Complete
____________Tafe yake yana jogging da misalin ƙarfe bakwai da rabi na safe da gani sa ya jima yana yin gudun, sanye yake da J.C red tare da wandonta wanda yake sample na team ɗin nan na kwallon ƙafa wato Manchester United, matashi ne wanda ba zai haura shekara ashirin da takwas zuwa talatin ba, fuskarsa babu annuri ko kaɗan, dogo ne sosai, yana da faɗi ƙarfafa ne, figure ɗinsa ya fita sosai saboda yawan exercise da yake. He is complexion,long hair ɗin kansa wanda ya kwanta har wuyarsa sai shaining yake, ya yi gumi sosai amma hakan bai sa ya tsaya da wannan ɗan gudun da yake ba, SAIF kenan, Ɗa ga professor Ibrahim Waziri shahararrar ɗan boko wanda duniya ta san da zamansa.
Ƙaramar door ɗin da ke jikin gate ɗin gidan ya tura dan shiga, jin a rufe ya sa ya hau bugu cikin fusata, " waye nan?" ce war Mato (gate man), jin ba amsa ya sa shi saurin buɗewa, tsaye ya ga SAIF ya haɗe rai, " barka da dawowa ranka ya daɗe, afuwa bansan ka dawo garin ba, shiyasa ban kawo kai ne ba" SAIF ya wuce ba tare da ya tanka ma Mato ba.
"Oh yau kowa ya shiga hankalinsa wannan burkitaccen ya dawo" ce war Mato yana komawa tebur ɗin da ya ke zaune.
"Ya SAIF good morning" ce war wani matashin saurayi mai kama da SAIF ɗin fuskar ɗauke da fara'a, hannu kawai SAIF ɗin ya ɗaga masa cike da isa ya wuce,taɓe baki ASH (Ashir) yayi yana ɗaga kafaɗa ya wuce.
"Malam Mato barka da asuba" ce war ASH,cikin fara'a Mato ya ce" barka dai malam Ashir har an fito kenan?" da sakin fuska ya ce" to ya za'a yi lacture ne da ni takwas na safen nan" Mato ya ce" Allah ya ba da sa'a kai maza ka ƙarasa kam" inda machine ɗinsa roba-roba (Lifan) ya ke ya nufa, da sauri Mato ya buɗe gate yana ɗaga masa hannu da faɗin Allah ya tsare.
Ta inda halin su ya bambanta kenan ASH akwai sakin fuska da barkwanci while SAIF ba shi da wannan attitude ɗin, shi mutum ne mai jin izza da isa.
Prof. Ibrahim wanda suke kira da Abba ne zaune ya na karanta jaridar Daily trust, sanye yake da medical glass ya ɗora shi a kan karan hancinsa, a ciki SAIF ya yi sallama ya shiga parlour'n Abba ya gani yana karatu.
Wajensa ya nufa cikin ladabi ya ce" barka da asuba" Proff. Waziri ya gwale ido ya na kallo SAIF ɗin ta ƙasan glass ɗinsa ya ce" morning big boy how are you" SAIF ya amsa " Alhamdulillah and you" hahh I'm fine" ta shi ya yi ya wuce dan shi ba mai yawan magana ba ne tamkar wani kurma haka yake.
Umma ce ta fito daga ɗakin autanta Noor (Nuraddeen) wanda ake ta addu'ar ya zo a matsayin baby girl dan ƙa'idar prof.Waziri yara uku sun ishe shi rayuwa, lokacin da Umma ta haifi Noor duk da taso samun ƴa mace, amma ba ta haifa ba,ta so prof. Ya bata dama ta ƙara haihuwa ko za'a da ce,amma ya fututtuke shi yara ukun nan sun ishe shi, so ya rufewa Umma ido tana ji tana gani aka juyar mata da mahaifa, still SAIF ya gaishe ta sama-sama ya wuce, taɓe baki tayi tana faɗin " ni narasa meke damun SAIF Prof, yaro har yanzu ba zai iya buɗe baki ya yi magana ba as his age ai ya kamata ya dinga magana saboda Allah fa" prof Waziri ya yi dariya irin ta su ta manya ya ce" kinsan dai halinsa ko ciwo yake ba faɗa yake ba,ni har mamakin yanda akayi ya samu girlfriend ma nake hahh"
Umma ta ce" uhm kai ma dai ka faɗa".
Ta wuce dan cigaba da aikinta,shi kuma ya ci gaba da karatun jaridarsa.
* * *
"Ni fa burina ko Fauza, in auri Miji mai fara'a da son mutane, nayi-nayi da my luv ya dinga sakin fuska amma sai ya ce min wai ai yanayi, sai nayi magana goma da ƙyar zai amsa min biyu" wacce ake kira da Fauza ta ce" to kuma kika bari akai muku baiko da shi?" Zahra ta ce" ke duk da hakan inason abina a hankali zan sauya shi yanda nake so" Fauza ta ce"uhum ai naga kina son SAIF ɗin nan sosai"
Fari da ido budurwar da ake kira da Zahra ta yi tana faɗin " more than my self ma kula,I love him so much"ta faɗa cike da shauƙin love.
Kallonta kawai Fauza ta yi tana dariya.
Zahra da Fauza ƴaƴa ne ga Alhaji Saminu Sabo Gashuwa babban ɗan kasuwa ne yana saro suttura daga ƙasashe daban-daban, ya na da mata biyu.
Zainab(Mama) ita ce uwargida tana da yara takwas, Zahra ita ce babba sai Fauziyya wacce ake kira da (Fauza) sai Hafsa, ganin ta haifi mata har uku yasa dangin miji uzzura mata ana kiranta uwar mata, ko a jikinta, yau da gobe akasa dole ya ƙara aure, ya auro ƴar danginsu, wacce ake kira Khadija(Aunty) lokacin da aka auro ta yaran Mama uku, watan Aunty'nsu Zahra takwas Mama ta haifi Namiji, murna wajen Alhaji kamar me, sai kuma danginsa suka hau jin kunya, ganin har yanzu ta su ƴar uwar ko cikinma babu.
Tun da aka haifi Muzammil aunty take ɗawainiya har tausayinta Mama take ji, ranar suna yaro aka sa masa suna Muhammad ana kiransa da Muzammil, cikin ikon Allah aunty ma ta sami rabo, tare da Mama akayi rainon cikin, Muzammil yana da wata goma aunty ta haihu Namiji anyi sha'ani sosai ƴar uwa ta haihu, dan da Alhaji da aunty cousin ne, yaro ya ci sunan Muhammad Mudassir, su Zahra sai suka daina ɗaukan Muzammil dan ya yi musu nauyi, suka koma ɗaukar Mudassir, daga arba'in aunty ta kuma samun wani ciki, wata goma sha ɗaya tsakanin haihuwa ta farko da ta biyu nan ma ta sake samun Namiji, wato Fahad, dangi aka cika da murna, ana kiranta uwar Mazaje, Mama dai sai dai tayi dariya dan ita burinta shine Allah ya ba ta masu albarka da jin ƙai imma Mata ne ko mazan sawa'un.
Shekarar Muzammil biyu Mama ta sake haihuwar Usman, sunan mahaifin Daddy wato (Sabo) Zahra da Fauza sun tasa lokacin sun gama primary ɗinsu, Hafsa na primary four.
Bayan Mama sai aunty ta haifi Abubakar maza uku kenan ana ta faɗin ita dai uwar maza ce, Mama ma ta sake haifar Aliyu, daga nan aunty ta haifi Amina, su Zahra sukai ta murna dan burinsu suga an haifi mace, gata dai Amina tana sha, bayan shekara ɗaya da rabi Aunty ta sake haihuwar mace Hauwa'u (jiddah) Mama shiru, Daddy da ya ke son tara zuri'a ya shiga zargin ko ta tsaida haihuwa ne, har Allah ya isa yayi musu dukkansu duk wacce ta yi family planing bai yafe ba.
Sai da akayi shekara uku sannan Mama ta haifi Saudat, sai da Saudat ta shekara biyar Aunty ta sami ciki, ana ta murna ciki yana girma sai ya zo da matsaloli ana zuwa asibiti aka ce ba ciki ba ne ƙarin mahaifane, sai an yi aiki an cire, Daddy ya biya aka cire ƙarin tun daga nan ba'a ƙara samun ciki a gidan ba, daga Mama har aunty, sai ya zama ƴaƴan aunty biyar, Mudassir, Fahad,Abubakar, Amina da Jidda.
Mama kuma bakwai, Zahra, Fauza, Hafsa, Mudassir, Usman, Aliyu da kuma auta Saudat(Ihsan).
A yanzu Zahra ta kammala karatunta na N.C.E a federal collage da ke Jigawa.
Fauza kuma tana digree a Dutse dan tafi Zahra nacin karatu, Hafsa kuwa tana s.s 2 a yanzu sai ƙannensu da ke ƙananan secondary wasu kuma primary.
Sun haɗa da SAIF ne sanadin zuwansa ziyara wajen abokinsa anan yaga Zahra har ya jira ta kammala N.C.E ɗinta akan Computer/Chemistry
A rashin son maganar suke soyayya sai SAIF ya kwana bai kira Zahra ba, wani lokacin sai ita ke ƙoƙarin kiransa kullum,wani lokaci ya amsa, wani lokaci ya yi burus da ita.
* * *
"Humaira!Humaira!! wata matashiyar mata ce ke ta faman kira, "Na'am Umma ina zuwa" wata black beauty budurwa ce ta faɗa tana ta faman ƙara mulke fuska da powder sanye take cikin uniform light blue riga da wando da farin hijab, bata haura shekara goma sha shida ba.
"Wai me take har yanzu da bata tafi makaranta ba?" Malam Abdullahi (malam) ya faɗa yana shirin fita hannunsa ɗauke da littafan addini.
Da hanzari Humaira ta fito tana ɗauko sandal ɗinta wanda yake jingine ƙofar ɗaki ta sanya, Malam ya ce" ke kullum ke ce ƙarshen tafiya kina babba,amma duk ƙannenki sun fiki hankali"
"su fa ko wanka ba su yi ba fa" ta faɗa tana cuna baki gaba.
Duk cikin ƴaƴan Malam babu wanda yake mayar masa da magana sai Humaira, duk da tana da yayu maza har biyu, Ya Anas da Ya Ahmad amma bata ji.
"Allah ya shirya" ce war Umma.
"ni na tafi" ta faɗa ta bi bayan Malam.
"Ungo hamsin ɗin nan ki ƙara" ta ji Malam ya faɗa yana miƙa mata naira hamsin, karɓa tayi tana nagode.
Allah ya jarabci Malam da son Aisha(Humaira) sunan mahaifiyarsa ta ci.
Malam Abdullahi Ahmadu shi ne cikakken sunansa haifaffen garin Kano ne, karatu ya kai shi jahar Jigawa, sai ya taso acan har ya yi aure ya auri ƴar malaminsa Khadija(Umma) malam yana son karatun boko shiyasa ya sanya duk ƴaƴansa, Anas shi ne babban ɗansa ya kammala degree ɗinsa a fannin agriculture, yanzu ya fi mai da hankali a gona, tunda aiki bai samu ba har yanzu,sai Ahmad yana level two yana karantar fannin lafiya health education,tunda ya yi diploma ya buɗe chemist ɗinsa a ƙofar gidan, Malam da almajiransa na rumfa. Sai Aisha(Humaira) tana s.s two sai Asiya tana j.s three,da kuma auta Abubakar (sadeek ) wanda yake j.s one a yanzu.
Aisha Humaira ita ce wacce ta fita zakka duk cikin ƴaƴan Malam Abdullahi, ƴar ƙarya ce dan idan ta fita bata nuna ita ƴar malam ce, Allah ya yi musu kyau gaba ɗayansu dan daga wanda ya yo kyan Umma sai wanda ya yo farinta wasu kuma suyi baƙin malam.
Umma ƴa ga Malam Bala asalinsu Shuwa ne na can yankin Maiduguri, shi ma daga karatu ya zauna anan har ya kafa tsangayarsa.Tun haihuwar Asiya Allah yayi masa rasuwa, sai kakarsu Inna Abu wacce ta tsufa sosai, sai ƴaƴa da jikoki dan su takwas Inna ta haifa, Alhaji Muhammad, da Alhaji Jamilu waɗanda suke zaune a garin Kaduna da nasu iyalan, sai malam Umar wanda yake zaune a gidan da matansa biyu da ƴaƴansa,sai Halima ita ma tana nan da nata iyalan har da surukai, sai Khadija(Umma) sai Ɗahiru sai Bilkisu dukkansu sun manyanta kowa yayi nasa iyalin.
Inna Abu mahaifiyarsu ta tsufa sosai dan komai sai anyi mata, jiran wa'adi kawai take.
Duk jikokin gidan suna zuwa gidan dan Kawu Umar akwai kafaɗar ɗaukar ƴaƴan ƴan'uwa yana da zumunci sosai duk da ba shi da ƙarfi, duk jikokin gidan suna zuwa amma banda Humaira dan ta tsani a ce wannan gidan ne gidan kakanninta, duk da ta kasace ƴar talakawa bata ƙawa da ƴaƴan talakawa sai ƴaƴan masu hali, ganinta kyakkyawa yasa ta tara ƙawaye ƴaƴan masu farcen susa(Riches).........
__________SAIF na shiga bedroom ɗinsa direct ya wuce toilet, sportwear ɗin dake jikinsa ya cire ya watse cikin washing machine ya sakarwa kansa warm water, almost thirty-five minutes ya ɗauka yana wanka sannan ya ɗauro towel a ƙugunsa, ya sa ƙarami akansa yana goge sumarsa,sai da ya tsane jikinsa,sannan ya shafa body lotion ɗinsa Oars+Alps, still ƙananan kaya ya sa sannan ya ƙara gyara gashinsa ya sa masa nasa mayukan, sagensa ya gyara tsaf ya fito, blue black ɗin jeans ya sa da j.c red mai hoton kan lion a gaban rigar,lokaci ya duba goma saura,cikin hanzari ya yi parlour, Proff.Waziri da Umma ne zaune sai auta Noor wanda, ya ke kwance yana jiran a gama zana masa S.S.C.E ɗinsa, yaron ma kamar su ɗaya da su SAIF bai wuce shekara sha biyar ba.
Sallama SAIF ya yi ya ja kujera ya zauna a dinning ɗin, Umma ta ce" ina ka ce an tura ku?" SAIF ya ce " Niger state ne" Proff ya ce" i proud of you my soldier Amma ba wai permanent zama zakuyi a can ba ko?"SAIF ya ce" no Abba akwai wasu waɗanda ake tunanin suna fasa bututun petroleum shi ne zamu je dan sa ido akan hakan, da zarar munyi nasarar cafke su,shikenan zamu dawo ma nan gida" Umma ta ce"to zai kai ku tsawon wana lokaci, dan ni gaskiya banaso ka ajiye ƴar mutane a gida kai kana can wata uwa duniya" SAIF ya ce" i don't know" proff ya yi murmushi ya ce" ki bar shi mana,ai ya san da auren nasa ya kusa, nasan dai duk abu ba za su shekara a can ba" surutun da suka saka shi yi ma ya fara damunsa tea kawai ya sha, ya miƙe don zuwa gidansu abokinsa Ahmad Sulaiman wanda suka shigo tare a daren jiyan,dan lokacin da ya dawo,Mato baya bakin gate, ya zaga bayi Labaran ne ya buɗe masa zai fita kenan uzurinsa ya ga SAIF ɗin.Shiyasa bai san da zuwan sa ba.
Major Ahmad da SAIF tasu ta zo ɗaya tun suna secondary school suke da burin zama sojoji,su na kammala s.s.c.e aka kai su military school da ke Abuja acan sukayi karatu,a yanzu sun kammala suna amsa sunan Major S.Waziri, da Major A.Sulaiman, Ahmad mutum ne mai neman mata da shan basara saɓanin SAIF ba ya ko wanne ciki dan some times idan aka yi posting ɗinsu wani state ɗin to har kawo musu mata karuwai ake gamasu buƙata.
Labaran driver ne ya ga fitowarsa, dan takunsa ma na musamman ne ƙato ne sosai,duk da irin baƙar wahalar da suke sha a camp bai sa ya yi duhu ba,bare yanzu da jikin ya saba.
Sanin SAIF da izza ya sa Labarin tashi yana faɗin "fita ne Yallaɓai?" SAIF ya ce " ina car's key ɗin?" a aljihunsa ya ɗauko mukulli had uku ya na miƙawa SAIF, ɗaya ya ɗauka na wata mota ƙirar sedans black color, da hanzari Mato ya nufi gate dan kar ya yi abinda za'a sa shi tsallen kwado ko gwale-gwale.
Cike da ƙwarewa ya ke driving ya fice daga gidan, dukkansu suka sauke ajiyar zuciya,Mato ya ce"na rantse ni dai ina mugun tsoron yaron nan, tun ranar da na bar Alhaji a tsaye na zaga bayi ya fito ya ga kamar na wulakanta masa uba ne, yasa ni gwigwayar guiwata, kasan Allah ranar na wahala"Labaran ya kwashe da dariya ya na fadin nima shaida ne,na ji ance aure zai yi ai"
Mato ya ce"wai wacce mara rabon ce,amma na tausaya mata" Labaran ya ce" kai bar irin waɗan nan ai basa iya yiwa mata komai, alkur'an kar kayi mamaki ka je gidan bayan auren kaga yana tuƙa mata tuwo hahhh" Mato ya sa dariya ya na faɗin "amma da anyi Namijin hotiho alkur'an ka na bawa Mazaje kashi kuma kai mace ta baka kashi hahhh"haka sukai ta hirar SAIF wanda ya jima da barin gidan ma.
Major.A.S na parlour yana ta bacci dan ya gama buguwa, anan ya kwana ma. Mamansa ƴar kasuwa ce bata ma gidan ya dawo, mahaifinsa General Sulaiman ya jima da rasuwa tun a wani yaƙi aka kashe shi, ya mutu ya bar musu dukiya mai yawa shine Hajiya Binta take business ita ce Dubai, ita ce Saudia ita ce Italy, China shigo da kaya irinsu kayan kitchen da na furnitures, su labulaye, gas cookers, refrigerator da sauransu.
Ahmad shi kaɗai ne ɗanta a duniya shiyasa duk wani gata ta ba shi, ba kwaɓa bare tsangwama.
