Chapter 16-17
by @oumyasmeen
*DESTINY LOVE*
_Story and writing_
*By*
*Oum yasmeen*
*KING AND QUEEN WRITING CHAMBER*
*PERFECTLY PEN'S*
*Ina godiya masoyana ina ganin saƙon fatan alkhairi nagode sosai Allah ya bar zuminci*
*Episode 16 שש עשרה (Shesh Esreh)to 17 שמונה עשרה (Shmoneh Esreh)*
*TARÉËK*
Kallon kallo a ka shiga tsakanin tareek da jameel lumshe idanuwansa yayi da suka kada sukai ja yawa garwashin huta ƙara kasa kunne yayi domin yana tamtama anya kuwa kunnuwansa gaskiya sukaji wani uban kambara aka saki inda me shela yace
"A yau aka ɗaura auran MUHAMMAD TARÉËK da zanka ɗeɗiyar amaryarsa SAFNA ABDULNUR a kan sadaki dubu dari biyu,
gaban jameel ne ya waɗi ya dubi tareek tabbas abba bewa tareek adalci ba shin besan wace ce SAFNA ba yarinyar da bata ji wani irin bugawa zuciyar sa tayi da yatuno da lalurar tareek kafin yace wani abu tareek ya buɗe murfin mota ya fita cikin izzah da ƙasaita yake tafiya wanda cikar kamala da mazantaka wanda tarin shekaru da ilimi suka haifar mai ita kallo daya zakai mai kasan cewa tabbas namijin gaskene ko a cikin maza sunan shi mazaje
malam liman wanda shine limamin babban masallacin BN NADER dake unguwar gadan ƙaya ajikin estate ɗin su yake ya fito murmushi ya sakarwa tareek ɗin kallo daya zakai mai kasan cewa ransa ya ɓaci fuskarsa tayi ja abinka da farar fata ba kowa yake iya gane wannan fushin kamilalliyar fuskarnan ba amma a yau sai gashi kowa na iya gani takowa malam liman yayi ya ruƙe shi shine mutum na farko daya fara koya mai karatun addini a gunsa ya sauke yanzu haka yana iya rubuta Alkur'ani dan haka wasu suke ce mai gwani yana da wani mutunci da ƙima a gunsa mazai iya tuzarta shi a gaban mutane ba amma yau ace ƙannan mahaifinsa ne suka ruƙe shi da wallahi sai yayi hulli da mutun cikin nasiha yace
"Me babban suna kai hakuri kai hakuri a duk lokacin daka ga an cuce ka hakan na nufin nasara wallahi Ni shedane mahaifinka be so ba dan Allah in zaka tashi a bunka ka cire mahaifinka wallahi fin ƙarfinsa akai kadena tunzura ko dan ciwon ka yana bukatar sanyin zuciya in baka bi iyayen ka kana tare da taɓewa suna da wani ƙima da daraja a gunka tilas ka bi umarnin su inhar ba saɓawa mahaliccin ka suka umarceka kayi ba shine zaka bujere musu anan ba biyyah gun saɓawa mahalicci wannan auran auran manufa ne insha Allahu bazasu yi tasiri ba andade ana ruwa ƙasa na shanyewa kai hakuri kai haƙuri tareek,
tabbas inyace nasiyar malam bata shigeshi ba yayi ƙarya duk wani gana most go da ya cika na rashin mutunci da zai zube musu ba rabi amma bawai ya haƙura bane sai ya tauna tsakuwa dan aya ta ji tsoro ita kuma safna yayi muskilin murmushi saita gwammace kida da karatu saisaita kaisa yayi yace
"Malam nagode Ni zan shiga ciki,
Malam ya karanci TARÉÉk tsab a kwai abunda ya ke ɓoyewa amma koma mene Allah yasan ya mai sauki da salama a zuciyar sa domin yasan bawai ya haƙura bane yace
"To afito lafiya Allah yayi albarka,
Lips ɗinsa ya motsa yace amin
Can kuwa babban floor tun zuwa tareek an sanarwa da sitti amma batayi tsammanin zai barta ba batare da ya zo ya gurza mata rashin mutunci ba shirunsa na nufin abubuawa da yawa gwara yayi a yanzu da ya shirya wata gada zaran wacce tasan zata iya afkawa da mutane da dama na estate ɗin mama amina tace
"Sitti yanzun nan salim yake cemin tareek yana floor sa anya kuwa wannan taƙadirin yaron ba wani abu yake shiryawa ba shirunsa matsalane fa sitti?,
