ƊAYA CIKIN BIYU

ƊAYA CIKIN BIYU

by @mrsisham12

5–6⚔️👑👑 ƊAYA CIKIN BIYU 👑👑⚔️

🔥A story of love,hatred and violence ⚔️🔥

🤍*Story and written*🤍

~By~

Aisha Abbas (*MRS 🌹 ISHAM 🌹*)

(*Yar lelen jarumai writers*).

Jarumai writers association 📚📚📚🖋️🤩

❤️🔥Page 5____6

Wani dishi dishi ta soma gani a idanunta,Jiri ya soma yunkurin kayar da ita,da sauri Haseena da kuma taimakon Mubeen suka dedeta mata tsayuwarta, dukkanin su jiki a sanyaye

A hankali ta soma faɗin " yanzu dagaske Aba ya tafi ya bar mu!?,kenan kiran da ya mana a daren jiya ya kira mune dan ya mana ban kwana ?,innalillahi wainna'ilaihi rajuun,Abaaaaaaa meyasa zaka tafi ka barmu!?" Ta karasa maganar tana fashewa da marayan kuka, Haseena dake kuka ce ta rungume ta tana bata hakuri sannan a hankali take furta mata a kunne

" Aba addu'ar mu yake bukata a yanzu Muzna baya son kukan ki, ki ɗaure ki masa addu'a ko kin manta abinda yake yawan faɗa muku ne?, kuka ga mamaci baya taɓa dawo dashi ko kuma sauya komai ".

Share hawayenta tayi ta dubi Mubeen tana goge majina tace " ka kira min Ummi a waya ina son in san a wani hali take ciki ".

Dasauri yayi abinda ta ce masa sede number Ummi a kashe.

" Haseena ki ɗauki gimbiya Muzna ku koma gida kawai kin ji ko!?, Allah ya jikansa da rahama halinsa da ayyukan sa na gari su bi shi".

Motar suka shiga a wannan karon Mubeen ne yake tuki, Haseena kuma na rungume da Muzna tana bata baki,duk da yanzu bata kuka se hawaye da ke sintiri a Idonta da suke a kumbure.

Tana office din ta gabanta kuma system ne tana aiki a ciki dakatawa tayi da aikin sakamakon jin ringing din da wayarta ytake,wanda yanzu yayi kusan sau uku kenan, dubawa ta yi taga sunan Yarima Haysam ne ke kira yasa ta ɗaga.

" Innalillahi wainna'ilaihi rajuun Yaushe?". Abinda ta faɗa kenan bayan ta miƙe tsaye hankali a ɗan tashe.

" Okay,okay bari zan kira Muzna din,ko kuma zan wuce gida kawai nasan zan sameta a can" ta faɗa tana kashe wayar da sauri ta ɗauki wayar ta kawai ta fito cikin sauri-sauri. ma'aikatan ne suka tsaya kallon ta suna mamakin yau meye ya samu boss din tasu haka, manager din ta ne ya tawo da sauri yana tambayar ta meyafaru.

" Aba ne ya rasu " sosai ya ji babu dadi ya mata ta'aziya sannan suka fice a tare.

Suna zaune a falo Muzna har yanzu bata dena hawaye ba musamman in ta tuna yanzu fa sarki ya mutu bazata sa'ke sakasa a Idonta ba har abada,tana tuna watanni bakwai da ya wuce sun zo shi da sarauniya Fatima, kuma basu ga alamar bashi da lafiya har sosai ba? ashe yana fama da Cancer wannan abu ya tsaya mata a rai.

Haseena se hakuri take bata Elizabeth me aikinsu tana daga tsaye a gefe tana kallon su duk da bata jin larabci amma ta fahimci wani abu ne gagarumi ya faru hakan yasa jikinta yin sanyi sosai.

A falon ta same su zaune itama ta zauna tana dawo da Muzna jikinta haɗe da shafa bayanta tana bata hakurin rashin da suka yi.

Da mamaki sosai Haseena take kallon fuskar Muzaina wanda ko ɗigon hawaye babu a ciki se de yanayi na damuwa kawai, ita de kullum bata dena mamaki da kuma tambayar kanta wai Muzaina wata irin mutum ce,.

Haɗa ido suka yi ta kamata tana satar kalllonta hakan yasa ta watsa mata muguwar harara.

" Muzna addu'a zamu yiwa Aba. Allah da ya fi mu son shi ya karɓi abinsa".

" Muzaina mu tafi gida a yau bazan iya kwana a wannan ƙasar ba ". cewar Muzna.

" Kin san bazeyu mu koma gida ba ,saboda ba mu da password ɓalle viza,an ƙi yi mana ne saboda kar mu je Kuwait batare da sanin Aba ba".

A haka suka kasance a zaune har bayan ƙarfe tara babu abinda suka iya sawa cikin su,babu wanda ya yi sallah a cikin su,se da goma ya yi ne Muzna da Haseena suka yi sallah mangrib da ishai, a cikin wannan daren Elizabeth da Haseena suka haɗawa Muzna kayanta gaba daya da duk wani abinda take buƙata,itama Muzaina tana can bedroom dinta tana haɗa kaya.

A wannan daren Muzna bata rintsa ba bacci gaba daya kauracewa idon ta yayi.haka ta kasance a zaune a kan gadon dakin Haseena dan dama tun da safe ta yiwa nata dakin hijira saboda abinda taji a ciki.

Washe gari sallah suka yi aka fitar da kayan su zuwa compound ɗin gidan,dakyar suka rarrashe ta taci abinci duk da babu yaw. Abaya gaba dayansu suka sanya,haɗe da Pakistan hijab.bakaramin kyau suka yi ba dukkan su uku,duk da Haseena bata kamo su kyau ba,suna zaune a falon sun yi jugum suka ji dirin saukar private jet din masarautar su a compound ɗin gidan.

Se da jirgin ya gama dedetuwa kafin nan suka fito nan suka tadda ma'aikatan gidan suna a tsayayye dake Haseena ta sanar da su batun tafiyar da zasu yi din.

