KOWA YA GA ZABUWA…

10

by @gureenjoh

KOWA YA GA ZABUWA...

   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.             

         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:

Zuhraa

Hamrah

Igiyar Rayuwa

Noor Iman

Ruwan Sama..

Lelewal

GAMON JINI paid

And Now

Kowa Ya ga zabuwa..

                      PAGE 10

FREE BOOK

Dama Sila ummi ke nema kuma ta samu, Seda ta tabbatar tayiwa Surayya mugun duka kan ta kira police waenda basu da nisa dasu aka zo aka kwashe kowa aka yi police station, banda kuka babu abunda hidayat take cikin tashin hankali don umma ma Seda aka fitar mata da jini.

A police station ɗin ma ba'a natsu ba kace nace gabaɗaya ya cika wurin, Seda Dpo ya fito da kanshi don jin ba'asin abunda ke faruwa, umma ce tayi Charab tace

"Yallaɓai mijina, marikinta kuma surikinta ta kama da maita, shekaran shi bakwai ana neman na takwas yanzu yana jinya kan daga zuwan yarinyar nan sati biyu da suka wuce ya ce ga garinku, ni kuma alkawari nayi jininshi ba ze tafi a banza ba"

Dpo hidayat kawai ya kurawa ido kaman yana so ya ga ta inda maita ya bayyana a suffanta, ummi tace

"Wallahi karya take! matarnan azzaluma ce, marar tsoron Allah ranka ya daɗe tun hidayat na tsummar goyo take hannunta, banda azabatarwa da bauta babu abunda ta sani na farin ciki a rayuwarta, tare muka yi karatu har zuwa matakin secondary kan kaddarar auren ɗan wannan azzalumar ya hau kanta, shima a gidan bata yi sukuni ko farin ciki na ko da second guda ba, daga mijin har dangin shi sun hanata sakat a rayuwa ai ko me tayi musu abun yayi yawa..! Bare babu abunda ta musu, laifinta ne don bata fito cikin gata ba? Laifinta ne don bata da dangi? Laifinta ne zaɓan wannan rayuwa da take ciki? Ai babu ɗan Adam da ze so zaɓarwa kanshi rayuwa cikin kakani kayi irin na Hidayat..."

Kuka ne ya ci karfinta tayi shiru tana shesheka, kowa a wurin jikinshi yayi sanyi, Asabe tace

"kwarai kuwa yallaɓai tun da muka san hidayat a matsayin makociya bata da wani banzan hali ko mugunta, yarinya ce me cike da kalubalen rayuwa bata jin daaɗi wurin ko ɗaya daga cikin zuri'ar dake kewaye da ita, daga miji har danginshi har ma wasu daga cikin maƙota, wannan matar"

Ta Nuna umma

"ita da yaranta basa sati guda chur basu zo sun musgunawa rayuwar baiwar Allahn nan ba, yanzu ba don Allah yasa akwai jama'a a gidan suka zo da wannan babban maganan ba da kila sede wan labarin ba wannan ba, wallahi duk abunda suke hidayat ko iya ɗaga kai ta kallesu bata yi abun takaicin ma dube ta nan faɗa har police station kuma wai da takaba a kanta"

Dpo da ya tausayawa hidayat sossai sede bashi da wani hurumi a kan aurenta sede ze sama mata sauki ta wani ɓangaren, su Umma ya sa aka saka a cell yace Gobe da yamma hidayat ta dawo a karasa shari'ar don yana so kan gobe suma su ɗandana kaɗan daga cikin halin da suka jefa hidayat.

Kowa tafiya yayi, ummi kaman ta daki hidayat don kuka take tana rokon DPO ɗin akan kar a saka su umma a cell be saurare ta ba har Seda aka cika umarnin shi.

Jiki a sanyaye hidayat ta dawo ita kaɗai take hango masifar da ummi da su Asabe suka sakata, da sun bar umman ta buge ta ta huce ba se abun ya kai ga hukuma ba tunda dae duka baya kisa, ko da ta kawowa ummi maganan ummi cewa tayi

"se kiyi, ina nan a gidan nan har se na ji hukuncin da DPO ze yanke gobe wallahi babu me taɓaki, karki manta ɗinki ne a jikinki ɗanye sharaf sannan taya zasu yi accusing ɗinki da kashe Abba alhali su da wannan banzar hallayar nasu su suKayi sanadin shi, wallahi su kiyayi sakayya da kuma hakki don baƙin cikinsu shine ya kashe Abba"