gyara zamanta tayi ta ɗauki tufa na gutsura duk zakinta ɗacinta taji tasan halin tareek tsab to wallahi abun da zai zo musu yafi shirin su tace
"Maman amina ina zansani amma kwai lauje cikin naɗi kinga wannan malam liman din hmmm akwai wata a ƙasa,
Mommy Hafsah tace
"Sitti ai ba liman ka dai ba kinga wannan munafukar Aysha daki ke ganin ta ɗan dai tana ji da mutuwar makahon danta ne da tuni ita zata maye gurbin malam liman,
SAFNA da tun dazu take ta juyi tana rawa burinta ya cika amma inta tuno cewa ita ba cikakkiyar buɗurwa bace hankalin ta na tashi ƙarfa a first night ɗinsu ya sake ta amma ai mommy tace zata bugemai baki
*Hmm muje zuwa yanzu wasan ya fara*
__________________________
"TAREEK tun ɗazu kake haɗa jaka ina zaka kuma naga ka ajiye jami'an tsaron a kofar shashin ka me hakan ke nufi ?,
Passport ɗinsa ya ɗauka ya zora a briefcase ɗinsa sai a lokacin yaga damar magana yace
"Kai ma inzaka haɗo kayan ka yau sai Palestine daman a gobe ce tafiyar amma na yi booking tickets yau har da naka nan da karfe 5:39 jirgi zai tashi,
sakar baki jameel yayi yana kallon sa ya yarda tareek shegen me raine shi daman yasan shirunsa na nufin abubuwa yace
"So fa wayan nan jami'an tsaron?,
banza yayi mai sallamar aunty Ayesha suka shi da sauri tareek ya amsa yana bata izinin shigowa shikwai gogan ko motsi beba yana aikin gabansa gaban tane ya waɗi ganin logges a gaban su tace
"Ba dai tafiya za kuyi ba ?,
Jameel yace
"Akwai wani project da zamu gabatar a ƙasar Palestine zamu je samo bayane ne shine tafiyar ta taso,
Kallo ta maida ga tareek tace
"Ka fadawa abba?,
Sai a lokacin ya ɗago ya dube ta zai yi magana tace
"TAREEK kai min alkawari fa ba jayayya tsakanin ka da abba please kaje kai mai sallama ko addu'a yayi maka zaka samin ninƙin nasara fiye da yarda zaka sameta nasarar mu ta tafiya tare da albarkacin iyaye tareek,
Kallon kallo aka shiga tsakanin MUHAMMAD da jameel sun san zancan ta gaskiya ne amma shi baya iya jin zai je yayiwa mahaifin sa sallam mutunmin dake cinye dukiyar al'umma mutumin da ke danne hakkin maraya shifa ya tsani siyasa amma wallahi yana gab fitowa matemaƙin gwamna tareek gwamna domin su kwatowa talakawa hakkin su ko ruwan gidan su baya iya sha dan yasan duk haramunne yace
"Bara in kira hajiya in mata sallama amma dady nasan yana office yanzu bazai ɗauki waya ba ,
Aunty Aysha tace
"Duk da haka kira shi ko kai mai text message,
bayar da ya iya haka ya kirawo su sun mai fatan alheri tafiya suke cikin nutsuwa yayin da aunty Ayesha tayi shashinta su kuma suka shiga shashin abba bazai iya tuno yaushe ne ranar sa ta karshe shiga shashin abba ba haka badan ya so ba ya tura kai yana zaune abban floor ashe sitti ma na floor a lamar wata magana suke tana ganin sa tace
"Yauwa dan ƙanin ubanka Abdullah Ka ɗauke min wayan nan mutanen da kakawo min gidana tun kafin ran kowa ya ɓaci amarya kuma yau zata tare a shashinka,
be kulata ya sami gu yayi ya zauna cikin ladabi suka gaisheshi tareek yace
"Abba daman nazo in maka sallam zanyi tafiya,
Sosai mahaifin nasa yaji dadi yace
"To Allah ya tsare ya bada abin da aka je ne ma,
Amin suka ce ban da sitti da zuciyar ya ke a tunzure yama raina mata hankali tana magana yayi kunnan uwar shegu
Abba yace
"Zuwa ina?,
Ƙasa da kai tareek yayi yana jin wani ɗaci a zuciyarsa jine ya gangaro ta hancin sa da sauri jameel ya ɗauko mai tissue sai dai be ƙarɓa ba ya ɗauko farin
handkerchief ya goge sosai hankalin abba ya tashi yace
"Sannu Allah ya baka lafiya,
Runtsai idanuwansa yayi yace