Zuro kyakyawar ƙafafun sa da suke cikin takalmin sarauta yayi, kafin ya fito gaba daya, masha Allah kyakkyawan tsayayyen namiji cikin shigan kayan sarauta da suka matukar dacewa dashi,ta ko ina ya haɗu ga tsayi da faffadar kirji,gashin kansa ya kwanta a bayansa yana da tsayi se sheki yakeyi yasha gyara sosai,kallo daya zaka masa ga ka ainihin jinin sarauta na yawo a jikinsa. isa inda suke tsaye yayi kafin suka rungume juna shida Muzaina

" Amincin Allah ya tabbata a gareku ya ku ya'yan sarki adali me adalci".

" Ameen Ameen Yarima Farasat ".cewar Muzaina.tana sumbatar hannun sa.

Wajen da Muzna take yaje suka rungumi juna ta sumbaci hannunsa.

" Ina me tayaku bakin cikin rashin mahaifin ku, Allah ya jaddada rahama a garesa ".

" Mun gode yarima Farasat" ta faɗa tana yin gaba cikin jirgin suka shiga su uku a yayinda suke jiran Muzaina da take sallamar ma'aikatan nasu.

Tunda suka shiga cikin jirgin babu wanda ya yi magana har suka sauka a cikin babban farfajiyar masarautar Bayaan me matukar kyau da tsaruwa haɗe da burgewa jirgin yayi.ya Salam masarautar Bayaan babba ce wanda duk bin kokkofin mutum baze taɓa ganin karshen sa ba,yana da girma wanda baze iya misaltuwa ba,ko ina ka duba yana da kyau ginunnuka masu kyau ne a ciki wanda suke a tsaftace tsaf kuma bana kowa bane face na bayin dake ciki,shashin su yana da girma da kyau ko na wasu masu ƙananan karfi ma iyakaci kenan,ga bangaren mayakan masarautar shima yana da kyau kuma ko wani shashin akwai gate me kyau da aka saka domin bada tazara tsakanin bangarorin maza da mata. Filin kuwa ko ina zaka taka intalok ne Malale a kasan duk inda ka juya akwai shukoki masu kyau.ga rumbu.

Design masarautar Bayaan kadai abin kallo ne,babu mahalukin da ze shigo beji ya kaunaci rayuwa ta har abada a ciki ba.in na ce zan ci gaba da zayyana muku kyau da tsari haɗe da girman masarautar Bayaan to ko pages biyu baze ɗauke mu ba. Ga bayi da kuyangu ta ko ina se shawagi suke yi kowa na harkokin sa,mata na sanye da doguwar riga jikinsa babu kwalliya launin shuɗi,mazan kuma na sanye da kaya launin ja da shuɗi.

" Wowwww wai dama wannan shine masarautar mu da aka hana mu rayuwa a ciki!?, gaskiya ya haɗu oh my god Muzna duba ki gani " Muzaina ta faɗa tana ta waige-waige a cikin masarautar domin kyau da komai na masarautar nasu ya gigita mata lissafi da kuma ƙara kwadaita mata son mulki.

" Uhmmm ".

Kawai Muzna ta faɗa duk da itama masarautar ya tafi da ita,amma abinda ke damunta daban,haka itama Haseena se kalle-kalle take yi komai na cikin masarautar was so unique.

Wasu bayi ne masu sanye da kaya iri daya wanda ya kasance launin shuɗi me haɗe da baki hannun su riƙe da Kwando dake dauke da furanni masu yawa a ciki,wanda aka tanada domin yi musu Barka da zuwa.

mata guda ashirin suka iso gaban jirgin da sauri-sauri suka tsaya bisa layi duk mutum goma sun yi layi daya.

Wasu zaratan maza ne jikin su sanye da court bakake jikinsu murde fuska babu walwala suka taho ɗauke da wani babban jan carpet me girman gaske. suka soma shinfida sa wanda tsayin sa yakai daga inda suke tsaye har cikin entrance din palace din nasu, kafin duk suka tsaya hannunsu a baya kan su a sun kunye,kallon carpet din da jikin sa aka rubuta WELCOME da manyan baki suka yi, soma takawa suka yi,suna tafiya akai wa'yannan bayi matan ne suka soma musu wanka da furanni. Cikin nutsuwa suke tafiya duk inda suka wuce se bayin sun runsuna a ƙasa har su wuce, sannan su biyo su a baya.

Cikin babban palace din suka shigo, Allahu Akbar, tundaga kofar mashigar palace din ma abin kallo ne, domin da zallar zinari aka yi sa ɓalle kuma abubuwan kayatarwan da suke ciki,baki baxe taɓa iya faɗan yanayin tsaruwan cikin ba sede kawai ku masu karatu ku ƙiyasta, fada ya matukar haɗuwa, kuma a cikin babban fadan sarki ake zaman makoki inda kowa yana sanye da fararen kaya ga kuma makaran da sarki Taifur Rahman ke kwance a ciki lifeless,an masa wanka,an yi mai komai kawai jiran zuwan gudan jinin sa ake yi kafin a sallace sa. Kowa ka gani a cikin faɗa zaka fahimci mutuwar sarki Taifur Rahman ya jijjiga sa, domin sarki ne da yayi mulkinsa a bisa gaskiya da amana.

Tunda suka shigo faɗa nan fa Muzaina kwadayinta ya sake hauhawa,duk da ta kama kanta ta nutsu kar a fahimci abinda ke zahirin fuskarta da gangan jikin ta,amma hakan baya hanata satan kallon fadar.

Kallo ne ya dawo kansu cike da girmamawa kowa ya miƙe haɗe da sunkuyar da kawunan su a garesu a domin kuwa suna da yakinin tabbas a cikin su daya zata shugabance su,.

Kamar yadda suka yi a gare su haka suma suka mayar musu da martani. wajen Ummi dake tare da matayen galadima da waziri Muzna ta nufa tana me rungumeta, sarauniya Fatima da Idonta yake jajir saboda kukan da tayi ne tayi hugging ƴarta back,a cikin kunne Muzna ta dinga yiwa sarauniya rada me kwantar da hankali. Isowa wajen su Muzaina tayi tana me rungume su duka.

