KOWA YA GA ZABUWA…

9

by @gureenjoh

KOWA YA GA ZABUWA...

   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            

         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:

Zuhraa

Hamrah

Igiyar Rayuwa

Noor Iman

Ruwan Sama..

Lelewal

GAMON JINI paid

And Now

Kowa Ya ga zabuwa..

                      PAGE 9

FREE BOOK

"Aisha..! Mutum ne ya baki duka wannan? Ya aka yi kika karɓa? Me wannan..!"

A tsorace dukansu uku suka zubawa kuɗin idanu, bunch ɗaya na 1000 kenan har dubu ɗari, Kuka Aisha ta fara tana rantsewa wallahi ita bata ma san ya saka ba.

Ta yarda da ita sede tsoron kuɗin take in ya dawo yace yana son wani abu daga garesu fa? Usman ne ya kwaso suka mayar cikin envelope ta mayar cikin jakar ta ajiye, da taimakon yaran ta rama sallolin dake kanta ta basu sauran tea ɗin da spring roll suka ci, har yaran suka sake bacci bata yi ba Tunanin wannan mutumi ya rufe ta, wanene wannan mutumin? Me manufarshi na taimakonsu?..

Banda magungunanta da allurar da be saketa gabaɗaya ba da ta san ita da bacci a daren nan se Allah, tana lallaɓa talaucinta bata shirya cin mutuncin Yusuf ba Sam.

Washegari da safe da Aunty jamila ta zo hidayat ta tambaye ta akan wani Muhammad da ya taimake su, tace

"Raed ne nima se da na bar wurin yaran nan nake jin ya shigo, karki damu mutumin kirki ne sannan kyauta ce fisabilillahi ba da manufa biyu ba Inde shine duk shekara yana shigowa asibitin nan taimakon bayin Allah"

Ajiyar zuciya ta sauke kan ta mata godiya sossai bisa kirkin da tayiwa yaranta da ita kanta, bayan Abba da Muhammad itace mutum na uku da bazata manta da ita ba, da taimakon Aunty jamila tayi wanka, da snacks ɗin nan suka sake karyawa babu yadda bata yi da Aunty jamila ba ta ci snacks ɗin ta ƙi, ta so taje gidan na Hidayat ta samo mata kaya sede hidayat ta ƙi a Cewar ta hidimar ze mata yawa amma a baɗini bata son zuwa ne taga sirrin su.

Se da rana ya ɗaga sossai kan aka kawo mata yaron, lulluɓe cikin zanin ta da bismillah ta karɓeshi tana rungumeshi cikin jikinta ƙaunar yaron na shiga har jininta, leƙa fuskanshi tayi masha Allah babu abunda ya bar mata, hawaye ne ya zuba mata Aisha ta sa hannu ta share tace

"Mama yayi kyau dayawa ko?"

Murmushi tayi tace

"hawayen farin ciki ne da godiya ga Allah da ya bani wannan kyakyawar halittar a matsayin kyauta wadda babu mahalukin da ya isa ya baka shi banda Allah"

Kafin ta haihu sunan Abba ne yake mata kai kawo a zuciya ta kudiri aniyar idan har ta haifi namiji to Abubakar ne sede yanzu zuciyarta ya chanza, kiran sallah tayi mishi hagu da dama kan ta kira shi da suna 'Muhammad Raed'

Aisha tace

"Mama ya sunan shi?"

Usman dake ta kallonshi ta kalla tayi murmushi tace

"Sunan Daddy ya ci, Allah ubangiji ya raya shi yasa yayi halin me sunan"

Murna a Wurin Aisha ba'a magana an saka sunan Daddy haka kawai take ƙaunar Daddy Muhammad, ita kuwa Hidayat idanu ta zubawa yaron bayan ta sa mishi nono a baki ya kama da sauri yana sha, a zuciyarta take raya...

