KALBIM

4

by @mamuhgee

*_KALBIM_*

_Mamuhgee_

#ZafafaBiyar




4

*ZUZEAMVENTURES*

***

Aslm barkanmu da wannan lokaci 

Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka

 Mallaka Maganin sanyi

Maganin cire tumbiMaganin farin jini

Maganin matsiMaganin mata

Maganin sa ni’ima da dandano

Dulka Amare Set na gyran jiki

Set na amarya

Tabaje tsumin Gomba

 Xuma kiba ta hips and Brest

Magungunan gyran Brest

Magungunan Karin hips

Maganin sliming

 Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa 

Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi ***

Idan maganin mata kikeso akwai 

Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips 

DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no *** DOMIN mgn da ita whatapp ***muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah πŸ₯°πŸ‘ŒπŸ»

Bononza Bononza Tsimin mangoro 1kπŸ₯­ Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500

Garin bata gaban kishiya 500

Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500

Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500

Za a bakisu akan 3800

Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k

πŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALAπŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜πŸ˜πŸ˜ da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜ƒπŸ™ƒKazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadΔ±πŸ˜‹800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki




*************

Duk duhu da tsit din daren baitaba jin tsoronsu ba dan a haka ya taso komai dare haka yake ratsasa gurin nemowa ummansa Abincin da zata sakawa cikinta sbd ita da babyn datake cikinta su rayu.


Tafiya yayi mai nisa kafin ya isa gidan da zashi din,


Kofar gidan ya tsaya idanuwansa da sukai jajir ya dago ya kalli kofar gidan yana jin zuciyarsa na quna sbd baida ikon buga kofar bisa ga dokar mai gidan,


Ya saba komai dare haka yake zuwa ya buga kofar gidan idan mahaifiyarsa bata lafiya sbd Mama Sakina taje ta taimaka mata,

Mama sakina kuwa komai dare yaxo ya buqaceta bata taba fashin xuwa komai fadan da mijinta zaiyi kuwa,


Duk masifarsa da tsanar da yayiwa Abdul din da mahaifiyarsa sbd sun hanasa kwanciyar hankali da masifar rayuwarsu amma hakan bai taba saka sakina janyewa daga garesu ba sbd kauna ce sosai a tsakaninta da Fatimar da bazata iya barinta a mummunan halinda take ciki ba itada Abdul.


Ba so daya ba mijinta ya saba yiwa Abdul din dukan tsiya sosai akan zuwar masa gida tsakiyar dare.


Zafafan hawaye ne suka cika idanuwansa yana kallan kofar gidan kaman zuciyarsa zata fashe da ciwo da radadin bazai iya kiran Mama sakinar ba dan yana taba kofar gidan baba ilan dukan da bazai iya bawa ummansa kulawa ba a yanzu datake tsananin buqatansa zai masa shikuma bazai iya barin komai ya samesaba a yanzu dayake son kulawa da umman da 'yar data haifo musu.


Gefen kofar gidan ya koma kadan ahankali ya durqusa yana sunkuyar da kansa qasa dan jiran ayi kiran asubar da yasan lokaci yayi insha Allah.


Wani irin sanyi ake kadawa sosai

Sauran ruwan da aka dan dauke suna yayyafowa akansa ahankali suna ratsasa amma bai ko matsaba bare alamar tashi bakin kofar gidan.


Jiran kusan awa daya da mintina yayi kafin masallaci daya kwal dayake kauyen suka rangada kiran sallan daya sakasa miqewa da dauri kafafunsa da sukai wani irin riqewa suka kasa daukansa ya zube a gurin cikin ruwa da lakar datake lalace sosai da kofar gidan.


Rintse idanuwansa yayi zuciyarsa data fara bushewa tin yana karamin nasa ta masa wani irin nauyi yana jin kirjinsa na masa ciwo.


Hawaye masu dumi ne suka gangaro masa ya dafa yana kokarin miqewa aka bude kofar gidan.


Baba ila ne da babban dansa dayake uztaz wanda shi yake sako uban nasa gaba zuwa masallaci lokutan asuba a gida yake sallan baya zuwa masallaci da asuba.