Kafin su tafi military school duk wata house made ɗin da Hajiya Binta tayi sai ya lalata ta, kuma haka Hajiyan zata toshe wa iyayen yarinya baki da maƙudan kuɗaɗe har su bar maganar, bata san adadin yaran da ta zubarwa ciki ba, tun tana yi masa faɗa har ta daina ta dawo nasiha, idan aka kwana biyu kamar ya daina sai ya kuma ɗauko mata magana, ita ta ba shi lacis na bin matan banza.
SAIF yana bakin ƙoƙarinsa wajen ganin Ahmad ya shiryu amma abun kamar turi.
Tun daga gate maigadi ya sanar da shi, Hajiya bata nan,amma Ahmad na ciki, a baje yake a parlour ga bottles nan na wine har biyu a ƙasa, ya na ta bacci, chief osaro yana ta gyara parlor'n dan yanzu Hajiya ta daina ɗaukar mata yan aiki, saboda Ahmad.
Good morning Sir,ce war Osaro sanye da rigarsa da hularsa ta kuku daga ni girki ya ke yi.ko amsawa SAIF bai yi ba, zama yayi yana faɗin "oh my God!" gami ta dafe kai, Osoro ya kwashe bottles ɗin ya na gyara wajen, "A.S.,A.S!! SAIF ya shiga buga gefen kushin ɗin da Ahmad yake, a hankali ya buɗe idanunsa ya na miƙa,ganin SAIF ya sa ya saki murmushi, sai ya hau sosa kai, dan yasan kallon da SAIF yake masa, dan ya same shi ne a wannan yanayi ne.
"Ka yi sallah?"
A.S ya miƙe da sauri yana duba clock ɗin da ke tamgamemen parlourn nasu, sha ɗaya saura, "subhanallahi" da gudu ya yi sama dan zuwa ɗakinsa, sai da yayi wanka sannan ya yi sallah, SAIF da ke parlour yana kallon football, ya ji ringing wayarsa dubawa ya yi dan ganin wanda ke kiran, my Zahra ya gani kamar yanda ya yi sarving numbers ɗinta, sai da ta gama ringing sannan ya bi kiran.
Zahra da zumuɗi ta amsa "hello hayatee" SAIF ya ce" ya akayi?" bata ji daɗin wannan kalmar da ya faɗa ba, amma dole Zahra ta dake ta ce" nayi missed ɗin ka ne, ashe ka dawo shine ba noticing" dafe kansa ya yi yana faɗin" ayyah sorry na ɗauka already kin sani ne" Fauza ta taɓe baki tana faɗin" iska na wahal da mai kayan kara" ta bar ɗakin, Fauza na da saurin fushi, tana mamakin yanda akayi Zahra ta ke iya jure faɗin ran SAIF.
"Yanzu kana ina my luv?" SAIF da yaga zata fara zuba, ya katse ta da ce wa" I'll call you later"ya yi cutting call ɗin.
Murmushi Zahra tayi tana faɗin" oh my luv kenan, kullum busy!busy !! Haka suke fama, Allah ya sakawa soldiers ɗin mu da alkhairi irin wannan ƙoƙari haka, ko lokacin kansu ba su da shi" ta na ta surutai ita kaɗai, duk a tunaninta wani important issue ne ya taso masa.
Aunty ce ta shigo ɗakin nasu, tana faɗin" idan kin gama wayan ki je Umma na kiran ki" Zahra ta tashi tana murmushi ta ce" kai aunty nifa ba waya nayi ba" aunty ta ce" ke kika sani" ta wuce ta ɗauki ribbon ɗin Jidda da Fauza ta gama yi mata kitso ta yarda shi a nan.
Muzammil da Mudassir, da Fahad ne suka shigo ko wannensu ɗauke da school back, sai ka ɗauka sa'anni ne dan Fahad da Mudassiri kansu ɗaya da yake tsiran nasu babu yawa, Muzammil ne ya ɗan fisu da ke shi ya bawa Mudassir shekara,Fahad kuma shekara biyu, kansu a haɗe yake ba wanda yake iya gane ɗan wancen ɗakin da wannan ɗakin.
Tarbiyya dai-dai gwargwado su Umma na bawa zuri'arsu.
"Sannuku ƴan albarka" ce war Umma da take ɗinki akan kekenta, dukkansu suka durƙusa suka gasheta, Fahad ya ƙarasa zama a carpet ɗin yana faɗin"wallahi nagaji" cikin kulawa ta ce" ai dole tun safe sai uku Allah dai ya bada sa'a" Mudassir ya ce"ina su Haidar?" Umma ta ce"duk sun tafi islamiyya shiyasa ka ji gidan shiru"
Aunty ce ta fito daga ɗakinta, a tare suka ce "sannu da gida aunty, ya aiki" ta amsa tana jin daɗin yanda suke su ukun nan komai a tare suke, ta ce" ku wuce ga abincinku can a dinning idan kunyi sallah sai ku ci" duk suka amsa da to,suka nufi ɗakinsu.
Sai da sukayi wanka sukayi sallah, sannan suka ci abinci, uniform ɗinsu na Islamiyya suka sa sai la'asar suke shiga.
Muzammil yana hadda ta biyu ne, Mudassir da Fahad ne ta farko.
Suna girmama yayunsu watukun su Zahra, da Fauza, Hafsa ce dai suka raina dan har dambe ake da ita, sai da aunty ta yi musu da gaske sannan suke barinta, amma dole wani lokaci sai anyi musamman ita da Mudassir (ɗan aunty) dan Muzammil bai cika hayaniya ba.
Alhaji Saminu ne zaune a kasuwa cikin katafaran shagonsa wanda yake tamkar plaza dan shaguna bakwai ne a jere ya mai da shi ɗaya.
Ganin bikin Zahra sai gabatowa yake, proff.Waziri ya kira dan su sada zumunci jin su shiru kusan wata biyu SAIF bai zo ba, duk da yasan baya gari amma Proff. Yakan kira lokaci zuwa lokaci su gaisa.
Proff.Da ya kai ziyara cikin Dutse University wajen abokansa.
Yaga kiran sirikin nasa, amsawa ya yi, cikin mutunci suka gaisa, Proff ya ce " ai ɗan naka ma ya zo, ko ya shigo ne ma bansani ba hahh?" Ya tambaya da fara'a, Alhaji ya ce" to ni ina nasani Proff, kasan yaran nan ai sai dai a barsu, daman na kira ne dai a gaisa" proff ya ce " wow I'm very happy, thanks"Alhaji ya ce" never mind"Sun jima suna hira sannan su ka datse wayar.
"In-law ɗin SAIF ne" ce war proff, Dr. Uwaisu ya ce"to,to, naji, bikin ya na ta ƙaratowa proff"
"wallahi kuwa i think January ne ai"
Kai ma sha Allah,abu ya zo kenan, Allah ya sanya alkhairi ya sa muna da rai da lafiya" proff ya amsa da amin, nan suka ci gaba da tattaunawa.
* * *
Cikin yanga ta nufi class ɗinsu, s.s.three a,Mathematics teacher ne a ciki, sanin ba sa shiri ya sa ta ƙara haɗe fuska ta shiga da sallama, Malam Balarabe ya ce"get out!!!, cikin tsawa, ajin cike yake da ƴanmata dan makarantar mata ce, Humaira ta saɓi jakarta ta juya tana faɗin" so what dan ka kore ni aikin banza mtsww" take ran Malam Balarabe ya ɓaci, a fusace ya fito yana faɗin" kneel down here, useless, stupid" Humaira ta kalli ƙasar wajen da yake faɗin tayi kneeling ta yi gaba, a fusace ya janyo hijab ɗinta ya ɗauke ta da mari, ihu ta fasa ta hau faɗin wayyo Allah idona, bai saurareta ba ya kuma kifa mata mari a ɗayan kuncin,yana faɗin ni kike zagi, mara tarbiyya" gaba ɗaya ɗaliban da ke area sun leƙo, class ɗin su Humaira gaba ɗaya sun fito suna ihu, wai ya cakumeta.
Malamai ne suka tawo, ganin Humaira a durƙushe tana faman zumduma uban ihu, abinda ke faruwa suka tambaya kafin ya yi magana ƙawar Humaira mai suna Zee Musa ta ce" Sir late tayi shine ya koreta dan ta fita bata ba da haƙuri ba ya cakumo mata hijab ya mareta" sai ita ma ta sa kuka, gaba ɗaya ƴan class suka hau faɗin hakane.
PC ya ce " every body go back to your class, who are ask you iyee munafukai" komawa sukayi su na murna yau zaa sallami Malam Balarabe Dan ya ishe su, sun tsane shi kullum sai ya ba su assignment, idan ba ka ci ba ya zane ka kuma dole sai ka sako masa, idan ka makara ya koreka kuma kai ma sai ka yi wannan assignment da ya bayar duk da baka nan ya yi aikin.
Jikinsa har rawa yake jin suna neman ƙulla masa sharri, ya ce" wallahi ba haka ba ne, ta zo ne late dan na koreta daga class ɗin shi ne ta zage ni"
Malamai mata ne suka ce "ke dalla yi mana shiru mara kunya futsararriya za ki ta shi ko sai an tashe ki" ce war wata malama.
Humaira dai sai faman murza ido take, tana kuka, Malam Jamilu ne ya ce"ku duba idonta dai" wata malama ce ta je ta ɗago Humaira, kuncinta ya ɗaga idonta yayi jajir ana ta buɗe tana ƙara runtse shi, hankalin Malaman ne ya tashi, Pc ya ce" haba Malam Balarabe meyasa ka cakumi mace sai ka ce zakayi faɗa da ƙato"
Malam Balarabe ya ce" wallahi ranka ya daɗe sharri sukayi min, marinta kawai na yi"
Ɗalibai duk sun fito ana ta kallo.
Malamai mata dai sun san Humaira da tsiwa da rashin kunya, wasu suna a kaita asibiti wasu suna faɗin babu inda zaa kaita makirci ne, kamar haɗin baki students suka fito suka nufi gate za su fita wai zanga-zanga za su yi, Malami ya taɓawa ɗaliba nono, maigadi na ƙoƙarin rufe gate, suka take shi, suka bi ta kansa, suka fice a guje suna ihun ba za su yarda ba...............
(Malam Balarabe ka taɓo tsuliyar dodo loll🤪).
_____________Hankalin jama'a gaba ɗaya ya yi kan waɗan nan ƴanmatan da suka cika kan titi,su na ihun ba za su yarda ba, mutane sai tambayar meke faruwa ake yi kafin wani lokaci ƴan jarida sun hallara, da ƙyar akayi control ɗin su, da taimakon policemen ɗin da ke kusa da school ɗin, dan ba su da nisa da station.
Ɗan jarida ya shiga tambayarsu akan me suke zanga-zanga? take wasu zaƙwaƙurai suka ce" akan wani ɗan iskan malamin mu da aka kawo mana, ba za mu yarda ba sai ya fake da displing ya dinga cakumo mu yana duka yanzu ma gashi can ya fasawa wata ido" Matasan da ke wajen suka fusata, masu ɗaukar katako nayi, masu ɗaukar barandami nayi suna faɗin "wallahi muma ba za mu yarda a fake da koyarwa ana lallatse mana ƙanne ba, dole sai mun ɗauki mataki" gari gaba ɗaya ya hargitse.
A cikin school kuwa Pc ya ce kowa ya bar makarantar nan, hankali tashe malamai suka fara hawa abin hawarsu masu machine suna goya waɗanda ba su da abin hawa,masu mota ma suna ɗaukar wasu dan tsira da ransu da kuma mutuncinsu.
Malam Balarabe ya kalli Humaira wacce take nan a zube ta na faɗin idona,wayyo idona, cikin ƙunar rai ya ce"Allah ya isa sharrin da ku ka yi min" Malam Bashir ya kamo shi yana faɗin " ta taso mu je asibiti, kasan dole gwamnati sai ta magantu akan wannan al'amarin" Balarabe da idanunsa ya yi jajir, dan yasan aikinsa yana rawa a yanzu,ga nauyin da ke kansa na iyayensa da matarsa da ƴaƴansa guda biyu, a hakan ma manage yake da salary ɗin sa dan baya isar sa, sati biyu ne abincinsu ya ƙare haka zai ta buga-buga har wata ya ƙare, kafin ya samu wani salary ɗin ya ci kusan rabin kuɗin a bashi.
Malam Bashir na ƙoƙari dan Humaira ta tashi, su ka ga mutane sun shigo makarantar ga ƴan jarida har da ƴan sanda ga matasa da ake ta hanasu shigowa dan kwantar da wannan tarzoma, " dole sai mun ɗau mataki, akan cin zarafin da ake wa ƙannenmu Mata, ba za mu yarda ake ɓata mana ƙanne ba,tunda aka tsiyayar mata da ido sai mun ɗauki fansa" ce war wani ɗan daba da katako a hannunsa.
Su uku suka rage a school ɗin kowa ya gudu, wasu police ɗin ne suka zo, suka fara kame matasa anasa su a mota, Malam Balarabe da cikinsa ya ɗuri ruwa gabansa sai faɗuwa yake.
Humaira na jin jama'a ta ƙara bajewa tana wahalallen numfashi.
Human rights sun zo, dan kare haƙƙin wacce aka ci wa zarafi.
Ƴan jarida suka nufi wajen su Malam Bashir dan jin kanu.
"Malam barka dai ko ka san abinda ke faruwa a wannan makaranta na cin zarafin ƙananan yara da neman keta musu haddi da wasu malamai ke yi?"
Malam Bashir ya ce "innalillahi wainnailaihirrajiu, gaskiya babu wannan maganar yau shekarata goma ina aiki a wannan makarantar, gaskiya makamancin haka bai taɓa faruwa ba" Ɗan jarida ya ce" amma ga wata yarinya can a kwance naga ma Ambulance ta zo dan tafiya da ita,shin me ya faru da ita ne?" Take Malam Bashir ya ce "hatsaniya ce ta haɗa su da wannan malamin shine ya mare ta,to shikenan yara suka zuzuta abin"
Ido ne ya dawo kan Malam Balarabe,wasu ƴan sanda guda biyu suka cafke ƙugunsa kamar wanda ya yi sata, wasu na ƙoƙarin a bar su su dake shi, ma'aikata na hanasu, ƴan jarida na son jin ta bakin Malam Balarabe, amma ƴan sanda har sun saka shi a motarsu suka tafi da shi, wasu kuma suka shiga Ambulance ɗin da aka tafi da Humaira, daga nan mutane suka watse, students ma suka nufi nasu gidajen dan kai rahotu.
Tunda aka fara hatsaniyar su Asiya ba su san da Yayarsu abin ya faru ba, sai da taga Zee Musa da ƴan class ɗinsu, suke faɗa mata Humaira akayi wa haka, hankalinta a tashe, ta dinga kuka jin an zubarwa da Humaira ido, ana fita zanga-zanga ta nufi gida wajen goma da rabi na safe.
A guje ta faɗa gidan tana haki, dan tun da ta fice daga makatantar bata tsaya ba, gudu kawai take.
"Umma! an tsiyayarwa da Humaira ido a makaranta" gaban Umma ne ya faɗin, jin wannan mummunan labari, almajiran da suka rage a gidan ne suka shigo ganin yanda Asiya ta shigo a furgice, jin Umma na salati ya sa su tambayar abinda ke faruwa, Asiya ta faɗa musu tana kuka, take suka shiga kiran Yaya Anas dan yana can gona tare da ma'aikata yana ba da umarni, sanar da shi halin da ake ciki, Yusuf ya yi, shima nan da nan ya baro gona ya tawo gida, yana kiran ƙaninsa Ahmad, yana kasuwa saro magungun da suka ƙare a chemist ɗinsa, ya ji Ya Anas yana sanar da shi abinda ke faruwa, dukkansu sun ɗauka Humaira na gida suka yo gidan.
Malam ne ya shigo hannunsa ɗauke da kayan miya, dan wani lokacin baya aiken kowa da kansa yake yo cefanensa ya kawo, Asiya tana kuka ta ke yi musu bayanin abinda ya faru, gaba ɗayansu suka nufi makarantar Asiya da Umma aka bari, a hanya suka ji ana labarin an tafi da ita asibiti, shi kuma malamin police sun tafi da shi.
Anas sai mita yake, yana faɗin" yarinyar nan ba ta jin magana, ai gashi nan an nakasata" Malam kuwa kawai jefa ƙafa yake yana ta addu'ar akan Uwarsa(Humaira) direct suka nufi A&E na asibitin Palace, dan nan ne asibitin ido.
Ahmad ya kira abokinsa Dr.A.A dan jin yana ciki, ashe ma shi ne ya auna idon Humaira, pc da vice ɗinta duk sun zo asibitin dan daman lafiyarsu suka gudarwa dan kar mutane su fusata ganin zanga-zanga.
Suna ganin ƴan uwan Aisha Abdullahi Ahmad pc ta tawo, haƙuri ta shiga bawa Malam, yana yi musu bayanin abinda ya faru, Ahmad ne ya wuce ciki dan an hana kowa shiga, shi da Dr.A.A ne suka wuce, tana zaune a gadon marasa lafiya, ta na tunanin abinda zata ce a gida, dan kar yayunta su casata.
Ganin Ahmad ya shigo, ya sa ta miƙe da sauri, ta shiga yar fa hannu tana faɗin" dan Allah Ya Ahmad kayi haƙuri,wallahi lokacin da ya mare ni na ɗauka idon ya cire ne" Ahmad da ya ganta lafiya, ya furta Alhamdulillah a ransa, amma a fili ya ce" ni ina ruwana ke kika ɓatawa kanki suna ai" Dr.A.A ne ya ce "zo ku tafi, Allah ya kiyaye gaba.
Lauyan gwamnati ya sa hannu, dan an sanar da ce wa idonta lafiyarsa lau, suna fitowa wajen a cike yake da mutane dan jin result, kowa yaganta ƙalau,Malam ya kamo hannunta yana faɗin" meyasa me ki uwata?" Humaira ta ce" wani malami ne ya mammare ni akan na makara"
Ƴan jarida sun sami abin faɗa aikuwa aka yi mata caaa ana tambayarta akan cakumar da ake faɗin malamin yana yi wa ƴan mata, take Humaira ta ce eh haka yake.
Daga nan akai ta yi wa malam Allah ya kiyaye gaba, a mota mai kyau aka dawo da su gida.Anas na faɗin daga yau kin daina zuwa makarantar ma.Humaira tayi shiru,Malam ya ce " kai ne za ka yi mata jarabarwa ƙarshen ko kuwa?" Ahmad ya ce" za mu biya ta zana s.s.c.e a private school kawai" Anas ya ce " final" Ɗadi Humaira ta ji, jin zatayi candy a shekarar ji tayi kanta ya ƙara girma.