''Me sunanka is our life savior, shi ɗin kaman wani mala'ika ne da Allah ya aiko mana cikin tsanani, a ranar da be zo asibitin nan ba da kila na mutu tare da kai a ciki, da kila Usman ya ɓata kenan ya shiga gararin rayuwa walau ya zama ɗan daba, walau ya kare a almajiranci da wahala, da kila Aisha rayuwarta ya gama lalacewa a matsayinta na ƴa mace me kankantan shekaru babu wadda ta sani babu wadda ya Santa''

Hawayen da ya ɗiga a kumatun yaron ne yasa ya fara mirmir da idanu alamun son buɗewa, murmushi tayi tana share mishi ɗigon hawayen.

Satin su biyu a asibitin, da Aunty jamila ta gaji da ganin hidayat da kaya guda ita ta kawo mata kala biyu, yayinda yaron hidayat ta bata kuɗi ta karo mishi kala uku, kayan su Aisha kuwa in sun sa sau biyu se ta wanke asalin nasu su saka na kwana biyu ta sake wanke na Wurin Aunty jamilan, abinci safe rana dare saya suke a bakin asibiti, sati biyu da suka yi a asibitin har wani kiba suka yi na zama wuri ɗaya da hutu.

Ranar da aka sallamesu napep suka samo ya kwashe musu kayansu har gida bayan tayi ta yiwa Aunty jamila godiya ta kuma rubuta lambar wayanta a paper..

Ko da suka isa gidan sun samu kwaɗon gidan a ɓalle, ta san aikin yusuf ne suka fiffatar da ƴan kayansu suka shiga gida, a kan shimfiɗarta ta kwantar da yaron ta hau tattare gidan Dukda yadda take jin kiɗa na tashi daga sashen Yusuf alamun yana gidan, Usman ta ba kuɗi yaje ya sayo icce ta zo ta hura wuta ta ɗaura ruwa.

Tana tsaka da sharar tsakar gidan kenan taji sallamar Asabe, ɗagowa tayi fuskanta a washe tana mata sannu da zuwa Asabe tace

"Hidayat kin tsoratamu, ina kika shiga sama da sati biyu kullum se na leko tunda naji dawowan baban su Aisha sede shiru ba ki ba yara? A'ah haihuwa kika yi ne?"

Murmushi hidayat tayi tace

"eh wallahi ranar da abun ze faru na tura su Aisha su kiramin ke sede bakya nan"

Tace

"la shakka ranar na dawo su habiba ke cewa kina ta aikowa na saɓa hijabi na zo na samu gidan a garkame"

Hidayat tace

"ranar ne aka yi min aiki, kuma a ranar Abbana ya rasu"

Salati Asabe ta saki tana mata gaisuwa, ita ta karbi Sharan ta karasa, a varender ɗinsu ta shimfiɗa taburma Nan Asabe ta fita chan se gata da daidaikun matan unguwan masu yi mata ta'aziyya na yi masu yi mata murnar karuwa na yi.

Zulai da ta shigo tace

"yanzu kenan kun yi suna a asibitin kenan?"

Hidayat na murmushi tace

"eh sunanshi Muhammad Raed"

Habiba tace

"Raed..! Me kuma hakan?"

Hidayat na murmushi tace

"Sunan larabci ne kuma yana cikin ma'anonin sunan Muhammad wato Shugaba ko jagora"

Baki Zulai ta taɓe, sauran matan na masha Allah.

Wata A'i daga gefe tace

"to yanzu baza'a mishi yanka ba kenan?"

Hidayat a zuciyarta tace dole kuwa in mishi yanka in shaa Allah, a fili tayi murmushi tace

"Ina gayyatarku duka in shaa Allah jibi za'a yi sunanshi"

Aah masha Allah! Kawai suke ta cewa.

Bayan dayawa sun watse ta ari wayan Asabe ta tura Usman ya saya mata credit ta zo ta saka ta kira Ummi.

Ummi na ɗagawa Hidayat ta fashe da kuka, ummi ta rikice duk yadda ta lallashi hidayat kasa shiru tayi tace tana zuwa yanzu yanzu.