Addu'a suka yiwa sarki Taifur Rahman suna yiwa fuskar sa kallo na karshe,duk yanda ta yi domin ta shanye hawayen ta amma abu ya ci tura se da ya gangaro,suna a durkushe a gaban makaran da aka saka shi,taji an dafa mata kafaɗa,a hankali ta juya dan ganin waye, tsohon da ta gani ne yasa ta sunkuyar da kai ƙasa alamar girmamawa.

Murmushi ya yi ya mayar da hannunsa bisa kanta na tsawon dakiku arba'in kafin ya cire yana sauke numfashi.

" Muzna akwai haske a tare da ke,ke me kawo gyara ce da zaman lafiya bayan ran mahaifin ki,da kuma ni din nan abubuwa da yawa zasu faru wanda ni bana kusa ɓalle in nuna miki hanya,amma tunda har aka haife ki to da yardar Ubangiji za ki bawa wannan masarautar da kuma ko ina kariya ".

Tunda ya soma magana take satan kallon sa,ita har yanzu ta gagara gane wa'yannan maganganun ina suka dosa, a ina yakamata ta yi musu mazauni,.gaba daya zantukan sa ɗaure mata kai yayi,ya kuma jefata a duhu.

Har zuwa lokacin da yake maganganun bata dago kai ta ɗaura Idonta akan fuskar sa ba sede satan kallon farar fuskar sa me ɗauke da farar kasumba me matuƙar tsayi da yawa wanda tsayin sa yakai kusan kirjinsa,kansa kuma yasha rawani irin na manyan malaman larabawa.

" Meyasa ka ke faɗa min wannan maganar!?,meyasa nake shiga rudu a cikin yan kwanakin nan!? " Ta jero masa tambayoyi a lokaci guda, murmushi kawai ya mata ya furta

" Hhhhhhhh, Muzna ke yarinya ce qarama.Za ki fahimta yanzu ai lokaci ya yayi ".

Still fuskarta na cikin damuwa domin kuwa be bata amsar da ya dace ba,ba ta samu amsar da zata gamsu dashi ba wanda ze kwantar mata da hankali ba.

" Shin ko zan iya sanin ka!?" Ta fadi hakan a hankali domin lakar jikinta ya gama narkewa lakwas.

" Sheikh Abu Dhabi,shine sunana " yana faɗar haka ya miƙe tsaye riƙe da sandarsa yana dogarawa ya soma tafiya,da kallo kawai ta rakasa.

" Meye abinda wannan tsohon yake faɗa miki Muzna " Muryar Muzaina ya dawo da ita cikin tunanin ta.

" Manta kawai" ta faɗa tana duƙo da kanta izuwa fuskar mahaifin su ta manna masa sumba a goshi haɗe da ci gaban da yi masa addu'o i,bayan sun gama ganawa da shi ne, aka zo aka ɗauke sa domin kai sa gidan sa na gaskiya.

Amintacciyar baiwa ce ta yiwa ko waccen su rakiya izuwa shashinta da ke ɗauke da komai na bukata,wanda Haseena da Muzna suka tafi tare. Makeken falon dake sashen Muzna na zagaye da wasu luntsuma_ luntsuman kujeru wa'yanda suka kasance royal cushions white color ga throw pillows din su blue color, carpet din dake malale a falon me laushin gaske da idan mutum ya taka se ya ji kamar ya taka katifa tsaban laushi ya kasance blue in color haɗe da touches din fari,a tsakiyar kujerun akwai center table da saman sa ke ɗauke da mini glass flowers,se tafkeken Tv plasma dake zaune akan standard Tv. Kamshi ta ko ina yake tashi sai sanyin AC dake ratsa jikin ɗan Adam, yanayin design din falon, bedrooms da komai kana gani kasan manyan kuma shahararrun magina ne suka ƙawata sa.

Bayan sun yi wanka ne suka shirya cikin fararen kaya kamar yanda kowa yayi suka fito aka zauna a faɗa ana ci gaba da zaman makoki. Muzna na tare da sarauniya Fatima sabanin Muzaina dake zaune a ɗan gefe da su.

" Barka yar uwa " ta ji anyi mata magana daga bayanta, slowly ta waiga nan suka haɗa ido da wata kyakyawar matashiya dake zaune a gefen su tana sakar mata murmushi.

" Barka dai Hamra" ta faɗa,tun daga nan babu wanda ya sake magana saboda basu wani saba sosai ba se de a waya ne suke ɗan gaisawa duk da ba sosai ba.

Bayan an yi sallah la'asar ne kowa ya watse aka bar iya shakikan sarki tare da iyalan sa,se a sannan ne sarauniya Fatima ta samu magana da ya'yan ta.

" Ummi nayi kewar Aba sosai" cewar Muzna da fuskarta da har yanzu yake a marairaice domin mutuwar ya shigeta sosai.

Murmushi kawai sarauniya tayi kasancewarta jarumar mace ce me juriya da tawakkali ta furta

" Muzna Aba din ku yana wajen da ya kamata,wajen da mu ma duk daren daɗewa tofa se mun je".

Gyada kai ta yi, Muzaina ta ce " amma Ummi dama Aba bashida lafiya ne ko kuma!? ".

Se ta sauke numfashi kafin ta amsa mata

" Aba din ku,ya kasance yana fama da ciwon hanta an yi magani iri-iri amma Allah be sa an dace ba ".

Da kallon mamaki Muzna da Muzaina suke kallon ta domin basu taɓa sanin wannan maganar ba,basu taɓa sanin cewa sarki Taifur yana da ciwon hanta ba,.

" amma Ummi yarima Farasat ya shaidamin ciwon daji ne yayi fama dashi “. Cewar Muzna.

“ ah ah hanta ne ba daji ba,kamar yanda bakuda masaniya su ma ba dukan su bane suka sani”.

Koda jin maganarta shuru suka yi. babu wanda ya kuma iya magana a cikin su,ko da dare yayi babu wanda ya iya saka abun kirki a cikin sa,duk suna zaune a dinning,Ummu Zaheenat matar galadima Abdul Aleem ta ce

" Muzna wannan kawar ki ce !?" Ta faɗa tana duban Haseena.

