KALBIM

3

by @mamuhgee

*_KALBIM_*

_Mamuhgee_

#ZafafaBiyar




3

*ZUZEAMVENTURES*

***

Aslm barkanmu da wannan lokaci 

Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka

 Mallaka Maganin sanyi

Maganin cire tumbiMaganin farin jini

Maganin matsiMaganin mata

Maganin sa ni’ima da dandano

Dulka Amare Set na gyran jiki

Set na amarya

Tabaje tsumin Gomba

 Xuma kiba ta hips and Brest

Magungunan gyran Brest

Magungunan Karin hips

Maganin sliming

 Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa 

Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi ***

Idan maganin mata kikeso akwai 

Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips 

DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no *** DOMIN mgn da ita whatapp ***muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah πŸ₯°πŸ‘ŒπŸ»

Bononza Bononza Tsimin mangoro 1kπŸ₯­ Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500

Garin bata gaban kishiya 500

Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500

Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500

Za a bakisu akan 3800

Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k

πŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALAπŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜πŸ˜πŸ˜ da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜ƒπŸ™ƒKazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadΔ±πŸ˜‹800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki




***********

Mahir Zadeen shine kokarin naci akan komai saiya gano komai akan duk abinda yaga zai shiga rayuwarsa ko ta familynsa,

Baya maamala da mutune ko abu ko wane iri ne kuwa batareda ya samu sanin mai zurfi akansa ba,

Bayan familyn baya son kowa dan hakan ne ma baya shiga mutane sosai ko hulda dasu hakama bai yadda kowa ya kusanci fmlynsa ba sbd bai yadda da kowa ba akansu,

Hakama tin kafin shekarunsa sukai ya fara shiga huldodin familynsa sbd bi da kauce duk wani abu da zai cutatar dasu ko dukiyarsu.


Allah ya basa wani irin sharp kai da qwaqwalwa kamar maye dan hakan ne yasa dole da wuri su Dad suka bari ya shiga huldan duka zadeens babu wanda  bai sani ba.


Hakama tin daga Dzad da daddy mahmoud babu wanda yake boye masa komai sbd ganin wani sharp kaine dashi.


Ammar ma yanada ilimin sosai sedai trauma dinsa tana damar masa da lissafi so da dama dan haka shi ya kasance kamar mara hankali akan abinda yakeso,

Akan familynsa zai iya komai me kyau da mara kyau bai damu ba,


Kaf familyn ZADEEN's babu wanda yake kallan gaskia ko adalci akan yan uwansu,

Sunada wani irin son kai da basa duba komai da kowa sai kansu,

Babu ruwansu da ko rai zaa rasa indai akan buqatarsu ne ko abinda suke so kuma hakan tamkar a jininsu yake dan kuwa babu wanda bazai iya komaiba a cikinsu akan abinda suke so ko buqata,


Inda tsananin son zuciyarsu da son kansu yayi mugun munana shine ko dayansu yake buqatan abu to zasu hadu su samar masa da abin nan koda kuwa hakan na nufin wasu zasu shiga mummunar matsala koda kuwa ta rasa rai ce su ba damuwarsu bane.


ZADEEN's sunada power me karfin gaske,sunada kudi,sunada kwarjini sunada isa,sunada duk abinda dibbin mutane da yawa ke tsananin nema da so na rayuwa basu samu ba,


Duk wannan lokacin da aka dauka bayan qara habbaka da samun power babu abinda sukeyi dan hakan ne ma ya saka koda basa zama a qasarsu sunyi suna da ficen da aka sansu dan kuwa ko a Nigeria din sunada power din da ko wasu masu mulkin basuda ita.


Sukan taho Nigeria din sosai dukkaninsu sedai basa wani jimawa sosai suke komawa dan hakan kan yayan yake sake budewa da gogewa a harkansu sosai.



Wani cikin Mimi ta samu wanda ya saka ya saka Ammar ajiye komai ya koma kulawa da ita sbd dukkanin qawa zucin dayake dashi da mommah akan mimin ya dawo

Hakama wani irin tsananin so da kaunar cikin Allah ya jarabcesa dashi wanda ya ringa rokom Allah yasa mace zaa haifa a saka mata sunan mahaifiyarsa.


Yanda Ammar ya kwallafa rai akan son cikin da fatar a haifi mace ya saka kusan kowa familyn tsananin son hakanta shigesa sai gasu dukansu kaf sun qwallafa ran Wata zayneb zaa haifa.


Kusan komai ajiyewa sukai suka maida kaf nutsuwarsu akan cikin dan haka Mimi ta dage da adduar Allah ya bata mace sbd samunta shine hasken dazai qara cike rayuwar zadeens da suka kasa manta radadin rashin zayneb.



