa anan na sama Daddy yana duba wasu bayanai cikin laptop. Yayin da Zaynerb take daga can gefe tana Assignment cikin littafan ta na school.

Ae Tunda na shigo palon a guje ban tsaya komai ba. Nayi fatali da wannan laptop wacca Daddy yake aiki ciki. Ban tsaya bah, nanfa nan na shiga birgima ina faɗin shikenan kwanana ya ƙare zan mutu nima wajen Haihuwa tunda Jini yana fito min, shikenan nayi ciki a taimake ni.🙈

A lokacin Zaynerb da ta fahimci komai, in banda dariya babu abin da take min. Yayin da shi kuma Daddy kallona kawai Ya tsayi yi, saida kyar aka samu nayi shiru da kyar da ban baki, sannan ne fa, Daddy da Zaynerb suka min bayanin komai, domin kuwa violence highly highly da nake ciki bai bari na fahimci komai ba, duk da dai lokacin ba wani yawau ne dani ba sosai..."🤣


Tunda Afeefah ta fara zuba zance babu abin da Deejarh da Hameeda dake saman 3sieter suke yi banda dariya, Deejarh harda Birgima a ƙasa tana riƙe ciki saboda mugun dariya. Yayin da Hameeda kuwa sai da ta faɗo daga saman 3sieter da take kwance tsaban dariyar ƙeta.


Shiru Afeefah tayi tana kallon yadda suke dariya babu ƙaƙƙautawa, ita ma kawai saita fara dariyar cike da Nishaɗi.😅🤣😂


Su na cikin Haka sai ga Lailah, Zaynerb, Haleesat, Nainarh, Nailah, da gaba ɗaya Yaran Uncle Yusuf da kuma Haseeya da Mah'eesha Yaran Uncle sagir suma sun shishshigo gaba ɗayan su, gaisar da granny tasu suka fara yi.


Gaba ɗaya tsayawa suka yi suna kallon yadda su Hameeda suke ɓaɓɓaka dariya cike da kamar zararru, yayin da Amma ta zuba musu ido tana kallon ikon Allah.


"Ikon Allah sai Look, toh mu dugu ko kuwa mu tsaya?, domin naga kamar Babu Lafiya anan fa."

Cewar Yasira tana zare idanu.


Ido cike taf da qwalla saboda tsaban dariya Hameeda ta kalle su cikin ɗan dariya take faɗin 


"Please ku tsaya, ku zazzauna."


"Ah taya ya zamu zauna bayan kuma kuna dariya sai kace waɗanda suka sama taɓin kwakwalwa. Ni tafiya ma zanyi dama nazo nayi ma Amma sallama ne." cewar Nailah tana shirin fita.


Ganin Haka Yasa duk suka yi tsit Afeefah ta ce 

"Please Auntie Nailah zoki zauna, ae mun gama dariyar, jin Haka yasa gaba ɗaya Ƴan matan suka zazzauna a tsakiyar palon, gaba ɗaya suka gagaisa da Amma ɗin tasu sannan.


Lailah ta ce

"Mu fah har Yanzu Bamu ji abin da Yasa kuke wannan dariyar da muka shigo muka samu kuna yi ba, sai kace waɗanda suka shaqa Laughing gas."


Hameeda da dariyar bai ishe ta ba take faɗin


"Kedai Lailah bari kawai. Wani Labari mukaji wanda ya sakamu nishaɗi."


Wannan kuma wani Labari ne haka, a gaskiya muma a bamu Musha, Zaynerb ta faɗa tana gyara zamanta saman tattausar carpet na Palon.


Hameeda ta ce 

"Ae kinma san Labarin, sai dai kuwa idan kin manta."


"Mu dai bamu sani ba, saboda haka a bamu musha."


Wannan karon Yasira ta kuma maganar.


Satar kallon Amma Hameeda tayi sai taga hankalin ta baya kansu, saboda haka kallon su ita ma tayi cikin Dariya ta ce

"Dama kawai Afeefah ta bamu labarin first Period nata fa."


Aikuwa jin abin da ta faɗa gaba ɗaya suka gyara zama sunji gossip.


Yasmin ta ce 

"Please Auntie Hameeda bamu Labarin daga ji Abin zai bada jitta highly higher highest ma."


Aikuwa nan bada ɓata lokaci ba, ita ma Hameeda da take sarkin surutu obaa, ta basu labarin da Afeefah ta basu wurin da tayi mistake Afeefah ta gyara ma ta, babu ko kunya.


Habba ae nan gaba ɗaya ƴan matan wurin suka kwashe da dariya. 😅🤣😂


Mah'eesha ta ce, Bayan sunyi shiru.


