KOWA YA GA ZABUWA…

24

by @gureenjoh

KOWA YA GA ZABUWA...

   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.             

         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:

Zuhraa

Hamrah

Igiyar Rayuwa

Noor Iman

Ruwan Sama..

Lelewal

GAMON JINI paid

And Now

Kowa Ya ga zabuwa..

                      PAGE 24

FREE BOOK

Readers! Wai kuwa kun san magic ɗin dake cikin comment? Bari in baku wani takaitaccen labari, na tashi yau da ciwon kunne wadda rabona da in taɓa wayana ma tun 8am, se da karfe bakwai na dare ya buga nace bari in ɗan leka online tunda kunnena yayi sauƙi wallahi ban da niyyar typing yau, but to my biggest surprise se in na shiga nan in ga doguwar muhawara, in na shiga chan in kalli ruwan comments nace kai I cannot disappoint u guys dole in daure in baku page...! Wannan page ɗin naku ne masoya littafin kowa ya ga zabuwa😍🥰 one love

Shanyayyun idanunsa masu cike da kwarjini irin na cikakkun maza ya zuba mata na ƴan sakanni.

Se a sannan kuma ta fahimci irin katoɓarar da ta zabga sede Hausawa na cewa Magana zarar bunu... Kasa Kallonshi tayi tana jin yadda idanunshi ke ladabtar da ita yadda ya kamata.

A maimakon karatun Tsam ya miƙe ya fice daga wurin cikin salon takunshi, da kallo ta bi bayanshi har ya maida kofar ɗakin shi ya rufe..

A zabure ta mike tsaye ta koma tsakar parlorn tana zirga zirga, damuwa ta hango shimfiɗe a fuskanshi wadda ita a nata Tunanin damuwar ya ta'allaka ne da barin rayuwarsu da zata yi bayan sun fara sabawa da ita especially yaranshi, gabaɗaya ta rasa Tunanin da zata yi, da gaske tana jin hamza a zuciyarta kuma tana jin zata iya aurenshi.. Tana kuma son auren nashi ne ko ze samu natsuwa wurin fuskantar rayuwa guda ya dena raba hankalinshi saboda soyayyar ta.

Sede ita kanta in ta ɗaura Tunanin ya su Norah zasu yi se taji wani tashin hankali ya lallaɓo ya rufeta, kenan abunda ta fara ze zama a banza?

Alkawarinta da Daadida ze zama ta karya shi kenan?

Shi kuwa a nashi ɓangaren yana shiga ya zube bisa gado rigingine, da sauri sauri yake fitar da numfashi, ambaton Allah yayi tayi har ya soma jin zafin da zuciyarsa ke masa na raguwa,gabaɗaya iharin jikinsa ya mutu murus... Har abada baza'a taɓa jifan shi da kalamin da ya mishi zafi irin wannan ba kuma wadda ya rasa dalilin jin zafinta haka.

A iya tunaninshi bashi da wani businesses da ita banda kula da yaranshi se a yanzu da ta zaɓi gyara rayuwarsu da taimakon ubangiji zuwa hanya madaidaiciya, amma Sam be gane ba kuma girma da matsayin da wani sashe na zuciyarshi kuma ya bata ba.

Har lokacin magrib yana nan kwance a wurin kaman wadda aka sassara mishi gaɓoɓi, da sunan Allah ya miqe ya shiga toilet yayi alwala ya fito fuskanshi a dinke tsab, parlorn ya fita cikin I don't care manner ɗinshi na asali, duk sun yi alwala suna shirin sallah, ba tare da ya kalleta ba yayi gaba ya tada musu sallar.

Itama sau ɗaya ta kalli fuskanshi da ya koma mata sak na ranar da suka fara haɗuwa, bayan sun idar da sallah ya buɗe Alqur'ani ya cigaba da muraja'ar na baya.

Toh fah tun tana ɗaukan abun wasa se taga ya ɗau zafi sossai da ita kaman wacce aka ce ta zage shi ko wani abu, se kuma hakan ya sakata a damuwa rayuwarshi bata gama saituwar da tayi alkawari ba, har Hamza ya koma be sake gane mata ba.

Ranar da ya koma ba karamin daru suka kwasa da zainab ba wadda har ta kaisu gaban mahaifiyarshi dake goggo a gareta.

"Hamza Abunda zainab ta faɗa haka ne?" Ta faɗa tana Kallonshi.

"Eh hajiya, amma don Allah ki fahimce ni ba wai don cutar da zainab nake son shigo da Hidayat rayuwata ba, son ta ya samo asali ne daga tausayinta in bazaki manta ba a shekaru da dama su Abba ƙarami sun je nema min aurenta har sau uku a wurin marikinta.." Ya faɗa yana kallon Hajiyar cikin son tunatar da ita hidayat.