" Ehh ƙawata ce,Ummu Xulaihah. Sunanta Haseena Abdul Muxxalib".

Murmushi suka yi suna yaba nutsuwar Haseena,dan ta burgesu.

Tsaki Muzaina ta yi jin yanda suka cika mata kunne da zancen wata Haseena,duk dubanta suka yi, Yarima Farasat dake gefenta ya ce

" Meyasa ki ke tsuka ? ".

" Nothing " ta yi maganar tana haɗe fuska tare da Miƙewa ta ɗauki tissue tabar dinning din tana goge hannunta.

Girgiza kai Muzna ta yi domin tasan abinda yasa tayi haka,har ta shige basu dena bin bayanta da ido ba.

" Muzna je ku kwanta dare ya yi ". Cewar Ummu xulaihat matar waziri,. Miƙewa Muzna da Haseena suka yi suka wuce part din ta,maida kallonta kan Su Hamra tayi

" Hamra, Aliyah,Jadwah kuma kuje ku kwanta".

Miƙewa suma suka yi suna barin dinning din. Ya yi saura yarima Farasat ne da Yarima Haysam,se kuma su.

" Sarauniya Fatima, bana ganin boyewa yaran nan halin da ki ke ciki abu ne me kyau,yakamata su san da rashin lafiyar ki" cewar Ummu Zaheenat.

Ajiyar zuciya ta sauke " haka ne amma,in suka samu wannan labarin hankalin su tashi ze yi ni kuma banason su sa'ke shiga matsananciyar damuwa akan wanda suke ciki ,taya zan iya samun kwarin gwiwar sanar da su cewa nima ina da ciwon hanta kuma ina matakin karshe,ah ah bazan iya ba Zaheenat,na san lokaci ƙalilan nake dashi a wannan duniyar. kwanaki kaɗan ne suka rage min in bi mijina in da ya tafi,abun da nake sa'ke roko a gun ku shine,ku riƙe mun ya'yana domin marayu ne su,ku riƙe su kamar ya'yan ku " jiki a sanyaye suke kallon ta suna jin wani irin karyewan zuciya,.

A hankali ta furta " Haysam, Farasat ku nasan bayan raina baza ku bar kannen ku su kauce a kan hanya ba ".

" Mun miki wannan alkawarin Ummi " cewar yarima Farasat.

Murmushi tayi tana tunanin wani irin hali yaran nata zasu shiga bayan mutuwarta,domin lokaci ƙalilan gareta.

" Yarima Ishaq na hanyar dawuwa gobe" yarima Haysam ya faɗa yana Miƙewa da nufin barin falon babu wanda ya ce masa komai har ya fita.

Cire kayan jikin ta tayi ta daura lallausan towel ta nufi hanyar toilet domin yin wanka .har izuwa yanzu fuskarta a haɗe yake,ita kaɗai se jan tsaki take yi.

Kunna shower tayi ruwa ya fara zuba a jikinta kafin ta ɗauki sinadaran wanka masu kamshi ta fara gogawa lallausan fatar jikinta se da ta kwashe mintuna goma tana abu daya domin ba iya wanka tayi ba harda gashin kanta ta wanke sa.

Sauke numfashi tayi lokacin da ta gama, sannan a hankali ta nufi jikin hangan dake sakale da towels a jere a jiki. hannu tasa ta janyo daya,abinda ta gani ne yasa ta yi saurin jan baya tana ɗaura hannu akan al_auranta.

Bakomai ne ta gani ba face wani dattijon ba indiye sanye da jajayen kaya goshin sa na shafe da wani farar powder da ja,duk da tsoho ne amma tarin sumar kan sa baki ne,ga wasu manya-manyan hatimai ɗaure a damtsen hannayensa idanunsa a rufe yana fuskantar ta.

" Waye kai?,meyasa zaka shigo min nan?, wanene ya baka izinin hakan !?". Ta faɗa tana kuma ja da baya,tana kakkare jikinta.

A hankali ya buɗe jajayen idanunsa da kwayar bakin cikin yan ƙanana,ya ɗaura su akan fuskar ta.

Da wata iriyar murya me amo ya soma magana,wanda duk magana daya da ze yi se ta ji tsigan jikinta ya tashi.

" Muzaina,na zo wajen ki ne badan komai ba se dan taimaka Miki,nasan kina matukar son ki mulki Bayaan,wanda kina ganin za ki samu a ruwan sanyi,to ba haka abin yake ba, wannan mulkin da ki ke kwadayin sa kina ji kina gani a gaban idonki za'a bawa wata,bayan kuma kin fi ta cancanta,kin fi ta bukatar wannan kujerar,zasu juya miki baya a lokacin da kike kuka kina rokon da su bar miki kujerar amma ba zasu taɓa baki ba,sannan....."

" Dan Allah malam dakata,.kai din waye zakazo kana faɗa min wa'yannan maganganun marasa kan gado?,,tayama kasan duk wa'yannan abubuwan zasu faru,to bari ka ji yar uwata Muzna bata bukatar wannan kujerar, saboda babu kaunar abinda ya shafi sarauta a ranta koda kuwa akwai ni nan nafita cancanta " ta faɗa bayan ta katse sa.

Dariya ya bushe dashi wanda se da yayi sanadiyar bangon toilet din suka fara daddarewa.

" Yaro yaro ne,zaki fahimci hakan a lokaci kɗan dake zuwa,a yayinda danasanin ƙin karɓan tayina ze zo miki. domin kuwa ni aljani Suwami gautam bana faɗar abinda yake ba haka ba,amma bazan juya miki baya ba,kofa abuɗe yake a duk lokacin da kike da buƙatar taimakona kawai ki furta, zurfa_zurfa narash mani gumaaaaaal zaaararrrr,hamkam_hamkam zurfa-zurfa, za ki ganni tsaye a gaban ki batare da bata lokaci ba,hhhhhhhhhh ". Ya gama maganar yana bushewa da wani dariyar da yasa toilet din ya soma girgiza da karfi iska me karfi yana tashi wanda madubin dake manne ta ko ina suka soma fashewa suna fitar da wani ƙara na tsoratarwa,da karfi ta toshe kunnenta tana duk

ƙawa a ƙasa.