Sai da suka ga ta warware suka nufi station dan fitarda Malam Balarabe.
Mahaifiyarsa tana ta kuka tana faɗin ayi masa afuwa, tsautsayi ne, matarsa ma haka, da ƙannensa Mata, da Allah suka dogara,kuma da shi suka dogara.
Malam Balarabe da ke rufe a cikin cell, ya na jiyo ƴan uwansa,hawaye ne kawai ke zuba daga idanunsa, baya son sharri a rayuwarsa.
Jin ance Malam ne mahaifin yarinyar, tsohuwar ta durƙusa a gaban malam tana roƙonsa akan a sakar mata ɗanta, kowa sai da ya tausaya mata, wasu ƴan sanda da lawyers su huɗu suka shigo da result station ɗin,bayani sukayi akan an sallami yarinyar, kuma an dakatar da Malam Balarabe watukun an ba shi suspension, kuma an dakatar da salary ɗinsa,har sai an gama bincike akansa.
Belly ɗinsa su Ahmad sukayi,suna faɗin su sun yafe tunda Allah ya kiyaye. Sai da aka fito da Malam Balarabe sannan suka tafi.
Da yamma ƙawayen Humaira suka zo, anan ne Umma ta ji duk su suka shirya wannan badaƙalar.
Tun daga ranar Humaira ta bar zuwa school, duk da an hanata fita,amma da taga yayunta sun fita, ta ke ficewa, Malam dai lallaɓa uwarsa yake, dan ita yafi so, kuma ita tafi wahal da shi..........
* * *
Sanye suke cikin army's uniform ɗinsu kowanne ya sha stocking, fuskar nan ta sa ɗaure, Major A.sulaiman ne ya ce" Allah ya sa mu samu damar kamasu da wuri, mu je mu sha biki" Major S.Waziri(SAIF) ya yi banza da shi duk da yana son auren amma baya jin zai iya ɓata lokacinsa akan matar, duk da ita ce zaɓinsa.
Sai da sukayi sati biyar sannan sukayi nasarar kammala aikinsu na kame ɓarayin gwamnatin.
A can gidajen biyu kuwa ana ta shirye-shirye dan Proff ya sanar da su, biki ba bu fashi.
Amarya ana ta gyara sai zumuɗi take ita da ƙawayenta, tun suna ƙorafi akan ba su ga angon ba, tana faɗa musu ita fa matar soja ce, baya nan, suna can daji sai gab da bikin zai zo, komai ASH ne akai da wasu abokan SAIF ɗin.
Tsaye yake jikin machine ɗinsa ya sha wanka, sanye yake da farar riga da black jeans idanunsa sanye da black shade wanda ya bayyanar da asirin kyawun fuskarsa, bai kai tsayin SAIF ba, hakama bai da faɗi sosai, fuskarsa ɗauke da smile yana jiran fitowar amaryar yayan nasa.
Ita kaɗai ce ta fito sanye da hijab onion color ta na yi masa fara'a kamar kullum, da sallama ta ƙarasa inda yake ya amsa yana washe baki " sai amaryar yaya, a' a wannan kyau haka, meye sirrin ne?" ce war ASH, dariya sosai Zahra ta yi ta na faɗin"kai Ƙanin nan nawa halinka sai ke, ina kyan yake anan" ASH ya ce" ba za dai a gayamin ba ko, okay daman zuwa nayi ko akwai abinda kuke buƙata naga lokaci sai ƙurewa yake yi?"
Zahra ta ce" kenan har yanzu bai dawo ba?" cikin sanyin murya, da gani abin na damunta.
ASH ya sa dariya ya na faɗin " to wai ba gani ba, ni da shi fa abu guda ne hahhh" dole Zahra sai da tayi dariya ta na faɗin "mijina ya fika kyau" ASH yana faɗin" wallahi ƙarya ne, mutum sai ka ce basamude kullum fuska kamar ta zakuna" Zahra ta ce" one, zero wallahi zan rama ne" nutsuwa ya yi ya ce" naga isha ta kusa bari na zo na koma, babu wani abu dai burina kawai in sauke nauyin da ke kan Yayana"Zahra ta ce" sannu masu wa, um kawai dai abinda ya rage yanzu shine inda za mu yi dinner amma tunda baya nan ina ga ba sai anyi ba na haƙura" ASH ya ce " wannan ba zai gagara ba, za'ayi dan nasan duk inda yake hankalinsa na nan, wai ma ba ga ni ba, sai in sha shaddata in zauna a high table ɗin.
Murmushi tayi tana faɗin "Allah ya shirye ka" daga nan sukayi sallama.
Ana saura kwana uku ɗaurin aure SAIF ya iso gida da yamma, ƴan uwa aka rufe shi da guɗa, ji ya yi kansa ya sara, abunka ga ƴan boko abokan wasansa sai jansa suke,amma uhum bai ce musu ba, gaisuwa ce kawai ta haɗa shi da su.
ASH ne ya kira Zahra dan yi mata albishir da dawowar SAIF, tayi murna sosai dan tun jiya suka fara event ita da ƙawayenta sunyi Fulani day, yau kuma za'ayi cock-tail party,Zahra har rama tayi na rashin ango, ga shi sau ɗaya suke waya hakama dan gabatowar bikin ne wai nan yana sane da ita.( A hakan).
Sai da ya yi wanka ya nutsu, har ɗaki Umma ta sa akai masa abinci, sanin ba zai fito ba, saboda jama'a.
Zahra ya kira, tana gidan make-up, ta na ɗauka ta ce " welcome back my groom, hope ASH ya sanar da Kai event ɗin yau, dan Allah kar ka ce min ba za ka zo ba" ta ƙarasa faɗa cikin shagwaɓa.
Wani iri ya ji a jikinsa tsigar jikinsa na tashi, take ya amsa da " okay maybe i'll coming but he don't tall me anything" take ta hau zayyana masa, tana faɗin wai ASH bai tura maka invitation cards ɗin ba?" SAIF ya ce " aiki naje yi ba wai chatting ba, bansani ba ko ya tura ma, i don't know" haushi kamar ya kashe Zahra dole ta danne ta ce, ni dai tunda ka dawo dan Allah ka zo, yauwa nasan ASH zai sanar da kai komai"
Suna wayar kuwa sai gashi ɗauke da wata box mai ɗan girma.
Katse wayar ya yi yana kallon ASH ɗin da ya ajiye masa akwati, Ya SAIF sannu da dawowa, yauwa ga ɗinku nan nan, kamar naji tana faɗin yau ne cock-tail party, shigar purple and pink ne,ku zaku sa purple friends ɗin ku pink, already su Hamza duk sun yi, naka na ciki"
Ya buɗe box ɗin ya na fito masa sa wata shadda mai bala'in kyau, ta cike wajen da ƙamshi na musamman da hula ita ma mai kyau wacce take marti color, ta shiga da kayan sosai.
SAIF ya ce" okay komai dai ya yi normal ko" ASH ya ce" eh mun haɗa komai ni da su Hamza da Umar" SAIF ya ce " okay tnx" ya koma ya kwanta.
Haushi bawa ASH,ganin yana ango ya wani je ya kwanta a ɗaki, ko shiga cikin abokansa bai yi ba.Ɗakin ya bari yana mitar halin SAIF.
Sai da amarya ta gaji da jira sannan angwaye suka zo,ɗaukarta daga wajen make-up ɗin, sunyi kyau iya kyau, dan wajen ya haɗu sosai, hakama abokan ango da amarya, duk wanda ka gani a wajen anko ne a jikinsa.
ASH sai fara'a yake tamkar shi ne ango, ango kuwa kamar an aiko masa da mala'ikan mutuwa fuskarsa murtik.
Su Major A.S da wasu daga cikin abokan aikinsu sun iso, wasu kuma sai ranar ɗaurin aure dan za'ayi faret na taya murna ga ango.
Cikin farinciki aka gama wannan sha'ani.
Ka she gari akayi dinner wacce ta tara manyan ƴan boko da ƴan kasuwa dan iyaye maza ma ba'a barsu a baya ba su proff da Umma an gwangaje, dan rasa su waye iyayen su waye ƴaƴan akayi, har su make-up Umma aka je.
Mama da Aunty ma da ba su kai Umma tsufa ba, sun sha make-up kowa ya yi kyau a wajen sai wajen ɗaya na dare aka tashi. Bayan an gama cashewa su Baba da Abba an yi liƙi sosai, haka ma ASH da abokan ango.
Baccin gajiya kowa ya yi, da safe akai oder na abinci da snacks na ɗaurin aure,
Gidan su Zahra kuwa tukwane ak a ɗora tun cikin dare ake girki, ƴan uwa ba suyi bacci ba.
Sojoji ne danƙam suka cika wajen ɗaurin aure, Ango da abokansa ma sun iso wajen cikin fararen shaddoji gaba ɗayansu ango ne ya sa milk color, yawanci sojoji ne da musulmai da Christians.
Ƙarfe sha ɗaya aka ɗaura auren Major SAIF Ibrahim Waziri da Zahra Sabo Garba Gashuwa akan sadaki naira dubu ɗari..............
________A zaune take gaban Daddynsu fuskarta a lulluɓe tana ta sharɓar kuka, ga ƴan'uwan sa nan duk a zaune cikin dakiya Alhaji Saminu ya fara yi mata nasiha kamar haka: "Zahra'u ki yi haƙuri, ki yi haƙuri, shi aure gaba ɗaya ya ta'allaƙane bisa doron haƙuri, daga yau kin bar hannuna Alhamdulillah Allah shi ne shaida na baki tarbiyya dai-dai gwargwadon iyawa ta, yanzu ke wakiliya ce ta gidan nan, duk abinda kika aikata a gidan ki za'a danganta shi ga mu ne, ki yi biyayya ga Mijinki da iyayensa ki ɗauke su tamkar su suka haife ki, ki kula da amanar aure Allah ya baku zaman lafiya, ya kaɗe duk wata fitina Allah ya yi muku albarka" ameen ameen kowa ya amsa.
Aunty ce ta ɗagota tana faɗin "mu je wajen Mama" Zahra ta ta shi suka nufi ɗakin Mama, jikin Mama ya yi sanyi tana zaune a bakin gado ita da danginta, Zahra na shiga ta rungume Mama tana kuka mai tsuma zuciya, rarrashinta Mama ta hau yi, tana danne nata kukan, haba Zahra'u me ye na kukan kuma, haƙuri za ki yi kinji, ki riƙe mijinki da ƴan'uwansa tamkar naki, kar ki yarda wani ya yi kuka da ke, ki yi haƙuri kin ji Allah ya sa kinje a sa'a Allah ya yi albarka" nan sauran iyaye kowa ya yi nasa faɗan, aunty da wasu ƴan uwan Mama suka fito da ita, ɗaya daga cikin jerin motocin ɗaukan amarya aka shigar da ita, tana kuka, ƙawayenta duk sun cika mota dan zuwa ganin gidan Amarya.
Rantsattsen gidanta aka kai ta, wanda ya gaji da haɗuwa, daga gate sai babban compound wanda zai ɗauki motoci biyar ba tare da takura ba, sai wani ɗan corridor da zai sadaka da main parlour wanda yake ɗauke da bed room guda uku kowanne ɗauke da toilet sai spare guda biyu, sai kitchen babba a jikin parlor ta bayansa dining area ne, komai na parlour ash and white color ne, set biyu na chairs aka sanya mata da karuwar t.v tare da home theater da receiver, daga side wasu flowers ne masu wearing da electric, suna ba da different color ƙamshi na tashi ta jikinsu.
Kowa santin gidan yake.
Su aunty sun so kai ta gidansu SAIF proff ya ce a'a su za su zo da kansu, bayan an gama kintsa mata komai sannan suka tafi, aka bar Zahra da ƙawayenta guda uku.
A can gidansu ango kuwa, yana ɗakinsa hankali kwance, su Major Ahmad sun shirya suna ta jiran ango ya fito su rakashi, daga ce wa bari ya yi wanka ya barsu a parlor ya shige ɗaki ya yi kwanciyarsa.
Tun ƙarfe tara har goma bai fito ba, Ahmad ya je yana kiransa, shiru bai amsa ba, proff Waziri yana zaune yana jiran ganin angwaye sun fito,shiru dole ya nufi inda ɗakin SAIF ya ke, ganin abokan a zaune a madaidaicin parlor'n nasa.
Ya ce" me kuka tsaya yi ne, an bar ƴarinya tana ta jira?" wani mai suna Mubarkar ne ya ce"bai fito ba har yanzu" proff Waziri ya ce" nonsense wannan ai zancen banza ne,sai ka ce auren dole akayi masa"ya na niyyar zuwa ya buga ƙofar bedroom ɗin,SAIF ya fito cikin shiga shadda ash color ɗinkin three-quarter, hularsa mai ash da fari ya sa, sai tashin ƙamshi yake yi.
Proff.Waziri ya hau washe baki yana faɗin" king of groom in the year, happy marriage life Major Saifullah Ibrahim Waziri" huging juna sukayi kowanne fuskarsa cike da murmushi, a tare suka nufi ɗakin Umma dan yi mata sallama.
Ta na tare da Noor ɗinta yana bata labarin biki dan shi ma yaji daɗin bikin nan.Sauran dangi da ba su tafi ba suna ɗakunan da aka basu, rayuwar gidan proff ba takura.
Gaba ɗayansu suka shiga ɗakin har proff, Umma ta ce" a'a kaga angon Zahra gaskiya ka yi kyau, Zahra ta sami zankaɗeɗen Miji hahhh" du aka yi dariya, proff ya ce" hurry up dear za su tafi ne idan kina da abinda za ki ce ki faɗa masa" Umma ta ce" ni babu abinda zance sai Allah ya kawo ƙazantar ɗaki nan da shekara in ɗauki grandkids ɗi na hahhh" proff ya ce "hahhh kai dear ba ki da dama" SAIF dai in banda yatsina babu abinda yake.
Ba addu'a bare fatan alkhairi haka suka rako su har harabar gidan.
ASH ne zaune a kan plastic chair Yana chatt yana ta yi wa abokansa bangajiya su Mato ma suna zaune a teburin su bakin gate suna ta hira, gidan tar da haske tamkar rana.
Da fara'a ASH ya tashi yana mai da wayarsa aljihu ya ce" da ni za'a je rakiyar nan Abba" Ahmad ya ce" waye tsaranka anan?" ASH ya ce " haba Major ni ɗin ai kuwa idan baa je da ni ba na tabbata amaryar ba za ta karɓe ku ba" Proff ya kwashe da dariya yana bawa ASH hannu yana faɗin "give me five" ASH ya miƙa suka tafa, kamar wasu wawaye haka suke.
Tare da ASH aka tafi rakiyar.
Suna jin motsin motor angwaye su Kausar suka gyara wa Zahra lulluɓinta suka ƙara sanya airfreshner take ɗakin ya ƙara gaurayewa da sassanyan ƙamshi mai sanyaya zuciya.
ASH ne a gaba yana riƙe da ledar da suka siyo gas Turkeys da chicken masu zafi da drink da su fresh milk, su major ne suka ƙaraso da cartoon na ruwa da lemuka, kamar wani party za su yi.
Da sallama suka shiga, su Kausar suka amsa, ba wani wasa dan duk sojoji ne, civilian ɗin biyu ne Umar da Hamza sai ASH.
Dubi Hamsin suka ajiyewa ƙawayen wai siyan baki, su Kausar suka karɓa suna guɗa dan ba su zata za su sami haka ba.
Sai sha ɗaya na dare suka bar gidan, SAIF ya yi wa sojan da ke gate magana a rufe gate, Zahra dai na nan jigum har SAIF ya dawo, a hankali ya ce" ki sauko ki ci abinci" Zahra ta ce naƙoshi, ya ce" okay ki je kiyi alwala muyi sallah dan nuna godiya ga Allah da ya cika mana burinmu" Zahra ta tashi ta na ajiye laffayar da ke jikinta ta nufi toilet ɗin a hankali.
Bayan sun idar da sallah ya kama goshinta ya yi mata addu'a, ya ɗauko plate ya zuba naman ya ci ya ƙoshi Zahra dai gabanta nata faɗuwa, abun ya ɗaure mata kai dan ita dai taji ana ai lallaɓa amarya ake amma ita ba wannan harkar gabansa kawai yake, Allah ya so ma, aunty ta sa ta ci dahuwar Kaza irin ta ƴan sokoto mai tsuma mata, da ƙyar ta cinye dan a gaba ta sanyata, ba dan haka ba yau yunwa ce zata kasheta.
Bata san sanda ya gama ba, tana cikin bacci ta ji hannu na bin jikinta, a zabure ta tashi zata miƙe SAIF ya mai da ita, ya fara yi mata raɗa a kunne, kuka ta hau yi jikinta na rawa, nasarar rabata da kayanta ya yi,ya shiga sarrafata, wani irin nishi yake yana jinsa kamar ba shi ba, sai da ya jigata ta, dan bai iya wani soyayya ba, sannan ya samu nasarar shiga jikinta, tamkar zata mutu haka take ji, wani irin azaba da raɗaɗi ne ya ke kaiwa brain ɗinta saƙo.
Ji take kamar abin zai fito ta bakinta, sai yunƙurin amai take yi, SAIF da baya ganewa sai abu ɗaya yake yi da zafi-zafi duk ta jigata, sai da yaji ya gamsu sannan ya barta.
Wahalallen numfashi take saukewa, hawaye sai gangarowa yake, ji take tamkar bata da ƙafafuwa a jikinta.
Bai bi ta kanta ba ya kwanta yana mai da numfashi, bai san haka abin yake ba, ni'ima da nutsuwa ya ji ya samu, sai da ya huta ya nufi toilet yayi wanka, duba lokaci ya yi huɗu saura na asuba.
"Ki tashi ki je ki gyara jikinki" ya faɗa fuska a haɗe, kamar Zahra zata mutu, cikin dauriya ta rarrafo ta sauka a gadon, tafiya tayi zata faɗi ya tare ta da sauri, shi ya kaita toilet ɗin sannan ya fito, da kanta ta gasa kanta dan idan ta tsaya san jiki, kanta zata cuta.