Bude kananun idanuwansa masu kama da kamar an kashe kwarkwata ya waresu akan Abdul din duk da akwai duhu sosai har lokacin amma baya buqatan wahalarda kansa gurin sanin waye dan kai tsaye yasan baida tsohon dan iskan dazai zuwar masa gida bayan Abdul din wanda yake fatar Allah ya nuna masa sunbi duniya sunbar kauyen ko gidansa zai huta da maitar Abdul din.


Cikin zafin rai ya harbi Abdul din da kafarsa yana cewa


"Uban waye a kafar gidana cikin duhun nan??


Cikinsa daya harba ya dafe da hannunsa daya yana dagowa cikin tsananin azaba ya dafa hannunsa daya ya miqe yana kokarin bude baki zaiyi magana Baba ilan ya rigasa da cewa


"Nace uban waye ne a gurin?


Gali dayake gefen baban fitilar hannunsa ya kunna yana haske Abdul din da ita cikeda mamakin ganinsa duk da yasan yana zuwan amma a cikin ruwa da sanyin nan me yakeyi a kofar gidan wanda da alama ya dan jima.


Wasu hawayen ne suka sake gangarowa daga jajayen idanuwansa kafin ya bude bakinsa muryansa a sanqare da sanyi duk da yasan suna sane da waye din amma bude baki yayi yace


"Nine Abdul"


Katsesa Gali yayi da cewa


"Lafiya kuwa cikin sanyin?


Bude baki yayi zaiyi magana amma Galin ya wuce cikim sauri yayi masallaci sbd jin angama kiran.


Baba ila ne ya kallesa cikeda baqin ciki da tsana me tsananin gaske yace


"Allah ya tsinewa sanayyar datake tsakanin Sakina da Uwarka dan kuwa babu abinda kuke qararta dashi sai baqin talauci da baqaqen masifun da kuke yawo dashi,

Ace har tsakar dare bata huta da masifunku ba,

Yanzu ubanme zatai muku da asubar farin??


Wani abu me daci da nauyi Abdul ya hadiye kafin ya bude baki yace


"Haihuwa ummana tayi"


Cikin sabon baqin cikin daya tirniqe baba ilan ya tsaki tsokin daya saka Abdul din rintse idanuwansa yace


"An haifowa sakina wata sabuwar Masifar kenan,to wlh tallahi baa gidana ba,

Na gaji bazan iya ba,duk yanda nake shan rantsuwa da masifa sakina ta ture bata ji bata gani saita ringa daukan abincin danake wahala ina nemowa na gidana ta baku to daga yau ankai karshe sbd bazai yiyu ni ban tara nawa yaran dazan ringa ciyarwa ba haka kawai na koma ciyar da 'yayan wani katan"


Juyawa yayi ya koma ciki yana fasa zuwa masallacin bakinsa na cikowa da kumfan masifa sbd yasan yana tafiya wlh sai an dauki abincin gidansa ko wani abin antafi dashi sbd sakina dai sedai ya barwa fatima da 'danta dan bazata iya rabuwa dasu ba.


Abdul cikin tsananin sanyi da azabar data gama shigarsa ya bi bayan baban da sauri dan kada ya hanasa ma shiga.


Kai tsaye dakin sakina ya nufa ya kiran sunanta cikin tsananin baqin ciki da masifa taresa bacin rai yana cewa maza ta fito.


Daman ba wani nauyin bacci ne da ita ba dan haka cikin bacci taji yana kiran sunanta da karfi ta bude idanuwanta tana kokarin tashi zaune ya shigo dakin sbd daman baa dakinta ya kwana ba ranar a dakin uwargidansa ya kwana.


Yana shigowa dakin ta lalubo fitilarta ta kunna haske ya wadata dakin,


Akan Abdul dayake tsaye a kofa bai qarasa shigowaba idanuwanta suka sauka.


Faduwa gabanta yayi da sauri ta janyo dankwali tana daurawa akanta ta miqe daga katifar datake kai tana ambatar sunansa baba ila ya katseta da cewa 


"Ayau idan har kika fita gidan nan kika bi yaron nan gurin uwarsa wlh tallahi a bakin aurenki hakama abinci na ko wani abin dayake nawa a gidan nan kika basu shima a bakin aurenki,

Bazan iya ba na gaji da renan 'da da uwar da banda hadi komai dasu bare yanxu wata wahalar da aka sake haifowa......


