YAR MACE

19

by @maidambu41

YAR MACE....🌺


*Mai_Dambu*



Paid book


19

Kallon Mama nake bakina kamar an daura min dutse, na lumshe idanu ina son yin kuka amma na kasa, na juya na kalleta kafin nace mata. "idan kika ji labarin mutuwata, ba dad'i ya kashe ni ba damuwa ce, idan na rayu kuma ki taimaka ki min Alfarma daya!" Jikinta ne yayi sanyi, kaina na dafe ina jin kamar zuciyata zata fita waje saboda bugawa. A hankali na juya na kalleta na ce mata. "Me yasa baki tab'a tambayata meke faruwa a gidan aurena ba?" Na sha mamaki da naji amsar da ta bani wanda ban yi mamakin fitar shi daga bakinta ba, "Idan na tambaye ki meye ribana? Na tambaye akan me? Kowa yasan kina zauna lafiya tow akan me zan tafi lafiyar aurenki, Ummu indai ba so kike a zage ni ace na kashe miki aure ba, ki rufa min asiri ki zauna lafiya wannan wacce irin rayuwa ce? Daga tambayarki kin ga kudi zaki yanki jiki ko fadi!" Ware idanu nayi akan Mama. "waye ya gaya miki haka? Sharrin sata suka daura min fa!" "A'a Ummu yayar Mijinki ta gaya min Ummu bakya son zaman lafiya." Kallon ta nayi kafin na fashe da kuka, ina yi ina yada kaina saboda yadda kirjina yake zafi da ciwo. "Ke kika haife ni kin san abinda xan yi da wanda ba zan yi ba, a tsawon rayuwata ban taba kawo miki kara ko nayi musu da wani ba, me yasa yau daya don an gaya miki abu kaina zaki amsa? Me yasa baki jira ki tambaye ni ba? Indai ke kika gagara min adalci a duniyan nan waye zai min adalci? Zan tafi wurin Babana na gaya mishi." Anan na ga ta ɗan yi jim kafin ta ce min. "Ai maganar ba sai ta kai wurin Malam ba,.akan abin da bai taka kara ya karya ba, kiyi hakuri tow zan cigaba da miki addu'a!" Da wannan tayi ta kwantar min da hankali, har nayi shiru na zuba mata idanu, kullum Tafida da Abbansu suna hanya, amma ni ko sau daya ban taba mishi magana ba, kwananmu goma aka sallame ni, gidana na dawo na cigaba da jinya duk da ana dawowa da ni Mama ta wuce gidanta, sannan wani abin da ya kara cin tuwo a kwarya yadda Tafida baya ganin girman Mama, har gara Deen yana girmamata. Shi yasa nima nake girmama Ammah. Sai da muka kwashe sati uku muka koma abuja, sai dai nayi mugun fita barkan Tafida, ban da aikin da aka dauke ni ba zan kara bin shi ba, haka a hankali nayi ta fuskantar kalubale daga danginsa, ana haka aka sake wani bikin ban je ba, sannan tun dawowarmu Tinah ta dauke kafarta ashe sun yi fada kaca-kaca da Tafida tun a Maiduguri, tayi mishi alkawarin sai ta saka ya bar inda yake samun kuɗi kamar hauka, da shi yake saka shi jin shi wani ne, lokacin da ta gaya min murmushi nayi na ce mata. "Ina kika yi sanadin da ya bar aikin bashi kika yiwa ba, ni kika yiwa ki barshi yayi aikinsa Allah ta bashi Sa'a duk abinda ya gadama yayi."tunda na hadu da laluran nake gudun abin da zai d'ago min shi,.sannan bana son tashin hankali bakiɗaya gani nake kamar xan mutu yadda nake fama da ciwon. A hankali lokaci yayi ta gudu ana haka har watan azumi ya cimma na, a lokacin na gama aikin da aka dauke ni, ai kuwa na ce sai Maiduguri, dake kusan wata bakwai babu me kula dan uwansa, don nayi kokarin koyawa kaina shanye iskancin, sai dai mafi girman kuskuren da zuciyata tayi min fadawa soyayyar Tafida. Wani irin mahaukacin sonshi nake kamar zan yi hauka, idan nace ban fada jarabawa ba nayi karya haka yasa nake rufe kaina a ban daki nayi ta kuka, tun ranar Monday na shiga tattara kayana, yana gani bai min magana ba, nima kuma ban ce mishi kome ba. Sai bayan Isha na same shi a parlour. "Barka da hutawa!" "Yawwa yar gajeruwa, au ashe likita ya ce zuciyarki zata buga!" Ya fada yana murmushi. "Dama ina son na koma gida!" "Ban yi niyyar ki koma ba!" "Shi kenan!" Na fada daga haka na koma na cigaba da zama abina, na zata maganar ta wuce tunda ya ce min bai yi niyya ba. Kawai