Sai da ta ji dama-dama sannan tayi wanka ta fito, ji take gaba ɗaya bata da nauyi tamkar iska zata ɗauketa, alwala tayi ta fito ɗaure da towel, bacci yake ta yi ya sauya bedsheet ɗin ya sanya sabo bai ma iya shimfiɗawa ba.
Kyau ya yi mata sosai, Zahra na son mutum mai kyau, a zaune tayi sallah sannan ta shiga tashinsa, a hankali ya buɗe idonsa, ganin asuba tayi ya tashi ya shiga bayi ya yi alwala ya fita masallaci.
A yunwa ce ta janyo ledar jiya ta ɗauko zabin ta hau ci, dan yunwa take ji sosai, da fresh milk ta kora, wacce ta yi ɗumi, gyatsa ta yi tana faɗin alhamdulillah sannan ta samu dan nutsuwa.
Daga gidan proff Waziri aka aiko musu da breakfast, SAIF na parlour yana kallon ball ɗin da yake mugun so, tunda ya leƙa ɗakin yaga tana bacci, ya koma parlourn dan ya saba da rashin bacci, ba wai dole sai ya rama ba.
Bayan sati daya
Ƙannen Zahra duk sun zo, hakama su Noor da Umma da Proff.Tun tana jin kunyarsu har suka sa ta ware aka ci gaba da hira da ita, ASH ne bai sami zuwa ba.
School ta saka shi a gaba, ba shi da wani specific time da zai samu ya je.
A cikin kwanakin Zahra ta gama sanin wa ta aura, SAIF mutum ne mara son wargi, ko da suna tare sai ya dinga ɗaure mata fuska, tun tana damuwa har ta saba.
Duk lokacin da yake da buƙata yakan je ne ya yi abinda yaga dama ya kwanta ya yi baccinsa.
Yau dai Umma ta aiki ASH gidan SAIF dan kaiwa amarya wasu turarukan wuta da ta siya mata, dan ta ɗauki zahra tamkar ƴa.
Waya yayi lokacin sa ya je bakin gate, SAIF ne ya sa aka buɗe masa ya shiga da machine ɗin sa,sau tari ASH yafi son ya hau machine akan mota.
Zahra da ke sanye da top mai buɗallen wuya yellow color, da mini skert ɗin rigar duk jikinta a waje, SAIF da yake ta aiki a system bai ma kula da kayan da ta sa domin sa ba, kawai aikinsa ne a gabansa.
Sallamar ASH ta ji, da sauri ta koma kitchen ɗin tana mai ɓoyewa, SAIF ya ce sai yau kaga daman zuwa?" ASH ya yi dariya yana faɗin" wallahi ya ba lokaci ne, ina aunty'n tawa ne?" SAIF ya ce" kina ina ne?" Zahra ta kasa fitowa sai ta hau faɗin..........
* * *
Saɗaf-saɗaf ta ke tafiya takalminta a hannu, "ina za ki je?" a razane ta juyo ganin ya Ahmad na cikin chemist ɗinsa a zaune yana kallo soron gidan nasu, duburbucewa Humaira tayi ta hau kame-kame" uhm...Umma ce ta aike ni?" Ahmad ya tashi dan zagayowa ya fito, a guje ta koma cikin gidan, ɗakin Umma ta faɗa tana faɗin "Umma dan Allah ki ce ke kika aike ni" Umma da take bacci tsakanin azahar zuwa la'asar ta tashi kafin tayi magana Ahmad ya shigo.
"Ina aka aike ta Umma?" Umma ta ce "ta dai aiki kanta, dan ni ban aiketa ko ina ba" wani kallo Ahmad ya yi mata, ta yi tsuru-tsuru ta hau magiyar "dan Allah kar ka dake ni wallahi ba fita zanyi ba" Malam ne ya fito daga nasa ɗakin jin magiyar Humaira.
"Hayaniyar me nake ji haka?"ce war Malam.
Umma ta ce" satar fita tayi shine Ahmad ya ganta"Malam ya ce"wani abu kike so ne uwata?"Humaira da gabanta yake faɗuwa ta ce" wallahi ba fita zanyi ba, dubawa nayi ko zanga su Kamilu a amsomin klin"
Ahmad ya juya dan tunda Malam ya fito, ba zai bari ayi mata faɗa ba bare duka.
Malam ya ce "ai sai ki sanarwa da mahaifiyarki kafin ki fita" Umma ta ce" wallahi Malam ƙarya ce kawai take ai muna da klin ɗin" faɗa Malam ya hauta da shi jin abinda ta ce, a dole Umma tayi shiru.
A wata private school mai suna Hamdan college ya Anas da ya Ahmad suka biya wa Humaira kuɗin jarabawa har dubu saba'in, dan neco kaɗai suka biya, ba su da ƙarfin biya mata guda biyu. nan fa Humaira ta ƙara ƙaro ƙarya ganin ta haɗu da manyan ƴaƴan masu faɗa a ji a ƙasar.........
___________Wanki Asiya take yi a tsakar gidan, rana ta take sosai tana ta sauri dan ta yi ta kammala kafin lokacin makaranta ya yi.
"har yanzu ba ki yi da jiki kin ƙarasa wankin nan ba Asiya?" Umma ta faɗa tana ɗaukan bota dan zagawa bayi, "Na kusa Umma rubutun nan ne ya tsaida ni" ta faɗa tana nuna allonta.
" Assalamu alaikum" sallamar Ya Anas suka ji, Asiya ta amsa tana gaishe shi, amsawa ya yi yana faɗin " ina Humaira?" Asiya ta ce" bata dawo daga makaranta ba" Umma ta fito daga bayi ta na faɗin" daman ta ce yau sai ƙarfe biyar za su dawo"Durƙusawa ya yi yana gaishe da Umma, sannan ya wuce ɗakinsa ya cire kayansa da sukayi kura sosai, ruwa zai janyo a rijiya, Asiya ta ce" kawo in zuba maka yaya" barshi je ki ƙarasa wankin ki, lokacin makaranta ya kusa.
Ya Anas yana da sauƙin hali, ba shi da hayaniya amma akwai duka, baya son raini, sai da ya yi wanka sannan ya ɗauki abincinsa a flask, dambun tsakin masara da dafaffen wake akayi da mai da yaji, fita ya yi yana faɗin "bari in amso ɗan lemo a shagon Haruna" yana fita yaga malam ya dawo yana alwalar la'asar, gaisawa sukayi Malam ya ce" uwata ta dawo kuwa?" Anas ya ce"a'a" Malam ya ce" yauwa to kaga jarabawa ce ta zaunar da ita, do Allah kar ka daketa" Anas ya yi murmushi ya ce" to Malam kana ji da uwan nan taka" murmushi ya yi yana faɗin "na dai faɗa maka"
Wuce wa ya yi ya siyo coke, ya siyowa Malam da Umma nasu mara sugar.
Tun ƙarfe biyu su Humaira suka gama exam ɗin ranar, ta bi Sadiya Sadauki gidansu, dan ranar da ta fara zuwa suka saba da ƴan class ɗin musamman sadiya, dan idonta a buɗe yake, tunda ta ji ƴar sarauta ce Humaira ta nane mata, ita ma ganin Humaira kyakkyawa ce ya sa ta ji tana sonta, mahaifinta shi ne Galadiman Gumel shikenan Humaira ta zama ƙawarta.
Driver'n da ya kai su ma yaga wulaƙanci wajen Humaira dan nunawa take ubanta wani ne,
bata tsinke da lamarin Sadiya Sadauki ba sai da taga irin daular da take ciki, watukun gida ne mai kyan gaske, bangon ƙofar gidan an yi masa kwalliyar zane-zanen nan na tambarin arewa, kuma kakaki da kalar green, da read da ka gani kasan gidan akwai sarauta, wani gate ne mai nauyin gaske fari tas aka buɗe musu, driver Sani ya tura hancin motar ciki, wadatattun trees da flowers ne ta gani burjik, akwai bishiyin dabino, dana kwakwa,gwanda, da su roses da folamboyant, hibiscus da sauran flowers masu kyau, wasu masu rawani ne ke gadin gidan.
"Tawo mu je ciki,yau Ummi zata ga my new friend"cewar sadiya tana murna, Humaira ta yi murmushi ta na kalle-kalle ta ƙasan ido, dan gidan ya yi mata ji taka ina ma ita ce a gidan, ina ma ba Malam ne babanta ba.Ɗan tsaki ta ja, da haka suka ƙarasa asalin cikin gidan.
Door ɗin glass ne,Sadiya ta danna wani guri, ji sukayi na'ura na magana, sannan ƙofar ta buɗe, wani sanyi da ƙamshi ne ya yi musu maraba, shiga sukayi cikin main parlour'n Humaira na sa ƙafarta ta ji tamkar zata nitse tsabar taushin carpet ɗin, komai na parlor'n green and black ne, wasu bayi ne kawai a ciki suna ta kaiwa da kawowa, wasu na ta jera abinci daga can ciki inda dining yake, wasu na ƙara goge kayan da ke parlor da alama masu gidan na gaf da saukowa daga wani bene mai ziza na silver.
"Have a sit dear" ce war Sadiya, Humaira ta zauna tana basarwa bata son Sadiya ta fahimci ta ruɗe da ganin gidansu.
Benan Sadiya ta nufa, ɗakin Umminta ta shiga tana faɗin " Ummi albishirinki?" Matar da bata haura shekara araba'in ba ta ce" an dawo kenan, yau kuma da me aka zo" Sadiya ta kwantar da kanta saman cinyar Matar tana faɗin " tare da Aysha Abdullahi muke" Ummi ta ce" wace kuma haka?" cuno baki sadiya tayi tana faɗin "my Humaira fa friend ɗina da na ke faɗa miki"
"wai,wai ki ce yau zanga ƴata kenan, daga school ɗin kuka tawo, Allah sarki" Sadiya ta ce mu je ki ganta, tare suka sauko, da fara'a a kan fuskar matar,kamar su ɗaya da Sadiya ita ma fara ce tas.
Ummi na zama Humaira ta ce"ina wuni" ganin tarbiyyar Humaira Ummi tayi, dan Sadiyanta sai a hankali ita ce zuwa club ita ce bin saurayi, a yanzu hakama tana tare da Abid ɗan Governor, shi ya koya mata shaye-shaye amma babu wanda zai fahimci tana shan syrup da shisha dan drug-abuse ɗin mai aji sukeyi.
Mami ta ji daɗi ganin Humaira dan daga yanayinta taga kamar akwai tarbiyya a tare da ita.
"Yau dai naga Humairan baby yakike ya su Mama?" Humaira ta ce" lafiya ƙalau tace ma a gaishe ku" Ummi ta ce "muna amsawa" sannan ta ce "baby kinga yanda ake ko, natabbata da ke ce ba za ki sanar da ni zaki biya ko ina ba"
Wata baiwa ce ta zo ta zube gaban Ummi tana faɗin " ranki ya daɗe an kammala,Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana" hannu kawai Ummi ta ɗaga, matar ta ta shi tana faɗin "na barku lafiya" Abin ne ya ƙara birge Humaira.
"Ku je ku ci abinci" ce war Ummi, Sadiya ta ce" bari muyi wanka ko sweetheart?" ta faɗa tana kashewa Humaira ido, Humaira ta ce"ni dai sai na koma gida" Ummi ta ce" haba ke kuwa na ɗauka a nan zaki wuni" Humaira ta yi yaƙe dan Allah ya sani ba za ta bar gidan yanzu ba sai ta ga kwal uwar daka.
Kamo hannunta Sadiya tayi tana faɗin " ta so mu je dan Allah" Humaira ta bita suka nufi sama, parlour'n saman wanda yake mallakin na Galadima Sadauki ya fi na ƙasa kyau da tsari duk da bai kai wancen girma ba.
Ɗakin Sadiya suka nufa tana shiga ta ce "zauna mana, sai wani ɗari-ɗari kike sai ka ce zan siyar da ke ne?" Humaira ta cire ɗan hijab ɗinta tana faɗawa gadon Sadiya tana faɗin " nagaji ne kawai" Sadiya da ta ke bin jikin Humaira da kallo bata taɓa ganinta ba hijab ba sai yanzu, take ta ji tana sha'awarta.
(wa'iyazu billah).
Sanin Humaira bata lesbian ya sa tayi ƙoƙarin mai da maitarta ta ce" bari nayi wanka" Humaira ta ce"okay" cewar Humaira tana kallon ɗakin da yake na Sadiya wanda ko amarya albarka.
Sadiya na shiga Humaira ta miƙe tana kallon ɗakin, mirror ta je tana duba wasu kayan make-up wanda bata ma san amfaninsu ba dan bata taɓa ganinsu ba "uhum arziki kashi ina ma ɗakina ne burar uba da anga cili dan wallahi sai na zama cele a gari oh arziki kashi" ta baro nan ta nufi wardrobe,kaya ne different colour and materials da yawa ko Ina a cike, dan roll daya ya fi dukkan suturar Humaira ma.Kamar idanunta za su faɗo kasa, ahankali ta rufe.
Wata drower ta janyo da ke jikin Italian bed din Sadiya, wani abu ta gani a ajiye Wanda ya sa Humaira saurin dafe ƙirji tana faɗin " na shiga uku meye wannan?............
* * *
"Ganinan zuwa" a dole ta yi fuska ta fito tana tsantsane jikinta.
Da fara'a ASH ya ce" sai aunty na kai gaskiya mun iya kiwo haka kika koma?" Murmushi tayi tana faɗin" ya su Umma" ya ce" lafiya ƙalau ita ce ma ta aiko ni" ya faɗa yana tura mata jakar ledar da ke gefensa.
ta ce" Allah sarki Umma nagode sosai Noor shima ka koya masa ƙin ziyara, tunda suka zo tare da su Abba bai ƙara zuwa ba" ASH ya ce" school ke hana kowa sakewa muna busy, kiyi mana afuwa"
Maganarsu ce ta damu SAIF ta shi ya yi yana faɗin" kun fiya surutu talkatives"ya wuce yana ɗaukar system ɗinsa ya shige ɗakinsa.
Zahra ta ce"ina zuwa" da sauri ta tashi tayi nata ɗakin ta sa hijab, kitchen ta shiga tana faɗin" bari in kawowa ɗan ƙanina ruwa" ASH ya yi murmushi yana faɗin" har na fara tunanin aunty'n nawa marowaciya ce hahhh" tana dariya ta wuce, samosa da spring rolls ta kawo masa da su dubulan cikin plate sai lemon exotic pineapple and coconut mai sanyi da cup.
ASH ya ce" kai du wannan ni kaɗai ki ce abincin Umma yau zai yi kwantai" zama tayi facing ɗinsa tana murmushi, ji take ina ma kullum ya dinga zuwa.
Ci yake yana santi daga ya kawo labarin restaurant kaza sai ya kawo labarin bakery kaza, sun jima suna hira sai da yaji ana kiran sallar azahar ya miƙe yana faɗin" kai aunty kin daɗar da ni, idan yaya ya fito ki ce masa ni na wuce"Kamar Zahra za ta yi kuka ta ce" yanzu tafiya zakayi, ka bari sai anjima dan Allah" ta faɗa da sigar shagwaɓa, ASH ya kwaikwayeta yana lanƙwasa murya, abin duka ta ke nema ganin haka ya sa ya fita yana dariya, binsa tayi da remote a hannunta, wai zata kwaɗa masa, da sauri ya hau machine ɗinsa yana mata gwalo, mai gaɗi ya buɗe masa ya bar gidan.
Jiki a sanyaye ta koma ciki tana zubewa kan kujera, ta ji daɗin zuwan ASH sosai, fuskar nan a murtuke ya fito da gani masallaci zai je, ya ce" ya tafi ne?" Zahra ta ce " eh yanzu ya tafi" okay ya faɗa yana wucewa.
Binsa tayi da kallo tana faɗin" a gidan ma sai ya nuna shi soja ne mtswww" ta ja tsaki sannan ta nufi ɗakinta.
Kusan minti talatin yayi, ya dawo, ganin bata ɗauke kayan da ASH ya ci abinci ba ya sa SAIF fara kiranta" Zahra, Zahra!! tana ɗaki ta idar da sallah ta na chat da ƙawayenta, dan zaman gidan da mijin yake baya tsinana mata komai.
"Na'am" ta amsa tana fitowa, " ga yanda kika bar guri haka wannan ai ƙazanta ne"
Ba ta ce komai ba ta shiga ɗauke kayan, ta gyara wajen, zama ya yi yana waya.
"Eh Umma a samo mata ko yarinya ce, aikin yana yi mata yawa" take ta fahimci ƴar aiki ya sa a kawo mata, taɓe baki tayi a ranta tana faɗin " abanza wai nan dan naji daɗi.
Sai da ta gama ta zauna kusa da shi tana faɗin "darling" uhum ya amsa a hakan ta ce" house made zaa kawo min?" ya ce"uhm" ta buɗe baki zata ƙara magana kenan ya ce" ke haba wai bakya gajiya da surutu ne, na ce miki eh ita zaa kawo, to mekike so kuma?" hawaye ne ya taru a idon Zahra ta na matsawa tayi shiru.
Wayarsa ce ta shiga ringing, daga wajen aikinsa aka kira shi, Yes sir" ya wani bada attention yana saluted, Zahra ta bi shi da kallo, ya jima yana saureren mutumin daga ƙarshe ya ce next week ne, in sha Allah on Sunday zan dawo, okay ,thank you Sir" ya ajiye wayar.
"Oganku ne ya kira?" still ta kuma jefo masa wata tambayar, eh tambaya ya yi saura kwana nawa na koma, ni kaina nagaji da zaman gida"
Zahra ta shiga matse hawaye tana faɗin "amma tare zamu tafi ko?" Ina?" ta ce" can garin da aka yi posting ɗinka ya ce" Yobe ɗin, ke babu inda zanje da ke, ai ba daɗewa zan dinga yi ba, ga ma ƴar aiki zaa kawo miki kuma ga waya zamu yi magana ai"
Zahra ta ce" yanzu ka daina sona idan kai ba za kayi missing ɗina ba ni zanyi missing ɗinka"
Tausayi ta ba shi ya matsa kusa da ita ya na rungumota jikinsa ya haɗa hannyensu ya shiga messaging hannun ya ce" ga ASH nan zan sa kullum ya dinga zuwa yana ganinki nasan zai ɗebe miki kewa alot" ta ce" yanzu kenan ba zan yi farinciki ba sai SILAR ƘANIN MIJI?" Ya ce "common baby forget it" takaici ya kama ta,tsabar haushi bata ƙara magaa ba.
