MUMMUNAR DABI'A

Chapter 3 Book1

by @asmabaffa1

🪸MUMMUNAR DABI'A 🪸


         11-15



Official


By

AsmaBaffa



SADAUKARWA NE GA 'YATA TASNIM



Page naki ne 

Mrs Chief




MASU AUDIO BAN YARDA A SATAR MIN NOVEL A JUYA BA,DUK WANDA YA DORA A CHANNEL SAI AN SAUKE.







     Gidan nasu yana da kyau sosai Sahil har palo Khalisat ta shigar da shi wanda palon ya gaji da kyau da tsaruwa, murmushi tayi tace sit,zama yayi ta shiga kwalawa Mum kira tana cewa Aunty dake duk ta hanasu kiranta da Mama ko Mum kawai Aunty ce kar su kara cewa ita ta haife su,Aunty ce ta fito tare da Khairat,suka zubawa Sahil ido suna kallonsa,Aunty ta hadiyi yawu dama ace saurayinta ne,itama Khairat haka,Aunty tana yiwa Sahil kallon duniyanci tace wannan fa? Khalisat tace he is my friend zai dan zauna damu for a while kafin ya samu gidan zama,ai dakin nan a gyare yake? Aunty ta saki murmushi tace a ranta da alama akwai kudi a hannunsa.


  A fili ta furta ba damuwa a gyare yake ai ki kaishi sai a kawo masa abinci da ruwa, yaje yayi wanka ya huta,Khalisat tana murna ta riko hannun Sahil tace lets go,hannunsa ya fisge tare da hade rai ya mike ya bita har bedroom lafiyayye me dauke da gado da sip da mudubi tare da toilet dakin yayi kyau,ac ta kunna masa tace kayi wanka bari naje nima zanyi wanka sai na sa yar aiki ta kawo maka abinci,Sahil dai yana kallonta da mamaki abinda suke masa ba tare da sun san shi waye ba.


  Bayan ta fita yace karfa ko yan mafia ne ban sani ba,no..no..kaina yafi karfinsu baza su iya dani ba,Allah bazai basu iko a kaina ba,wani tunanin ya sake ya furta kaiiii....karfa naji na bace kar a siyar da kaina,su din banza nafi karfinsu yace sannan ya shiga toilet abinsa,wanka yayi ya fito ya saka kayansa kanana riga da wando,Navy color ya sha uban kyau sosai, gefen rigarsa ma da yar laimar ruwan jiya da ya zane shi.


  Knocking yaji anyi,yace come in,a hankali aka turo kofar tare da shugowa dauke da sallama a bakinta,Sai yaji kamar yasan muryar,Islaha ce ta shugo dauke da tire a hannunta na abinci da ruwa,sanye take da Hijab har kasa tana wani dari dari,a hankali ta dago kanta suka yi ido biyu,yace you.....yana nunata da yatsa,kanta ta sadda kasa fuskarta dauke da murmushi ta dago a hankali


  Fuska taga ya daure kamar bai taba saninta ba a duniya,mamaki ya kamata matuka,ransa a bace yana mata wani mugun kallo yace kalle ki kamar ta kirki a haka,munafukar banza,ido ta zaro tana kallonsa,yace ban san me ke damunku ba matan wannan zamanin masu fuska biyu,a fili kuna nuna ku na Allah ne a badini ashe kuna da wata mummunar Dabia da ba san da ita ba,daga yau karki nuna kin sanni a duniya,kuma duk wani abu nawa karki sake kice zaki taba,avoid me duk inda kika ganni karki sake ki kulani kuma karki taba min abu,abincinki dauki ki kara gaba bana bukata.


 Islaha tsoro da mamaki ya kamata,ita tasan bata masa komai ba ita,a tsorace ta juya! Ya ja mata wani wawan tsaki tare da furta stupid,yana uban huci ya kwanta a saman bed din,tuni Islaha ta fita ta bar masa dakin tana mamaki me ta masa sannan me ya kawo shi gidansu a ina yasan Khalisat,jajayen lips dinta ta turo gaba tace koma mene zan gani wlh Allah yasa ace dan iska ne me neman mata wallahi sai ya hadu da rashin mutunci na sai na fito da sabuwar bad character dina a gidan Nan,kowa sai yasan Islaha bata da mutunci,kowa sai yasan ni ba a gaban uwata na taso ba,kuma sai an san ni yar tuwo tuwo ce ta raini ni,badai suna bada gabansu ba maza suna ishiriniya abinsu,mace kawai ki bada jiki namiji ya dinga ishiriniya a kanki zan gani ta ja kwafa.


  Khalisat ce ta shigo dakin Sahil cikin wata gown guntuwa maroon wacce da kadan ta rufe duwawunta,Sahil dai kamar yaga namiji again,tace ya an kawo maka abincin? Yana kakkafe idanuwa yana masifa kamar ubanta yace wata banzar yarinya ce ta kawo bana so ta sake kawo min abinci,Khalisat tace Islaha ce yar kauye,ai wannan yarinyar dabba ce gaba daya,Sahil nan take yace a'a fa Allah ya gani dai mutum ce,Khalisat zata sake magana yace ba ruwana da ita ni kawai kiyi shuru,sam baya so a zageta,Khalisat tace yar iskar yarinya.....kafin ta rufe baki ya fara waka dan kar ma yaji yana kida da bakinsa gijib... gijijib...tsayawa Khalisat tayi tana jinsa tana dariya wakar tasa ta hausa ce yake yin abarsa,Juyawa tayi tace bari na kawo maka abincin da kaina ta fice.


  Dauke da abincinsa ta dawo a plate jullof rice ce ta sha hadi da naman kaza ga ruwa da lemo,zama yayi ya fara ci Khalisat ta zauna a gefensa tare da dafa kafadarsa,ya zame a hankali yana cewa hannunki nauyi,kasar da aka halicce ki da ita wajen nauyi aka ebo,,kyale shi tayi tare da furta sorry tana lasar labba,yace ko ci zaki yi ne? da sauri ta furta a'a,sai bayan ya koshi sannan ta mike ya gabatar da sallolin da ake binsa har ya idar,Khalisat tana zaune a gefen bed din tana jiransa,juyowa yayi ya kalleta tare da furta zanyi bacci,Khalisat ba kunya tace zan iya taya ka kwanciya? idanuwa ya zaro sai da ta tsorata tun kafin yayi magana a fusace ya mike ya jawo jakarsa yace ki tayani kwanciya a wanne dalili raping dina zaki yi? Mikewa tayi tana bashi hakuri I'm sorry kwanta akan yar wannan maganar zaka tafi? Kayi hakuri kwanta abinka,ta fice da sauri sannan ya kwanta abinsa.