Ba'a yi awa guda ba se ga ummi har lokacin kuka hidayat take, tana ganin ummi ta tashi ta rungume ta, she really needs a shoulder to cry abubuwan sun mata yawa da shekaruntan nan, kwarai ba don Muhammad ba da rayuwarta ta gama nakasa, baabinta maybe da an jima da rufewa, ummi tace

"Hidayat kina ruɗa ni, menene? Me ya faru kike kuka haka?"

"Na Rasa Abba ummi, Abba ya tafi ya barni"

Salati ummi ta saki ta sallame, zama suka yi tayi ta rarrashin hidayat har tayi shiru ta yi mata ta'aziyyan Abban, nan hidayat ta ɗauko yaron ta mika mata, cikin sanyinta ta mata bayanin duk abunda ya faru, Albarka tayi ta sawa wannan Muhammad ɗin da duk basu san shi ba in ka cire Aisha da Usman.

Asabe ce tayi mishi wanka, yayinda hidayat ta zare dubu hamsin cikin dubu saba'in da ya saura a hannun su tace ta je tayi duk abunda ya kamata, ummi na fita gidansu tayi ta sanar wa mamanta tare da diban kaya akan bazata dawo ba se bayan suna, suma ƴan gidansu sun yi alkawarin zuwa mata sunan da gaisuwan Abba don duk wadda ya san ummi se ya san ƙawarta hidayat.

Kasuwa ummi taje ta samo tunkiya ƴar dubu ashirin da biyar, tayi sayayyan kayan abinci har na dubu goma, akan zata ɗibi wadda zata yi abincin suna sauran ta ajiyewa hidayat ɗin su dinga amfani dashi kan suyi Tunanin sana'ar da zata fara kuma.

Dubu goma ta sake fitarwa ta sayi atmpha kala biyu da yadi me saukin kuɗi kala biyu, ta bada ɗinkin turamen za'a yiwa hidayat da Aisha tunda duk ba jiki ne dasu ba zasu iya shearing turmi, yadukan ta bayar aka dinkawa Usman se ta sayi kayan jariri da showel na karamin kudi wadda ze saka a sunan.

Haka ta dawo da kaya niki niki, aka daure rago kayan abincin suka shigar ciki, ta samu Asabe har tayi musu tuwo miya ne Seda ta dawo suka yi anfani da ƴar naman da ta sayo aka yi romon daddawa me jego aka zubawa sossai ta ci, Su Aisha se daaɗi suke ji, da wayon su dae ba'a taɓa ɗaura irin wannan sanwar don su a gidan ba sede baban su ya bayar kuma naman shi a kirge yake sede su sude bojuwa.

Se Dare Yusuf ya fito ya gansu, a kanta ya tsaya da yaron ya gama kare musu kallo kan yace

"Ashe kina da liver da kuma guts ɗin sake dawowa min gida bayan kin kashe mana uba?"

Kanta ta duƙar ƙasa tace cikin rawar murya

"A'a! Taya zan fara kashe Abba?"

Hannu ya sa ya buge mata baki ko damuwa da Ummi dake zaune a wurin be yi ba yace

"Umma zata miki karya kenan, ban yi tunanin kina da idon da zaki sake kallonmu ba bare har ki dawo garemu, Toh bari kiji ni na gaji da ɗawainiya dake da yaranki gaki kullum ke a haihuwa kaman Akuya, tunda har zaki iya mana ajalin uba muma kenan ɗaya bayan ɗaya zaki yi namu to baze saɓu ba, bari na turo miki Umman duk yadda kuwa tace ayi dake haka za'a yi Gayyar tsiya."

Ummi tace

"Haba Yusuf, kai kam wani irin miji ne? Wani irin uba ne kai? A gaban yaranta kake mata irin wannan cin zarafin? Sati har biyu baka ga matarka ba ta dawo bazaka iya tambayar lafiyar ta da na yaranta ba se ma ka sakata kuka? Baka ganin jarirink...."