Haka suke zaman auren ba wani wasan soyayya ko nishaɗi, idan taga SAIF yana rawar kai akanta to kuwa akwai abinda yake so a wajenta ne.
Kullum sai ta ce da ASH ba zai zo ba, yana faɗin ba shi da lokaci ne.
Kowa yana ɗakinsa yana abinda yafi masa, SAIF ya shigo yana faɗin "ki shirya mu je ki gida" Zahra ta tashi tana washe baki ta ce" are u seriours dear?" haɗe rai ya yi ya ce" idan ba za ki je ba ai is ok" tsalle tayi ta ɗane jikinsa tana faɗin "yi haƙuri dan Allah" sakinsa ta yi, ya fice.
Wajen ƙarfe takwas na dare, Zahra ta shirya cikin shigar doguwar riga abaya milk ta yi rolling,ta sa hill shoe milk da pulse milk mai stone sosai tayi kyau, SAIF ya fito duk da yaga tayi masa kyau,amma ya kasa buɗe baki ya ce mata tayi.
"follow me"ya faɗa yana wucewa gaba, black troser ya sa da rigar sojoji, sai ƙamshi suke.excorts ɗinsa biyu suka taso, dakatar da su ya yi, su kaɗai yake son su tafi, mota suka shiga ya ja suka bar gidan.
Proff da Noor suna ta buga t.v game, Noor na ta winning sai ihu ake ana shewa ASH da Umma kowa akwai wanda yake aporting Umma na bayan Noor ASH na bayan Abba.
Sallamar Zahra ce ta katse musu musun da akeyi.
Da fara'a suka amsa, Umma na faɗin " sai yau zaka kawo ta, ai daman ido kawai na sa maka" proff yana faɗin "welcome bride we are Happy to see you" Zahra ta yi murmushi tana durƙusawa ta gaishe su.
ASH ya ce" wow aunty kinyi bala'in kyau wallahi, inda kikasan Balarabiya"
Daɗi Zahra ta ji tana ɗan darawa ta ce"nagode ƙanin" Umma ta na fara'a ta ce" ai Zahra ma sha Allah SAIF ya iya zaɓe kam" SAIF ya murmusa yana sosa ƙeya.
Noor ne ya ɗauko waya yana faɗin aunty tsaya in miki one camera pls"
ASH ya ce" ai dole ma ayi salfie hahhh" duk suka sa dariya.
Umma ce ta ce" bansan da zuwanki ba dota da an shirya miki liyafa" Zahra ta ce"babu komai Umma" ba kunya ASH ya taso ya dawo kusa da Zahra shi da Noor suka shiga selfer hotuna.
Abu har da yi da su proff da Umma, har goma suna gidan anan sukayi dinner da za su tafi ta ce sai ASH ya faɗa mata randa zai zo, a gaban su Proff dan ayi alƙawari, aka yi masa cahh dole ya sa rana ya ce sai gata, ta ce bata yarda ba sai dai ya ce gobe, gobe yana da abinyi, dole dai ta hakura sai gatan.
Har suka fita yana faɗin "aunty kinyi kyau sosai"
SAIF ya taɓe baki yana faɗin " akwai saƙo da zaa kawo min gobe ka karɓa ka ajiye min" carab Zahra ta ce" kawai ya kawo maka gida dear" SAIF bai bi ta kanta ba ya shige mota, ta na tsaye tana ta faɗin ka kawo masa gida ƙaji ƘANIN MIJIN"
ASH ya ce" bazan kawo ba tunda kika ɓata min suna" cikin nishaɗi Zahra ta bar gidan.
Bayan kwana uku, ASH bai zo ha, tayi mitar har ta gaji, ƴar aikin da aka kawo mata mai suna Abu bata fi shekara sha biyu ba, ta na goge-goge Zahra na chatting da ASH sai murmushi take, SAIF ya fito cikin shigar kakinsa na soja, a razane ta miƙe ta na faɗin "ba dai yau zaka tafi ba?".............
___________Murmushi ya sakar mata yana mai jinjina kansa alamar eh, "Haba dan Allah du-du satin mu nawa da aure amma ace har zaka koma, yana gyara zaman belt ɗin da ke ƙugunsa ya ce" wani aiki ne ya taso urgently, already you know I will going on Sunday but I can't wait for that day.
Friday da Sunday ai inaga duk ɗaya ne" tuni idanun Zahra ya fara hawayen takaici, ta ce" kawai ka ce kagaji da ni ne da kasan hakane ai da baka auro ni ba, aure ko wata ɗaya ba'ayi ba na fara nadama" ran SAIF ne ya ɓaci, tsawa da daka mata" ke!!! dalla malama ya ishe ki, dan na aure ki shine bazan yi aiki na ba yanda ya dace ba, zama zan tayi da ke ko me, to yau naga damar tafiya idan kinga zaki iya zama ki zauna idan ba za ki iya ba ga hanya nan mtsww shashasha stupid girl" ya fice da sauri, ba dan yana sonta ba, kuma aurenta yake babu abinda zai hana shi zare belt ya zane ta kafin ya tafi dan tayi matuƙar ɓata masa rai
kan kujera ta faɗa tana fashewa da marayan kuka.(Allah sarki abin tausayi) cewar Zinariya😢
Abu da ke gyaran toilet ɗin parlor ta yi shiru jikinta sai rawa yake, tana tsoron masu kaki ko ba soja ba ne, tausayin Zahra ne ya kamata duk da ƙarama ce amma tasan ogansu bai kyauta ba,a
gaban Zahra ta durƙusa ta ce" aunty dan Allah kiyi haƙuri, ki yi masa addu'a" Zahra ta tashi ta shige ɗakinta, da gudu ta faɗa gadonta ta ci gaba da zabga kuka mai cin rai, Abu ta zabga tagumi tana tunani.
Gida SAIF ya nufa, prof da ya sami aikin contract a Dutse yana marking exams a garden glass ɗin nan nasa a karan hanci, gefensa bottle ɗin ruwa ne, ya ji shigowar motar SAIF da muƙarrabansa, ya ɗago, cikin izza ya ziro zaratan ƙafafunsa, saluted escort ɗinsa suka yi, da ba shi hanya ya wuce, bakin prof kamar zai tsage yana alfahari da SAIF sosai.
"Welcome my soldier" cewar prof yana buɗe hannuwansa, da smile SAIF ya shige jikin Abban nasa yana faɗin "good day Abba" prof ya ɗago shi yana faɗin " day my son ba dai yau ne tafiyar ba?" SAIF ya ce"in sha Allahu yanzu zan koma wani aiki ne ya taso mana ne" prof ya ce" okay Allah ya ba da sa'a ina dota hope dai ka lallaɓata kasan mata sai da rarrashi hahhh" ya ƙarasa faɗa yana dariya, SAIF ya ɗage kafaɗa yana taɓe baki ya ce"ita ta sani babu abinda zai dakatar da ni dole ta yi haƙuri tunda haka aiki na yake" prof ya ce soja,soja marmari daga nesa. A tare suka ƙarasa shiga ciki dan yin sallama da Umma,
Ta na zaune tana kallon wani american film mai suna Guardians of the galaxy, su ASH duk ba sa nan daga ita sai mai aikinta wacce take zuwa kullum tana tafiya.
Ita ma ganinsa cikin shigarsa ya sa ta ce" ba dai tafiyar ba ce ta tashi?" SAIF ya yi murmushi yana ƙarasawa kusa da ita ya zauna, gaishe ta yayi sannan ya ce" eh daga nan sai Ibadan daga nan kuna za mmu wuce Osun State Umma"
Ta ce" haba nikam banji daɗi ba wallahi yanzu ina Zahran take?" ya ce" na barta tana can gida tana kuka" ita da prof ne suka ce" kaga ni ba" Umma ta ƙara da faɗin " ai da sai ka kawo ta nan ta wuni in ya so da daddare sai ASH su rakata gidanta ai ta ɗebe kewa" SAIF ya ce"no Umma idan ta fara zuwa ai ba za ta saba ba, gara kawai a barta ta saba" prof ya ce" a'a duk da haka dole ɗan uwanka ya dinga zuwa yana dubata ba za abarta haka ba gaskiya"
SAIF ya ce" to shikenan ayi mana addu'a zamu tafi" Sai kuma yaushe?" ce war Umma SAIF ya ce" baza mu wuce wata uku ba in sha Allah" Umma ta ce"haba SAIF yanzu fa ba da ba ne, kana da iyali, to me zai hana ka tafi da ita?" a razane ya ce"what!!! haba Umma ni bazan je da ita ba banason tayi zaman barrack, nifa shiyasa naƙi auren nan da wuri an takuramin" kai ya riƙe yana zama dan da gaske maganganun nan da yayi sun saukar masa da headache. "Ok I'll take care of her, sorry our Hero"cewar Umma cikin rarrashi, ta na ɗan bubbuga kafaɗansa, ruwa Prof ya ɗauko yana ɓalle murfin ya ce" sha wannan zamu kula da komai" karɓa ya yi ya sha, sannan ya tashi,Allah ya kiyaye ya ba da sa'a" suka faɗa a tare,
Amin ya Allah, idan ASH ya dawo zamuyi waya, a kula da Noor a ce zanyi missing ɗin young bro" cikin walwala suka rako shi har inda sauran sojojin suke, akan idonsu suka fice daga gidan suna ɗaga masa hannu.
Sai da suka fara nisa sannan ya kira Zahra dan kwantar mata da hankali, ta gama kukanta idanunta sunyi luhu-luhu,fitowarta daga wanka kenan ta ji kiransa dan ringing ɗinsa daban yake, kamar ta share shi,amma ta fasa sanin halinsa bai zama lallai ya ƙara kira ba, kuma yanzu tasan baya gari dole ta kula da shi.
"Assalamu alaikum" zazzaƙar muryarta ce tayi masa sallama, sai da ya lumshe sexy eye ɗinsa ya na jin kewa ya amsa, "waalekissalam kin gama kukan kenan" ɓata rai tayi tana jin kamar ta ajiye wayar, "ihum" ya kuma faɗa dan jin tayi shiru, some seconds babu wanda ya ƙara magana, sai daga can ya ce" kiyi min addu'a mun ɗau hanya" cikin sanyi ta ce"Allah ya kaiku lafiya, ya tsare ya ba da nasara" ya amsa da ameen i hope kinga saƙon da na ajiye ko?" Zahra ta ce" a'a" okay za ki gani take care my wife bye" kafin ta ce komai ya ajiye wayar.
"Mtswww saƙon banza da wofi me zanyi da shi" ta faɗa ta na jan ƙara jan tsaki, cigaba da tsane jikinta tayi tana masa fatan alkhairi, dan so fa ba ƙarya ba ne tana son abinta a hakan lol🤪.
Sai da ta gama komai ta kira ASH, suna zaune tare da su prof Waziri ASH yana faɗin "yanzu har ya koma, to ita aunty'n fa?" Umma ta ce ka dinga duba masa ita, kaga kenan yanzu ma idan ka kammala sai ka je can gidan ka ɗebe mata kewa" Prof ya ce" ai tasan wanda ta aura ba mazauni ba ne dole ta yi haƙu...Ƙarar wayar ASH ne ya katse prof.
My aunty ya gani "aunty ce" ce war ASH, hello ya faɗa muryarta a dashe ta ce" kana ina?" ya ce"ina gida yanzu nake jin wai Yaya ya koma ba sunday ya ce zai tafi ba?" Zahra ta sauke numfashi wanda ya kai har kunnen ASH ta ce" tsoro nake ji ASHhhhh" yanda ta ja sunan sai da ya ji har cikin brain ɗinsa, da hanzari ya tashi yana faɗin "ganin zuwa gidan" Zahra da ke bedroom ɗinta a kwance tana hawaye ta ce" tom dan kayi sauri" ture shawarmar da yake ci ya yi yana faɗin" Abba tsora take ji bari in je yanzu" Umma ta ce" Allah sarki kowa da haka ya saba ai sai haƙuri, ka kwantar mata da hankali" prof ya ce"make sure sai tayi bacci sannan ka tawo" da okay ya amsa ya ɗauki key ɗin machine ɗinsa ya bar gidan, sai da ya tsaya a Rufaida ya siya mata ice cream da pizza ya kuma tsayawa a super market ya siyo mata biscuits da chocolates sannan ya nufi gidan,securities ɗin da ke gadi duk sun san shi, duk abinsu sai da ASH ya sa sukayi dariya dan babu ruwansa da wasu sojoji kowa nasa ne, ƙarfe takwas da minti ɗaya ya shiga parlour'n babu kowa a ciki, sallama yake ta yi amma shiru.
"Aunty, aunty Zahra dake ciki bata ma san an shigo ba, Abu ce ta fito daga ɗakinta ganin ASH tayi yana zaune ya na latsa waya dan kiran Zahra, sannu da zuwa yaya" ASH ya ɗago yana faɗin" ina matar gidan, hello na zufa tun ɗazu" Zahra ta tashi cikin zumuɗi ta fito, fuskarta har ta kumbura, ASH ya kafeta da ido yana son karantar zuciyarta.
"Kaiii haba Aunty ba dai akan Yaya ya tafi ba ne yasa kika zama Ninja haka ba" take ta sakar masa murmushi tana zama ta ce"ba dole ba Miji ya tafi ya barni" dariya sosai ASH ya yi ya ce"to ai nima mijin ne ko?" ya faɗa yana ɗage gira ɗaya, hararar wasa ta yi masa tana faɗin "ƙaton gauro dai" da haka Zahra ta sake, suka shiga hira da ASH sosai ta ke dariya har gashin kanta ya barbaje tamkar tana tare da Mijinta haka ta saki jiki daga ita sai ƴar ɓigil ɗin riga da skert, Abu ta kawo masa ruwa da drinks ta koma ɗakinta tayi bacci har sha ɗaya ASH bai tafi ba, hamma ya fara yi yana faɗin "gaskiya bacci nake ji aunty tafiya zanyi" cikin tashin hankali ta ce" dan Allah ka kwana anan banaso ka tafi ka barni" ASH ya zaro ido waje yana faɗin " kwana kuma yanzu dai ki tashi in raka ki ɗaki ki kwanta kiyi bacci kamar yanda aka ce in saka ki bacci " tashi tayi suka nufi bedroom ɗin tare, tana faɗin "ka kwana nan pls" ASH yasa daeiya ya ce"ok naji" ba kunya ta ce "to ka tsaya in yi wanka" ASH ya ce to, tana shiga toilet ya fice daga gidan, dan bayason shaƙuwarsu tayi nisa, tun yana zuwa ƙofar gidansu yake ganin ta fi masa dukkan ƴan mata kyau da kyawun hali, ba dan yayansa ya riga shiga da ya ce yana kamu, amma ina bakin alƙalami ya riga da ya bushe.
Daga ita sai towel ta fito tana faɗin" naji daɗin zuwanka ɗan ƙani n....wayam ta ga babu shi,da hanzari ta yi parlor nan ma bayanan, ɓata rai tayi ta na jan ƙwafa " guduwa yayi ko zai sani ne" a dole ta haƙura ta na kwanciya ta hau online ɗaya saura, magana tayi masa da nuna rashin jin daɗinta akan guduwan da yayi, ASH baya kai, juye-juye take tayi bata san lokacin da tayi bacci ba.
Haka ASH da Zahra suke ta ci gaba da shaƙuwa, satin SAIF uku da tafiya Zahra ta saba da rashinsa, idan bai kira ba ita ma bata kira sai suyi kwana uku ba suyi waya ba.Kullum ASH yana tafe gidan, basu kubyar zama a kujera ɗaya.
Yau ASH bai je school ba, Prof ne ya takura akan sai ya je gidan SAIF, ya ce sai yayi sallah zai je, amma su Umma suka matsa, haka ya hau machine ya tafi.
Ta gama dafa indomie ita da Abu dan ma'aikatan gidan da kansu suke girki.
ASH ne ya shigo da sallama ya na tsokanar Zahra gwauruwa ya dai" Zahra ta sa dariya ta ce" wallahi kasan ni da aure na ahee, pork ɗin da take ci ya ɗauka ya ɗebo ya ci, yana faɗin "ohmm delicious wai daɗi" ɗauke plate ɗin tayi tana faɗin " ba da kai nayi ba" marairaicewa ya yi yana magiya, a taƙaice dai tare suka cinye indomie da one pork, tamkar maaurata.
Ɗaki ta shiga tayi wanka shi kuma ya tafi sallar azahar har ya dawo bata fito ba, kasa zuge zip ɗin rigarta tayi a haka ta fito tana faɗin "ƙanin dan Allah zuge min" ASH da yake chatting ya ɗago, baya ta juya masa tana rage tsawo dan a zaune ASH yake.
Bayan ya zubawa ido, skin ɗinta har wani ƙyalli take masa, bra ɗin ta mai kalar red yake kallo, ka zuge min mana" muryarta ta dawo da shi hayyacinsa, haɗa zip ɗin yayi ya ja shi sama ya rufe mata, thanks ta faɗa tana juyowa, sosai shape ɗin ta ya fita breast ɗinta sun botsaro ta sama haka hip ɗinta ya zauna sosai a cikin skert ɗin atamfar da ta sa.
"Kina da kyau aunty...........
* * *
Penis din roba ne a ciki, da hanzari Humaira ta rufe dirowar gabanta sai faɗuwa yake, komawa gadon tayi ta zauna jikinta sai rawa yake ta na tunanin meya kawo gaban Namiji ɗakin Sadiya Sadauki.
"Sweety ki je ki watsa ruwa" muryar Sadiya ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta ke.
"A'a gida zan tafi kar gobe a hanani zuwa" Sadiya ta shagwaɓe fuska wacce take tsaye daga ita sai ɗan guntun towel pink colour" ni dai a'a idan kika tafi yanzu babu ruwana da ke kowa ya yi sabgarsa" Humaira da ƙwaɗayi ya sa ta ce " haba me ya kawo maganar rabuwa kuma" toilet ɗin ta shiga tana mai da ƙofar ta rufe, kallon toilet ɗin kawai ta ke tana mamakin irin kuɗin da aka narka wajen gina shi, soaps kala-kala showerjelly su toothpaste bathspray kayan gyaran gashi da sauransu,ko Ina mirror ne, uniform ta cire ta ajiye a kan sink, ta cika bahon wankan ta zuba sabulan da turaruka ta shiga cikin kumfar, wata nutsuwa ta ji a ranta, ji tayi an turo ƙofar an shigo, a razane ta buɗe ido, Sadiya ce tana yi mata shu'umin murmushi.