Ɓacewa ya yi bat,nan take komai ya dawo dede,tsit,kamar babu wani abinda ya faru komai ya koma mazaunin sa,a hankali ta cire hannun ta a kunne tana miƙewa tsaye haɗe da bin toilet din da ido. ganin komai na nan yanda yake hakan yasa ta fara zullumin ko mafarki take yi towel din da ta zaro zata daura ta gani yashe a ƙasa da hanzari ta ɗauka tana me ɗaurawa a jikinta ta fice da sauri.

" Bamu taɓa tunanin zamu gan ku a nan kusa ba gaskiya, saboda tun muna yara muke tambayar yaushe zaku dawo. se a ce mana kun kusa " cewar Hamra dake zaune akan makeken royal bed din Muzna,ita da Jadwa, Aliyah,se kuma Muzna da Haseena dake zaune a tsakiyar gadon,suna saurarar Hamra.

Domin tun lokacin da suka shigo su ma suka biyo su a baya domin tayasu hira,da samun lokaci tare da su,kuma hakan yayiwa Muzna dadi sosai sede ta fuskanci duk yanda take da surutu tofa su Hamra sun fita.

Murmushi tayi ta ce " to ai mu ma haka yanzu ga shi dalili me ƙarfi ya dawo damu batare da mun shirya dawuwa ba" ta faɗa a sanyaye,dafa kafaɗar ta Haseena tayi.

" Gimbiya Muzna duk sanda wani sabon magazine din ki ya fito tofa se na kalla wallahi kina burgeni,nima zaki koyamin yanda ku ke tafiya da tsayuwa ko?,domin nide ina son jaruman finafinai sosai,ba domin ni engineer bace da na shiga harkan film gaskiya " cewar Jadwah da tunda ta soma magana ko haɗiye yawu batayi ba.

Dariya sosai Muzna tayi domin Jadwah ta sata dariya sosai duk da yanda take cikin damuwa,.

" Gaskiya Jadwa kina da abin dariya". Ta faɗa hakan tana me kwanciya,.

" Ke gobe yaya Yarima Ishaq na hanya" cewar Aliyah.

" Wani ya'ya Ishaq din !? ".

Hararan Hamra da ta yi tambayar Aliyah tayi tana faɗin

" Ya'ya Yarima Ishaq nawa muke dashi !?".

" Tabb dijam ki ce kwallon kwankwalatin ɗan iska na hanyar dawuwa de ". In ji Hamra.

“ ahhhh lalllai Hamra kin riƙa ya'yan naki ki ke cewa dan iska ?“.

Muzna dake jin su batace komai ba,amma tana tunawa da Yarima Ishaq din da suke magana akai tun suna yara,amma tunda suka baro masarautar Bayaan bata sake ji daga garesa ba sede taji ana kiran sunan sa.

Se da dare ya soma yi sosai ne kowa ya tafi in da yake kwana domin yin bacci,a yayinda Haseena suka kwana tare da Muzna, Muzaina kuma tana can bacci ya kauracewa idanunta se tunanin abinda aljani Suwami Gautam ya faɗa mata take yi.

Washe gari da wuri Muzna ta shirya cikin doguwar riga fara ta ɗan saka ƙaramar farin gyale akan ta ta rufe gashinta,komai fari tasa sannan ta fita zuwa bedroom din Muzaina zaune ta sameta akan gado ta mike ƙafa jikinta na jingine da gado,tana sanye da kayan bacci da alamu ko sallah batayi ba,ɓalle kuma wanka,zama tayi a gefenta tana kallon yanda ta lumshe Idonta, tabbas idonta biyu amma ta tsunduma cikin kogin tunani wanda hakan yasa batama san da shigowar ta ba.

Daura hannu tayi akan cinyar ta wanda hakan ya dawo da ita daga duniyar da ta tafi,...

" Wai Muzaina lafiya na gan ki haka,ko wani abu na damunki ne? ".

Sauke ajiyar zuciya ta yi kafin a hankali ta ɗaura hannunta akan na Muzna ta runtse da nata hannun kafin ta soma faɗin

" My Muzna ina cikin wani yar damuwa ce kaɗan daga daren jiya zuwa yau ".

" Daga kallon fuskar ki na fahimci hakan, menene abinda yake damunki yake yar uwata!? ".

" Muzna na san yanzu babu yanda za'a yi abar Bayaan babu sabon shugaba,dole a cikin ni ko ke za'a zaɓi ɗaya,kin san yanda nake son mulkar wannan ƙasar,nasan bazaki taɓa tsayawa akan hanyata ba ko da wasa,domin ke babu sha'awar hakan a ranki kuma farin cikina shine naki ".

Tunda Muzaina to buɗe baki ta soma magana, Muzna ta tsareta da ido tana me bin ta da kallon al ajabi,tabbas tasan Muzaina na masifar kaunar mulki amma batayi tunanin jin wannan maganar daga bakinta ba musanman yanzu da ake jimamin rashin sarki Taifur Rahman ba.

Girgiza kai tayi kana ta furta " ban taɓa sha'awar rayuwa irin na sarauta ba saboda ina da nawa burinkan daban,as far as kowa ya amince da ke to ni banida matsala da hakan,amma ki sani muna cikin jimamin mahaifin mu be dace ki kawo wannan maganar yanzu ba ".

Wani irin dadi taji yana ratsata ga kuma sanyin da taji zuciyarta yana yi,kamar wacce aka daurawa kankara akan zuciya,duk wani damuwa da tantama ta ji ya warware mata lokaci guda.

Rungumeta tai tana " nasani,ke me son farin cikina ce ".

Murmushi ta mata kafin a zuciya ta furta " Muzaina ba za ki taɓa sauyawa ba".

Kafin a fili ta ce " Yanzu ki tashi ki yi wanka ki shirya ina jiranki a fada".

Cewar Muzna.

" Okay".

A haka suka rabu ita ta fice a yayinda Muzaina kuma ta shiga wanka.