"Allah sarki Rayuwa, Auntie Hameeda da kika bada wannan Labari sai naji na tuna Baya, lokacin muna Boarding school nima haka nayi fama, first period nawa lokacin yazo min ana cikin tsakiyar Assembly, ae lokacin naci wuya ba kaɗan ba, abin ku da babu yawo sosai. Haka na dingi kuka, sai yanzu da naji wannan Labari sai naji na tuna Baya, sai naji dama ace baya zata dawo, habba ae kawai Abin Ba'a magana domin kuwa Rayuwar ƙuruciya tayi wallahi, Barin ma dai ace muku school Life, habba hummm." 🔥


Mah'eesha tayi maganar tana lumshe kyawawan idanun ta. Alamar dai tayi missing Baya highly highly.


Yasira ta chafe zancen da cewa 

"Ke dai Mah'eesha Bari kawai. Abin cike yake da nishaɗi obaa."


Habba nanfa suka buɗe sabuwar fira tsakanin su. 

Yayin da kowa sai ya bada Labarin shirmen da ya tafka a lokacin ƙuruciya, Especially ma Lokacin suna school kuma ace J.s.s.😘


Kowa bada labari yake a cikin su cike da Nishaɗi harda Haleesat da take miskilar gaske, ae ita ma tuni ta a je miskilanci a gefe aka shiga fira da bada Labari da ita. 😛


"Kun kammala kuwa?, nace kun kammala fitsarar taku Ja'iran Yaran zamani kawai, wato Babu kunya kunzo kun sakani, ni kakarku mahaifiyar ubannin ku a tsakiya, wato kowacce taji da farar fuska, sai kace zabiya, kuna bada Labarai koh?.

Wato ga marasa kunya har Gida, zakuci ƙaniyar ku domin kuwa da Babannin ku zan haɗaku duka."🙄


Gaba ɗaya tsit shiru suka yi suna jin Yadda kakartasu take ƙare musu tsiya.


Yayin da Lailah da Yasira da kuma Mah'eesha Waɗanda sune nan Ja'iran ciki sai faman tiƙa dariya suke yi.


"Eh dariya koh? Kuyi dariya da kyau, ke Lailah ɗiyar Abubakar kar kiga Sunanki Lailah, kiyi Tunanin zanji tsoron ki, dan kina Lailah, a'a Lailah kike ba dare bah."🌚

Ke kuma, ta nuna Deejarh wacca Tayi tsuru tsuru saboda yadda taji mararta ta ɗauki ƙugi.


Na dawo kanki wato kece wacca take al'adar ko kuwa ba ke ce ba, naga kinyi tsit kina kallona?."


Tayi maganar tana kallon Deejarh.


Cike da jin raɗaɗin ciwo Deejarh ta amsa da


"Eh Ni ce,"


Amma ta ci gaba da cewa abin da nakeso dake kije ki sama Ruwan zafi a gora ki ɗaura a saman cikin ki, sannan kuma ki dinga yawan shan ruwan zafi akai akai harki kammala kinji?."


Da toh kawai Deejarh ta amsa.


Miƙewa Afeefah tayi sannan ta kalla Deejarh ta ce


"Taho muje na rakaki domin ki fara tun Yanzu."


Aikuwa da sauri Deejarh ɗin ta miƙe sannan tabi bayan Afeefah suka fita.


A hanya kafin su ƙarisa ɓangaren Auntie Suwaiba ba, suna tafiya duk da ciwon da Deejarh take ji bai hanata kallon Afeefah ba, sannan ta ce 


"Balarabiyar India wai dama fassarar sunan Lailah Yana Nufin Dare ne?. To ke, Kuma Menene fassarar Sunanki?."


Afeefah tana tafiya batare da ta juyo ba ta ce


"Eh Haka Lailah Yana Nufin Dare. Yayin da Afeefah kuma Yake Nufi 'TAGARI.''


"Aikuwa dai Sunan ya cancanta dake it's really deserved to you highly."


Cewar Deejarh cikin murmushi, Buɗe ƙofar palon Afeefah tayi Bayan sun ƙarisa sannan suka shiga ciki domin aiwatar da umarnin Amma ɗin.


**


Da Marece wuraren ƙarfe _-_05:00pm_-_ gaba ɗaya Ahalin Uncle Yusuf suka yi sallama da mutanen Gidan har dasu, Afeefah sannan suka tafi Airport domin komawa BORNO STATE.