"Meye haka za ki shigo ina wanka?" Sadiya da ta tsuguna a gabanta ta sa hannu cikin kumfar ta na faɗin........
___________To meye dan na shigo, kinga fa abinda zan ɗauka" ta faɗa tana nufar inda ta ajiye ribbon ɗinta, Humaira ta ja tsaki tana hararta cikin wasa, Sadiya ta fito tana alƙawarin sai ta ɗanɗana zumar Humaira ko ta wana hali, kasa shiryawa tayi dan ta gama ƙwaɗaituwa da Humaira,tunanin yanda za ta yi ta janyo ra'ayinta kawai ta ke.
Har Humaira ta fito Sadiya na zaune tana tunanin yanda zata yi ta ja ra'ayin Humaira, Humaira ta tabata ganin tayi nisa a tunani ta ce"ke lafiyan ki kuwa?" Sadiya ta ɗago tana ƙallon Humaira wacce take sanye da uniform ɗinta duk da jikinta akwai danshin ruwa.
"Ya zaki mayar da uniform kuma?" ce war Sadiya tana ɓata rai, Humaira ta ce" daga school fa nake idan ban mai da su ba ya zanyi,so kike a gane na biya gidan ƙawa, kinga ni gaskiya tafiya ma zanyi" ta faɗa tana ɗaukar hijab ɗinta, da sauri Sadiya ta riƙe tana faɗin "okay bari na shirya sai mu ci abinci" Humaira ta ce'yanzu kika yi magana, ba ni abin sallah inyi azahar" Sadiya ta shimfiɗa mata tana faɗin"gaskiya baby kin haɗu wallahi kinga uban hips kamar na wata big mama" Humaira ta ce" ke kika sani kuma" ta tayar da sallarta.
Sadiya na shiryawa tana kallon yanda Humaira take sallah cikin nutsuwa, doguwar riga ta zura kawai ba wani bra ko pant hakanan ta saka, ba wani make-up tayi ba, ta zabga uban turaruka, tare suka fito da Humaira tana ta ƙorafin taƙi zama.
Ba su tarar da Ummi a parlor'n ba, ganin manyan food flasks ɗin da ke kan dining, kawai ya sa yawun Humaira tsinkewa, Sadiya sai uban murmushi take mata tana nuna jin daɗinta da zuwan da Humaira tayi."
Da hanzari wasu ƴanmata biyu suka nufe su, dan serving ɗin su, da hannu Sadiya ta dakatar da su, baya sukayi cikin girmamawa suka bar parlorn.
da wanne za ki fara, wanne zan zuba miki?" ta shiga buɗe dukkan flasks ɗin, white rice and kidney soup, sai pepper soup din chicken, da soyayyun naman ɗawisu,da na kaji, soyayyar taliya, ga different fruits nan cikin wani babban tre a gyare, hakama drinks.Humaira ta ce" kinga zauna kawai, ai nima gidan mu ne" ita ta yi serving na su a tare suka cin abincin.
"Ina Dad ɗinki ne, ko yana kasuwa?"Humaira ta jefo tambayar, cike da son jin gulma Sadiya ta ce" no yana Madagascar sun je hutawa tare da Maimartaba"
"Ke dan Allah, tab kuma yaushe za su dawo?" Sadiya ta ce"oh besty kin fiya surutu, ki ci abinci" sai Humaira ta ji kunya, ta yi yaƙe ta ci gaba da tura ɗawisu sai da ta ƙoshi ta ce"bari in wuce sai jibin in mun haɗu a school" Sadiya ta tashi tana faɗin" bari in kira Ummi kuyi sallama.
Tana kishingiɗe a parlor'n Galadima, ana yi mata tausa, Sadiya ce ta shiga tana faɗin" Ummi besty zata tafi" take Ummi tasa aka ɗauko ledar da ta sa aka haɗawa Humaira shatara ta arziki ta ce" ga wannan a bata" Sadiya ta fara dire-diren ƙafa a dole sai ta fito sunyi sallama.
"Oh Baby kin cika daru, mu je a tare suka tawo Humaira na tsaye, ta na kallon ƙofar da ke parlorn tana mamakin wai wannan ƙofar har magana take, ji tayi an rungumota ta baya, ana dariya.
sanin ko wace ya sa Humaira murmusawa, Ummi ta ce" baby sai kin kada ta ne" sakin Humaira tayi tana faɗin"kai Ummi ai ta fini girma ta ina zan kayar da ita"
Ledar tasa Kursum ta miƙawa Humaira sannan ta ce" ga wannan ki gaida umman naku" ta juya.Baby ta ce" Besty sai munyi waya" Humaira ta riƙe leda taji nauyi sai washe baki take tana godiya ga Allah da ya haɗata da masu arziki.
Driver aka sa ya kaita har unguwarsu kafin a zo layin makarantar Malam ta sa aka ajiyeta.
Kantin Badamasi ta je ta bada ajiyar kayanta sannan ta nufi gidansu.
Hayaniyar karatun almajirai ta fara jiyowa, wani mugun tsaki ta ja, tana baƙincikin kasancewarta ƴa a gidan nan.
Ɗalibai mata na daga soro Malam na hango kowa, Asiya da sauran ɗaliban duk suna ta karatu kowa yana ta biya allonsa, Humaira ta ɗan durƙusa tana gaishe da Malam, cikin tausayi ya ce"sanninki da dawowa uwata, ya jarabawar?" ta ce"alhamdulillah ta yi sauƙi sosai"Malam ya ce" Allah ya bada sa'a maza je ki ki huta" ta wuce tana yatsina.
Babu kowa a tsakar gidan sai Umma tana kitchen tana ta fama da hidimar girkin dare.
Da sallama ta shiga tana nuna alamun gajiya da yunwa, Umma ta amsa tana mata sannu, " wash Allah wallahi nagaji sosai" ta faɗa tana zubewa akan tabarmar da ke wajen, gami da hammar ƙarya.
"ai da gajiya wannan jarabawa tun safe har dare, lokacin da su yayanku sukayi ba su wuce awa uku sun dawo, wata ma sai anyi sallar azahar suke tafiya" Humaira ta ce"tab to ai su ta gwamnati sukayi, ni kuma private ce yanzu ma a aji ɗaya muke exam da ƴar Galadima da kuma ƴar gidan sanator Aliyu A. Hadeja fa" Umma ta kama baki ta ce " kai shiyasa naji kuɗin ya yi yawa, to dan Allah ki nutsu ki yi karatu sosai kinga duk cikin ƴan uwanki ke kaɗai aka fi yiwa wannan hidima,ki daina shashanci"
Humaira ta tura baki gaba tana tashi dan shigewa ɗakinsu " ga abincinki" Cewar Umma.
" to ina zuwa" ta faɗa tana wucewa dan a ƙoshe take.
Har Umma ta manta Humaira bata fito ta ɗauki abinci ba, kwanciyar kawai Humaira tayi tana hangota cikin daula, tana tunanin hanyar da zata bi dqn zama babbar yarinya gudun kar su Sadiya su rainata.
Sadiya kuwa, tana komawa ɗakinta ta kira ƙawarta Lumcy ƴar ƙasar Ethiopian ce, half-caste ce, Mahaifinta ne ɗan can, mahaifiyarta kuma ƴar Nigeria ce, aiki ne ya kaita can, shine sukayi aure, auren bai daɗe ba suka rabu ta tawo da ƴarta.
Lumcy da ta ke tare da momcy da wani gay Cristian mai sune Ashade Kayode wanda yake yi mata lesson ya zama kamar ɗan gida wayarta ta fara ƙara, ganin my luv ya sa ta saki murmushi, amsawa ta yi ta ji Sadiya a mawuyacin yanayi, da alama tana buƙatar agaji, take Lumcy ta ruɗe tana faɗin" what's happened to you my luv?"
Momcy da Ashade ma duk suka bita da kallo dan ganin yanayin da Lumcy ta shiga,Sadiya ta ce" where are you my love, I need your assistance?" Ajiyar zuciya Lumcy ta sauke tana fadin" I'm at home" ok I'll coming" ta katse wayar, Lumcy ta koma ta zauna tana faɗin " she 's my best friend Baby" Momcy ta ce" me ya same ta?" Lumcy ta ce" wai fa zuwa zatayi"
Momcy ta ce" kai Baby kullum ba ta girma, Hajiya Fati na fama"
Lumcy ta saki dariya dan babu wanda ya san suna yin lesbian daga su sai abokan harkansu, abinda iyayen ba su sani ba, har da ƙawayensu matan manya dake state ɗin da other states ana yi da su, sai su kwana a hotel ba tare da iyayen sun damu ba, a ganinsu an bawa yarinya freedom ne dan morewa rayuwa.
Cikin shigar tantirai Sadiya ta fito ta na faɗin " Ummi zan je gidansu Lumcy a can zan kwana" Ummi ta ce" kinsan Dad ɗinki bayason kina kwana outside" Baby ta ce" sai dai in ke ce zaki faɗa masa, ai naga baya nan" Ummi da bata son ɓacin ran Baby ta ce" okay you can go" ko ba ki faɗa ba, cewar Baby ta na banko ƙofar, Ummi ta yi murmushi tana faɗin " oh my baby hmmm childish" ta ci gaba da chatting ɗinta.
Da magriba Baby ta isa gidan su Lumcy,Babu Wanda ya yi yunkurin yin sallah daga uwar har ƴar dan ba damunsu tayi ba, Ashode daman bayi yake ba, Cristian ne, cikin murna Lumcy ta rumgumo Baby suna murnar ganin juna, Momcy da Ashode sai fara'a suke, ganin Lumcy cikin farinciki ya fi komai yi wa Momcy daɗi, tana tsananin son ƴarta ta, wacce take kama da ubanta sosai wato Theodore, da ganinta ansan ba ƴar nan ba ce.......
* * *
Juyi ta yi a gaban sa, ta kuma juyawa ta ce" tnx ina jin daɗin yabon da kake min ɗan ƙani" ASH ya shafa kansa wanda ya zame musu al'ada shi da SAIF ya yi murmushi yana ɗaukar ruwa ya sha, zama Zahra tayi ta na facing ɗinsa, duk halittar girjinta a waje, duk yanda ASH ya so ɗauke kansa daga kallonta kasawa ya yi a haka suke ta hira, har la'asar tana ta kaiwa da komowa a gabansa.
"Ƙanin me zan girka maka?" ASH ya ce " kaiii yau na canji Yaya ni ake tambaya kenan hahhh" cikin hararar wasa ta ce" kaima kasan ko kusa ba ka isa ka canji mijina ba wallahi dan na tausaya maka ma" ASH ya ce"au watukun ni ki ka tausayawa ba wai ni nake tausaya miki ba saboda ba miji a kusa kin zama gauruwa ko" ya tashi yana ɗaukar makullin lifan ɗinsa yana faɗin " na tafi tunda ba ni da amfani"da sauri ta riƙe hannusa, wanda ya sa sukayi saurin janyewa a tare dan wani irin shocking suka ji at the same time, ta marairaice gami da dire-diren k'afa kamar a gaban Mijinta take, ta shiga ba shi haƙuri tana kama kunnenta, yanda take yi ne ya burge ASH zama ya yi yana sakin dariya ya na nuna ta da yatsa" yanzu waye yake taimakon wani?" A shagwaɓe ta ce " kai ne ka ke taimako na" ya saki fara'a yana faɗin yes I'm the winner" murmushi Zahra ta yi,tana faɗin "duk abinda naga dama zan girka kuma" ASH ya ce"idan bai yi min ba kuma in bar miki abinki ahee" da haka ta shige kitchen ɗin, ASH na kallon wani film mai suna Plane, ya ga wayar Zahra na ringing, My hubby yagani, sanin ko waye ya sa ya shiga kiranta " aunty bro is calling you" Zahra da take kwaɓin alkubus ta ce" amsa mana, baka ganin aiki nake" ASH ya shiga kitchen ɗin da hanzari yana picking call ɗin ya kara mata a kunne, riƙewa ta yi tana faɗin "hello my"
Daga can SAIF ya ce" ina kika shiga ina ta kira ba ki ɗauka ba sai yanzu?" cikin jin haushinsa ta ce "ina kitchen yanzu ma ASH ne ya kawo min bana kusa ne" SAIF ya ce " ok,is there any problems?"ta ce "Babu"a taƙaice.
Miƙawa ASH wayar tayi ta ci gaba da aikin gabanta.
ASH ya ce" bro how far?" SAIF ya ce" zan tura maka money, end of this month ka kai madam saloon, ta yi min maganar zata je"ASH ya ce "ok"SAIF ya ce" idan ka sami lokaci tomorrow or next tommorow ka Kai ta gidansu, da yamma ka koma ka ɗauko ta" nan ma ya ce"in sha Allah" daga nan SAIF ya ce" ka gaishe da su Abba" ya kashe wayarsa.
ASH ya langwaɓar kai ya ce" hahhh sorry ɗin ki aunty na, bro ya ce idan naga dama Ina da chance in kai gidan gyaran gashi,kuma in Kai ki gida,idan ban sami lokaci ba, kiyi ta zama a gida hahhhh"
Mantawa da matsayin ko waye Zahra ta yi, ta shiga dukansa tana faɗin " ai wallahi baka isa ba dole ka kai ni"karewa ya ke yana dariya, Abu mai aiki ce ta shigo, turus tayi ganin yanda suke wasan banza da ƘANIN MIJIN nata..............
FREE PAGES ya kusa kammala, ki yi hanzarin biyan naki, domin ayi tafiyar da ke, ɗari uku ne ba tsada, za ki biya ta wannan account ɗin 2206087564
Rahinat Hussain
U.B.A Bank
Zaki tura shaidar biya ta wannan number ***
Idan recharge card ne zaki tura ta number da ke sama.
___________Dariya sosai ASH yake ganin yanda duk ta bi ta tada hankali, "okay,okay naji zan kai ki but sai na fara kai ki saloon dan ya ce ƙarshen wata a kaiki, daga baya sai mu je gidan ko" Zahra ta ce "gaskiya a'a ba dan yamma tayi ba ai da yau zanje inga Mama na da aunty amma gobe da sassafe ka zo ka ɗauke ni dan Allah"
"am....Ganin Abu ne ya sa maganar ta katse.a bakin ASH.
"Uban me kike yi anan?" Zahra ta faɗa da tsawa, da rawar jiki Abu ta ce" ba..ko...mai "
Kinga ki barta, wai har yanzu ba ki gama girkin ba ne, nifa da wuri zan tafi dan yau akwai inda zanje bayan magriba"
Abu da ta fice tana ganin rashin dacewar hakan da aunty take yi.
Zahra ta ce" oh zance zaka je kenan ko?" ASH ya yi murmushi yana faɗin "ba zan dai faɗa ba" ita ma tayi murmushi ta ce" ai shikenan idan tayi tsami ma ji" fitowa ya yi ya koma parlour, lafiyayyen alkubus da miyar taushe ta yi.
ASH ya taso yana faɗin" ni kam ba zan jira har sai in gama wanka ba" ya ja kujera ya zauna, Zahra ta harare shi tana faɗin "acici mala'ikun hajji" naji dai, ce war ASH, Zahra ta shige dan sake wanka, kafin ta fito har ASH ya bar gidan dan yasan dole ma anjima a ce sai ya zo sai eleven wani lokacin ma eleven thirty na dare yake barin gidan.
Tunda ASH ya ke zuwa ya ɗauke mata kewa da duk wata damuwa, shaƙuwarsu har ta fi ta baya dan yanzu bata kunyar cewa zata dake shi, zuge mata zip kuwa har ya zama aikin ASH dan indai ya na gidan shike yi mata.
Yau Zahra za ta je gida, sai shiri take yi cikin murna
"ASH,ASH Ƙanin" Zahra ke ta fama ƙwalla masa kira kamar wata makauniya, da hanzari ASH ya ajiye wayarsa ya nufi bedroom ɗin cikin azama, kici-kicin zuge zip ɗin take, ta kasa, " zuge min dan Allah" ASH ya ce "kai aunty wannan wana irin kira ne" wani lace ne ta sa ɗinkin riga da zani dan yau gida za'a je, ASH ya haɗa zip ɗin yana niyyar ja dan zugewa, zip ɗin ya cije, ya sa masa ƙarfe take ya karye ya lallace" ashhh aunty ya lallace"
Cikin jin haushi ta ce" kai kafiya gaggawa ka lalata min zip, ta na ƙoƙarin saɓule rigar dan sauyawa, a gabansa take kiciniyar zame wa har ta zare hannu ɗaya zata cire ɗayan ASH ya yi saurin barin ɗakin, ba tare da damuwa ba Zahra ta cire ta sa wani lace ɗin ɗinkin buba, se-green mai bala'in kyau, hular lace ɗin ta sa tana ƙara gyara fuskarta, turare ta feshe jikinta da shi, ta ɗauki mayafinta milk tare da hand bag ta fito parlour.
Ido ASH ya zuba mata ganin ta yi masa wani azababben kyau, wow beautiful babe" ya faɗa cikin yabo da shauƙi.
Fari Zahra ta yi masa ta na juyawa ta ce "ya ka ganni" hannu ya ɗane alamar ya yi👌 a tare suka sa dariya.
Abu!" Zahra ta kira dan sanar da ita za su fita,
"ga ni aunty" ce war Abu ta na durƙusawa, Zahra ta ce" ki kula da gidan, sai dare zan dawo" Abu ta ce"to Allah ya tsare a dawo lafiya" ASH ya ce" kawo bag ɗin in riƙe miki" ya karɓa yana yin gaba, a baya ta bishi tana kallon yanda ya gyara gashinsa yayi irin step,step ɗin nan ba shi da cika sosai sai ya yi mata kyau.