Da dare a haukace Yusuf ya shigo gidan yana me hargowan ina ta kai su umma? Ummi ce ta amsa mishi da

"inda ya dace a kaisu mana tun farko"

Ze yi kanta ta shata mai layi tare da zaro numbern DPO tace

"Wallahi kana taɓa ni tare zaka kwana da ƴan uwanka a cell, karka ji da wai ba iya nan abun ze tsaya ba wallahi se mun je kotu, kotun ma na addinin musulunci se ka gayamin wani addini ne ya baka lasisin zina, wani kuma addinin ne ya baka lasisin musgunawa matar aurenka da yaran ka"

Baya ya koma yana kallonta, tabbas daga kallon idanunta zata aikata kwafa yayi yace

"Zaku gani!"

Ummi tayi Charab tace

"Alkhairi ba! Se Alkhairi in shaa Allah"

Juyawa yayi ya fice, hidiyat dae haka ta kwana cikin zullumi da sanyin jiki ummi kam ko a jikinta se hira suke tayi da su Aisha tana basu labarai kala kala suna dariya.

Washegari bayan la'asar suka yiwa police station tsinke, a nan suka tarar da Yusuf da ba yadda be yi ba a bada belinsu sede DPO ko bari ya ganshi be yi ba se da time ɗin da ya dibar musu yayi yasa aka fiddo su zuwa office nashi hidayat dae banda faɗuwa babu abunda gabanta yake musamman da ta ga yadda su umma suka firgice sukayi zuru zuru da alamu sun ci duka duk a kwana ɗaya.

Gyaran murya yayi kan yace

"kun riga kun amsa laifin ku so Bama bukatar wani sake maida magana, yanzu doka zan kafa muku wadda duk kuka tsallake da human rights zan Haɗa ku tunda ita ba dabba bace kai ko ita dabba ce akwai animal right so ku buɗe kunnuwanku da kyau ku jini"

Yayi maganan yana Kallonsu ɗaya bayan ɗaya kan ya cigaba

"Wallahi ko me kama daku aka ce min an sake ganin gilamawarta a unguwan nan wlh ba zamu yi ta daaɗi ba, ba zan hana danku zuwa gare ku ba sede ita na haramta muku zuwa kusanta, please idan kuna Tunanin wasa nake just try me and see fileing ɗin ku zanyi as attempt murderer, ke kuma uwa ce kaman yadda aka haifeta haka kika haihu babu wadda ya san inda Rana zata faɗa in banda jalihci da ƙarancin addini taya zaki fara fitowa kawai don tashin hankali da takabar mijinki? Allah yayi gaskiya da yace mafi koluluwar jin daaɗin namiji a duniya shine mata ta gari, hakanan annabi ya horemu da samawa ƴaƴayenmu iyaye nagartattu amma ke kam baki daga cikin ko guda Allah ya shirye ki in na shiriya ne"

Kuɗin beli ya fadawa Yusuf, jiki na rawa ya cire ya biya yace ya sallame su, shi kuma kar ya bari su haɗu.

Godiya ummi tayi ta mishi shi kuwa hidiyat yayi consoling yace karta damu babu abunda ze sake faruwa she's safe.

Ko da suka dawo shawarwari ummi ta bata ganin har lokacin hankalinta be kwanta ba yasa Ummi sake kwana, anan suka yanke shawarar sana'ar da zatayi da dubu ashirin din nan.

Kaman da wasa aka saukewa Hidayat Gawayin dubu goma da kuma icce na dubu goma nan take ta fara sana'arta ba kama hannu yaro tana kula da yaranta cikin rufin asirin Allah da ikonsa, babu abunda ya gagaresu na daidai talaka Yusuf ya kan shigo sede kallo kawai yake hadasu baya ce mata ci kanki in ta gaishe shi ba amsawa yake ba.

Raed junior na wata biyu ta sayi freezer ƙarami ta kara sana'ar Kankarar zobo da na nono da su kankarar tsamiya at dsame time tana icce da gawayin ta.

A lokacin kuma ta fara lura da Yusuf da ya kan shigo kullum a birkice, sannan yanzu da kafa take ganinshi ƴan matan ma ya dena kawowa, bata dae dena gaishe shi ba Dukda baya amsawa haka yaran ta kan yi musu dole su gaida uban nasu Dukda tsoron shi da ya riga ya rikide zuwa tsanar shi da suke suma don tun tana iya kare shi har ta dawo shiru, yaran yanzu ne da ake haifar su da wayaun su.