Tare da Rakiyar wasu daga ƴan Gidan, Yayin da ita ma Nailah ta bisu Airport ɗin zatayi jiran awa ɗaya a Airport ɗin domin komawa Lagos Birnin da take Aure ita ma da yake akwai wata ƙawarta wacca take ma'aikaciya ce anan Airport ɗin.

Yayin da ita kuma Nainarh sai zuwa gobe idan Allah ya nufa zata bi Jirgi ita ma domin komawa ƙasar Auren ta wato Eritrea.


*ABUJA*

       *NIG£RIA*


Misalin Ƙarfe Tara Na Dare _-_09:00pm_-_


Zaune yake saman ɗaya daga cikin Royal sofa's waɗanda aka ƙawata qaton palon nashi dasu.


Hannu sa kuwa tsadaddiyar wayar sa ce yana latsawa, a zahiri zaka yi tunanin tsadaddiyar wayar hannun sa yake kallo.

Yayin da kuma cikin zuciyar sa tunani yake yi shin ya kira ta ne, ko kuwa dai ya barshi kawai.😀


Haka kawai yaji yana buƙatar jin daddaɗar muryarta cikin daren nan, ko da suna Yara yafi shiri da ita sama da kowa cikin Yaran Uncle's nasa da kuma Mamy's ɗin sa.


Shiga Contacts na wayar nasa ya yi sannan ya lalubo lambarta wanda Ya yi saving da, mí afortunado polola { My lucky girlfriend} daga yakai hannu zai danna call, sai kuma ya fasa, daga yakai hannu zai danna call sai kuma fasa, Haka ya shigayi yana maimaita wa, aikuwa cikin mistakenly ya danna kira.


Waro ido Ya yi waje ganin kira ya tafi harta fata ringing, ke nan dai babu damar katse wa tunda kiran ya rigatda ya tafi.


Ajiyar zuciya ya sauke ganin Tayi picking call ɗin, har tana rangaɗa sallama cikin daddaɗar muryar ta wacca duk ta karaɗe palon.


"Hello.! Hello Yaya Maleek are hearing me, shin kanajina kuwa?."


Ɗan Shiru Ya yi Yana kallon wayar domin kuwa baisan abin da zaice ba, sai da yaji ta ƙara magana sannan ya fara maganar shima.


"Ba'a koya miki Gaisuwa bane, kin wani ishe mutane da hello hey."


*Husnee*


Da sauri ta ciro wayar dake manne a kunnen ta domin ganin anya kuwa Yaya Maleek ɗin ne, aikuwa dai shi ne domin kuwa sunan da tayi saving lambar sa ne, wacca tayi saving da 'My Yaya Maleek' ✴️

Bayan ta karɓa wurin Lailah ne.


Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta ce "Good evening Yaya Maleek, Fatan kana Lafiya, ya gidan?."


Tayi maganar ƙasa ƙasa.

Daga ɓangaren sa kuwa ƙayataccen murmushi Ya yi sannan Ya ce 

"Dama kawai na kira ki ne, domin ki rairamin waƙa."


Zumbur ta tashi zaune daga saman bed tana ƙara ƙanƙame wayar bakinta na furta.

"YaYa Maleek waƙa kuma?, toh ae ban iya ba, please ka canza wani abun amma banda waƙa pleased."


Ki shin giɗa Ya yi sannan ya bata amsa da cewa


"Eh mana kin iya, domin kuwa jiya ma da kika ce zakije tunani domin yanke hukunci nasan rawa da waƙa kawai kika je kika yi domin kuwa a Yadda gashin kanki yake zubowa yana rufe fuskar ki, da kuma Yadda mayafinki Yayi ƙasa da inci Biyar bisa baya, na tabbata rawa da waƙa kika yi, saboda Haka Malama Raira min waƙa ina jinki. Idan kuma bah Haka ba, bazan ƙara kiran ki ba, har Sai an ɗaura Aure, kuma Idan ke kika kirani bazan ɗauka ba, ko kuma na sakaki a Blacklist."🥵


Shiru Husnee tayi tana sauraron ikon Allah, sai da taji ya yi tsit alamar dai ita yake sauraro. Sannan ta sauke wata Nannauyar ajiyar zuciya, gyaran murya tayi, ta muka gyara zama, tana ƙara ƙanƙame wayar, sannan ta fara raira waƙa kamar Haka.


"Ya-masoyi-ina-jiranka-kazo-da-sauri-zuciya-tana-mini-ɗinlin-ɗinlin.."


Da sauri Maleek Yace

"Aikuwa bazan zo ba, saboda haka Malama canza wata, wannan batayi ba sam.