  Sohail....Adnan ya kwalawa kira....Sohail...ji wannan banzan yaron ina kiransa,Sohail ne ya fito daga kitchen da sauri,fada Adnan ya hau yi yace sabo da hauka kana ji ina kiranka,Sohail kansa ya nuna yace oh dama kirana kake yi? Uwarka nake yi cewar Adnan.

 Sohail yace ai ta mutu Maman,

Ba wannan ba ai ba ita ta haife ku ba,uwarku arniya ita nake nufi, Sohail yana tsaye sanye da jean black da riga arsh color yace kai ka santa ma ashe?

Dama muna da uwa? Kuna da ita arniya ba Adnan ya bashi amsa.

Arniya ce? Taji dadinta ba ruwanta da kishirwar azumi,ta tsula tsiyarta kawai ba komai.

Adnan ido ya zaro yace uwar taku? Sohail yace kai mu bamu da uwa.


 Yaya Adnan nayi sabuwar kawa me kirki,Adnan ransa ya baci nan take da kyar ya danne yace wace?

Wata ce sunanta Maheera kyakyawa ce sosai.

A ina take? A gaban layin nan take,Adnan yace lallai ya kamata na ganta mu gaisa

Sohail yace ba damuwa zan rakaka Sahil ma ya santa shima kawarsa ce mu kasan mace daya muke bukata,Adnan yayi dariya yace gaskiya ne mazaje yan biyu masu mace daya,Sohail yace ae mun sasanta kanmu ni da Sahil ko mace ta rungume shi nima sai tayi min nawa,Adnan yace nifa? Sohail yace direct yace a'a banda kai wlh ka kula mana mata sai gawarka.

Adnan ya jinjina kai yace matata zata zo anjima kayi girki me dadi,ba damuwa na kusa gamawa ma cewar Sohail"

Adnan yana takama ya juya ya haura sama abinsa.


  Zuwa yamma Zayna ta sauka a jirgi,Adnan da kansa yaje ya dakko ta,tayi kiba ta kara kyau ga wanka yabi jiki,Sohail yana shirya dining ya gansu Adnan ya rungumo kugunta sun shigo,Sohail ya kura mata ido yaga Zayna ce,mamaki ya kamashi da alama itace matar Adnan din.


  Nunawa tayi bata san ma Sohail ba,juyawa tayi ta kalli Adnan tace Baby wannan fa na tuna ashe fa kaninka ne,Sohail ko a jikinsa yayi murmushi yace yaya dama ita ka aura? 

Adnan kiss ya mannawa Zayna a kumatu yace ita ce,Sohail yace sannu Aunty ya juya ya wuce part dinsa cike da mamaki,wai Adnan ya auri budurwar su shi da Sahil,baki ya tabe yace suji dadinsu ni ina ruwana da Allah zai sa ma ni kuka yazo min ai kwana zanyi ina yi naji dadin jikina,ai kuka wani Exercise ne daban,kuka duniya ne,dama shi Sohail haka kawai ma in kan ya motsa kuka yake shi kadai haka kawai.


  Bayan Zayna ta huta dining suka zauna,Ibrahim,adnan da Zayna suna kwasar girkin Sohail suna hira abin su,Sohail ne ya fito ya wuce su da sauri,Zayna ta masa banzan kallo ta ja tsaki,bai ma san tana yi ba tuni yayi gaba,yana tafiya da uban sauri kamar zai tashi sama,wasu a layin sun sanshi sosai suna mutunci,sai magana suke masa amma sai dai ya daga musu hannu,ka rantse wani mummunan abu ne ya faru,bai tsaya ba sai da yaje shagon Maheera har ciki sannan yaci birki,ta dora kanta a table tana danna waya ya daki botiki da karfi ta tashi a firgice,dariya yayi yace nine,tace Oh Sohail ko sallama,kujera ya ja ya zauna yana so ya bata labari,yace bari na baki labari kinga ni gidanmu....gidanmu ..uhmmmm....katseshi tayi tace dan Allah ka kyale ni da surutun nan bana ganewa damuwa ta min yawa ka rabu dani,yace abu zan fada miki,tace no...ni kyaleni bazan ji ba kai labari ma kafin ka bawa mutum sai ya tsaya wahalar saurare.


 Shuru yayi,wasu suka shugo siyayya ya mike ya fara basu amma duk ya rage kudin abin dari biyar sai yace ku bada dari biyu an muku ragi dole mu kawo canji a kasar nan mu da araha zamu siyar,Maheera ta mike da sauri ta fisge ledar kayan tace ke kudinki ba haka ba ta lissafa kudin da kanta,matar tace me shago ya mana kyauta ki hana yar bakin ciki,Maheera tace ba shagon sa bane malama ta karbi kudinta ta basu kaya suka fice suna Allah wadai da Maheera me kudi yayi kyauta ta hana.


  Sohail ya kalli Maheera yana murmushi ya ja hancinta yace to bani alawa,kara maheera ta saki ta bige masa hannu tana shagwaba tace da zafi fa,Alawar ta ebo tace yau biyar zan baka ta mika masa ya zuba a aljihu tare da bare daya ya sa a bakinsa yace na gode na tafi gida.


 Sunansa ta kira tace "Sohail"

Amsawa yayi ya dawo ya zauna tace ina cikin damuwa yau,na rasa wanda zan fadawa naga munfi kusa da kai, sai ya nutsu kuwa yace ae ina jinki tell me.

Tace mamana tana da lalura tana Sule ja a gida ina da kanne biyu mace da namiji nice nake kula da karatunsu,Mamana ciwon sugar ne da ita ina shan wahala ta kashe kudin magani,gashi aikin nan da na samu oga ya sani a shago baya biyana akan lokaci gashi babu abin kirki a salary din,ga kula da kaina ga yan gidanmu,ubanmu tun muna yara ya rasu,yanzu aiki nake nema wanda ya dan fi wannan ko wanke wanke da shara ne indai yafi wannan albashi zanyi,Sohail ya nutsu yanzu.


