MAI KWAÊAYI

14

by @nafisatusasaal01

💔💔```MAI KWAƊAYI```💔💔

 ( shi ya san gidan mai rowa)




  ```By```

```SASAAL```



 ```Page 14```


________Manya da yaran dake Rayuwa a ƙauyen yabon Halime ne abakunan su.

Inna ma taji daɗin ganin yanda Halime ta saki ranta take Rayuwa kamar kowa.


Tsabar baƙin ciki daina kulata Baba Isiyaku ya yi kota gaisheshi baya amsawa hakan kuma bai sa ta fasa ba,lokuta da dama dariya yake bata,ta rasa wani irin kwaɗayi ne da Baba Isiyakun duk ni'imar da Ubangijin ya yi wa ɗanshi da duk dukiyarta da aka kashe wajen kammaluwar karatun Salmanu baya gani.shi dai burinshi ta haifi ɗa Namiji su samu Magaji.


Mutuwar Yayan Mubeena Uwa ɗaya Uba ɗayane ya tilastawa Halime zuwa Birni gaisuwa.


Abun mamaki da al'ajabin daya samata zazzaɓi nan take gidan da bazata taɓa mantawa arayuwarta ba ne har abada ake zaman makoki ɗan uwan Mubeena, Unguwar su Innarta,a wannan lokacin ma Motoci ne lafiyayyu da sojoji birjik.


Daƙyar ta mu su gaisuwa duk da bata wani samun tarbar arziƙi daga fuskokin dangin Mubeena da suke da tsananin kyau da burgewa ba,duk da itama Halime ba baya ba amma kyawun mazaunin birni mai kuɗi da kyawun mazaunin ƙauye talaka da banbanci.duk Salmanu bai san wainar da'ake toyawa ba yana zaune awajen ma su karɓar gaisuwa.


Shi ya kaita har gidan Innarta cikin matsakaicin Motar da bai jima da siya ba.


Baƙin ciki kamar ya kashe Inna Huwaila,batayi tunanin ganin Halime tsaf haka ba.

A tsakar gida ta yada zango Inna na tambayarta cikin farin cikin zuwan bazatan da tayi mu su. Ciki sanyi jiki da damuwar dake bijiromata batare da lura da yanda Inna Huwaila ta bazo kunnuwanta ba take bawa Innarta labari.


Shewa Inna Huwaila tasa harda guda.

"Na rasa kwaɗayi irin wannan, kina ƙauyen ma baki haƙura ba kin ƙara biyo su,nan gaba motocin gidan takan hannayenki za su bi" Inna Huwaila tafaɗa cikin hassadar dake danƙare acikin zuciyarta don batajin yau zata iya barci mai daɗi.


Kalaman Inna Huwaila sun daki zuciyar Halime, duk dauriyarta sai da ƙwalla ya cika idanuwanta.

Maimakon zuwan Halime ya yi wa kowa na gidan daɗi yanda ta ƙara kyau da samun kwanciyar hankali sai yazama abun baƙin ciki ga mutanen gidan duk inda taje gaishe su baƙaƙen maganganun ne su ke biyowa baya.


Tun kafin ta bar gidan zazzaɓin jikinta ya fara ƙarfi, Inna tayi kuka bayan tafiyar su Halime, Tanajin kamar ta dawo da nakasun Halime kanta.


Hankalin Salmanu a tashe suka ƙarasa gida,chemist yakaita wajen Abokinshi,batare da wani gwaje-gwaje ba yayi mata Allura da bata magani.


★washe gari jikin Halime ya ɗanyi sauƙi. Kwana biyu bayan nan Salmanu ya yi mata albishir ɗin komai na Makarantar ta kammala zata fara zuwa Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria don haka tare za su tafi idan ya ƙara dawowa ta ƙarasa shirye-shiryenta acan.

Dalilin ƙara samun ƙarfin jikin Halime kenan.

A daren da labari yajewa Baba Isiyaku ya shiga ya fita kan idan Salmanu ya tafi kar ya ƙara waiwayar gida har sai zancen tafiyar Halime Makaranta ya rushe.


Ranar da Halime ta yi sallama da Salmanu cikin soyayya da ƙewar junan da zasuyi tare kuma da yimata alƙawarin dawowa bayan kwana biyu ciwo mai zafin gaske ya kwantar da Halime....✍🏻