Ko da ta fito,tana cikin tafiya a babban bangaren me girman gaske tana koƙarin fita daga ɓangarorin domin nufan faɗa ta ga an sha gabanta.

Baya taja domin ta tsorata ganin yanda mutum ya faɗo gabanta kamar wanda ze rungumeta.

Ɗaura Idonta ta yi a kan fuskarsa tana ganin waye ta haɗe rai kamar wacce bata san murmushi ba,a irin haka yanda fuskarta babu wasa zakayi tunanin Muzaina ce,domin ita ce wacce fuskar ta ko da yaushe yake a turbune.

Kyakyawa ne sosai yanada tsayi ga jiki me ɗaukan hankali komai din sa abin burgewa sede kyawun nasa a iya fuska ne kawai,domin kallo ɗaya zaka masa ka fahimci,irin wayayyun samari din nan ne wa'yanda idanun su ya gama buɗewa da bariki,mazan da idanun su ya goge da rayuwar turai.

Wani munafukin kallo yake binta dashi daga sama har ƙasa.

Kafin cikin murya irin ta isassun yan iska ya ce " Barka dai gimbiya" yana me ɗan rangwafawa alamar girmamawa domin ya fita tsayi.

Shuru ta masa tana me kallon gefe,ganin ta ƙi kulasa ne yasa ya kuma faɗin.

" Shin da wa nake tare gimbiya Muzna ce ko kuma gimbiya Muzaina? Domin ba iya tantance ku ake yi ba ".

Ya faɗa yana sake matsowa kusa da ita.

" Yarima Ishaq kauce ka bani hanya in wuce".

" Wayyo na ji tsoro,na ji tsoro zan kauce miki" ya faɗa cike da shakiyanci yana me yarfa hannu alamar ya ji tsoron.

Ganin in ta tsaya biye masa ɓa ta mata lokaci ze yi,yasa ta bi ta gefen sa zata wuce, hannu daya yasa ya dawo da ita baya,yana me haɗe jikinta da nasa.

Kallon fadawan sa dake tsaye a bayan su yayi,ya ce

" Ku ɓace min da gani zan tattauna da yar uwata ".

Gyada kai suka yi kafin duk suka bar wajen cikin sauri dan kar ya kuma yi musu magana.

Da karfi ta turesa kafin tayi amfani da iya karfin ta ta wanke sa da kyakyawar mari a makwanci.

Hannu yasa ya shafa inda ta marensa kafin ya dawo da hannun wajen labban sa ya sumbata.

" Yanda ki ke hadaddiya haka marin ki ya kasance, gaskiya ke din ta musamman ce dan Allah dan ƙara marina mana ". Ya faɗa yana ruko hannunta da karfi, yana kokarin kai hannun kan fuskarsa ya ji an damki hannunsa ta baya juyawa yayi dan yaga waye,kafin ya fahimci komai ya ji an sharara masa mari a dayan makwancin nasa.

Da sauri Muzna ta koma gefen Muzaina dake tsaye a gaban Yarima Ishaq ta harde hannunta a kirji tana watsa masa harara.

Yana shafa dede inda ta marensa ya ce " yanzu na fahimta,kece boss din gimbiya Muzaina,yanda nake jin labarin ki ba haka nayi tsammanin ganin ki ba,se kuma naga kin ma fi gwarjini a ido,zafin ki ya burgeni,na san bakisan ni din waye ba da farko de sunana......." Katse sa ta yi ta hanyar daga masa hannu kana ta furta

" Sanin kai waye ko kuma sanin sunanka ba abu ne da ya shafe ni ba, babban abinda zan faɗa maka me amfani shine kar ka kuskura in sake ganin ka ɗaura wa'yannan kazaman hannayen naka akan Muzna ".

Ta faɗa cike da gadara da kasaita. Murmushi ya yi ya ce

" In kuma ba haka ba kuma fa ?".

Taku uku tayi ta matso kusa dashi Idonta na kallon cikin nasa kwayar idanun ta furta

" Zaka fuskanci hukunci me tsanani ".

" Muzaina ki rabu dashi mu tafi kawai " cewar Muzna dan tasan halin yar uwar'ta.

Jan hannunta tayi suka yi gaba suka bar sa tsaye kamar wanda aka dasa a gun yana bin bayansu da kallo,marukan da yasha a wajen su a maimakon yasa shi jin haushi se ma wani nishadin da ya riske sa,tafiya suke yi amma tana jin idanu a jikin ta hakan yasa ta waiga suka haɗa ido, kashe mata ido yayi sannan ya mata blowing kiss ,harara ta watsa masa tana me tunanin ya akayi Yarima Ishaq ya fito daban a cikin su yana abu se kace ba royal blood ba,haka Muzna ta dinga sa'ke-sa'ke a ranta har suka isa faɗa suka samu ana zaman makoki.su ma zama suka yi, aka ci gaba da ƙarban gaisuwa tare dasu,bayi sun shigo sun yi nasu gaisuwan, haka kowa ya dinga yin nasa gaisuwan.

Yau mako guda kenan da rasuwar sarki Taifur Rahman,an gama zaman makoki duk baƙin da suka zo kowa ya koma se kuma in za'a yi taron naɗa sabon shugaba a Bayaan. Tundaga ranar da Yarima Ishaq ya zo masarautar yasaka rayuwar Muzna a gaba muddin zasu haɗu a hanya tofa se yayi kokarin haɗa jikinta da nasa. tayi masifar hatta gaji domin ita ba mafadaciya bace. kuma babu wanda yasan da abinda yake mata,hakan yasa ta kauracewa duk wani abinda ze haɗa ta dashi kama daga hanya har inda ta san yana zama,domin ta lura Yarima Ishaq tantirin ɗan iska ne,haka kuyangu suma basu tsira ba duk wacce yaga ta masa tofa se ya kwanta da ita,kuma basu isa su yi magana ba.