  Ya dafa kafadarta yace akan wannan kike damuwa? Ki kwantar da hankalinki indai aiki ne zaki samu,zan nemo miki,kinyi karatu? Tace na fara university amma kasan bani da kudi dole na hakura yanzu ni kannena nake biyawa kudin makaranta,Sohail yace to za a samu wani karki damu kinji ke da kike da Allah,wannan ba matsala bace ki kwanta kiyi bacci in ta kama ma kina shan giya ki sha abarki aiki zaki samu Inshaallah.


Dariya Maheera tayi sosai da sosai,tace na gode to,aljihunsa ya duba ya ciro 4k yace suke nan gareni ragowar kudine da naje kasuwa siyo nama ungo ya mika mata,ta saki baki tana kallonsa yace karbi kyauta na baki kawarmu ce ke,

ta karba tana ta godiya kamar yasan bata da ko sisi sannan idan kana wajen wani a zaune dole ka dinga yiwa kanka wani abin, tace Sohail na gode,ya sake duba aljihunsa ya ciro naira ashirin yace ah sorry ungo wannan ma hada da ita.

Ta karba tana dariya tace na gode.

wajen shagon taga ya leka ya dawo da leda baka a hannunsa ya ajiye mata a table.

Mene kuma? Ta tambaya

Yace duba ki gani yana tsotsar alawa me tsinke,dubawa tayi taga naman kaza soyayye da yawa a ledar zai kai kaji biyu,ta zaro ido tace amma tun dazu baka bani ba kuma me yasa ka ajiye a waje jikin kofa?

  

  Yace ai bana so ki gani surprise zan miki kuma na manta badan kin tuna min ba da tuni na tafi na barshi a wajen,tace kai ka soya? Yace ae,na gode sosai,yace bani daya a ciki naci karki ce na saka miki wani abu"

Maheera harararsa take tace ai nawa ne bazan baka ba,Murmushi ya fice fit ko sallama bai mata ba.

Tayi dariya kawai ta fara cin naman.


  Yana komawa gida ya iske Zayna tana masifa a palo tace da Adnan ni gaskiya a kawo min mace yar aiki wacce zata dinga yi min girki da wanki da sauran hidima ta,shi Sohail ya muku naku,ni bazan iya cin girkin namiji ba,Adnan yana rawar jiki yace za a nemo yar aikin tunda haka kike bukata,Sohail yana ji yace yaya akwai wata ta iya girki sosai indai za a biyata albashi me kyau a kawo ta.


 Zayna tace karka kawo mana mahaukaciya irinka fa,Sohail yaji zafin maganar amma bai ko nuna ba yace ta iya fa, ina fada muku zan kawo ta nan ta fara yi muku na gwaji,idan kuka gwadata in yayi shike nan,Adnan yace ba damuwa tunda haka kace a kawo ta gobe tayi muji,yace an gama.


  Zuwa yamma likis Sohail ya koma shagon da Maheera take da sauri, Maheera tana zaune tana shan lemo da da naman da ya kawo mata, Sohail ya fado ciki yana sosa sumarsa wacce taji aski irin na kwallayen shegun gari,gashinsu kamar na mata daurewa suke da ribbon amma sun kwashe gefe da gefe an rubuta sunansu a gefe daya an saka Sohail daya barin Sahil,shima Sahil yaka yayi,Daddy yayi yayi su gyara sunki amma ba karamin kyau ya musu ba sai dai a al'adar mu ta malam bahaushe za ace ba tarbiyya.


  Maheera ta kalle shi tace Sohail ya ka dawo?

Yana murmushi yace albishirinki

Goro ta furta tana kallonsa"

Yace kin samu aiki amma sai dai ba irin na classy girls bane irinku,girki ne zaki dinga yi,matar Yaya tace baza taci girkin namiji ba,shine nace akwai wata zata yi,kin san nawa zasu biyaki duk wata? Maheera tace nawa?

Yace dubu dari,idan kina aiki me kyau zasu iya kara miki ma.

Zumbur Maheera ta mike tana tsalle da murna kamar yarinya,tace wannan fa dubu ashirin yake bani duk wata!

Yes zanyi zanyi ba matsala,wayyo dadi Alhmdllh Allah na gode maka,tana murna tace Alhmdllh.

Gaskiya Sohail kai mutumin kirki ne na gode.


Sohail yace na fada miki ai ko kina shan giya ki sha abarki kiyi bacci aiki zaki samu,gobe zamu je zaki musu abinci da yamma zasu yi miki test in kinci shike nan an dauke ki,kuma nasan ma kin iya girki!


Na iya girki sosai Inshaallah zanyi kokari zan dage Sohail.

Sohail ya furta aha Sahil yace a gaida ki,kin san da za a haifo mu a tare muka fito duniya ba wanda ya riga wani zuwa,Maheera ta iya bi da Sohail ta kalle shi tana dariya tace Allah? Aradu ya furta yana daukan alawa 


 Dariya ta sake saki tace amma yau naji dadi come ba zato Sohail yaji anyi hugging nasa,ido ya zaro da sauri ya janye jikinsa tare da ja baya yace mene haka? Sahil fa baya nan,to wlh shima sai kin masa na rantse.


  Ido Maheera ta zaro tana murmushi tace Sahil din? Sohail yace ke ba a wasa damu na fada miki sai kin masa shima ya hade rai,Maheera tace to never mind zan masa shima amma ai kaine abokina Sohail ka gane?

 Ni bazan gane ba kawai malama zamu yi fada,Sorry to zan masa shike nan? 

You promise? ya sake tambaya,tace yeah,yatsa ya mika mata yace mu kulla,ta kawo nata suka kulla ta furta shima sai an yiwa Sahil? yace kamar da kasa.


  Juyawa yayi zai tafi ta ruko shi tace na sallameka ne? Ban gane ba sai ma kin sallame ni? Ke mace fa ni baza ta juya ni ba in fada miki gaskiya 'yar nan, Maheera tayi dariya tace to fa,har ya tafi ya dawo yace na fasa tafiya zo muyi game? 

tace wacce iri ba kayan game a nan.

Wasan yar buya buya zamuyi,okay ka bari sai gobe idan naje test sai muzo muyi kaga ko Oga ya kama mu kawai korata zaiyi shike nan.