Turo Baki Husnee kamar zatayi kuka Ta ce

"Toh Yaya Maleek yanzu wanne kakeso nayi?."


Yana Lumshe kyawawan idanun sa Yace


"Koma wanne ne, kiyi."


Shiru tayi sannan ta fara Raira Wata waƙar kamar Haka.


"Eh-Zuciyata-kyauta-ka-riƙe-na-baka-babu-abin da-zaisa-na-naguje-na_barka.😅


"Aikuwa bazan Yarda ba, tunda waƙar Sani Ahmad kika Lauya, canza wata kawai ko kuma na gimtse kiran Yanzu nan."


Cewar Maleek yana murmushi, ita ma Husnee murmushi tayi ta ɓangaren ta wato dai Yaya Maleek yana buƙatar jin daddaɗar muryarta sosai ne, shi ne zai wani ce tayi waƙa ko?, aikuwa zataitayi har sai yace ya gaji daji. Nutsuwa ta kuma yi sannan ta fara.


"Ah_soyayya_dole_sai_kun_ɗanyi min_uzuri_Maleek_ne_shi ne_wanda_ni_Husnee_nake_son_aure_maleek_neh_maleek_neh_kaine_dai_kai_ɗaya_tun_a_dare_safiya_soyayya_kah_biya_ka_ƙaramin_lafiya_banajin_zance_na_kowa__ah_kanka_na_yadda_na_zama_gawa_na_ƙare_nazari_nah_ɗau_alƙawari_zancen_ayyiriri_aure_da_kai_zamuyi_bidiri_lissafina_haka_yake_soyayya_ta_haka_take_bana_ɗaukar_ta_da_sanyi_sanyi_nafi_sonta_da_zafi_zafi_highly_highly_.🤣😅😂


Fashewa Maleek Ya yi da dariyar da yake ta ƙoƙarin riƙewa yana faɗin


"Ah gaskiya wannan waƙa tayi daɗi sosai, duk da cewa ita ma waƙar Umar_M_Shareef ce Mai taken Ummitah kika Lauya, amma dai kinyi ƙoƙari highly highly sannan kuma..."


Ae Tun kafin Ya kuma cewa wani abu Husnee ta riga shi da cewa, "Ae Barima kaji Yanzu ƙasar India zan koma kaji salon su humm uhumm."


 Tayi gyaran murya sosai sannan ta fara.


"Munda_sona_hai_tu_kudi_main_crore_di.

Munda_sona_hai_tu_kudi_main_crore_di.

Tere_liye_maine_pehli_wali_chod_di.

Kahe_tujhe_Jawani_kar_shuru_kahani.

Tu_kar_mujhe_tang_sohneyahhh.


Sabko_na_kardi_tujhko_haan_kardi.

Main_jana_tere_sang_sohneyahhh......


Hmm_mere_jaisa_aashiq_hai_koi.

Banda_main_classic_hai_koi.

Main_jana_tere_sang_sohneyahhh


Mere_kad_kaath_sa_hai_koi_sir_phire.

Jaat_sa_hai_koi..

Tere_dad_se_lad_jaye_hai_koi.

Fir_pair_bhi_pad_jaye_hai_koi.


No_fat_fat_left_to_right_like_dhoom_chak.

Chak_dhoom_chakkkk

Chak_dhoom_chkkkkk." 😅🤣


Tunda ta fara Raira wannan waƙar na ƙasar India Maleek Ya yi tsit Yana sauraronta, har sai da Yaji Tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya sannan Yace


"Kin gama kuwa?."


Washe baki Husnee tayi tamkar tana kusa dashi ta ce


"E, Yaya Maleek na gama ina fatan dai tayi daɗi?."🙄


"Hmmm ae ina faɗa miki banma fahimci komai ba, cikin waƙar nidai kawai naji ana tayi ana tayi."


Maleek Ya yi maganar yana murmushi.


Dariya Husnee Tayi sannan tana faɗin 


"Kai Yaya Maleek waƙar film ɗin India ne fa, nah cikin wannan drama ɗin Wanda KARTIK_AARYAN, YaYi shida KRITI_SANON, ah kafcen su na $hehzahdah.

Tofah shi ne nayi maka waƙar magana suke akan banbancin soyayya da kuma kuɗi fa.🙄

Amma Yanzu bari na ƙirƙiro ta musamman nayi maka ta fara.


"Tahoo zoo garenii Yakai wannan masoyina, mai wahalar da zuciyata da bahamaƙiyar ƙauna, kazo ina jiran ka, kaji kuwa tahoo zoo garenii Yakai kyakyawan ƙayataccen saurayi Wanda Ya sace heart ɗita da masifar qaunar sahhh."🤭


 


😇😇😇


Shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya na dogon numfashin da Taja sannan ta ce "YaYa Maleek, Yaya Maleek to yah kaji wannan tayi kuwa?."