Da sauri sakina ta dago idanuwanta da ciko da hawayen tashin hankali da firgicin maganarsa ta farko ta kalli Abdul jin maganar haihuwar.


Shima dago jajayen idanuwansa yayi ya kalleta cikeda girgiza da tsoron abinda Baba ilan ya fada.


Gangarowa hawayensa masu tsananin zafi sukai ya dan ja baya ahankali batareda ya iya cigaba da tsayawa ba sbd bai san me zai fadawa mama sakinan ba kuma.


Bude baki tayi ahankali tace


"ABDULAZIZ"


Cak ya tsaya batareda ya dagoba.


Kofar inda kayanta suke tai batareda ta cewa baba ilan komaiba,


Zannuwan kayanta na sakawa masu tsafta ta dauko tareda guda biyu da rigarta ta sanyi daya da ita kadai takeda ita ta dauko wanda itace da kanta ta siya abinta da yan kudinta.


Inda take ajiye kudi ta duba tana saka hannu cikin kofin silver me murfi taji babu komai a ciki.


Juyawa tayi ta duba gurin ajiyarta daya taga dari bakwai ne kadai da ita dan haka ta dauko dari biyar ta juyo ta nufi kofar ta fito.


Kayan ta miqa masa cikeda kunyarsa duk da yana qaramin yaro ta bude baki asanyaye tace


"Ka siya mata koko me zafi sauran canjin ka siya itace ka dafa mata ruwan zafi tayi wanka itace da abinda aka haifa"


Hawayensa ne suka gangaro ahankali suka sauka akan dari biyar din data dora masa a tafin hannunsa.


Kasa magana yayi kai ya gyada mata ahankali yana damqe kayan hannuwansa na qara daukan sanyi.


Baba ila daya kasa motsawa sbd baqin ciki da mamaki kallanta yayi ita kuma taqi kallansa 

Baqin ciki sake rufesa yayi kamar zai fashe sbd baqin ciki yace


"Sbd ki nunamun ban isaba shine a gaban nawa ko matsawa daga inda nai maganar banba zaki dauki abubuwa ki basu??

To meye amfani na a rayuwarki sakina tinda kinada Fatima da 'danta ai saiki fice ki bisu kije na bar musu ke wlh"


Abdul kafafuwansa da sanyi yayiwa mugun shiga ya ja ahankali yabar gurin yana qanwame kayan data basa da kudin.


Yana ficewa gidan Mama sakina ta dago ta kalli baba ila har zatai magana sai ya katseta cikin tsananin zafi da cewa


"Wlh tallahi na barwa fatima ke kawai ki tattara ki bar mun gidana ki bita can saiki kwasheta kiyi kauyenku da ita da 'yayanta"


Kofa ya nufa yana ball da butarta dake hanyarsa ta wucewa yana jin zuciyarsa na wata irin tafasa da bacin rai me tsanani.


Numfashi me sanyi da mutuwar jiki ta sake tana danne zuciyarta akan furucinsa wanda shedan ke ingizata data bar masa gidan nasa ta tafin sbd su fatima sunfi buqatarta amma kuma girman auren nata take kalla ta danne zafi da bacin da ranta yayi dan yanzu ne zata biye masa suyita masifa a cikin gidan har wayewar gari da wuni zasu iya wuni suna masifa.


Butarta dayayi wurgi da ita ta nufa ta dauka tana qarasa zubar da ruwan ciki da suka rage ta nufi gurin diban wasu ruwan tana duba butar idan bai fasa mata ita ba.


Tana diban ruwan bandaki ta fara shiga tana fitowa tai alwala ta shige dakinta.

#MAMUH

#ZADEENS

#LIMBAS


ZAFAFA BIYAR


KALBIM 500

mamuhgee


A DUNIYATA 500

Huguma


AJIYA A DUHU 500

Billyn Abdul 


KIRJIN ME HANKALI 500

Miss xoxo


Pay at

0022419171 AccessBank 

Maryam sani gummi 


Shedan biya 

***


Or mtn vtu at

***