Sohail yace no ba a haka kuyi rabuwar mutunci basai munyi ba tunda baya so.

Okay tace kawai,kallo ya fara kare mata yace wai mene wannan a kirjin ku? 

Sam Maheera bata gane ba,yace gashi nan tulu tulu ana gani.

Maheera fuskewa tayi duk da taji kunya tace shi kuka sha kuka girma,yace Allah sarki na Mama yana kabari yanzu ina tunosa ke ya akayi naki chakare chakare ita kuwa Umma Nadia nata kamar na tsohuwar saniya wacce yunwa ta kamata.

Maheer ta dinga dariya ba shiri tace Umman taku guda?


  Sohail yace ke bafa ita ta haife mu ba Na Mama yana Kabari nata me kyau ne Daddy ma ya dinga ta yashe baki idan tana wajensa ya dinga ta dariyar dole hahahaha ranar girkin Mama,Allah ko ni sai na iya Auren Mamata.


 Dariya ta sake kama Maheera tace ashe ta hadu dai?

Yace tab ke kin isa ma kice shekarunta 47, Mamanmu ta iya sa kaya ko wanne wanka kyau yake mata ga kamshi,gata da mutunci ke Mama fa duniya ce,akwai uwar data kai tamu ma,Maheera tace Mamata fa? Sohail ya bata rai yace ko uwarki bata kai Maman mu ba.

 Da sauri Maheera ta kalle shi tace zagina kayi fa Sohail,yace to ba uwarki bace? Uwarki mana nace bata kai tawa ba,nifa in kika takura min zan iya miki dukan tsiya.

Maheera tace ni din? 

Kwalla ce ta cika masa ido tab da ya tuno da Mama Asmau.

Maheera tace sorry mene abin kuka? Yace baza ki gane bane... baza ki gane ba ina ta so na baki labarin damuwa ta sai kice baza kiji ba labari na akwai jira kafin a saurara,tsaki ya ja ya fice yayi tafiyarsa .


  Maheera ta tsaya kamar gunki tana mamaki.

Bata yi tunanin zata ganshi ba washe gari ba

Sai gashi da yamma ya sha farar shadda tana shining ba karamin kyau yayi ba ka rantse wani me kudin gaske ne,ga kyau,ita kanta Maheera tsayawa tayi tana ta faman kallonsa,hannu daya a aljihu ya shugo yace ya garin me shago? Tace lafiya lau tana murmushi.

Hannunta ya riko yace zo mu tafi.

hararsa tayi tace bazan je ba shine jiya kayi fushi?

Yace ni din? Yana nuna kansa da yatsa yace me nayi jiyan? 

Au ka manta? Yace na manta kuma har ga Allah har ya manta ma,sai da ta tuna masa yace Oh ya share zancen kamar ba shi ba.

 Mikewa tayi suka fito,zata rufe shagon ya karbe key din yana cewa kawo kamar namiji mace tana wahala haka Mama bata irin haka,ai ana taba ki kice wash zan mutu.....harda gwadawa! dariya Maheera ta fara yi ba shiri har ya gama rufe shagon yace muje 

Juyawa tayi tana rataya handbag dinta,yace kawo  handbag din na rike miki ki daina wahala zaki yi muscles kamar na maza ki bubbude.

Jakar ya karba ya rike a hannunsa suna tafiya suna hira,yayi hauka yayi hankali a haka har suka je gidan su.


  Maheera kanta ya kusa bugawa ganin irin unguwar da suke da layin da suke balle uwa uba gidan nasu tamfatsetse na gani na nunawa sa'a,tace a nan kake zaune? duk bata kawo gidan uban Sahil da Sohail bane,tunaninta ma yaran riko ne ko 'yan uwa.

Sanda suka shiga Maheera tana ta kalle kalle ya kalleta yayi dariya yace kinga gida me kamala ko? Yana dariya yace ai kamilallen gida ne wannan ba ballagazin gida ba irin naku,nasan gidanku ballagazin gida ne.

Maheera tayi dariya tace kaima ai ba naku bane,bai ce mata komai ba,yace muje na nuna miki kitchen din,In kin gama girkin ki shirya a dining sai na kira su masu gidan su dandana.

 Haka ya fisgi hannunta ya jata ko ina na gidan sai da ta dinga hakkin sosai yanda yake fisgarta sai hakki take da nishi, da sauri yana nuna mata ko ina har katafaren kitchen din katon gaske komai akwai ciki,ya nuna mata komai da kayan sarrafawa,kin gane? tace ae naga komai da nake bukata akwai,yace yawwa to fara girkin ni bari naje na gyara dakin Adnan da na Ibrahim kafin nan kin gama,ta furta ba damuwa,ya juya ya tafi.


  Farfesu ta fara yi na naman rago sannan ta tsara fried rice lafiyayya taji hadi da su hantar rago da naman kaza,sannan ta hada couslow da lemo ingantacce ta shirya a Dining, har da potatoe ball tayi da kwai da nama a tsakiya.

 Tana gama shiryawa a dining ta zauna a palo tana kallon tv,sai taji karar takalmi me tsini ana sakkowa daga sama ,Kamshi na mamaki ya mamaye palon.


  Zayna ce take sakkowa ta sha wata material gown ready made abinta golden ta tsula kyau,kana gani kasan taji hutu da kudi ba karya,Maheera tsabar tsananin kyawunta yasa duk inda mace takai bata isa ta fita ba sai dai daiku tunda a duniya baka rasa wanda ya fika dole ne wannan.


  Zayna wani kallo ta bi Maheera da shi sama da kasa ta ganta sanye cikin material silk black me adon flower pink sai dan mayafi siriri data dora a kanta,takalminta normal dai na talaka me dan kyau gashi nan dai,sai dai kyawun Maheera ya tsoratata amma ganin mijinta yana da class kuma sannan yana sonta gashi ma shi sai me kudi yake kulawa sai kawai ta fuske a ranta tasan itama me kyauce komai da namiji ke nema wajen mace tana da shi.