A bangaren Muzaina kuwa,bayi da duk wanda yake shigowa cikin fada ya gama sanin wulakanci da rashin mutunci irin na Muzaina.domin daga zaran ka yi ba dede ba bata duba da girman mutum ko shekarar da mutum ya bata.haka zata shararawa mutum mari da mugayen kalamai,ba ma iya bayi ba hatta su Jadwa basu tsira ba,hakan yasa basa rabanta domin gudun rashin mutunci,sam bata san ƙara ba,ko kai waye baka fi karfin wulakanci a wajenta ba. Galadima Abdul Aleem Rahman al amarin ya matuƙar kulle masa kai domin ya yi tunanin kamar yanda Sheikhy ya faɗa in an nisanta su da gida komai ze gyaru amma be ga alamar haka ba, domin shi kansa se da ta kusa masa rashin kunya sarauniya Fatima ce ta tsawatar mata.

Muzna da Haseena da suka riga suka san halinta hakan be dame su ba sede abinda suka fahimta shine tunda suka dawo,jiji da kai,izza,da kaisata nata sa'ke ninkuwa yayi,. wannan dabi'ar nata yana matuƙar damun sarauniya Fatima wacce ta sha samun ta domin yi mata nasiha amma sam bata dauka.

Shiryawa ta kammala yi cikin doguwar rigar Egyptian launin ja,jikinsa ko ta ina ado ne se ɗaukan ido yake yi, batayi kwalliya a fuskarta ba, gashin kanta ta haɗe a tsakiyan ta ɗaure su sun zuba ta baya se kuma na gaban ta sauko dasu gefen hagu da dama, bakaramin kyau tayi ba,tana tsaye tana fesa turare Jadwa ta fado dakin tana faɗin

" Gimbiya Muzna shin kin kammala in rakaki ganin cikin masarautar!?".

A jiye kwalban turaren Arabian Oud da ta gama fesawa ta yi a gaban mirror ta juyo a hankali tana sakar mata murmushi ta ce

" Jadwa!.." ta kira sunan ta a hankali kafin ta kuma cewa.

" Yanzu kin ga na gama shiryawa, Haseena zan tambaya ko in zata je ".

" Ah ah ni ba zuwa zanyi ba,kawai se kun dawo ".

Haseena dake kwance ta faɗa dan yau tunda ta farka bata jin dadin jikinta.

Tunda ta ce bazata samu zuwa ba,suka fita suka barta a dakin,suna tafiya suna hira sama sama ga bayi dake take musu baya.duk inda suka wuce se bayi sun gaishe su,da murmushi a kan fuskar ta take amsa musu.

Duk wani ɓangaren da suka shiga se Jadwa ta mata bayani a kai,haka suka dinga tafiya tana nuna mata wasu gurare a masu girma da kyau a ciki.

Wani babban fili da aka ke waye da wasu sanduna Jadwa takaisu,tana faɗin

" Nan wajen kuma,an tanada sa ne domin jarumai kuma sadaukan Bayaan,wato nan shine filin dambe a nan mayakan Bayaan suke fafatawa na atisayi ". Ta faɗa tana tsayuwa haɗe da harɗe hannu a kirji ta zubawa filin damben ido tana ganin gwarazan maza guda biyu da suke ciki suna dambe. Muzna itama gyara tsayuwar ta tayi kamar yadda Jadwah tayi,ta maida hankalinta akan damben da ake yi duk da ma ita irin wannan basa burgeta daga wrestling, boxing,da sauran su duk ba burgeta suke ba,amma haka kawai ta samu kan ta da son maida hankalinta akan fafatawan da ake yi a filin dagan.

Dukkan su biyu babu riga a cikin su se wando irin na yadi me fadi fari,duk da baya suka juya amma kana iya hango karfaffan jikinsu da kuma damatsan hannun su da yake a murde,dayan ya kasance fari dayan kuma fatarsa yana da duhu wato he's chocolate in color,daga ta baya kana hango sumar kansa da yake a gyare,dambe suke yi kowa na son samun nasara akan dan uwansa, wannan chocolate color guy din ne ya samu nasarar kayar da dayan,ihu da sowa mayakan suka yi kafin wani ya daga hannunsa yana nuna sa a matsayin wanda yayi nasara.

Haka kawai ta tsinci kanta da sakin lallausan murmushi tun kafin ta kai da ganin fuskar sa ta ji ya burgeta domin jarumtar sa ya yi tasiri a zuciyarta.

Cikin salo ya juyo yana tafawa da wani dake gefen sa suna faman dariya.kafin ya miƙawa wanda ya kayar din hannu ya miƙe suka rungume juna.

" Ohh my god he is so dam handsome" ta faɗa tana lumshe Idonta, Murmushi Jadwah ta yi jin abinda ta faɗa ta ce

" Kwarai kuwa yanada kyau sosai duk da ya kasance bakin fata kuma ba dan Afrika bane baƙin balarabe ne,sunan sa Sadauki ZUBAIR, jarumi ne da Bayaan take matukar alfahari da shi, mahaifiyar sa ta kasance baiwa ce a wannan masauratar kuma shima a cikin masaurata aka haife sa,shi kaɗai ta haifa, mahaifin sa ya rasu tun yana ƙaramin yaro,duk da shi kaɗai ne wanda ya rage mata amma haka ta turasa cikin mayakan Bayaan domin samun horo shima ya zama me bawa Masarauta tsaro da kariya, kuma ga shi burinta ya cika,yana da saukin kai sosai wannan kaɗan kenan a takaitaccen tarihin sa ".

" ZUBAIR..". ta kira sunan a cikin zuciyarta,a fili kuma ta riƙe kugu haɗe da kallon Jadwah ta furta

" Kai ya Salam Jadwah!. duk wannan dogon jawabin yaushe na tambaye ki!?,dubi yanda ki ka tsaya kina min bayani dalla-dalla kamar wacce na bukata,kai gaskiya Jadwah you're too much ".

Dariyar da ke taso mata take ta son dannewa amma ta ƙasa saboda yanda taga Muzna ta hakikice tana mata masifa,bayan kuma ita ce ta bukaci hakan tunda har ta ce yana da masifar kyau.

" Shikenan!, shikenan, wallahi gimbiya kin ban dariya ke fa ki ka ce yana da kyau shin laifi ne dan na miki bayani akan sa !?".