sai ga kiran Mama tayi ta fada akan me zance zan dawo Maiduguri, fada kamar ta ari baki ta kara, Abba ma ya kiranki ya tambaye ni ko akwai matsala ne. Nace mishi kawai zan dawo ne, na gaji shiru yayi kafin ya ce min. "shi kenan ki hada kayanki Alfah zai zo ya dauke ki!" Ajiyar na sauke ina me jin kamar anyi min albishir da gidan Aljanna. Nayi ta mishi godiya, sati daya da maganar ya kirani yace na shirya gobe za a zo a dauke ni. Yadda muka mai da Tafida gefe ba karamin zafi yayi mishi, ina kwance ya fado dakina, tashi nayi xan zauna ya nufo ni. "Me yasa kika rena ni? Ni nake aurenki ko Abbana? Gaya min me yasa?" Ya hauro gadon ya da karfi ya fisgo ni na fara ƙoƙarin kwace kaina, "Tafida bana son tashin hankali, don Allah ka kyale ni!" "Akan me xan kyale ki bayan kina kallona lusari ban iska kiyi abu na yi magana ba, ace bani da kirki bani da mutunci!" "Tow don Allah meye nayi maka? Na gaji da fitinarka zan tafi inda nake da gata da galihu.." "ai nan baki da shi? Tow bari na gyara miki zama!" Kuka na saka mishi ina rokon shi don Allah kada ya min haka, amma bai ji ba cikin shashekar kuka na rike hannunshi domin bakiɗaya karfi yake son gwada min. "Don kaunarka da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, ban san me akan wannan lamarin ba kada ka illata min rayuwa bayan ba son zama da ni kake ba!" Ina bai jin kira, ni dai nasan irin yadda ya zuba min karfi kamar jikan ilaya dan mai karfi, babu yadda xan kwaci kaina amma tabbas abubuwa da suka biyo baya, ban san yadda zan fade su ba, domin.nafi girmama fyade Tafida yayi min cikin mugunta da zalunci irin na ranshi. Haka ya ci mutuncina son ranshi. Sannan ya tashi a kaina yana me jan tsaki. Ya saka wandon shi ya bar dakin, dakyar na rarrafa zuwa ban daki nayi wanka tare da gasa jikina da nake jin kamar ba jikina yake ba, fatana kawai gari ya waye na bar garin Abuja. Kwana nayi ban yi barci asuban fari na hada kayana na fitar parlour wurin karfe biyar Alfah ya shigo yayi ta buga kofa, zazzaɓin da ya rufe Ni na lallaba na fito na bude mishi. "Kayi hakuri Alfa!" "Ba kome ina kayanki!" Na nuna mishi, sai lokacin Tafida ya fito ranshi a bala'in haɗe. "Kai haka ake zaka wani shigo gidan mutane da tsakiyar dare haka!" Dake basu shiri shi da Yaran Hajiya Salamatu. "Ayi hakuri!" Ya fada yana daukar jakata yana me barin parlourn, fisgo ni yayi yana me kallon fuskana. "Ki ka sake wani reni ya kara shiga tsakaninmu, sai na bi ta wannan hanyar sau goma wannan sau daya nayi tow idan kika bari na waiwaye ki abin ba zai mana dad'i ba." Tabbas duk macen da aka yiwa fyade matukar bata gigice ba, tow ciwon yana iya zama har cikin kwal-kwalwarta abin da ya faru da ni kenan amma ban gigice ba, sai dai wani irin tsoron tafida ya dasu a zuciyata, wanda ya ja na fara kuka yana ce min "shiii!" Na hadiye kukan kamar ba ni ba. "Ki kama kanki, shi kanina ne kada wani ya gaya miki cewa akwai wasa a tsakaninku, ki mai da kanki wata sakarai! Kina ji na!" Ya daka min tsawa, k'amkame jikina nayi tare da gyada mishi kai. "Yayi kyau maza muje ki shiga motar!" A hankali nake tafiya saboda yadda nake gogan wurin har cikin raina nake jin zafi, hawaye ne yake zuba ina sauke ajiyar zuciya. "Kukan na uban me kike yi?" Share idanuna nayi da sauri ina faɗin. "na daina!" Burina kawai na bar ganinnshi. "Ya tafiyarki ya sauya!" Ji nayi kafaffuna na rawa kamar ba su dauke ni ba. Fisgo ni yayi ya saka Ni a bayan motar yana faɗin. "Ki kula da kanki!" Gyada kai nayi ina kallon kasa. Motar na barin kofar gidan ya sauke ajiyar zuciya, idan haka aure yake tabbas ya tabbata asararre wanda ya bar damarshi tun farko. Zai barta ne kawai ta tafi don Abba yayi magana amma ba don haka ba, idan ya sakata a gaba sai ya ga abinda yake dadi a jikinta..(Ji dan iska mugu 🙄😒)