  Maheera mikewa tayi tsaye da sauri tace good day Ma,Zayna ta wuce Dining kawai ta zauna ba tare da ta wani amsawar kirki ba,Ibrahim ne ya fito yayi arba da Maheera ya bita da uban kallo ya dauke kai ya wuce Dining ya zauna,shima tace Good day Sir, har tana risinawa,hannu kawai ya daga mata,Adnan ne ya fito shima yana zuba kamshi ya hade cikin kana nan kaya masu tsada blue, ko kallo Maheera bata isheshi ba ya zauna a Dining,sai ga Sohail shima ya fito sanye cikin gajeren wando da riga singlet da bocket da mopper a ciki ya hada uban zufa.


  Hannunsa ya goge da karamin towel ya karaso wajen Maheera yana murmushi yace kiyi serving nasu cikin rada yayi maganar.

Maheera ta karasa da sauri tana cewa kuyi hakuri" nan take ta fara serving nasu har ta gama,suka ga girki sharr tun a ido ga kamshi.

Ibrahim ne ya riko hannun Maheera zata juya yace zo ki canja min Spoon 'yar kauye.

 Tsoro Maheera taji akan idon Sohail aka yi,daga haka Sohail kawai idonsa ya canja ya nufi Ibrahim gadan gadan ya sa baki a saitin keyarsa ta baya ya gartsa masa cizo sai da wajen ya fashe,Ibrahim ya saki kara da ihu ya mike zasu yi kokawa da Sohail!

Adnan yayi sauri ya rike Ibrahim yasan yana hada jiki da Sohail sai buzunsa karfinsu ba na mutane bane,yace kyale shi kai zaka biyewa mahaukaci,abin kullum karfi yake fa sun fara duka da cizo nan gaba sai tsince tsince a bola suna bin yara da gudu.

 Zayna ta tabe baki tace yo ni da suka ce zasu aure ni su biyu ma.

 Sohail yace in Allah ya yarda baza ki haihu ba,mahaifarki ta mutu a haka zaki gama aurenki,Adnan yace ameen da sauri kayi addua me kyau dama ni bana son haihuwa, Zayna kamar zata yi kuka tace da Sohail mahaukaci karya kake,Maheera tana ta kallo ta gaji ta janye Sohail tace relax mana ta jashi suka koma gefe suka zauna,Sohail yace da Sahil ne ya rikeki da sauki bazan damu ba ai wannan ba yi bane,kawai a rike mutum idan kika masa ciki fa,Maheera ta danne dariyarta,tace au ba ma shine zai min cikin ba nice zan masa? Ina ka taba ganin namiji ya haihu? 

Sohail yace ke wancen kwarto ne tsaf zai iya haihuwa,tayi murmushi kawai tana boye dariyarta.

Kallonta yayi yace ki dinga rufe wannan chakare din naki ni bana son ganinsa duk sai gani ake ta yi Mama fa Hijab take sawa idan zata fita ba a ganin nata,badan ma mama ce ba ai sai nace miki bata da Chakare din nan.

Amma ke kowa sai gani akeyi haba Allah za a daina ce miki Classy girl me shago kawai yafi dacewa dake,Maheera ta rufe bakinta sabo da dariya.


 Can gefe kuma su Zayna sai kwasar girki suke yi me shegen dadi suna ta ci,Adnan cikin santi ya kira Maheera da hannu,ta karasa a nutse yace aikinki yayi kyau na daukeki aiki,zan dinga biyanki dubu dari,tana murna tayi ta godiya abinta yace gobe ki dawo nan da zama ki fara aikinki,ga Sohail nan zai nuna miki room dinki,tace na gode Sir na gode ta juya ta fice.

  Ibrahim sai duri yake ko kala bai ce ba,itama Zayna haka.

  

  Maheera ta fice daga gidan tana ta murna,Sohail ya biyo bayanta yace dama na fada miki zaki samu baki yarda dani ba gashi kuma,tace na yarda ai yanzu na gode sosai Sohail,yace ki daina gode min ni,muje to ka rakani,yace a'a na gaji ni bacci zanyi,tace to bye,ya juya abinsa ya tafi itama ta wuce gidan da take kwana gidan wata kawar Maman su,matar tana auren me rufin asiri a Abuja,itace ma ta samowa Maheera aiki ganin halin da suke ciki a suleja ta kawota gidanta Abuja ta samo mata aiki,matar yaranta uku yare ce kuma na Igala,tana da kirki ga tausayi.


  Gida Maheera ta koma tana murna ta samu wacce suke kira da maman Rahmat a palo,maman Rahmat tace yau ya naga yarinya ta tana murna? 

Maheera ta bata labarin samun sabon aikinta da salary dinta,ta bata labarin Sohail,Maman Rahmat tace Alhmdllh sai dai zanyi missing zaki barni na daina cin girki me dadi amma na tayaki murna Allah ya taimaka ya bada sa'a,a kula sosai a tsare mutunci,sai kiyi waya ki sanar da yan uwanki da Mamanki ko?

Maheera tace ae anjima da dare zan kira su,kema ki kira Oga fadlu ki sanar masa ya nemi wani ko wata,Maman Rahmat tace yanzu kuwa zan sanar masa inshaallah,Yaran Maman ma suna tayata murna" tashi tayi ta shige bedroom tana cewa thanks.


  Washe gari da safe da wuri Maheera ta hada wasu kayanta a akwati me kyau ta tafi gidan su Sohail,har kofar gida me taxi ya sauke ta,knocking tayi dake Sohail ne ke bude gate basu da me gadi,shuru ba a bude ba sai da ta gaji ta turo karamar kofar ta jikin gate sai taga ta bude kawai ta shugo.

 A compound ta hango Sohail yana zaune a kujera ya harde kafa daya kan daya yana ji ana knocking bai kula gate din ba,tana shugowa ya bude idonsa da yake a lumshe ya kalle ta kawai,ta karaso inda yake tace Hey,Hey shima yace sannan ya wani tafi dogon tunani sai da ya jima a haka tana tsaye tana kallonsa sannan yayi zumbur ya mike yace oh wai kece?


  Akwatin ya fisge a hannunta yace idan an hanaki daukan heavy abu bakya jin magana kawo muje ciki,ta bishi tana murmushi suka shiga ciki ya nuna mata bedroom hadadde kamar dakin amarya yace ga room dinki,tace na gode Sohail,ya hade rai tare da furta ki daina min godiya ki godewa Allah,tace ai ina gode masa yace wannan ke ta shafa,kije ki ma matar gidan girki kafin 5pm suma su Adnan kiyi musu nasu,Maheera tace to ta mike ta wuce kitchen.