"Amin Palestine zamu an aika mune a gun aikin mu,
Da sauri sitti tace
"Wallahi baka isaba so kake ka maida min da jika ƙaramar bazzawara to wallahi a hir ɗinga sai tasa kuka yanzu Ubaidu kana gani ɗanka na cimun mutunci kayi shiru wane besan cewa gun nan ko tsuntsu ya huce sai sun kashe garin yan ta'adda amma kai shiru ga hukuma da yazo ya zube min a gida,
Cikin ladabi yace
"Ji haƙuri sitti kinga ga yace agun aikin sune sannan zan sa ya ɗauke su,
Majina ta fyece tace
"Wallahi yaron ne me zuciyarsa kafuran farko ya rainani wannan Allah ne ya ragewa aya tsaƙinta be fito a arne ba yaro yawa jikokin Bature ko da yake inji ke juyashi ba mamaki dan yana da taurin zuciya,
inda take tareek be kallah ba be ma nuna mata yasan me take faɗi ba ya tashi yayiwa abba sallama mama Amina tace
"Amma tareek ka ganmu ko ai wani kallo da ya jefa mata sai ta nutsu domin tasan ƙaramin aikin sane ya fara hulli da duk kayan da yaci karo agarin haka kwanaki yayi mata karaya in abin nasa ya tashi yawa zaki yake komawa
fita yayi cikin sarsarfa Muhsin jameel ya ƙiran sa ya kai su airport filin tashi da sauka na malam aminu kano international airport tuni jirginsu ya tashi sai Palestine Muhsin ya dawo da motar gida
*_________BABA GANA ƘYARI FAMILY*
knocking ya Shiga yi cikin hausar ta mara fita tace
"NUR bana faɗa miki ba zan fito shine kika dawo,
gyaran murya babah yayi yace
"Ummin nur nine,
Jikinta a sanyaye ta taso ta buɗe kallo yabi ta dashi bayan ta matsamai tace
"Múndú máá,
shigowa yayi ya zauna cikin sakin fuska yace
"Yauwa Kú fárá ndá?,
murmushin karfin hali tayi cikin kulawa da soyayyar mijinta kuma uban ya'yanta tace
"Ndá kú sírè,
rungume ta yayi yace
"Kalmtum kiyi haƙuri kinji komai yayi zafi maganin shi Allah kamata yayi ki manta da abin da ya faru ko dan lafiyar ki,
Kuka tasa tace
"Yauwa naga ahalinsu kuma me kama dashi sai ta ƙara fashewa da kuka,
da kyar tayi shiru yace
"Wanke fuskar ki muje floor yaran duk sun damu,
tashi tayi ta shiga toilet murɗa fanfon sink tayi ta wanke fuskarta da showar jel me daɗin kamshi fitowa tayi tasa towel ta goge fuskarta ta dansa power dariya yayi yace
"Wow kin yi kyau,
Murmushi tayi hannunsu asarke da juna suka fito da sauri nur ta rungume ta tasaki kuka ummi tace
"Ki shiru dan Allah ai na fito kaina ne yake ciwo,
Nur tace
"To Allah ya baki lafiya,
Amin tace
Zama sukai azizi yace
"Ku tayani murna yau andawo da king of journalists kula da lafiyar sa ta dawo hannuna hakan ba ƙaramar nasara bace a guna na zama consultant doctor insha Allahu zan kawo karshen matsalar sa,
Murna suka taya shi ace zai duba mutun kamarsa yace
"Wallahi ummi jinsa nake kamar dan uwana ina jin tashin lafiyar sa ajikina,
Baba yace
"Allah yasa ya sami sauki,
Amin suka ce
Aeesar yace
"Kasan ɗazu mun haɗu da shi ina sane na faffadamai magana wallahi girman kai ne da shi,
Saurin dagowa aziz yayi yace
"Daman kai katada mai da ciwonsa gaskiya aeesar baka kyauta ba yana gudun mutane ne saboda ciwonsa da kuma gudun bakin jama'a,
*Zuciyar ummi ce tayi wani irin bugawa ta dafe kirjinta tace.....✍️*
*🌹 Perfectly Pen's ✍️✊*
*Our Ongoing Book's...✍️*
*1_SHIRYAYYIYAR ƘADDARA.*
*BY: Queen Kainaat.*
*2_RANAR BIYAN BUƘATA.*
*BY: Nainarh KD Nkd's.*
*3_DESTINY LOVE.*
*BY: Oum Yasmeen.*
*Mun Shirya tsaf domin kawo muku daɗaɗan littattafan mu masu cike da ilmantar wa faɗakarwa tunatar wa wa'azantar wa har ma da Nishaɗantar wa.💝*
*🔥Kada ki bari wannan tafiyar ya kasance ba tare dake ba. Don't Miss It Dearest sisters 🔥*