Maleek dake faman tiqan dariya ƙasa ƙasa tunda ta fara Ya yi murmushi sannan yana faɗin


"It's Nice, 🙂 it's Very Amazing,😂 ae ina faɗa miki wannan waƙar taki ko Shakirah mawaƙiya ba zata gwada miki iya waƙa ba."


Ya yi maganar yana kuma ɓoye Dariyar sah.


Washe Baki Husnee tayi Sannan tana cewa

 

"YaYa Maleek ko kana so na ƙarayi maka wata kalar ce? Kaji salon iya saloh na burgewa da saka nishaɗi?."😘


Da sauri Maleek ya bata amsa da cewa


"A'a Doctor a ɓangaren waƙa Husnee na gode sosai. Yanzu abin da nakeso dake ki kashe wayar sannan kiyi addu'a ki kwanta kinji?."


Husnee tana dariyar nishaɗi ta amsa masa da

"Toh amma Yaya Maleek idan na kashe kiran, gobe zaka kirani kuwa?."


"Eh," Ya bata amsa sannan tayi masa sallama kana ta kashe wayar ta.


Ajiyar zuciya Maleek ya sauke yana kallon wayar. Yayin da Fuskar sa take ɗauke da ƙayataccen murmushi na musamman cike yake da nishaɗi. Wanda shirmen Husnee ya jefasa ciki.


A fili ya furta 


"Ina ƙaunar ki Husnee SARAUNIYATAH I Love You, For The All My Heart My Lucky Girlfriend..GN."👋💃


*KANO-STATE*


Misalin ƙarfe uku da rabi na ranar washe Garin zuwan su Afeefah Kano ita ma Nainarh tabi jirgin etritea domin komawa ƙasar Aurenta. Yayin da ta sama rakiyar Afeefah da Lailah da kuma Mah'eesha sai Deejarh.


Horn driver ya buga da ƙarfi ganin Mai gadi bai zo ba, da sauri gate man ɗin tare da da wasu securities suka wangale gate na gidan da sauri.


Sannan Driver ya cinna Hancin Motar cikin Katafaren Gidan na Uncle Sagir, sai da ya kammala parking a wurin da aka tanadar domin yin parking na motocin Gidan, sannan suka buɗe Motar suka fiffito a tare suka nufa ƙofar palon Gidan.


Afeefah tana shirin kai hannu ta buɗe ke nan saiga Hameeda ta fito daga ɓangaren su na yaran gidan mata.


Murmushi Afeefah tayi Hango Hameeda sannan tana cewa, Bayan Hameedar ta ƙariso wurin da suke tsaye 


"Yauwa Auntie Hameeda dama fa ke nake nema, na ɗauka ma kina ɓangaren Auntie Suwaiba ne ae."


"A'a sauke kawai domin kuwa ina nan a ɓangaren mu yanzu ma da kika ganni Gidan su Juwairiya Jabir Bici nah nufa dama Allah, Allah nake na same ki kafin ki fito raka Auntie Nainarh sai kuma kafin na fito harkin tafi, Yanzu dai zance Ya ƙare sai mu ɗunguma muje Gidan kawai tunda kince zakije ko?."


Hameeda ta ƙare doguwar maganar tana saɓa backpack nata irin na ƴan Jarida masu neman Bayanai.


Murmushi Afeefah tayi sannan tana faɗin


"Okay muje kawai babu damuwa don a shirye nake."


Kallon Lailah da Mah'eesha da kuma Deejarh tayi sannan ta ce


"Bari muje wani guri mu dawo."


Cikin sauri har suna haɗa baki suka ce 


"A'a ae koh ina ne muma zamuje domin Yawo muke ji highly."


 Lailah ta ƙara da cewa badai wannan Yarinyar da ta faɗi wajen gasar SARAUNIYAR KYAU na wannan Jahar Ba, aikuwa indai ita ce zani domin kuwa jiya da dare naga Labarin a Facebook."


Hameeda ta ce 


"Ita ce badai Juwairiya Jabir Bici ba, ae wannan Labarin Ya zagaye duniya sosai."


Mah'eesha ta ce 


"Ah gaskiya nima za biku saboda ina so na ganta ido da ido, domin kuwa sai da nayi Hawaye da jin labarinta."


Ita ma Deejarh ganin haka yasa ita ma da sauri ta ce.