  Tana tsaka da girkin Sohail ya shugo sanye da jallabiya wata fara dangalalliya duk kaurinsa a waje fari kal me dauke da kwantaccen gashi me kyau yace yana kallon Maheera ya aikin? Murmushi tayi tace Alhmdllh

Yana murmushi yana sosa gashinsa ya furta ko na tayaki?

tace a'a na gode,zai kara magana tace jeka kawai karka jawo min a koreni a aikin nan suce wani abu muke yi ka rufa min asiri,Okay....okay...ya furta yana kallonta ya juya ya fita ya barta tana aikinta, kamshin girkinta ya cika gidan,tana gamawa ta shirya dining Sohail yana can yana wanke mota.


  Maheera sai da ta tambayi Zayna ko za a miki wani abu Hajiya? Zayna tace no sai anjima ki dora abincin Ogana, okay tace,taje kitchen ta kwashe ragowar a plate da Spoon ta fito har inda Sohail ke wanke mota,tace ga abincin naka,yace harda ni? tace ae mana,yace ki daina dafawa dani kar su gani suji haushina ke 'yar aikin su ce ba 'yar aikina ba,to yanzu dan kaci abinci sai ya zama matsala? Yace hmm kawai......Adnan ne ya shigo da motarsa wata benz me shegen tsada,a idonsa yaga Maheera tana mikawa Sohail abinci,mantuwa yayi ya dawo gidan shima.


  Fitowa yayi a nutse cikin suits me tsada yana danna waya,yana zuwa inda suke tsaye ya dakawa Maheera tsawa sai da ta firgita,yace ke waye ya dafa abincin da kike bashi? jikinta ya hau mazari tace ni..ni...nice na dafawa Hajiyanka shine da ya ragu na bashi.

hannu Adnan ya sa ya fatalar da plate din a hannun Maheera,abincin ya watse a wajen a kasa ya furta look daga yau ke ba yar aikinsa bace,ni na daukeki aiki ni kadai zaki yiwa aiki tare da matata da kanina,idan ba haka ba zan koreki a aikin,idan yana son yaci abinci ga kitchen ya dafa da kansa.


  Juyawa yayi ya kalli Sohail yace ka dakko abin shara ka share nan kayi clearing komai ya ja tsaki ya juya abinsa ya wuce ciki.

 Maheera tace ikon Allah haka kake shan wahala? Murmushi Sohail yayi yace rayuwa kenan ya za ayi ko a jikinsa ma taga ya dakko abin shara ya share wajen tas ya tattara plate din ya maida kitchen.


   Maheera tana ta kallonsa cike da tausayinsa,yace kina ta kallona zan dafawa kaina karki damu.

 Jikinta a sanyaye ta koma ciki gaba daya tausayin Sohail ya kamata duk tunaninta dan aiki ne suka dauke shi a gidan.

  

 Daddy Ali ne ya kira Adnan ya sanar masa cewar zaizo Abuja wani aiki zai kawo shi amma a ranar zai koma kano ba zama zaiyi ba,Sohai ma bai sani ba washe gari Zayna a kitchen ta samu Maheera tace ke Maheera kike ko wa? kiyi abinci lafiyayye da wuri before 2pm surikina zai shigo,Maheera tace Alright ma.

 Ta fara girke girkenta Sohail ya sameta yace yau girki da wuri? Wai surukin Madam ne zaizo,Sohail baki ya tabe yace na sani ai,sun fada maka ne? Yace sai sun fada min ma,ko sunanki ai ji kika yi na fada miki to ko basu fada min ba na sani yana hanya yanzu ma.


  Maheera bata karyata shi ba,kira Sohail yaji Ibrahim yana kwala masa kamar zai fasa gidan,Maheera tace jeka ana kiranka,fitowa yayi da sauri,Ibrahim yace kawo min glass of juice,Sohail ya koma ya kawo masa lemo glass cup,yana karba yace jeka dakina zaka ga wani note book green ka dakko min shi sauri.

 Sohail ya wuce sama da sauri har hadadden dakin Ibrahim yana dubawa ya hango notebooks guda uku daya green,daya blue,daya grey color,Sohail ya dauki daya ya duba yace wanne ne green din a haka ya daga sama yana karewa ko wanne kallo,blue din ciki ya dauka yace yesss....wannan shine green ya fito ya kawo.


Ibrahim takaici ya kamashi yace wannan yayi kama da green? shine green din? Sohail yace idonka baya gani wannan ai shine green,wannan color din itace ta dace da green haba Yaya kalli ko idon naka computer ta fara kashe shi,uwarka ce computer din ai.

Sohail ya furta ai kuwa da mun huta sai muyi ta danna ta ba ruwanmu muyi game muyi kallo,computer uwar mu guda ai sai game kawai,tsaki Ibrahim ya ja cike da takaici ya fisge littafin ya tafi da kansa ya dakko abinsa.


 Sohail ya bi littafin da kallo yace wannan ne green? blue fa ka dakko,Ibrahim yace Sohail dan Allah tafi ka bani waje just go....

Sohail ya nuna hanya yace na tafi kake nufi? 

Ibrahim bakar magana ya fada yace a'a ka zauna nace,Sohail ya dawo palo ya zauna tare da harde kafafu yace na gode Yaya yana dagawa Ibrahim gira kamar dan iska,Ibrahim yace kai Sohail karuwa ka gani a nan a zaune? kana wani daga min gira kamar dan iska yaga karuwa.


  Sohail ya sake kashewa Ibrahim ido yace ai mu idan iskanci zamu yi karyar karuwa ta kama kafar mu,dariya Ibrahim yayi ba shiri,yace gaskiya haukarku shahararriya ce, Sohail yana jinsa yace Yaya Ibrahim jiya Allah kaje kayi iskanci da wata mace sunanta Bilkisu,mamaki ya kusa kashe Ibrahim,yace a gidan uwarka? 

Sohail yayi murmushi yace Allah kayi Sex da wata kuma shine na farkonka ta rinjayeka,ka cuci kanka tunda kakai wannan shekarun baka taba yin iskanci ba sai jiya,duk shekarun da ka kwashe kana hakuri sun tashi a banza fa.