Tunda muka dauki hanya nake sauke ajiyar zuciya, sai da muka bar Abuja zazzaɓi ya kuma rufe ni, yadda nake rawan sanyi yasa Alfah kashe ac motar, sannan ya yi parking ya ciro min panado ya bani na amsa ina godiya. Bayan na sha yace min. "Ki kwanta ki huta!" Haka na kwanta a bayan motar, tuni barci me nauyi yayi gaba da ni. Ban farka ba sai da ya tashe ni, wurin karfe daya na rana, a lokacin muna fataskum zare idanun nayi ina son nayi magana. "Ga abinci ki ci, zuwa anan da karfe hudu zamu shiga Maiduguri." "Tashi motr sama kayi?" Na tambaye shi ina bude abincin. "A'a gudu nayi kawai!" A hankali na fara cin abincin har muka bar fataskum, a yanxu na tabbatar da ba tashi yake sama ba, irin matasan nan ne masu mugun gudu, Alfah akwai wasa sa rayuwa kamar yadda ya fada karfe hudu cib yayi mana a garin Maiduguri. Wani wawan ajiyar zuciya na sauke ganina a gidan. Abba da kanshi ya tarbe mu, a nutse na gyara tafiya ta duk da ba karamin wahala nake sha ba, na gaida su . "Ummu baki da lafiya ne?" Yake nayi ina faɗin. "Bana jin dadi ne amma da sauki!" "Allah ya baki lafiya!" "Amin Ya Allah!!" Na wuce bangarena a hankali kamar kazar da kwai ya fashe mata, ina shiga ruwan zafi na daura na jira ya tafasa, na jure a flast na nufi dakina da shi, na zuba a bawo na a zauna sai lokacin kuka ya zo min ina yi ina karawa, sai da ruwan ya huce na fita, na kara wanka na sha magani nayi sallah, sannan na kwanta ban farka ba sai karfe bakwai ashe har Nabila sai da ta shigo yafi sau nawa, Alfah yake gayawa Mamansu ai bani da lafiya, haka yasa Alhaji ya saka lallai a kai ni asibiti, gudun abin kunya na ki yarda, haka nayi ta jinya a hankali na manta da wani Tafida can. Haka na bude sabon shafin rayuwa, satina biyu aka fara azumi na nutsu sosai nayi rabon kayan azumi har garin Babana na je da kaina a cikin azumin yana uku sai da nayi aka kai azumi goma na dawo na nutsu nayi kyau, na dawo da kwana uku sai ga Tafida, sai da naji kamar xan yi hauka, kome da nake yi a tsorace nake yin sa, sai dai zuwanshi ya zo min da ban mamaki domin kici-kicin ya hana Saadi shigo mana, ranar da ya zo nayi aiki na gaji, cikin dare ina kwance naji yana lallubena janye jikina nayi tare da matsawa can. "Ke meye haka?" "Na gaji sosai don Allah kayi hakuri!" "Ni mayunwacci ne daga lokacin da na bukaci abinci ci kawai nake son yi na tashi idan zaki bani hakkina a dadin rai ki bani ko na saka karfi na rusa kofar da take rufen nan!" Yadda yayi maganar yasa na mika wuya salin Alin, ina kuka ina jin yadda yake murzani son ranshi, ba zance nasan wani abu bayan nan ba, amma tabbas Tafida ya kashe kome nashi a zuciyata. Yana gamawa ya mike ya fita abinsa. Yau ma Dakyar na kai kaina ban daki nayi wanka da Tsarki na kwanta, wani