SUMAYYA

Page 20

by @sanazdeeyah

*SUMAYYA*

_Wattpad@SaNaz_deeyah_

_Arewabooks@sanazdeeyah_

Youtube: ***

*KARAMCI WRITERS ASSOCIATION*

_[tushen mu'amula tagari]_


```Page 20```


Ƙofar take bugawa amma sam Ayrah taƙi buɗewa, har sai da suka kira daya daga cikin ma'aikatan gidan wani ya ɓalla ƙofar, suka sameta tana kuka tana ɗaura gyaluluwanta a jikin fanka.

"Kashe kanki za kiyi Ayrah?"

"Daddy babu mai ƙaunata gara na mutu" Ta furta cikin matsanancin kuka.

"Muna sonki" ya furta yana rumgumeta, tasha kuka sosai shi kuma yasha rarrashi tare da faɗa mata illar abinda take shirin aikatawa.


"Kamal ɗin ma yazo Mommy" Nihal ta faɗa tana dawowa daga taga zuwa kan kujera, ita kuwa Mommy rai a ɓace ta kafawa ƙofar ido. A sanyaye ya yi sallama dan kallo ɗaya za ka masa ka gane yana da damuwa. Da ido kawai Mommy ke binsa har sai daya samu kujera ya zauna, kafin ya gaisheta.

"Mene yake faruwa a gidanku da ka ɓoye min har tsawon sati biyu muna ta neman Sadeeq?"

Kafin ya yi magana Daddy ya fito, dan haka gabaɗaya kallonsu gareshi ya koma. Har ƙasa Kamal ya duƙa ya gaidashi sai dai maimakon amsa kawai sai jin saukar mari ya yi, da sauri ya riƙe kuncinsa. Nihal ganin haka ya sa tayi saurin tashi ta bar parlour.


"Mene gaskiyar abinda ke faruwa naji wasu maganganu marasa daɗi." Shiru ya yi baice komai ba.

"Kayi magana ko na maka hukuncin daya fi wannan." "Daddy wallahi gabaɗaya setup ne"

"Setup?" Daddy ya sake faɗa.

"Eh kuma ba wani bane face Laila da Sumayya, Daddy sun yi amfani da damar su ta ganin ina shaye-shaye suka ƙulla makirci kawai dan su rabani da Jidda, amma sam babu abinda ya haɗani da matarsa"

"Karka raina min hankali, nayi magana da ita Jidda da iyayenta, amma taƙi tayi magana sai kuka, sannan ta rantse ba zata koma gidanka ba, har mahaifinta ya tabbatar mana da lallai sai dai a raba auren, sannan ita Hamdiyya Sadeeq ya saketa ya kuma tafi bamu san ina ya yi ba wayoyinsa sam basu shiga dole kaine zaka faɗa mana gaskiya"

"Daddy wallahi duk makircinsu ne amma ni sam babu abinda nayi kawai sun yi amfani da shaye-shayen da nake sun san idan suka faɗa masa zai yarda saboda shi dama yana da saurin yarda"

"Idan har na bincika na gane gaskiya ranka zai yi mummunan ɓaci"

"Na amince Daddy" Ya faɗa a ɗan tsorace.


"Ni dai auren yarinyar nan ya zame mana masifa, domin duk shi ne abinda yabi ya hargitsa lissafi, wallahi na tsani Sumayyar nan ni dama tun a farko ma bata min ba."

"Yanzu dai ba wannan ne a gabanmu ba, kuma babu wanda zamu bawa gaskiya a yanzu."


          ******* *******


"Kin yi babban kuskure Hamdiyya, ni nayi tunanin tunda kin yi aure za ki ajiye duk wasu makaman yaƙi."

Ajiyar zuciya tayi sannan ta janye pillow data ɗora a cinyarta ta kalli ƙawarta "Mansura shi fa shaiɗan da kike gani ba rago bane, ni kaina yanzu nadama nakeyi da tunanin ruɗin shaiɗan dana bi"

"Ni wallahi Sadeeq ɗin ya fi min Kamal ɗin ma"

"Ni duk bama wannan ba, wallahi in kin ga yadda aka sakoni gaba a gida za ki sha mamaki, Abba fa har yanzu bincike suke kan lallai sai sun san dalilin daya saka ya sakeni, ni dai ce masu nayi ba laifin dana masa"

"Idan kuwa suka gano wallahi sai sun tsine miki"

"Faɗa ma ɓata harshe ne Mansura, ina cikin gagarumar matsala wallahi ko baccin kirki bana samu nayi"

"Ai duk laifinki ne anyi rufa-rufa anyi auren amma sai da kika nuna hali maimakon ki tuba"

"Wallahi Mansura sai na koma gidan Sadeeq"

"Kin san darajar rantsuwa kuwa?"

"Sosai ma, ai sai dana rabu dashi nake jin mugun son shi"

"Lallai Hamdiyya na yarda shaiɗan ya gama fitsare miki kai, taya za ki koma gidan mutumin da a yanzu babu aure tsakaninku?"

"Zan yi auren kisan wuta kafin ya dawo, na san ya gudu ne saboda ɓacin rai amma tabbas zai dawo"

Baki kawai Mansura ta saki tana kallonta.