  Ibrahim ya hade rai yana muzurai yace kai karka min sharri zanci ubanka,in nayi ma ina ruwanka? Ku aljanun naku ma munafukai ne,Sohail yace shike nan dama tambayarka zanyi...Adnan ne ya shigo palon,Sohail yace Yaya Jiya Ibrahim yayi zina,dubu dari ya bawa karuwar,budurwarsa ce ta kaishi ta baro.


 Adnan ko a jikinsa yace to ina ruwanka munafuki yayi din rayuwarsa ce bazai huta ba,idan ku baku da lafiya shi kalau yake,mu da lafiyar mu,Sohail yace ba a dai kuri da lafiya,mu ko zazzabi ai bama yi sam.

 Tashi yayi ya bar wajen nasu,Suka ci gaba da hirarsu shi da dan uwansa.


 Ali ne ya karaso da escort dinsa motocinsa da securities dinsa,Sohail ne ya karasa jikin motar Daddy dinsu ya bude masa kofa,Alhaji Ali ya fito ya sha farar shadda,kana gani kasan akwai kudi,Sohail yace Daddy ina kwana barka da zuwa,Daddy yayi dan murmushi bai ma amsa gaisuwar ba kawai tambaya yayi ina Adnan? Sohail yace Adnan kafi kowa? Daddy yace wanne sunane haka sabon nick name ya samu? Sohail yabi Daddy suna tafiya yace to ai kai kace kafi sonsa kaga ai yafi kowa ka sa masa kafi su kawai.


  Shuru Daddy yayi suka shiga ciki,Sohail sama ya haura yana kwalawa Adnan kira Yaya ka fisu kazo ga ubanku yazo,da Adnan yazo Sohail ya kara furta ka fisu kaje ubanku ya zo,kai fa banda kai? Adnan ya tambaya.

Sohail yace to gashi nan wa ya sani uban mu ne ko ba shi bane Allah ne ya sani,Adnan ya ja tsaki ya wuce abinsa.


  Zama suka yi suka gaisa da Daddy suka fara hirar aiki da harkokin kamfani da yanda kudade suke shigowa,Zayna tana cikinsu a zaune suna ta hira abinsu,Sohail kuwa yana dakinsa sai da ya gaji ya fito ya wuce kitchen ya samu Maheera tana fitar musu da abinci,tayata yayi suka shirya abincin a dining,Daddy Ali yana kallo ko a jikinsa sai ma murmushi da yayi yace Sohail akwai aiki wai ina Sahil? Sohail yace yana Lagos,Ali bai ma san dansa ya tafi Lagos ba,Ali yace amma baku fada min ba? 

Wanda kafi so din naka basu fada maka ba?

Ali ba kunya yace wallahi basu fada min ba, Kai Adnan me yasa banji labari ba?


 Adnan yace wata harka ta samun kudi Sahil ya samu wacce zai tsaya da kafafunsa,aiki ne me tsoka kuma shi yasa muka amince ya tafi,duk wani kudi da komai mun bashi yana can ya fara aikinsa ba matsala yana samun kudi,Daddy ba bincike yace to ai hakan yayi amma Sahil zai iya tsinana wani abu kuwa a duniya? Kar ya zubar min da mutunci ina so zan fito takarar gomna next year, Adnan yace to wa ya sani ne zanje na bincike shi naji.

Daddy yace kayi gaggawar hakan bana son abinda zai taba min siyasa ta.


  Maheera dai tana jinsu Daddy ta gaisar sannan ta koma kitchen tana tsaye ta lula tunanin abinda akewa Sohail wai dama baban su ne? Mamaki ya cika ta,Sohail ne ya shigo da fara'arsa ya manta sam yace ki kaiwa Daddy tissue,tace wai da gaske babanku ne? Sohail yayi murmushi yace ae mana ai babanmu ne nida Sahil shine ya haife mu,ba ina ta cewa zan baki tarihina zan fada miki matsalata sai ki nuna bakya son jin labarin.


 Amma baban mu ne mahaifi, Maheera ta tuna sanda yake zuwa shagonta yace zan baki tarihina,zan fada miki wata magana,sai ta dauka shirmensa ne kawai zai mata sai tace baza taji ba ita ya kyaketa.


  Idonta ne ya ciko da hawaye tace kayi hakuri ban sani ba wlh,yanzu ina Mamanku ko itace ta mutu? Sohail yace ni ban sani ba tunda ni ban taba jin labarinta ba amma dai ance tana England sannan arniya ce itace tace bata son mu shine Daddy ya kawo mu wajen Mama Asmau itace ta raine mu har muka shiga University sai ta rasu bayan ta rasu kuma shine aka cire mu daga makaranta muka dawo nan da su yaya muna musu aiki,suna dan bamu 1k 2k,Daddy kuma shike daukan nauyin cinmu da shan mu sai sutura ana siya mana sai dai muga an kawo mana,ba a bamu ko sisi mu siyi abu da kanmu,sabo da mu bamu da amfani ance.


  Maheera tana ta hawayen tausayi tace wlh kuna da amfani kuna da kyawun hali da hankali kawai su basu gani ne amma ni na gani kuma na sani na yarda da kai Sohail,Sahil ma haka you are the same kuna da hankali wlh,kunfi su Adnan hankali da kyan hali,Sohail yace Allah? Ke kin yarda muna da hankali? Maheera tace sosai ma Sohail na yarda da kai.

Kin yarda dani? Ba wanda ya taba cewa muna da hankali sai mama Asmau sai ke,kin yarda da mu? Maheera tace ae.

Zamuyi magana bari na gama aikina,yace to ya juya ya fita sai murna yake da farin ciki yau an samu wacce tace suna da hankali.


  Sahil kuwa bacci ya sha sai yamma ya fito palon su Khalisat ya same su gaba daya a palo suna kallon film, Dukkansu suka zuba masa ido kamar mayu ko wacce tana sha'awar su har uwar tasu,Islaha dai tana kitchen tana aiki sai gata ta fito tana shirya Dining,Sahil ya kalleta da muguwar tsana suka hada ido,jikin Islaha ya hau rawa,tsoronsa take ji sosai,kanta ta dauke ta shirya dining,Khalisat tana ta jan Sahil da hira yana sharewa.

Islaha ce ta shiga kitchen,yace kitchen ne can? Aunty ta karbe zancen tana kwarkwasa tace ae kitchen ne zaka iya zuwa ka dauki abinda kake so,feel free ka zama dan gida.