Yanda kaf familyn suka duqufa da rokon samun Zayneb suka manta da komai zaka roqa ka roqi me albarka ko kuma zabin mafin alkhairi,

Ita haihuwa sam ba sai wanda kakesoba 

Duk wanda Allah ya baka ka roki me albarka kawai kokuma lafiyayye.


Tin daga kan ummah datake tsohuwarsu har kan duk wanda yake familyn Allah suka ringa roqo akan zayneb sukeso kota yayane Allah ya basu wata zayneb din da suka rasa.


Hankalin Mimi fara tashi yayi ganin yanda duka hankalinsu ya gushe ko yayane so suke Allah ya karbi Addua da fatansu.


Damuwa da tsoro ya saka naquda zuwar mata batareda cikin ya isa haihuwa ba dan haka suka dunguma asibiti.


Ko asibitin da aka kaita babu me zuwanta sai wanda yakeda matsayi da kudin da kusan koina ka san dashi dan haka tin tana ciki aka fara yada ZADEEN's na shirin welcoming sabuwar princess din familyn.


Tsaron asibitin kadai zakasan masu abin duniya ne a asibitin dan haka Kusan su kadai ne a asibitin ranar.


Naquda sosai Mimi tayi kafin Allah ya bata ikon haihuwar abinda suka roka

'Ya mace Kyakkyawa da ita fara tas kuma kusan kammanin mommah zayneb din ta dauko dan kusan familyn kamanninsu daya shiyasa suke da wani irin kyau da kwarjini dukkaninsu tin daga kan su dzad din.


Tin a asibitin Dad ya saka mata sunan ZAYNEB BOUKHAR ZADEEN bayan ya dauketa da hannuwansa yanajin soyayyarta da kaunarta fiyeda duka sauran yayan daya haifa sbd tsananin kaunarsa ga zayneb da suka rasa.


Mahir ma jin yayi tafi masa duk abinda suka mallaka dan haka ya rungumeta sosai yana addua.


Saleem kuwa take yaji zai iya komai akanta.


Ammar ne na karshe a daukanta sbd idanuwansa da suka ciko da hawaye zuciyarsa na harbawa da wani irin tsananin kaunarta dan fuskan mommansa kawai yake gani akan nata ga kuma sunan da Dad ya ambaceta dashi na mommansa.


Ahankali ya rungumeta a kirjinsa hawayen dake idanuwansa na gangarowa ya bude baki Ahankali yace


"JANNAH"


Tausayinsa me tsananin gaske ne ya rufe Mimi ta miqa masa hannu tana kokarin boye nata hawayen sbd rasuwar momman data dawo musu sabuwa.


A sanyaye ya qaraso gurinta ta nuna masa gefenta ya zauna ahankali yana kama hannunta daya datake miqa masa ta dan kwanta gefen jikinsa tana cewa


"Ka samu jannah"


Murmushi yayi yana zubawa fuskan babyn idanuwansa tana baccinta hankali kwance kamar ba rai a jikinta.


Saida Mimin ta kwana asibiti kafin aka sallamesu suka koma gida cikeda farin cikin da suka manta rabonsu da irinsa.


Haihuwar Jannah zadeens itace babban Farin cikin daya cike gaba daya rayuwar ahalin gabaki dayanta dama duk wanda yake muaamala da huldan business dasu,

Duk wanda yake aiki a karkashinsu ma yayi farin cikin samun jannah sbd tayasu farin ciki dan haka tin tana jaririyarta duniya tasan da irin tsananin son da Ake mata,

Duniya ta sheda jannah zadeen itace hasken idaniya da rayuwar ZADEEN's.


Rayuwarsu ta dawo kamar sabuwar duniya da suke barewa a leda yanzu,

A baya komai ma wasa ne a yanzu ne ZADEEN's ke sake zamowa ZADEEN's da kowa yake shakka gashi daddy mahmoud ma ya dawo da familynsa sun hade sun sake bunqasar datake bawa mutane tsoronsu amma har lokacin matarsa shi bata haihuba amma bai wani damuba sbd yayan 'dan uwansa da Ammar dan zayneb sun ishesa.




*******A DAYA BANGERN KUWA CAN BAYA.


Kauyen Bondi Ruwa akeyi sosai tsakiyar dare guraren karfe daya da rabi gari yayi tsit babu kowa babu komai bayan ruwan da suke sauka sosai da karfi.


Qaramin gidan ne sosai wanda rabinsa yake a zube katangar ruwa ya zubar tintini.