"Nima zan biku."


"It's okay tunda na fahimci kowa ma so yake yi yaje, kawai kuzo mu tafi kawai tun kafin wasu su ƙaru, domin kuwa naji ita ma Haseeya tana cewa zataje."


Hameeda tayi maganar tana nufar hanyar parking, gaba ɗaya ɗunguma suka yi suma suka nufa parking lot ɗin, Afeefah na faɗin 


"Aikuwa dai Haseeya ba zata sama damar zuwa ba tunda Auntie Raheemarh ta riƙeta da aiki."


Hameeda dake shirin buɗe mota ta ce 

"Ke nan dai kun biya ta gidanta daga Airport ɗin ko, no wonder naji kun daɗe sosai, ashe akwai wurin da kuka biya ne."


Tayi maganar tana tayar da Motar sannan ta karya kwana ta nufa gate Lailah tana bata amsa da


"Ae dan ma Afeefah ce ta wani ce mu dawo Gida akwai wurin da take so taje, badan haka ba, ae dama har Gidan Yaya Shahid sai munje."


Mah'eesha ce wannan karon tayi magana Bayan gate man ya wangale musu gate sun fita ta ce 


"Ae wallahi da sai dai kuje ku kaɗai domin kuwa ni babu inda zani, saboda wannan baƙar matar tasa ba tasan Menene mutunci ba sam."


Lailah ta kuma cewa 

"Ae badan ita zamuje ba, saboda Yaya Shahid zamu je, kuma tunda naji kince Haka toh wallahi sai naje bari mu dawo daga nan inda zamu, sai naga ƙarshen rashin mutunci mu da muke siyan rigima da kuɗin mu ma."


Murmushi kawai Afeefah tayi sannan ta ce 

"Ah gaskiya Dangin miji su nada matsala tasu ta musamman, wani lokacin zata iya Yiwuwa Mah'eesha kune baku biyo ma ta ta inda zata dinga muku kirki da mutun taku ba."


Hameeda dake ƙoƙarin karya kwanar da kai tsaye zai sa dasu da Street na Yankin da unguwan su Juwairiya Jabir Bici yake. Tayi murmushi tana faɗin


"Hehehh Afeefah ke nan bazaki fahimta bane kawai, domin kuwa wannan matar Yaya Shahid ɗin tafi ƙarfin duk tunanin ki Allah kuwa."


Afeefah mayar ma ta da martani ta hanyar faɗin


"Kune dai bazaku fahimta ba, domin kuwa mafi yawan samun rashin fahimta da ake yi tsakanin dangin miji ko kuma ƙannin sa da matar sa. Tofa mafi Yawa Laifin su waɗannan Dangin mijin ne fa, amma fa a Tunanina aha."😁


"Hahaha feefah mai kyau ke dai kawai tunda bazaki fahimci abin da ake so ah ganar dake ba, Bari kawai nayi shiru, duk Ranar da tsautsayi yakai ki zuwa Gidan zaki fahimta gaskiyar Mah'eesha ne."


"Toh Allah ya kaimu Gobe ni kuma zan biku zuwa Gidan domin nah ganewa ido na komai."


Cewar Afeefah daga haka kuma motar ta ɗauki shiru suka ci gaba da tafiya dama ita Deejarh ciwo sama sama da taji mararta tana yi ne yasa ko tsunduma Bakinta cikin firar tasu ba tayi ba.😌


  


"Dakata ina ga wannan ne, Gidan tsayawa driver na a daidaita ɗin Ya yi a ƙofar gate na wani makeken Gida, sannan suka fito.

Miƙa masa kuɗinsa tayi sannan ta juya tana kallon ɗayar Budurwar wacca suka zo tare tana faɗin.


"Mu shiga ciki ko."


Murmushi tayi sannan ta ce "Muje tohm."


Kwankwasa ƙaramar ƙofar gate ɗin tayi Sannan gate man ya buɗe Suka shiga ciki.


Sai da suka isa dai dai ƙofar palon Gidan sannan budurwar ta kalla ƴar uwan tafiyarta ta tana cewa


"Yanzu Humaira idan muka shiga mai zamuce ne?."


Murmushi Humaira tayi tana bata amsa da cewa


"Kawai zamu ce ne munzo ganin Juwairiya Jabir Bici domin mu tayata jaje, ko kuwa dai ke Jiddarh ba zaki iya faɗar Hakan ba ne?."


Ajiyar zuciya Jiddarh ta sauke tana shirin magana aka buɗe ƙofar palon saboda haka basu tsaya jiran komai bah

 suka shiga ciki.