Yau tana zaune tana lissafin kuɗin da zata ware uwar kudin ta sake sayan kayan sana'a sannan ribar kuwa ta je kasuwa ta sayo musu abun bukata zuwa Abinci kaman an jefo shi haka ya faɗo ɗakin, idanunshi kan hannunta kuwa yayi saurin zuwa ya fusge a razane ta mike sede ko sake kallonta be yi ba ya juya ya fice.

Sauke idanunta da suka kara kyau yanzu sbd hankalinta dake kwance tayi se suka hada idanu da Aisha dake kwance zazzaɓi ya dame ta bata je islamiyya ba, maida kwallar da ya cika mata idanu tayi saboda yarinyar ta zauna kawai tana me ɗaukan Raed da su Aisha ke ce mai Junior ta hau bashi Nono.

Abu kaman kar ya fara nan fa ya kulla mata, daga ta ɗan yi ciniki kaɗan ze zo ya kwace wani lokacin ko ta ɓoye haka ze wargaza ɗakin kab ya bincike se ya samo haka zasu rakube da yaranta in ya gama ya fice su tashi su gyara ɗakin.

Tun ɗan sauran da yake barin mata yana juyuwa har ya kare aka koma square one1 freezer ɗin ta sayar ta sake fara gawayi sede shima ba'a je ko ina ba ya sake kwacewa.

Wani Ranar Alhamis da misalin karfe biyu suna zaune da yaran suna cin abincin da shine kaɗai ya saura musu a hatsi wadda suka dafe yau, a fujajan ya shigo kaman ba Yusuf ɗan wankan nan ba ita dae hidaya se mamakin abunda ke faruwa dashi take a baɗini ta san ba lafiya ba sede tunda bata da hurumi nata ido.

A kansu ya tsaya yace

"Ke! Bani kuɗi"

Duk idanu suka zuba mishi se da ya daka mata wani tsawa a firgice junior ya tsala kara, yayyun shi suka haɗe kansu cikin rawan murya tace

"ba..babu"

Hannu ya ɗaga ze Mareta Usman yayi saurin cewa

"Abba ta fa ce maka babu"

Juyo idanu yayi kan shi yace

"kai don ubanka har ka kai ina magana kana sa min baki? Irin banzan tarbiyar da uwar taku ta koya muku kenan?"

Da sauri tace

"kayi hakuri! Wallahi babu ko Naira biyar hannuna yanzu"

Kafa ya sa ya harɓe ta yace

"Bani kudi nace! Na san akwai kin boye ne.. Ai dama an fada min kece duk farar kafanki ce ta sa na zuba duka kudadenmu na gadon Abbah a hannun ƴan damfara wallahi se kin fito min da kuɗina!"

Dukanta ya fara, hakan yasa Usman tashi da gudu yaje ya faɗi a jikinta yana cewa

"Abba! Abba ka dena dukanta tace babu, bamu da komai duk ka karɓe"

Yaron ya ɗaga yayi wurgi dashi wadda ya saka Hidayat runtse idanu tana kiran sunan Allah da karfi, Aisha dake rungume da junior duk suna kuka ta kara kankame shi tare da rufe idanu tana cewa

"Abba kayi hakuri! Abba ka dena dukan su basu yi komai ba Abba! Mama ki bashi kuɗin ya dena dukanku, mama kan Ya Usman na jini..."

Da gudu Hidayat ta miƙe tayi kan Usman da tunda kanshi yayi mugun gwaruwa da pillar ɗin varender ɗinsu be kara motsi ba, ɗago shi tayi tana furta..

"Innalillahi wainna ilahi rajiun Usman! Usman..! Usman tashi, buɗe idanunka ka gani kaji? Ka buɗe ka gani wallahi ya dena dukana ba kuma ze sake ba, don Allah ka buɗe idanunka..!"

Kuka take yi me gunji da matukar ciwo, wani irin baƙin duhu ne ya mamaye ilahirin zuciyarta, da sauri ta ɗago Usman wadda yanzu ya fi karfinta a dauka haka ta saka shi a bayanta, daga ita se doguwar rigar sunan junior ta ɗaura ɗankwalin a kanta haka ta fice cikin tashin hankali don Yusuf ya jima da ficewa Abun shi.

Gudu gudu sauri sauri haka take tafiya dashi a bayanta hawayen dake zuba mata yasa ko ganin gabanta bata yi, damuwanta kawai ta samu asibiti kusa inda za'a duba mata Usman, she can't take it! Bazata iya jure rayuwa babu su ba, wani irin ƙara ne ya ziyarci kunnuwanta, wadda babu tantama na birki ne sbd yadda taji mutane sun saki salati, se a lokacin ta lura da hancin motar dake dab kafafunta..