  Mikewa yayi ya shiga kitchen din,ba zato Islaha ta ganshi tsoro ya kamata ta fara rawar jiki,Sahil yace kyayi rawar jiki ai, wajen maza kuma kin iya cire pant a sauke shi kasa,Munafuka me fuska biyu na tsane ki.


  Islaha muryarta na rawa tace wlh ni ba yar iska bace ban taba iskanci da namiji ba,tsawa ya buga mata enough....a mota muna tafiya haka kika ce ke ba yar iska bace harda cewa cinyata ba safe waje bane,har na miki gata na zame miki uwa da uba na doraki a precious cinyata safe waje irin wannan,harda ce min dan iska to gashi an tsinci iskanci a wajenki,na rainaki ma wlh,akan kudi a tafi a bankadewa maza Taskira shame on you, Allah yasa Sohail yayi mana kawar mu Maheera ta ishe mu useless girl.


  Islaha ta fara kuka da hawaye ita bata san me tayi masa ba ya tsaneta,ya juya zai tafi tace wlh ban taba zina b....kafin ta karasa yace rufe min baki makaryaciya na ganki da idona to,Allah ya nuna min gaskiya anje an bankade taskira,ke kuwa nawa za a baki haka?


  Islaha tace wlh idan ka kula su Khalisat wallahi a gidan nan sai anyi yaki ai dai nice nan na fara saninka,lalataka zasu yi, 

Indai ina gidan nan babu wacce ta isa ta lalataka Sahil yace au fashi da makami na zaki yi? Tace ae? Baza su tsinci komai a jikinka ba face wahala,sai na fito da bad character dina da nake dannewa a gidan nan,za a ga bad character, sai nayi fashi da makami,Khalisat ce ta samo ka to sai nayi fashinka,yace to nidai abar nan tawa daya ce ina kuke so na sata,kai ku tsaya sai na fadawa Sohail ya fada muku gaskiya ni ba dan iska bane,wannan iskancin da zinace zinace na zamani bama yi,bamu iya bude taskirar mata ba.


 Daga fadan da yake yi kuma sai ya koma hira yace da na sauka ruwa ya zaneni ranar da muka zo,Islaha tayi dariya tace sannu ai na tambayeka tun farko ina zaka je kaki kulani,kasa kasa yayi da murya yace ya kike fama da aiki a gidan nan tace uhm ba a magana ina shan wahala a rayuwa.

 Sahil yace ai wahala yanzu kika soma gani tunda kike bada Taskira ana saka mazari a ciki kin gama yawo,ke da albarka har abada a haka zaki kare,karshen ki bazai kyau ba,bayan sun gama hira kuma ya koma masifarsa.

 Ki daina kulani na fada miki na tsaneki ya bata rai ya fice yana huci.

Su Aunty duk tunaninsu Sahil me hankali ne murna suke ganin ya tsani Islaha gaba daya,yana fitowa yace wannan wacce mahaukaciyar me aiki kuka samo ne? Na tsaneta bana sonta,Aunty tace uhm yar gidan yar uwata ce ta ishe mu muma,tsaki ya ja ya sake mikewa yace bari na koma wajenta sai na mata rashin mutunci ni zata raina,Su Khalisat har wani dadi suke ji Islaha duk kyawunta baza ta kwace musu Sahil ba.


  Kitchen din Sahil ya koma,ya kalli Islaha yace kina da saurayi wai? Mutumin da yace yar iska ce ita tana kula maza tana Zina amma yanzu kuma yana tambayar saurayi,Islaha ita kanta mamakinsa ya isheta,tace a'a bani da shi,yace yafi miki mutunci mu maza da kike gani ba 'yan goyo bane mu,ko an goya mu sai an sauke mu,Islaha tana dariya kasa kasa tace harda kai yace ae mana harda ni da Sohail karki sake ki goya mu,Islaha tace wai wanne aiki kazo yi nan? Kujera ya ja ya zauna yace bariki nazo yi,zobo me sanyi Islaha ta zuba a cup ta mika masa,yace mu a baki ake bamu bama cin abu da kanmu,har yaushe aka haife mu yara ne mu fa,Islaha duk wasa ta dauka yana yi shi kuwa da gaske yake fadar komai,tace to bari na baka a baki.


Su Khalisat suna palo shuru shuru sun ga Sahil shuru yaki fitowa tsoro ya kama su,Khairat tace bari na leka ta mike sadaf sadaf tace dole abi sahu bako ne ba a san halinsa ba,Islaha tana ta bashi zobo a baki yana shanye abinsa sai da ya kusa gamawa ya tankade cup din ya fadi kasa ya tarwatse yace da girmana,nifa ba dan iska bane irinki me neman maza yaja tsaki ya juya sai suka yi karo da Khairat.


 Khairat ta matsa da sauri taga Islaha tayi zugum ga cup a tarwatse bata sani ba Sahil aljaninsu fada musu abu suke yi iya tsiyarka watarana baza ka iya kure su ba,kafin kazo sun sani,Khairat ta harari Islaha tace stay away from him yafi karfinki,gashi nan kin jawa kanki sai ki gyara wajen.


  Sohail yana komawa wajen su Khalisat kamar munafukin miji yace yawwa ni gaskiya indai itace kar ta dafa min abinci a gidan nan,kar ta yi min komai,Aunty tace karka damu girkin ma da hannunmu zamu dinga yi maka har wanki da komai,yace yafi muku,Khalisat tace bari nazo mu fita a mota na kaika yawo,Aunty tace da kin bari tunda zan fita na fita tare da shi,Khalisat taji haushi da kishi tace ai na shirya,Khairat tana jinsu tace ni na kaishi next week.

 Sahil yace ayi haka? Kunki sharar masallaci zaku yi ta kasuwa,ko girki bakwa yi ga me yi can bakwa wanki duk yi muku akeyi yanzu da kanku zaku yi min nawa? Aunty tace laaa ba komai ai bakonka annabinka,Sahil yana kallonsu dai dai yace alright ku kuka ga zaku iya ai! ya furta kai tsaye ba ko darrr.


 

Free page

400 ne



0175487861

Asmau Garba Muhammad

Gtbank 


'Yan Niger

+22790795939





AsmaBaffa

***