Nuna musu kujera budurwar da ta buɗe ƙofar tayi, sannan bayan sun zauna ta ce 


"Wurin Auntie Juwairiya ku ka zo ko?."


Tayi musu tambayar daga inda take miƙe.


Murmushi Jiddarh tayi sannan ta ce "Eh wurinta mukazo fatan dai tana nan?."


Murmushi ita ma budurwar tayi sannan ta ce


"Eh tana nan barima na kira muku ita kawai."


Tayi maganar tana nufar staircases.


Ya ye Niƙab ɗin da ta rufe kyakyawar fuskarta dashi, Jiddarh tayi tana faɗin 


"Zufa wallahi sosai."


Dariya Humaira dake latsa wayarta tayi tana faɗin


"Ni dama ban san gulmar da ya saka kika wani sanya Niƙab ba sai kace wata ɓarauniya, ba sarauniya ba.🥰


"Kedai kawai Humaira Ba za ki fahimta bane, kawai saboda tsaro na sanya fa badan tsoro ba."


Ta ƙarishe maganar tana kallon kyakyawar budurwar da ta sauko palon da suke zaune ita da wannan budurwar da ta buɗe musu ƙofar.


"Sannun ku fatan kuna lafiya. Ya Hanya."


Budurwar tayi musu maganar a lokacin da take zama a kujerar dake fuskantar nasu. Yayin da ita ma ɗayar da alama ƙanwarta ce ta zauna kusa da ita.


Fuska washe Jiddarh ta amsa da cewa


"Lafiya qalau wallahi,bFatan kema Hakan, sannan kuma ya jiki, ya aka ji da al'amuran?."


Tayi maganar tana ƙarewa Budurwar kallo ta cikin Niƙab ɗin fuskarta, ta fahimci ba wata Babba bace cancan domin iya Lissafinta zasu iya zuwa sa'anni da ita.


"Jiki kam Alhamdulillah, Ina Godiya sosai da nuna kulawar ku a gareni."


Cewar Budurwar cike da fara'a.


"Aunty's please ga abin taɓawa fa, Bismillanku fa."


Budurwar tayi maganar tana musu nuni da saman center table na Palon.


"Mun gode sosai."


Cewar Jiddarh still bata cire Niƙab dake fuskarta ba.


Ƙarisawa Humaira tayi Sannan ta ɗauki Juice a cup daga saman tray dake kan center table ɗin, sannan ta koma ta zauna suna ɗan taɓa fira sama sama kai daga ganin Yanayin da suke kasan ba wani sabo ne a tsakanin su ba.


Knocking ɗin ƙofar palon da suka ji ne. Yasa budurwar da ta buɗewa su jiddarh ƙofar palon.

Nufar ƙofar tana faɗin

"Mudai Gidan nan muna shan baƙi sosai, gashi kuma Mamy bata nan."


Ta ƙari sa maganar a daidai lokacin da ta buɗe ƙofar tana kallon kyawawan Ƴan matan da suke tsai tsai ye bakin ƙofar su Biyar, mace ɗaya ta gane cikin su.


Da sauri ta matsa gefe domin basu Hanya tana faɗin 


"Lah Auntie Hameeda kece?, barkan ku dai ku shigo Please."


Ƙari sa shiga palon suka yi gaba ɗaya sannan suka zazzauna. 


Kallon su Humaira bayi babu shiri ta waro idanu tana faɗin

"Kaga wani katari Hameeda Sagir kece dai ko kuwa gizo ne?."


Murmushi Hameeda tayi bayan ta zauna a kujera 2sieter ita da Lailah. Yayin da Afeefah da Mah'eesha da kuma Deejarh suka zauna a 3sieter kusa da Jiddarh wacca har zuwa lokacin bata cire Niƙab dake fuskarta ba.


Da yake palon ƙatone kuma kujeru set Biyu ne, shiyasa ya wadace su duka.


Ta ce 


"Ni ce mana Humaira kice dai kuma kunzo ganin Juwairiya Jabir Bici ce, me yasa bakizo da Jiddarh ba ne."


Tayi maganar tana kallon Jiddarh dake zaune da alama bata gane ko wacece zaune ba.


Murmushi Humaira tayi sannan ta nuna ma ta Jiddarh ta ce 


"Ga Jiddarh ɗin, anan gulma ne kawai ya sakata rufe fuska da niƙab, hala dai baki gane ta bane?."