" Ehh laifi ne babba ma kuwa,and ni bance yana da kyau kar ma ki min sharri ".

Dariya ta fashe dashi harda riƙe ciki ganin yanda ta wayance mata,ita kuwa Muzna dariyar da take yi ne ya kular da ita ta galla mata harara, tsagaitawa tayi ta ce

" Na tuba kimin afuwa gimbiya ".

Ta faɗa tana danne wani sabon dariyar dake kokarin tasowa suma bayin dake tsaye a bayan su dramar ta su ya basu dariya.amma babu wanda yayi gangancin darawa domin kuwa sun san halin Jadwah itama akwai zafin kai.

" In kin gama min renin hankalin se mu tafi ko?".

Ta faɗa tana yin gaba da sauri bayin suka take mata baya kafin Jadwah ta biyosu a baya,har sun yi nisa taji tana me son juyawa domin ganin sa,kallon filin tayi taga babu su a gun su ma sun watse,bataji dadin hakan ba domin ta so ta kuma sakasa a ido kafin ta tafi sede hakan be yu ba.

" Ya ke amintacciyar baiwa , wannan sakon ina sone ki damka sa a hannun duk wacce a ka tantance a matsayin sarauniyar masarautar Bayaan,domin yana dauke da muhimmiyar sako a ciki ". Sarauniya Fatima ta gama faɗa tana damkawa amintacciyar baiwa wani farar takarda a cikin envelope, ƙarba ta yi tana cewa

" Yake uwar gijiyata na miki alkawari in sha Allah,zan yi yanda ki ka faɗa duk wacce aka tantance a matsayin wacce zata hau karagar mulki tabbas ita zan damkawa wannan sako ".

Fuska ɗauke da yar damuwa ta zauna akan royal bed din ta,.

" Na so a ce ina da tsawon rai da zan kai lokacin da zan ga wacece a cikin ya'ya na za'a bawa sarauta da zan yi farin ciki matuƙa,se de kash hakan ba me yuwa bane,kin san shi rayuwa kana naka Allah na nasa". Ta faɗa tana jingina jikinta da gadon.

" Wannan haka yake uwar gijiyata, Allah yakara miki lafiya fara me farar aniya, Allah ya cika miki burikan ki,mace me zuciyar zinari,takawar ki lafiya uwar gijiyata baya goya marayu,duk wani me jin haushin ki sede ya mutu domin kin yi musu nisa kin musu fintinkau, kin sha gaban su,makiyan ki fadawanki,su ƙi biyayya kuma su shiga tashin hankali,.da yardar Ubangiji aljannatul Firdausi ita ce makomar ki". Wannan kirarin da amintacciyar baiwa ta yi mata ne yasa ka ta yin murmushi me sanyaya zuciya,domin a duk sanda take mata kirari har cikin bargon jikinta take jin dadin sa,hakan yasa ta mayar da ita ta hannun damar ta,ta kuma amince da ita dari bisa dari.

Suna tsaka da wannan tattaunawa wata baiwa ta tsaya daga bakin kofa tana kallon ƙasa ta soma magana

" Ina me neman afuwar katse muku tattaunawar da ku ke na tuba,nazo ne domin nemawa Ummu Zaheenat izinin karasowa ne ".

Amintacciyar baiwa ta furta " sarauniya ta yafe miki,ki mata iso an bada izni".

Shigowa Ummu Zaheenat ta yi ta zauna akan gadon tana me kallon amintacciyar baiwa alamar ta basu waje, cikin girmamawa ta sunkuyar da kai kafin ta fice.

" Amincin Allah ya tabbata a gare ki sarauniya,,na zo miki da labari me dadi ".

Gyarawa daga kishingiden da take sarauniya Fatima tayi hannun ta na riƙe da casbi,.

" Menene abinda ki ke tafe da shi Zaheenat!? ".

" Magana ce akan sadaukarwar da Sheikhy ya ce za'a yi domin kammala aikin da aka soma kuma Alhamdulillah an samu kalar dabbar da a ke nema,muna da yakinin da yardar Ubangiji in aka kammala komai ze tafi yanda ake so, za'a karya mummunar ƙaddara dake bin Muzna ko Muzaina ".

Ba se an faɗa ba fuskar ta ma kadai ya isa ya yi nuni da cewa wannan labarin ya matukar kayatar da ita, abinda suka jima suna jira ne ya lokaci yayi,domin irin dabbar da ake nema yau tsawon shekaru goma kenan ana jiran a haifesa amma aljanar dabban da zata haifi abinda suke jira din ruhinta ya yi tafiya me nisan gaske,duk yanda Sheikhy ya kware wajen aikinsa amma be iya gano inda ruhin yayi wannan doguwar tafiyar ba se yau ta haifi yar jaririyar dabbar da za'a yi sadaukarwar da shi.

Cikin nutsuwa ta riƙe hannun Ummu Zaheenat haɗe da manna mata sumba ta furta

" Kin kawo min labari mafi abin bukata a gare ni,na miki imani da Allah tunda mijina ya bar wannan doron duniyar ban kuma tsintar kaina cikin farin ciki ba irin na yau ".

Murmushi itama Ummu Zaheenat din take ,saboda wannan babban abin farin ciki ne a garesu domin muddin wannan dabbar bata haihu ba tofa ba iya wannan masarautar ba su kansu suna cikin halin ha'ula i.

" Godiya ga Ubangiji, godiya ga Ubangiji,shin ko kin san cewa nan da sati biyu masu zuwa za'a yi wannan sadaukarwar. Duk da de banida wani masaniya akan hakan amma ya Abdul Aleem shi ze zo da kan sa,duk wani al'amari ze fayyace Miki su dalla dalla". Ummu zaheenat ta faɗa tana sakin murmushi.

Haka suka ci gaba da tattaunawa.

Yanzu labari ya soma tafiya in har kun bani haɗin kai tofa zamu tafi,in kuma kuka ki bani haɗin kai se mu hakura da wannan daddadar labarin,yawan comment din ku yawan read more din ku.

Comments,like and share fisabilillahi.🥰🥰🥰🫶