Motar gidan ya nufa, turus Zahra ta tsaya tana faɗin" wai a mota zamu je?" ASH ya ce" eh mana" Zahra ta shagwaɓe fuska ta na faɗin " ni dai a machine za mu tafi" ASH ya ce" haba aunty ai yanzu kin wuce hawa machine dan Allah ki zo mu tafi" inda ya parker machine ɗin ta yi tana faɗin" ni wallahi a machine za mu tafi" dole ASH ya rufe motar ya yi wajen machine ɗin, kunnawa ya yi ya hau yana faɗin "hau mu je"
Hawa ta yi tana gyara zamanta, sojojin da suke gadi suka buɗe musu gate suna ɗan russunawa Zahra, ASH ya ja machine ɗin suka fice daga gidan, suna tafe suna hira abinsu, idan anzo tudu sai duk ta kwanto masa a jiki, sai ASH ya runtse idonsa yana faɗin " ni ki daina matsa ta" Zahra ta ce" ba kai ne kake bin tudu da gangare ba" to nine titin?" Zahra ta ce " waya sani ne" kafin a ƙarasa gidan anyi faɗa, yana ajiyeta ya juya, da harara ta bi shi sannan ta shige gidansu.
Aunty na tsakar gida ita kaɗai tana ta faman aikace aikacenta na gida, "Assalamu alaikum" sallamar Zahra ta ji, waalekissalamu" da gudu Zahra ta ƙaraso ta na rungume aunty, cikin farinciki, Aunty ta ce" oyoyo da Yaya Zahra'u ke ce tafe" da zumuɗi ta ce" eh ba kowa ne a gida aunty?" aunty ta ce" duk suna makaranta Umma na ɗaki ki shiga mana" sakin aunty tayi ta nufi ɗakin Mama, tana kan kekenta tana ɗinki, duk da taji zuwan ƴarta ta, kuma tayi murna, ko sallama Zahra ba ta yi ba ta faɗa ɗakin "mama na nayi kewarki sosai" ta faɗa tana rungume Mama ta baya, murmushi mama tayi tana ajiye ɗinkin ta juyo, Ina kwana" ce war Zahra tana ɗan russunawa Mama ta ce"lafiya lau, ya maigidan naki" Zahra ta ce"lafiya lau ai baya nan ma" Mama ta ce" har ya koma kenan" Zahra ta ce" eh ya kusa wata ma da tafiya" Mama ta ce" lafiya dai ko babu wata matsala ko"
?" Zahra ta ce" bakomai ASH ne ma ya kawo ni, duk sun ce a gaishe ku" muna amsawa ce war Mama.
"Abba yana kasuwa ko?" Mama ta ce eh, Zahra ta ce" ai wuni zanyi ma" aunty ce ta shigo , suka haɗu akai ta hira sai kallon ƴar ta su suke tayi kyau tayi kumatu, ita ta yi girkin gidan su Mudassir suka dawo daga school ganin Yayarsu a gida suka hau murna, jakarta ta ɗauko ta bawa kowa chocolate da biscuits masu kyau, Bayan sun shirya za su tafi islamiya Aliyu ya tubure ba zai je ba Yaya zai bi, sai da aka ce zata jira shi sannan ya tafi.
Zaune suke tare da Fauza tana tayi mata mitar bata zuwa gidanta, Fauza ta ce" kinsan su Mama wlh su suke hanamu da tuni mun zo sosai tunda mijinki baya nan"
Zahra ta ce" ni kamar ba sa so na babu wanda yake zuwa mun sai ƘANIN MIJI na" Fauza ta ce" to wai wana tsoro ma za ki ji, gida duk sojoji hahhh" Zahra ta yi murmushi, Hafsa ta ce" yaya kin yi kyau" murmushi Zahra ta yi tana faɗin "Allah ko Hafsan Mama" da haka suke ta hira cikin nishaɗi Zahra ta ji ina ma ta kwana, wayarta ta ɗauka ta kira SAIF, wanda yake kwance a ɗakinsa da ke cikin barrack, cikin isa ya amsa, da zumuɗi Zahra ta ce" dear yakake ya aikin?" ya ce" normal ya kai ki ko?" ta ce" eh yanzu ma ina can na ce dan Allah ko na kwana anan ɗin gobe sai na koma please" SAIF ya haɗe rai ya ce" eh da yake a garin mahaukata muke ba" ta ce " i beg you please my love" SAIF ya ce" okay let me call him kin gama ya zo ya mai da ke"
Da sauri ta ce "a'a dan Allah kayi haƙuri, an jima zan tafin"murmushi ya yi iya saman lip ɗinsa ya kashe wayar,
Fauza ta taɓe baki ta ce" ni wallahi yaya Zahra na tsani wannan m.....
* * *
"Good evening momcy " ce war Baby tana dan karya guiwa don respecting, Momcy ta amsa da fara'a evening ya Maman ki hope dai lafiya?" Baby ta ce" lafiya ƙalau kawai naji kewar Basty ne shine na zo" cikin jin daɗi Lumcy ta ƙara rungume Baby tana sakar mata hot kiss a goshi, Momcy ma taji daɗi matuƙa ta ce" ai gata nan sai ayi ta hira daman idan kuka haɗu ba'a jin ku hahh" ta ƙarasa da dariya, Ashode ya ga yanda Baby ta wani narke jikin Lumcy yasan yau ko ya kai dare ba zai sami damar hira da Lumcy yanda yaka mata ba, dole ya haɗa tarkacen ya ƙara gaba.
"Me kike so a kawo miki my babe?" no thing just i need the rest" ta faɗa tana yin hanyar ɗakin Lumcy, da sauri Lumcy ta bi bayanta, Momcy ma ta tashi tayi nata ɗakin, ta na jinjina wannan ƙauna ta ƴaƴan nasu..
Tarar da Babe tayi tana raba kanta da ƴar rigar da ke jikinta, da hanzari Lumcy ta nufeta tana ɗago kan babe, kiss suka shiga yi, cikin tsananin buƙatar juna, gaba ɗaya suka zube a gadon Lumcy, hawa kan Babe tayi tana ƙara kwashe duk wani sauran saliva da ke cikin mouth din Babe, a yunwa ce Babe ta shiga murza breast din Lumcy ta cikin rigar da ta ke sanye da ita, a tare suka sauke deep breath, ahaukace suka raba kansu da kayansu, babe ta shiga fingering ɗin Lumcy yayin da ita kuma ta kifa kanta a ƙasan babe tana lasa tamkar wata tsohuwar mayya, babu abinda ke tashi sai sound ɗin su, tamkar babe zata shiɗe, sai da suka gamsar da junansu sannan suka sarara, babe da ke kwance a kan ƙirjin Lumcy tayi matashi da breast ɗin, lumcy na shafa laulausan gashin babe, suna kallon juna da kyakkyawan smile, ta ce" my luv ya akayi ne?" ce war Lumcy, tuno Humaira babe tayi, ya sa ta tashi zaune in naked fuskarta kwance da damuwa ta shiga sanarwa da Lumcy labarin Humaira da yanda take tsananin sun tayi testing ɗinta.
Kishi ne ya sa Lumcy kasa magana, sanin haka ya sa Babe shafo ƙasan Lumcy tana mata tafiyar tsutsu a cinyoyinta dan tsarata dan ta bata shawarar yanda za'ayi a janyo Humaira harkar.
cikin jan hankali babe ta fara tsara Lumcy da nuna mata ita ɗin is a special for her, sai da suka ƙara tsotse lips ɗin su sannan Lumcy ta ce" don't mind sweetheart ko tana so ko bata so sai kin sami yarinyar nan ko waye ubanta a ƙasar nan"da jindaɗi babe ta rungume Lumcy, knocking ɗin Momcy suka ji tana faɗin " my daughter's the food is ready" okay mom we are coming"Lumcy ta amsa tana mai da pant ɗin ta, baby ta shiga tolet dan yin wanka ta yi sallar magriba da isha, zuciyarta fes dan ta san hatsabibancin Lumcy duk wacce suka ɗanawa tarko to kuwa tabbas sai ta faɗa........
___________Wacce ku ka yi yau?" Ya Ahmad ne ya ke tambayar Humaira wace ta ke ta faman yatsina tunda ta dawo, gaba ɗaya ta gama raina gidansu." chemistry practical da Catering" ya ce "ma sha Allah, saura nawa ku gama?" Humaira ta ce" saura biyu naji ma suna za su yi graduation party za'a kashe kuɗi sosai "Umma ta ce "to ke me ya dame ki da party'nsu kinga Humaira bana son shiga shirgin ƴaƴan masu halin nan tam" tura baki gaba tayi ta na faɗin" to ni me na ce" Fab!!! ta ji an make bakin, " dan uwarki Umman kike gayawa magana haka" ce war Anas wanda shigowarsa kenan, take Humaira ta shiga hankalinta,sanin idan ta ƙara magana jikinta ne zai gayamata.
Sum-sum ta tashi ta nufi ɗan ɗakinsu ta zauna gefen ƴar tsohuwar katifarsu,wacce ake faɗa duk dare ita da Asiya, akan matsuwa, kusan kullum Asiya ke haƙura ta koma ƙasa tana faɗin Allah ya isa.
"Aikin banza me za'ayi da rayuwar talauci, dan su ne manya duk sun bi sun takurawa mutane, ina ma ni ce Sadiya Sadauki mtsww Allah ka yi mana arziki" ta faɗa cikin tsananin son rayuwar hutu da jin daɗi.
Allah ya shirya cewar Umma, Anas ya ce" wallahi duk Malam ne yake ɗaure mata gindi shiyasa take ganin daidai take da kowa" Ahmad ya ce" barta yaya zan saita mata zama ne" Umma ta yi murmushi ta na faɗin " kuyi haƙuri ƙuruciya ce zata daina" Ahmad ya ce" wace ƙuruciya meyasa su Asiya ba sa yi, duk ba ƙannenta ba ne". Kiran sallar isha ne ya katse musu hirar , kowa ya tashi dan gabatar da sallah, Humaira na ganin su Anas sun fita, Umma ta yi ɗaki, hakama su Asiya duk an shiga sallah, ta tashi kamar alwala zata yi ta ɗauki buta, tayi banɗaki, ajiye butar tayi, ta nufi waje da sauri, dan ɗauko chocolates ɗin da Ummi ta hada mata a kayan da aka bata,kantin Badamasi ta je, ya rufe ya na masallaci, tsayawa tayi ta jira shi aka idar da sallah.
Cikin fara'a Badamasi ya ce" yauwa me za'a ba ki Humairan malam?" ta ce" ajiyata mana" cikin wasa ya ce" da kin bari na zo har gida na kawo" ya na faɗa ya na miƙo mata ledar, da zumuɗi ta buɗe tana dubawa, wasu manyan sweets da su biscuits ta ɗebo sai turaruka masu tsada da turmin atamfa da lace masu tsada da kyau. Murna kamar ta kashe Humaira.
Da hanzari ta kwashe kayan tana ce wa "dan Allah ka ajiye min wannan zan zo na karɓa" ya ce to, ya karɓa ya mayar, godiya tayi masa ta nufi gida, hango saurayinta mai suna Abubakar ta yi, yana shirin aike gidansu.
"kai Faruk tsaya, gani nan ba sai ka shiga ba" ta faɗa ta na kama ƙugu dan ba son Abubakar take ba, a ganinta ma me zatayi da talaka ta taso cikin talauci kuma ta auri talaka ta ƙare rayuwarta a talauci, ba da ita ba.
Abubakar ya ce" daga ina haka, masoyiya?" kallon up and down tayi masa tana faɗin" wai kai wana irin maye ne, na faɗa maka banasonka, bana sonka wannan wana irin masifa ne"duk da abin ya yi wa Abubakar ciwo, ya shanye dan ya saba da wulaƙancin Humaira, yana masifar sonta.
"Haba Humaira ai ko dan arzikin Yaya Anas bai kamata ki dinga yi min haka ba" to ina ruwana da abotar ku, kai bari ka ji, wallahi tallahi da na aure ka gara na mutu banyi aure ba,me na sama ya ci bare ya bawa naƙa" haka ta dinga yi masa cin mutunci, take ya ce" ke Humaira in sha Allahu ba za ki ƙara ganina a ƙofar gidan ku da zummar na zo wajenki ba" shewa ta yi wacce ta janyo hankalin Malam, ta ce"Allah ya raka taki gona mtsww" ta yi wucewarta.
Malam ya ce"yaki nan Uwata" cikin saita kanta ta je ta tsuguna, waye wancen kike ɗaga masa murya haka?" take ta zabga ƙarya dan tasan Malam ya san Abubakar kuma yana mutuntashi, ta ce" wani ne Malam" Malam ya ce" ba na son tara tarkace Uwata, ina wannan yaron Abubakar yana nemanki ko?" Humaira ta tura bak gaba "ni dai wallahi ba na son sa" ta faɗa kai tsaye.
Malam ya ce" to tashi ki wuce Allah ya zaɓa mana mafi alkhairi" ta ce amin ta shige.
Ƙara ɓoye su sweets ɗinta tayi a hijab, ta wuce "daga ina kike?" muryar Umma ta ji, kame-kame ta hau yi, Umma ta ce" da daddaren ma sai kin fita yawo kenan ba kya jin abinda nake faɗa miki ko" Humaira ta ce" ki yi haƙuri gidan su Wasila na je karɓar littafina da ta ara, tun a school ɗin mu, gobe muna da jarabawarshi da naje bata nan yanzu ma na jira ta ne kuma bata dawo ba, ganin kina sallah shiyasa ban faɗa miki ba na fita" take Umma ta yarda ta ce" au to shikenan ki dai kiyaye kanki" Humaira ɗaki.
A jakar kayanta ta ajiye abinta sannan ta fito ta yi alwalar sallar isha.
Wajen sha ɗaya na dare Asiya ta na ta bacci, dan da wuri take bacci, Humaira ta na ta cin chocolate ɗinta, taga jagwal ɗin wayarta keypad Itel ta na haske, alamar kira, Sadiya Sadauki ta gani.
Jikinta har rawa yake don ɗauka, ko Umma ce ta kira ta bata ɓarin jiki haka, hello ta faɗa tana siranta murya. Wai ita ma aji sun tada kai da mone,dan duk runtse ba zata bari Sadiya tasan gidansu ba.
Lumcy da babe da suke tare a gado, bayan sun kammala dinner, babe ta ce" hello ya kika je gida?" Humaira ta ce" fine ki yi min godiya ga Ummi irin wannan kaya haka nagode sosai" Murmushi Babe tayi tana faɗin" haba sai ka ce wani kaya na daban ɗan wannan ai ba komai ba ne, dan Allah ki daina godiyan nan kin fi ƙarfin haka a waje na" Humaira ta yi murmushin jindaɗi ta ce" uhm kina jin daɗinki Sadiya wai daman babe sunanki a gida?" jin haka Lumcy ta ɗaga wa Babe kai, eh baki sani ba ashe, Humaira ta ce" ta ina zan sani"
Sun jima suna hira, cikin dabara babe take dukan cikin Humaira a hankali ta gano ba ƴar kowa ba ce face ƴar talakawa.
Bayan gama wayar ne Lumcy ta ce" wow I like her sweet voice, da ga ji baby'n zatayi sweet hahhh" babe ta saki murmurshi tana faɗin "sai ma kinganta my luv" sai da suka raba dare suna tattauna batun yanda za'ayi da Humaira daga bisa ni suka shiga ƙwaƙwale junansu, sannan suka yi bacci, sai eleven'o clock Babe ta farka, da sauri ta diro tana faɗin"ina da exam around two" wanka ta shiga tana ciki Lumcy ta shigo a tare sukayi wankan, babe tayi alwala ta fito, goge jikinta tayi tana saurin shiryawa, wayarta ce ta shiga ringing, Umminta ce, da hanzari ta amsa "hello good morning" daga can Ummi ta amsa tana faɗin" kin tafi school ɗin ne?" Babe ta ce"no sai two nake da exam,yanzu zan tawo Daddy ya dawo?" Ummi ta ce"no ki kira shi, ya ce min yana ta trying no ɗinki baya shiga" ta ce" maybe network problem ne zan kira shi now" okay ki kula da kanki, ki gaishe da Mommy'n naku"
"okay take care bye" ta katse wayar.
Cikin shigar three-quater jeans na mata da wata crezy top ta fito, hakama Lumcy ta sa mini skert ɗinta da wata armless hammata duk a waje, ta baza kalbarta manya a bayanta.
"Good morning momcy" Lumcy ta faɗa tana sakar wa da mahaifiyar ta ta kiss a goshi.
Cikin so da ƙauna ta ce "morning dear hope kinyi bacci sosai" kai Lumcy ta ɗaga, Babe ta ce" ina kwana" Momcy ta ce" came and hug me daughter" da sassarfa Babe ta shiga jikin momcy ta ce" fatan kina lafiya" fine.
A tare suka nufi dining dan yin breakfast,a gurguje Lumcy da babe suka bar gida,babe tayi gidansu dan shirin school,Lumcy kuwa ta tafi park dan haɗuwa da boy friend ɗinta.
* * *
Gaskiya ya kamata ka sami time ka je kaga amarya?" ce war major Ahmad wanda yake kwance a bayan motarsu ta sojoji yana hutawa, SAIF ya ya tsina fuska ya ce" for what reason?" Ahmad ya ce" anya S. Waziri kana da lafiya kuwa, anya ba dutse ba ne kai?" Mtsww ka ga malam banason wannan shirmen ku mata suka dama, duk lokacin da na je ta same ni" Ahmad ya cika da mamaki ya ce "anya kai wallahi dole akwai matsala, jiya ma da daddare ina jin Luna ta na maka knocking ka koreta" S.Waziri ya ce" me zanyi da ita ko ina neman mata bazan nemi arniya, ƙazama ba" to ga su Zee madara da Zuby ai su musulmai ne" ce war Ahmad, tsaki SAIF ya ƙara yi yana fitowa daga motar ya wuce inda part ɗin da ɗakinsa ya ke.
Video call ya ke yi da prof.Waziri yana zaune daga shi sai singlet a parlour, Prof ya na ta fara'a ganin yanda SAIF ya ƙara fresh tamkar ba aikin soja yake ba, SAIF ya ce" Abba ina Noor na jima banganshi ba, take prof ya shiga kiran autan nasa, my boy, my little boy, where are you, your brother went to see you" da gudu Noor ya tawo yana fara'a hannunsa ɗauke da ball ya ce"hi big bro" ya ɗagawa SAIF hannu, murmushi SAIF ya yi yana kaɗa masa fingers yakake" noor ya ce fine and you"shima ya amsa da fine, ya school hope you are reading well"
"Yeah, yaushe zaka dawo I miss you a lot" soon in sha Allah, cewar SAIF.