Kan ta ɗaga kai taji wani tsawa a kanta wadda ya kara sakata birkicewa har Usman ya silmiyo daga bayanta saboda jikinshi dake sake.

"Hey! Are you out of your senses da zaki ke tafiya a hanya kamar animal? What nonsense for Goodness sake!"

Sam bata bi ta kanshi ba se Usman da take sake kokarin ɗagowa ta sa a bayan ta sede haki da take ya hanata, a haukace take a birkice.

Idanunshi da suke zube a kanta ya janye tare da mayarwa kan yaron within a second ya shaida shi, this is Usman Aisha's brother.

Da sauri ya karaso ya sa hannu ya ɗaga shi yana aikawa hidayat wani irin kallon takaici, what sort of parents does this children have! Yayi exclaiming a ranshi kan ya saka Usman a mota.

Da gudu ta zo ta shiga tana sake rukunkumeshi tana hakki da kuka at same time tana maganan da ita kanta bata san me take cewa ba.

Da wani kalar speed ya ja motar Dukda nashi matsalar da ta sha kanshi sede he can't leave them like that without help not for the sake of the mother or father but bcs of the loving children.

Wani asibitin kuɗi dake kusa yayi parking a take aka yi rushing Usman to Emergency, a jikin gini ya jingina tare da harɗe kafafu ya zubawa wuri guda idanu yana jin Hidayat dake going thou and fro tana gunjin kuka lokaci lokaci tana cewa

"Usman! Allah na banda su ya rabb"

Sun kusa one hour a haka ita bata zauna ba haka shima kaman be san da halittar mutum dake je ka ka dawo ba a wurin, ɗakin da aka shiga dashi ne ya buɗu likitan ya fito yana share gumi yace

"am sorry we cannot save him Jini yayi forcing kanshi to his brain wadda yayi ajalinshi, Allah ya gafarta masa ya baku ha..."

"Us..us..man ɗinaaa? A'aaaa A'aaaa ba shi ba dae! Ba shine bane! Dan Allah baze mutu yanzu ba..! Wayyoooo I can't, I cannot loose him! Yarona...."

Wani irin kukan da bata taɓa yi ba na tashin hankali take, he's just a little child yanzu ya fara rayuwa!

Sulalewa tayi kasa a sume, a take itama aka yi emergency da ita.

Moh Raed da ya runtse idanu tun jin rasuwar ya buɗe tare da bin gadon da aka wuce da ita da kallo, he's so heartbroken yana tuna sadda Usman yake ce mishi fuska cike da farin ciki cikin Salon maganan yara..

"Allah ya biya ka da gidan Aljanna yasa a mizani haka mama tace a cewa duk mutumin kirkin da yayi maka alkhairi.!"

Sake runtse idanu yayi yana tuna murmushin yaron, he can't imagine himself losing one of his child Norah or Farah.

Shi yayi komai har aka fiddo gawar Usman zuwa motan Ambulance, hidayat da wata nurse ta taimakawa ta fito ko tsayuwa bata iya yi ya kalla gabaɗaya ta firgice, kaman robot haka take tafiya.

Wayanshi da ya dauki ringing akallah na kusan shidda kenan ya kallah kan ya ɗaga a lokaci ɗaya ya lumshe kyawawan idanunshi yana sauraran faɗan da ake na mintuna kan ya saukar da wayan ba tare da ya ce komai ba, a Ambulance din hidayat ta zauna ya je motanshi ya dawo a kan cinyar ta ya ajiye envelope hakan ya sakata ɗago idanu.

Sarkewa idanunsu yayi cikin na juna a hankali ta sauke nata cikin muryar nan tashi me nauyi da be fita sossai yace

"May his gentle soul rest in Peace, he will be in a good place in shaa Allah"

Yana kai nan ya juya ya wuce, shi karan kanshi da sau ɗaya ya taɓa ganin Usman he felt the death bare mahaifiyarshi but, she's really too young for this.

Seda Ambulance ɗin ta fice a asibitin for some minutes kan ya iya tada motar shi ya fice da mugun gudu...

am in full tears😭😭😭🤧 kuyi hakuri gobe ba tabbacin Zaku samu sbd ina da abubuwan yi dayawa amma in na samu chance in shaa Allah Zaku jini

#like

#share

#comment

                    🖤Gureenjoh🖤