sabon zazzabin ne ya rufe ni, da asuba bayan mun gama Sahoor ya kara shigowa, a nan ne fa na fashe da kuka wiwi, amma kukana bai hana shi biyan bukatarshi ba. "Idan zaki daina kuka ki daina domin ke da takalmina kallo daya nake muku zan shure ki lokacin da yayi min na bar ki lokacin da ya min." Nayi kuka har naji anya Allah yana amsar addu'ata kuwa. Haka ya share sati daya ya koma a wannan kwanakin ba karamin azaba na ci ba, ga aiki ga hidimar shi da abokanshi. Akwai wani abu da ban gane ba shine duk mu'amalata da Tafida da wani abu yake kusantatta. Irin robar da yan iska suke amfani da shi. Tun abin yana min ciwo har ya daina na saka ido kawai. Ana jibi sallah ya dawo na gyara jikina ta hanyar Hajiya Kaltuma, domin kawai jikinta ya bata akwai wani abu da yake kawo Tafida Maiduguri babu dalili, bata tambaye ni ba amma yadda ya ga na kare wancan lokacin yasa ta da kanta ta hada min magani masu kyau ta bani yana gab da zuwa, ta ce maza nayi ta sha kada nayi wasa da su. Haka nayi ta sha,ashe ita taji shuwa da Yarta suna hiran Tafida ya zama munafiki bayan yace babu abinda zai yi da Ummu shi ne ya munafunce su ya zaga yana shagali da Matarshi. Wanann abin yasa ta jin bari ta taimakawa Ummu itama. Ya shigo gari ana shan ruwa bawan Allah nan ruwa kawai ya sha yayi sallah sannan ya shigo min daki da gajeren wando. Ganin yadda nayi na razana ya sa shi sassauta min murya yana faɗin. "Zan miki a hankali!" Kamar yadda ya fada haka yayi sai dai abubuwan da Hajiya Kaltuma ta bani yasa shi kauce alkawarinsa kamar bashi ba yadda yake abin da wasu yan kananun magana yasa ni fahimtar maganin yayi kyau. Bayan ya gama ya sauka ya shiga yayi wanka a ban dakina, ya fito yana faɗin. "Ke anan zan kwana a hada min kayan abinci na!" "Tow!" Ina jan hancina, ban daki na shiga nayi wanka sannan na nufi kitchen na hado abincin zuwa dakin ya zauna ya ci sannan ya huta kafin ya shirya ya tafi sallah tarawe. Bayan ya dawo ya kuma fita da abinci waje. Suka ci bai dawo ba sai karfe goma sha ɗaya, har na fara barci ya shigo min, sai da gabana ya fadi. Fita yayi sai gashi da kayan barcinsa yazo ya kwanta a bayana, bai nemi wani abu ba don yaga yadda nake dan kerma a gabanshi. Bayana ya sumbata, yana faɗin. "Kwanta babu abinda zan miki, sai asuba zaki bani kafi shayi." Ban yi wani barcin kirki ba, tunda mutumin nan ya maida ni tuwon laushi. Ranar jajiberin sallah, yana gidan bai fita ba a tare muka yi ta fama, wurin karfe daya na dare, kashe kome yayi yana faɗin. "malama muje barci naje ji!" Haka na bar kome na kwanta, don gulma mutumin nan har da min tausa, ai shi ba zai yi aikin banza ba yana ganin na huta ya fanshe aikinsa, haka muka yi bikin sallah ni dai bana jin wani dadin zaman shi saboda jaraba. Sati