"Ke dakata rufe min baki! Me ya kawo ki gidana? Sa ido da shiga sharo ba shanu? To ki kiyaye ni wacce ta kawo ki ma tayi kaɗan bare ke ina ruwanki da rayuwar gidana?"

Harara ta zabga mishi tace

"gida! Gida fa kace ai ni anan ban ga gida ba kurkuku na gani me cike da baƙin duhu da azaba! Wallahi ka guji duniya don tafi bagaruwa iya jima ni de na gayamaka"

Hidayat da ta mike ta kama ummi tace

"Ki rufamin asiri ummi kiyi shiru don Allah"

"ke dakata dallah! Wallahi a gabana wannan azzalumi matsiyacin ba ze ci mutuncinki in kyale ba, da me yake taƙama?"

Kuka ta fara hakan yasa Ummi yin shiru ta zabga mishi harara ta wuce ciki, shi kuwa Hidayat ya kalla kan yayi kwafa irin da ni kike zancen ya fice daga gidan yana ball da tukunya har Seda ya buge tunkiyar dake ɗaure.

"Ummi kin san irin bala'in da kika ja mini?"

Ummi tace cikin zafi

"se kiyi shiru ai kina Kallonsu suna cin zarafinki tun yaranki basu san zafin hakan ba har su zo su sani, har se yaushe zaki cigaba da haƙurin nan! Karshe zuciyarki ya fashe da hakuri ki mutu a banza? Toh wlh idan kika mutu duk a cikinsu babu me asara, yaranki sune da asara kuma suma ba tsira zasu yi a hannun su ba gwara tun wuri ki fara shirin kwatarwa kanki ƴanci"

Ummi bazata gane bane, hakan yasa bata kara magana ba se Raed junior da ta zubawa idanu, kan Aisha ummi ta cigaba da shafawa har tayi bacci.

Ranar suna tun asuba Ummi ta hau aiki ita da Asabe se wata makociyarsu maman Abba, kan karfe goma sun gama duk wani aiki na sunan daidai talaka mutane kuwa sun fara cika gidan, an yanka rago har ana suya, me jego tayi wanka ta saka kayan da ummi ta dinko musu haka ma Aisha da Usman se daaɗi suke ji.

Taron suna yayi kyau daidai gwargwado kuma an ci an sha albarkacin Muhammad, masu kawo kaya sun kawo wasu sun kawo sabulu da omo wasu pampams, ummi Atampha ƴar dubu biyar da Kayan jariri tayiwa Hidayat, mamanta ma Atampha da kayan jariri, har Aunty jamila da Hidayat ta kira da layin ummi itama ta zo showel me kyau da kayan sanyi ta kawowa jaririn.

Se yamma Lis gidan ya fara raguwa da mutane ana ta mamaki don duk taron sunanta batayi goshi irin na wannan yaro ba, kowa se cewa yake yaro ya zo da albarka.

Wuraren biyar Umma da yaranta suka diro gidan, matukar tashi hankalin Hidayat yayi ta zo ta zube kasa tana gaida umman ba tare da ta amsa ba ta hambareta da kafa tace

"da ban yini ba zaki ganni! Salon munafunci da tsugudidi... wallahi hidayat yau se kin bar gidan nan, bazaki kashe uban me gida kuma ki cigaba da cin moriyar gida ba"

Khausar tace

"Umma kiga wai harda taron suna"

Fahariyya tace

"Ai dole tunda ta gama yashe mana uba ta tara ba dole tayi taron suna ba, in ba ta yashe mana uba ba a ina zata samu kudin taron suna harda yanka rago"

Surayya tace

"a dadironta mana kin manta Ya Yusuf yace shi be yarda ma ɗan da aka haifan nashi ne ba.."

A matukar gigice Hidayat ta ɗago daidai lokacin da ummi ta karaso ta sauke ma Surraya wani bahagon mari... Ihu ta kurma ƴan uwanta suka yi kan Ummi itama nata ƴan uwan da ta gayyata suka yi kansu a take gida ya kachame.

#like

#share

#comment

                🖤Gureenjoh🖤