Dayan bangaren da bai fadi ba daki daya ne sai qaramin ban daki wanda shima rabinsa ya zube buhu ne a rufe da rabin,


A cikin dakin macen datake kwance tana hada wani irin zufa me tsananin gaske duk da sanyin ruwan da akeyi yana zubowa cikin dakin daga sama sbd gefe daya langa langar dakin ya bude.


Dan ta dake gefenta idanuwansa sunyi jajir sbd tsananin dacin ganin mahaifiyar tasa a hakan.


Tsohon cikin dayake jikinta ya kalla idanuwansa suka sake kadawa sbd damuwa da dacin a halinda mahaifiyarsa zata haifo masa kaninsa ko kanwarsa.


Hannuwansa ya miqa ahankali ya janyo zanin da bayada sanyi ya rufawa Umman tasa ya bude bakinsa da muryansa me sanyi yace


"Umma sannu"


Kasa magana tayi sbd wani tsananin azababben ciwon marar daya taso mata tanaji jini na balle mata amma ta danne cikin tsananin azabar da bata taba jinta ba sbd batason daga hankalin 'danta dayake shi kadai hasken rayuwarta da batada kowa sai shi hakama batason ya gani ya duk da tasan duk ayita a qare shine zai tayata haihuwar kila tinda batada me taimakonta a rayuwar nan yanxu bayan shi data haifa.


Daqyar ta iya bude idanuwanta da sukai tsananin nauyi ta kalli farar fuskansa ta asalin fulani da dasashiyar murya tace


"ABDULAZIZ"


kasa dagowa yayi ya kalleta sbd hawayen da suka ciko idanuwansa yanajin duk duniya babu abinda ya tsana kamar dangin mahaifinsa da suka kasa taimakon mahifiyarsa bayan rasuwar mahaifinsu.


Numfashi take kokarin saukewa cikin azaba sbd sanin taurin zuciya irin ta ABDULAZIZ har abada bazai taba so da kaunar ko mutum daya a cikin dangin mahaifinsa ba dan duk da abinda ya tsana da gaske yake tsanarsa.


Jini ne ruwan dayake zubo musu ya gangaro daga karkashin Umman.


Jajayen idanuwansa ya dago cikin duhun daren zaiyi magana sai kawai umman ta masa wata irin riqo me qarfin gaske tana rintse idanuwanta cikin azabar gaske tayi wani irin nishi take ta haifo abinda yake cikinta.


Hawayen azabar ne suka gangaro musu shida umman a tare sbd irin riqon datai masa amma jin kukan jaririyar ya sakasa bude idanuwansa duk da baya ganin komai sosai ya sunkuyar da kai yana Godewa Allah cikin hawaye duk da ba wasu shekaru ne dashi ba sosai iyakacinsa shekaru goma sha hudu.


Batason abinda zai saka Abdul din yasan meyake wakana dan haka ta dade da tanadar rezanta dan haka da kanta ta yanke cibiyar ta dauki yar hannunta na rawa da hannu ta shafa gabanta taji mace ce dan haka yaye zanin daya rufa mata ta saka yar a ciki ta miqa masa tana numfashi daqyar sbd jinin dayake neman bugar da ita.


Hannuwansa rawa sukeyi sosai ya karbeta tana bude idanuwansa sosai a cikin duhun dan yaga halinda umman take ciki amma baya ganin komai.


Shiru dakin ya sake dauka yana rungume da yar yana jin wani irin tsananin so da kaunarta da yakejin ko rayuwarsa zai iya badawa dan bata kariya itada ummansa.


Kanwarsa ce uwa daya ta haifesa hakama daga tsotsan uba daya suka fito kuma batada kowa bayan shi da umman,

Hakama ummansa batada kowa sai shi,

Shine zai zama gatanta itada umma koda kuwa zai rasa ransa to tabbasa zaiyi gwagwarmaya dan inganta rayuwar su biyun nan.


Guraren asuba ruwan saman ya dauke dan haka ya ciro yarinyar daga jikinsa ya kwantar gefen umman ya fita cikin duhun ya nufi can karshen kauyen gurin macen da ita kadaice aminyar mahaifiyarsa duk kauyen kuma ita kadai take taimaka musu.

#MAMUH

#AZIZ AY LIMBA

#BESTLOVE

#BESTSTORY

#HEARTTRANSPLANT

#JANNAH ZADEENS

#UMMITA LIMBA



ZAFAFA BIYAR


KALBIM 500

mamuhgee


A DUNIYATA 500

Huguma


AJIYA A DUHU 500

Billyn Abdul 


KIRJIN ME HANKALI 500

Miss xoxo


Pay at

0022419171 AccessBank 

Maryam sani gummi 


Shedan biya 

***


Or mtn vtu at

***