daya ya koma, bayan na ji rigimar su da Sa'adi, ban yi farin ciki ba domin kuwa har parlourna Hajiya Shuwa ta biyo ni tayi min tijara wai bokana yayi nasara amma na shirya ko bai auri Sa'adiyya ba zai zo da wata ai, me ilimi gogayya wacce ta fiki wayewa. Ko inda take ban kalla ba na cigaba da harkan gabana. Lokaci ya tura sosai ba zato ba tsammani kawai sai matar Sharif ta haihu, a lokacin aka sakani a gabana da habaici da magana,ko ta kansu ban bi ba na bawa Maijego gudummawata na bar gidan, daga nan na zo nayi shawara na bude online business dina, yayinda muka yi da Mudan zai na min deliver. Wasa wasa Sai gashi gidajen abinci sun fara gayyatatta ina zuwa na musu dan karamin program, haka yasa na zama sananniya, ai kuwa na koma yar kasuwa kamar me ina cake ina abinci sannan ana oda sosai, abin dariya sai ga Rukayya ta fara abincin itama online, wasa wasa Sai gashi ana son abincina haka suka yi ta sake min habaici da sharri kala-kala, dake akwai kyakkyawar manufa a raina. Kawai ina zaune wani zuwan da Tafida yayi, yana kallon kwallo. "Ummu ki barwa Rukayya online business dinki nan!" "Ban gane ba?" "Eh ina nufin ki daina sayar da abincin nan da kike yi na Baby's Mama kitchen!" "Fisabiilillahi;" "ba zaki bari ba kenan?" "Gaskiya ba xan bari ba domin da shi na dogara idan." "Ba zaki iya ba kenan!" "Zan gayawa Abba ya ji abin da kike nufi da ni!" Ina saka Abba cikin maganar ya bar zancen, ashe sun same shi da zancen ne ko zai iya hana ni, ni kuwa naki. Ba karamin haushina suke ji ba, ana haka Aunty Maryam ta haihu, tana haihuwa da kwana biyu na je barka na kai mata dubu goma, ko zama ban yi ba na bar gidan, sai ana jibi suna ya kirani wai Maryam ta ce wai ni zan mata abincin suna naje, shafawa idanuna toka nayi nace su kawo idan tana bukata ni ba zanje suna nuna ni a matsayin barauniyar su ba. Na zata zuciya zasu yi sai naga ba haka ba, washi gari sai ga kayan girki, duk abinda aka kawo a bai kai ba,haka na kwashi kayan mu na musu abinci me kyau. Kawai nayi ne domin bana son ayi shi a babu isashe. Da aka zo dauka Rukayya ce, naga ta fito da babban kula ta diba, ya kai gidan shuwa. Ko kallo bata ishe ni ba ina ruwana, ana kai abincin Aunty Maryam ta kirani bayan na dauka nace mata. "An fita bakwai lafiya?" "Lafiya lau! Ya abincin haka? Ko Rukayya ta diba ba ne?" "Hmm wato dama kin kawo min ne da nufin na dafa ace na sace na boye ko?" "Ba haka ba ne, abincin ne kamar an diba!" "Ok ki tambayi yar uwarki!" Na kashe wayar, ina jan tsaki. A can kuwa zagina suka yi tayi wai nayi abincin na kwashe dake Allah ba azzalumin sarki bane sai ga Sa'adiyya ta fasa mata taya a gaban jama'a, ta ce mata. "Aunty Rukayya abincin ki yana bayan Motar Mama." Shiru tayi tana wani zare idanun.