Da sauri Hameeda ta kalla Jiddarh tana washe Baki ta ce 


"Ikon Allah kunga dai wani katari again wato ga sᴀʀᴀᴜɴɪʏᴀʀ ᴋʏᴀᴜ ta Abuja anan, sannan kuma ga sᴀʀᴀᴜɴɪʏᴀʀ ᴋʏᴀᴜ ta Kano State. kunga wani ikon Allah ko?."


Tayi maganar tana kallon Afeefah sannan tana ci gaba da faɗin


"Feefah Mai Kyau gafah Jiddarh SARAUNIYAR KYAU ta nan Kano State."


Sannan ta kalla Jiddarh still murmushi ɗauke saman kyakyawar fuskarta take cewa


"Lah Jiddarh kema dai ga Feefah mai kyau SARAUNIYAR KYAU ta madinatul Abuja City anan. saboda Haka What next?."🔥💃🔥


Da Wani irin mugun sauri zuciyarta na mugun luguden bugu, Juwairiya Jabir Bici ta ɗago dara daran idanunta tana kallon su gaba ɗaya.🙄


Yayin da ita ma Afeefah fuska ɗauke da ƙayataccen murmushi ta juya tana kallon budurwar dake zaune wacca Hameeda ta kira da Jiddarh SARAUNIYAR KYAU ta kano State.🥵


Yayin da Lokacin Ya yi daidai da ita ma Jiddarh ta cire wannan niƙab ɗin dake fuskarta, ta juyo tana kallon Kyakyawar Budurwar wacca ita ma Hameedah ta kira ta da ita ce SARAUNIYAR KYAU ta Madinatul Abuja.💥💃💥


   💫💫 Ⓦⓗⓐⓣ ⓝⓔⓧⓣ?💫💫


Menene zai faru gaba a tunanin ku?.

Akwai chakwakiyoyi fa a gaba domin bana ce chakwakiya ɗaya ba🔥🔥


Na farko dai

Shin Momy Rafi'at zata rabu da su Afeefah kuwa, ko dai still akwai abin da take shiryawa?😟

Na Biyu

Shin bakwa tunanin kashe Hajarah akayi bawai mutuwa tsakani da Allah tayi ba😓

Na Uku

Shin wanene ko wacece ta shirya sace Haleesat Rashid Rayyan da aka yi, Menene Kalmomin guda shida da aka rubuta a hannun Haleesat Rashid Rayyan suke nufi?😔

Na huɗu

Shin Juwairiya Jabir Bici zata haƙura ne da burin ta son Zama SARAUNIYAR KYAU ko kuwa ya ya zata kaya?🤔

Na Biyar

Wai shin ba za ku so sanin Labarin Soyayyar Zaynerb ba?, Wani kalar ƙalu bale ta fuska da ya janyo ma ta shiga shaya shaye?😰

Na shida

Shin ba za ku so sanin Wacece zata zama Miss Nigeria ba wai, Afeefah Mai Kyau ce ko kuwa dai Jiddarh Komai Naga ne?🤑

Na Bakwai

Shin wanene Bardia Wacece Budurwar da yake gani a video?🙄

Na Takwas

Wai shin wanene wannan Official ɗin ne?🤔

Na Tara 

Wai Wacece Heart Cheng Jung ce wani kalar alaƙa ce tsakanin ta da Sunainah?🥺

Na Goma

Wai shin Auren Maleek da Husnee zai yiwu kuwa?…..

Wanene Likitan ƙasa da ƙasa da ya taimakawa Maleek a Rasha ne??????????🌀🌀🔥🔥


*You duk amsoshin waɗannan tambayoyin suna tafe cikin Takun Tsakiya wato SARAUNIYAR KYAU ba*


*Ke dai kawai ki hanzarta bi*

*With This Details.*


_-_-_-_-_-_

*The Phone Number*

*****

*The Acct Number*

*8081129487*

*The Bank Name*

*Palmpay Bank*

*The Acct Name*

*Khadeejarth Sabi'u Yahyah*


~Karku bari a baku labari fa🤩~


~*SARAUNIYAR KYAU*~🔥🔥Takun Tsakiya_-_

*Iya kuɗin ki iya shagalin ki Hajiya*


ALHAMDULILLAH END OF BOOK 1

______________________________________

DOMIN SAMUN CIGABAN LITTAFIN SARAUNIYAR KYAU BOOK 2, MUTUM ZAI BIYA 500 NE, VIP KUMA 1000, WANDA YA SHIRYA BIYA SAI YA TUNTUƁI NUMBER TA, *** KADA KU BARI ABAKU LABARI FAH 🔥


👸👸👸👸👸👸

👸👸👸👸👸

👸👸👸👸

👸👸👸

👸👸

👸

W_&_S

The Nainarh Kd💝