Umma ce ta fito cikin shigar abaya blue ta zauna kusa da prof ta ce" shine ni ba a nema na" SAIF ya saki smiling ya ce " barka da yamma Umma yakike" ta amsa cikin fara'a , alhamdulillah ya aikin?"shi ma ya ce Alhamdulillah,ta ce hope dai kana cin abinci sosai"ya ɗaga kai, ta ce" kuna dai waya da Zahra ko dan nasan halinka akan aiki" ya yi murmushi ya ce" kullum muna waya ai" sun jima suna hira daga ƙarshe sukayi sallama ya tashi dan yin alwala jin ana kiran sallar la'asar.
Osoro ne yake gyaran ɗakin Ahmad, wine bottle sun fi hamsin a cikin fridge ɗinsa,duk sun zama ice, gasu masa tsada, sunfi wanda yake sha kyau, kullum sai ya yi attempting dauka sai ya ji tsoro, yau dai ya yi ƙarfin halin zarar one bottle ya ajiye kan fridge ya shiga gyaran ɗakin ko ina ya yi tsaf, sanin Hajiya bata nan ya ɗauko giyarsa yana murna ya shiga ɗakinsa ya na juyata " oh nawawooo a'a this beer are different to all wines I should testing it now,now hahh" ganin ta narke ya sa ya buɗe ya ɗauko glass cup ya zuba ya shiga snapping har wani lumshe ido yake tsananin daɗin da tayi masa, tas ya shanye ya na bubbuga kansa biyu uku ya fara gani take ya shimfide anan sai bacci.
Hajiya Binta ce ta shigo horn mai taxi ɗin airport ya shiga yi, da gudu iro Mai gadi ya buɗe yana mata barka da zuwa, ƙasa tasa aka yi da glass ɗin motar ta ce" Son ya dawo?" Iro ya ce" a'a cikin damuwa ta ce "mu je" tana ƙara kiran number'nsa dan ya ce mata za su zo, ko kwana biyu ne suyi, dalilin da ya sa ma ta dawo ƙasar kenan dan ta ganshi.
___________Mijin nak...Cikin hanzari ta daka wa Fauza tsawa "ya ishe ki malama ba tun yanzu ai na san baki ƙaunarsa ba , haka nagani naji ina so" Fauza ta ce" Allah ya baki haƙuri" ta nufi wardrobe dan ɗauko kayanta ta rage guga, ganin an kawo wuta. Zahra ta tashi ta bar mata ɗakin.
Har Abba ya dawo Zahra na gidan, gaisawa sukayi sosai Abba yake son jin ya zaman nasu bata da wata damuwa, Zahra ta amsa da komai lafiya lau.
Ƙannenta duk sun zagayeta kowa ɗaukin ganinta yake yi, a tare suka ci abinci dare har Abba.
Zahra ta na ji inama ta zauna cikin iyayenta dan bata gama ganinsu ba.
Abba ya ce" yaushe za ki koma ne?" ganin takwas ta yi har anyi isha, Aunty ce ta ce" Ashir ne zai zo ya ɗauketa ƙila sai anjima" Abba ya ce" bari in kira shi banason tafiyar dare" sallamar ASH ce ta katse musu hirar da sukeyi, sanye yake cikin ƙananan kaya kamar kullum, farar riga da baƙin jeans fuskarsa cike da fara'a, da gudu Ihsan auta ta je ta rungumo ƙafafunsa tana yi masa oyoyo, dan yaran sun saba da shi sosai fiye da SAIF,
"wa'alekumussalam sannu da zuwa muhammad" ce war Umma, Abba kuwa ya ce" ɗan halak ka ƙi ambato yanzu nake shirin kiranka ai" ASH ya ƙarasa parlorn yana faɗin "wallahi go slow ne ya tare ni" cikin biyayya suka gaisa, ya kalli Zahra ya ce" tashi mu tafi" Zahra ta galla masa harara tana faɗin " idan naƙi fa" ASH ya ce" shikenan sai in yi tafiya ta" Abba ya ce" tashi ku tafi dare yana ƙara yi" a dole Zahra ta shiga ɗakin Umma ta ɗauko gyale da bag ɗinta ASH yayi musu sallama ya fita, Fauza da su Muzammil ne suka rako shi, rai a haɗe Zahra ta fito,ganin yanda take tafiya a hankali yasa ASH kwashewa da dariya hakan yasa su Fauza ma darawa.
Da sauri ya matsa yana buɗe mata motar, front sit ta zauna, duk yanda ta so riƙe hawayenta kasawa tayi, 2k ya bawa su Muzammil ya shiga motar da hanzari.
Ganin yanda ta rufe fuska yasa ASH fara tsokanarta.
"Toh wannan kuma wana irin salo ne, sai kace wata sabuwar amarya kin wani ƙunshe fuska" banza tayi mishi dan gaba ɗaya ta gaji da zaman kaɗaici ji take ina ma batayi auren ba.
Jin tayi shiru yasa ASH faɗin " aunty na wai mene ne ko ba ki da lafiya ne, ni banason na ganni a cikin damuwa wani abu ne?" shasshekan kukanta da ya ji yasa ASH rikicewa, parking ya yi dan bazai iya driving a haka ba, cikin rikicewa ya juyo facing ɗinta muryarsa har rawa take, cikin tashin hankali ya shiga faɗin" what's happening to you my aunty, me ke damunki" batasan lokacin da ta saki murmushi ba, duk da tanajin kewar gida,cikin tsantsan shaƙuwa ta shagwabe fuska ta ce" ba kaine ka wani zo ba ina cikin ƴan'uwa ka wani ɗebo jiki zungu-zungu ka zo ba" ajiyar zuciya ya saki yana jin hankalinsa ya kwanta jin kawai rigima ce, key yayi ma motar ya na faɗin" ai da kinsan hakane sai ki kira mijinki kice ba sai ya dameni da kiran inzo in ɗauko ki ba" Zahra ta ce" wallahi ba dan babu yanda zanyi ba da bazan bika ba" Hararar wasa ya daka mata yana yatsina fuska ya ce"daga baya kenan, sadaka da karuwa" haka sukai ta faman faɗa-faɗa, a Al'azahar gas meat ya tsaya yana faɗin "ina zuwa" kafin ta amsa ya tsallaka.
Chicken ya siyo two bags ya dawo yana ajiyewa a back sit sannan suka ƙarasa gida, misalin tara na dare suka isa gidan wanda yake tamkar rana, gaba ɗaya sojojin da suke gadi su biyun suna shan sigari, David ne ya buɗe gate ɗin bayan ya duba, ASH ya yi musu sallama yana parking, cikin fushi Zahra ta ɓalle door ɗin ta shige.
ASH ya ɗauko jakanta da ta bari, ya zaga ya ɗauko leda ɗaya ya bi bayanta.
Abu da ke zaune ita kaɗai a parlor taga Zahra ta shigo fuska a ɓace, sannu da zuwa tayi mata tana kawo mata ruwa,ta ajiye ta yi nata ɗakin kar a huce akanta, ASH ne ya shigo yana zama gami da faɗin" ni kam ba ni nakar zomon ba rataya kawai aka ba ni" cikinsa ya shafa yana faɗin " aunty dan Allah ki samamin wani abu na ci, rabo na da abinci tun safe" a zabure Zahra ta ce" dagaske!" kai ya ɗaga kawai, tuni ta miƙe tana ajiye wannan fushin ta ce "ina zuwa, kitchen ta nufa dan duna abinda zata kawo masa, tea ta ɗora tana ta rawar jiki, two cup ta yo, ta fito da plate tana ajiye a center table kazan da ya siyo ta buɗe ta juyo a plate ɗin tana faɗin" ka yi manage da wannan" ASH ya ɗauki tea ɗin yana faɗin "wannan ma is ok tawa ledar tana mota ai taki ce wannan" knife tasa tana yago tsoka jin yace haka ta ajiye tana turewa "nima bazanci ba indai baka ci ba" ganin haka yasa ASH dole suka ci tare, kafin ya bar gidan sun shirya, ɗakinta ta nufa tana faɗin ya jira ta yi wanka, ya amsa da to.
Kiran SAIF ne ya shigo wayarsa, amsawa yayi da sallama, SAIF ya ce" ka ɗauko ta?" ASH ya ce" eh yanzu muka dawo" ya kuma ce" kuma dan wulaƙanci saboda ta raina ni ina kiranta bata picking call ɗina" ASH ya ce" may be tana toilet ne yanzu ta ce min za tayi refreshing ne, sauri nake yi zan wuce" wani tsaki yaja Yana katse Kiran.
Ash ya sauke wayarsa yana takaicin halin yayan nasa mai saurin hawa, Zahra da ta zauna a toilet ta ci kuka, dan zuciyarta ta gama karkata akan KANIN MIJIN ta, kyawawan ɗabi'unsa suna matuƙar burgeta.Da hanzari ta katse wannan tunani ta share hawayenta tayi wanka, gami da alwala.
Ta ɗauki kusan mintuna talatin kafin ta fito,missed call ɗin SAIF ta gani, ajiye wayar tayi ta shiga shiryawa, Doguwan riga made in Indonesia tasa wacce take haɗe da mayafinta ta fito.
ASH ya miƙe yana faɗin, bro ya kira ki baki amsa ba, yana ta faɗa ki kira shi yanzu, ni zan tafi" Zahra ta ce" yanzu na ga ni, ina wanka ne, ASH ya ce " ni dai sai da safe" tare shi tayi tana faɗin " please dan Allah kar ka tafi yanzu" ASH ya ce" kiyi haƙuri aunty gobe ina da test so nake na je na ɗan duba karatu na" Ba da son ranta ba ta ce" to shikenan yaushe zaka dawo" ASH ya ce" sai kin ganni kawai" ya bi gefenta ya wuce.
Jiki a mace ta koma ta zauna tana kiran number SAIF.
Yana kwance yana tunanin maganar da Ahmad ya faɗa masa, jin kiran Zahra yasa ya kalli wayar kamar ba zai ɗauka ba dannan rejected sannan ya bi kiran, da sallama ta amsa, take ya shiga masifa" sai yanzu kika ga daman kira na" wani takaici ta ji ya tokare mata zuciya, tausasa murya tayi ta shiga faɗin " ina toilet ne yanzu naga kiran kayi haƙur....." aikin kenan kayi haƙuri- kayi haƙuri to wallahi muddin zaki dinga ɓatamin rai ba za ki ƙara fita ba,daga kin sami chance na zuwa gida har zaki sauya min" hawaye ne ya shiga sintiri akan fuskarta, ya dinga masifa daga ƙarshe ya kashe wayar yana cilli da ita.
A wajen Zahra ta fashe da kuka tana mai jin gaba ɗaya ta gaji da wannan al'amari ta ce" wannan wana irin rayuwa ne kenan ni bazanji daɗi a wajen MIJINA ba sai dai SILAR ƘANIN MIJI" ta kuma rushewa da kuka, haka tayi mai isarta ta gaji ta rarrashi kanta, wayarta ta ɗauka bayan ta kwanta ta fara neman ASH dan su ɗanyi fira ko zuciyanta zatayi sanyi.
Ɓangaren ASH kuwa, yana komawa gida ya tarar da ƴan gidan nasu a parlour Prof ansha gayu cikin wata dakakkiyar shadda fara da wasu mutum biyu cikin abokansa, sai Noor da Umma ga wani big cake mai kyau an rubutu Happy birthday Prof Ibrahim Waziri, wanda a yau ne professor ya cika shekaru saba'in a duniya, amma jinsa yake yaro sharaf tsabar gayu da boko.
Cikin mamaki ASH ya ƙaraso yana faɗin "wow Happy birthday to you Abba" ya na mai jin daɗi rungume shi Prof ya yi yana mai ƙara washe baki, ɗaya bayan ɗaya suka gaisa da abokan Abba wato Prof, sannan ya hau mitar ba'a tuna masa da wannan rana mai matuƙar mahimmanci a wajensu ba.
Nan Umma ta ce ai surprise ɗinsu ake so ayi shi da SAIF shiyasa aka jira shi ba'a yanka cake ba, da bai zo yanzu ba ma kiransa za'ayi, yanzu kuma sai aka kira SAIF video call dan ayi shagalin da shi.
Take ASH ya yarda yana kiran SAIF, su soja da rai yake a ɓace kamar ba zai amsa kiran ba sai da ga baya ya ɗauka, zai hau masifa yaga gidan nasu kamar ana sha'ani a daren, kafin ya ce komai ya ji ana waƙar birthday ga Abbansu take ya yi murmushi wanda yake na gefen baki, wanda yake nuna da shima ya yi farinciki, take ya bi sahun masu rera waƙa ga Abba ana tafi,SAIF ya ce" why Abba, meyasa ba'a bari na dawo ba" Umma ta ce" haba son ranar zamu ɗaga ko me, yanzu ba ga shi anyi joined da kai ba"nan dai Prof da Umma suka yanka cake aka hau tafi gami da watsa musu Flowers,Prof ne ya bi su da cake one by one Umma ma ta bashi a baki, SAIF ya yi masa fatan alkhairi, sannan ya katse kiran,haka akai ta nishaɗi har sha biyu sannan su Alhaji Kamal da Prof Ayuba suka tafi.
Duk kiran da Zahra take ASH bai gani ba, dan hidimar birthday ɗin Abba, sai biyu saura kowa ya nufi makwancinsa, anan ne ASH ya kula da kiran sanin rigimar Zahra ya sa ya ƙi kiranta, wanka yayi duk da a gajiye yake sai da ya duba karatun da yayi niyya sai uku ya kwanta bacci mai nauyi ya ɗauke shi.
M.ABDULLAHI HOUSE
Ya Anas ne ya fito da waya a hannu farinciki fal fuskarsa, yana faɗin Ahmad-Ahmad zo ka gani" ba Ahmad ba duk ƴan gidan ne suka fito, Malam ya na faɗin " lafiya Babangida" Anas ya ce" na samu aiki Malam yanzu naga anturo min ta Email ɗina" Alhamdulillahi" malam da Umma suka faɗa a tare, Ahmad ma yayi hamdala su Asiya kuwa ihun murna suka sa da tsalle Yaya Anas ya sami aiki, da zumuɗi Humaira ta ce" Yaya aikin me ne?" Ya Anas ya ce "na sami a aiki a Federal, a cikin wata ministry of Agriculture, zamuje interview Abuja ashirin ga watan nan" Abuja cewar Humaira sai lokacin tayi murna dan ko ba komai yanzu zata ce tana da Yaya wanda yake aiki a federal.
Nan su Malam suka dinga yi masa addu'a ana ta fatan alkhairi, take Malam ya ce"to kuwa babu mai fita sai anyi saukar alƙur'ani domin yiwa Yayanku addu'ar samun nasara"
Take Humaira ta ce"tabdijan ƙarfe tara zamu shiga exam fa Malam" Umma zatayi magana Malam ya ce" to maza ki kintsa ki tafi Uwata Allah ya bada sa'a" babu wanda ya bi ta kanta, duk da idan aka raba saukar har almajirai ba zasuyi cikakken awa ɗaya ba zasu kammala, amma Humaira ta noƙe.
Take kuwa Malam ya sanarwa da manyan almajiransa abun alkhairin da ya samu Anas, take aka raba saukar mutum talatin yaran kuwa aka sa sukaita hasbunallahu da waɗanda suke ta yin yazassana domin Allah ya bawa Anas nasara ya sa ya fara a sa'a ya tsone idanun makiya.
Sai biyu za'a shiga Exam amma Humaira tun tara ta shirya ta fita kantin Badamasi ta je ta karɓi ajiyarta, kasuwa ta nufa dan siyar da kayan da Ummi ta bata dan tasan ko giyar wake ta sha bata isa ta je da wannan kayan gidansu ba, dan dole ta faɗi inda ta samo su ko yayunta su yi ajalinta tsaf tasan gidansu.
Lace ɗin da zai yi dubu tamanin aka siya a duru arba'in, atamfar Holland wacce takai dubu sittin aka siya a talatin, take ta cefanar da kayan ta nufi bank, kafin azahar ta buɗe account ta zuba kuɗinta, sai murna take dan ita ma zata ba da nata contribution ɗin idan za'ayi candy.
Rufaida yoghurt ta shiga ta zauna ta ci ta ƙoshi 3k ta kashe a cikin 10k ɗin da ta bari a hannunta sannan ta nufi school, tana zama ta shiga karantawa ƙawayenta ai yayanta anyi masa minister a Abuja, akai ta tayata murna, ganin Sadiya Sadauki har yanzu bata zo ba, sai Humaira ta ji duk hankalinta bai kwanta ba, idan ta bar Sadiya Sadauki ba ƙaramar asara zata tabka ba.
Har aka shigo musu Sadiya bata zo ba, take Humaira ta tashi zata fito domin zuwa duba Sadiya, wata brown car ce ta shigo kirar Hatchback, tasha tinted glass,Sadiya sadauki ce ta fito, take Humaira ta hau washe baki gami da zuwa da sauri tana taro ta, sosai Sadiya ta ji daɗin wannan abu da Humaira tayi, rungume juna sukayi kowa fuskarsa cike da farinciki, hannunsu saƙale cikin na juna suka nufi exam hall.
Sai da suka gama Exam around four o'clock sannan Humaira take sanar da ita anyiwa yayanta minister a Abuja, sosai Sadiya ta tayasu murna sannan ta nemi Humaira da ta rakata wani waje, ba tare da tunani ba Humaira ta amince, motar da aka kawo Sadiya ba ita ce ta zo ɗaukarta ba ƙirar subcompact ce yanzu ta zo ɗaukarta, tare da Humaira suka shiga, kanta ne yayi wani girma tunda take bata taɓa tunanin zata hau irin wannan motar ba, Sadiya sai nane mata take a jiki tana faɗin " I'm tired besty" Humaira tayi murmushi tana faɗin "ayyah sorry babe yanzu ina muka nufa ne?" Sadiya ta ce "sai da ke zanyi" cikin wasa a tare suka fashe da dariya, wani big boutique suka shiga, Sadiya ta ce" zaɓi abinda kike so" Humaira ta dafe ƙirji tana faɗin "niiiiii!" Sadiya ta ja hannunta suka shiga ciki, kasa zaɓa Humaira tayi sanin ko ta ɗauka bata da inda zata ajiye bare ta dinga sakawa a jikinta.
Humaira ta kasa ɗaukan komai, Sadiya ce ta ke ta ɗauko mata, tana wannan zai miki kya besty" Humaira da hawaye ya cika mata ido, cikin nauyin baki ta ce" ki daina asarar siyamin wannan kayan nasan a gidanmu ba za'a barni na saka ba,nagode da soyayyanki gare ni" Sadiya tayi mu…