A shekara na uku da auren mu ne ya samu goyan bayan manyan dattijan borno, masu political powerful na arewa bakiɗaya suka goya mishi baya, aka fara hidimar yawon zabe, ni bai gaya min na domin a lokacin abin ya zo ne da maganar shi da Sa'adiyya wanda ya saka ni a gaba da fitina da wulakanci wai yana zargin nice nake hana Abba amincewa, a lokacin yanayin ya sauya min da sabon ƙaddara, domin haka kawai na fara wani irin ciwon da ta sa na bar duk wani abin da nake, na nutsu wuri guda, tun karshen shekarar na fara haka kullum ina fama da magani har na shiga sabon shekara, da ya gaji da ganina kwance ya saka ni a gaba muka tafi asibiti, gwajin farko aka tabbatar da cikin wata uku ne daram a jikina, hmm! Sai ga Tafida ya tashi hankalinsa domin ana maganar aurenshi da Sa'adiyya ne, haka muka fito yayi, y kalle ni da kyau. "Yaushe cikin nan ya shiga? Ina kina ganin nake saka condom! Ba don ni na fara koya miki ba da wallahi sai na musanta cikin nan nawa ne!" Rintsa idanuna nayi, naji kamar xan mutu, bayan mun isa gida bawan Allah nan bai huta na, yayi ta shige da ficce lallai zai zubda cikin jikina, a wannan yanayin aka yi bikin Mahmoud da Deen kusan sati guda ne a tsakaninsu. Ban samu damar zuwa ba, domin duk inda Tafida yaji zai samu magani sai ya kawo min ya tsaya a kaina na sha, wani hukuncin Ubangiji magani dai shi ake kira Daram ko jiri bana ji, duk abinda ya kawo zan sha domin ni kaina na kawo aurena ya zo karshe da Tafida. Haka aka yi ta fama ganin cikin ko nasha magani bana kome sai ya kai Ni asibiti wai a cire cikin, likitan yana min scanning ya gano yan biyu ne kwance mahaifata, nasiha yayi mana ya ce mana. "Cikin nan yan biyu ne, kana da damar da zaka iya zubarwa baka san arzikinsu ba, sannan kai ne ake tsammanin zama gwamnan jihar Borno, don Allah kayi hakuri ka barsu! Daga kansu sai ka ajiye haihuwar ma domin cikin ya shiga wata hudu idan aka tab'a za a iya rasa uwar da yaran ma!" Jin haka ya sa shi hakura amma shi kansa yana ganin da zaran ya zaman gwamna zai rabu da ni. Haka muka dawo gida cikin sanyin jiki, daga nan ya fara fito min da abin da yake shiryawa, cikina yana wata bakwai aka yi bikinsu da Sa'adiyya, akwia wani abu da idan kace Allah zai amsa maka, rawan kai da na kafa da Tafida yayi lokacin sai da na taba farkawa da wani irin ciwon ciki kamar haihuwa, ana gobe daurin aure a asibiti na kwana, a wannan lokaci yan uwanshi suka yi ta fitar da abinda yake ransu na idan na haihu zai rabu da ni ya kwace yaranshi, Abba kuwa ya ce . "A duk lokacin da kika samu dama, zan rike miki kan maciji kiyi wasa da bindin yadda ranki yake so," haka ma Inna ta goya min ba, kwana ɗaya nayi aka sallame ni washi gari da ya dace ango ya fito da kaudi sai ga Mutumin ya fito daga bangarenshi kamar ruwa yayiwa zakara duka...........

500

8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay

Shaida biya a turo ta wannan numbers din.

***

Or

***

Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76