"Eh kwarai na gane, wacce ka ce tana zaune ne wurin marikinta kuma bata jin daaɗin rayuwar gidan, daga karshe kuma aka aura mata ɗan gidan ko?"

Ta faɗa tana mishi wani kallo.

Yace

"eh hajiya!"

Cikin tsananin masifa ta fara magana

"ban gane eh ba? Kana nufin ita zaka sake tura mahaifanka a tozarta su kaman yadda aka yi a baya? Marar tushe da asalin? Wacce dama tun a wanchan lokacin karfin ikon me mazari ne(kakanshi na wurin uba) yasa na zuba muku ido, Ko kana so ka ce zainab bata wadace ka as mace ba da har bata shekara ba kake maganan yayibo wani aure?"

"Hajiya uban goyon ta ya rasu, bata da kowa se Allah don Allah karki hanani aurenta"

Ya faɗa cikin roƙo.

"Dakata ma tukuna! Yanzu a Paris ɗin wurin wa take zaune?"

"Hajiya tana aiki ne na kula da yara waenda suka rasa mahaifiyarsu shine baban ya ɗauke ta aiki kuma tana karatu" ya faɗa da iyakar gaskiyar shi.

Wata doguwar salati hajiya ta ja ta sallame nan fa ta fara balbale shi da masifa akan wallahi ba'a zuri'ar ta ba, ƴar bariki dake zaman kanta Inaaa..

Duk yadda ya so ya fahimtar da ita ta kasa fahimta, Hajiya irin manyan matan nan ne en duniya waenda duniya kuma tayiwa daaɗi, bata da mutunci ko na sule biyar bata san wani abu wai shi kawaici ko kunya ba, bata da kirki in ka taɓa ta kaman yadda girman kai da izzarta ba ze bari ta rabi kowa ba barin ma idan talaka ne, shi kuwa yana jin ba ze iya rayuwa babu hidayat ba.

Daga karshe korarshi tayi, ɗakin Abban shi ya nufa ya same shi kwance jiya e yau, rufe yake da blanket fari, hancinshi abun oxygen ne ba uhm ba um um kuma yayi shekaru da dama a haka, idan jikin yayi tsanani se an saka mishi oxygen da abun abinci ta baki amma idan da sauƙi ya kan yi numfashi.

Hannunshi hamza ya riƙe ya ɗaura fuskanshi a kai se hawaye, yana son hidayat son da be sani ba seda hajiya ta fara nuna mishi turjiya akan aurenta, kaman fa baze iya rayuwa ba tare da Hidayat ba, kwarai in hajiya ta raba shi da ita kwananshi kirgaggu ne a duniya.

****

Tafiya yake kaman sabon kamun hauka wurjanjan, riga daban wando daban na yaɗi kodadde wadda ake kira wanke kuɗin ka, kayan da da in ya gani jikin Usman yake kyarar shi saboda kyamkyami se gashi yau na Usman ma yafi nashi kyaun tsabta da sabunta.

Daga kafaɗun a yayyage yayi baƙi gabaɗaya ya koɗe kaman ba Yusuf ɗan kwalisa ba, buhun karshe na dako da yake yanzu ya kai ya karɓi Naira ɗari ɗaya da aka bashi yana juyata..

Me ɗari zata mishi? Ba Wa shi kaɗai ba harda familyn shi da suke gida suke jiran ya kawo? Ba ga matarshi da yake ji kaman ya mata sujada ba, ba ga mahaifiyar shi da ƙannenshi ba.

Hanyar gidan ya kamo a rikicenshi in ya ga yaro tsaran Usman se ya ruga da gudu ya kama shi

"Usman! Usman!! Baka mutu ba ko? Yauwa zo muje gida ba zan kara dukan mamanka ba don Allah ka barni in sarara"

Wani lokacin idan abun ya Motso se an yi da gaske ake kwace yaro a hannunshi se yace Sam Usman ne ze kaiwa Hidayat shi saboda ya dena zuwar mishi a mafarki da zahiri.

Gida ne na laka cikin wata kwaraɓaɓɓiyar unguwa da kwata shine abu mafi rinjaye da yayiwa anguwan ƙawanya, kudaje kuma suka zama ma'abotan huldarsu, kutsa kai yayi ba tare da ya damu da yayi sallama ba.

Zaune yaga Kausar wacce itama ta zama wata jagwal, tana Haɗa abubuwan da take anfani dashi wurin toya doyanta na yamma..

Harara ya zabga mata ba wata wata itama ta rama.

"Ni kike Harara?"

"An harare ka ɗin, in ban harare ka ba wa kake so na harara? Wallahi in na ganka wani baƙin ciki da takaici nake ji kaman in kashe kaina, in banda wawanci irin naka da daƙiƙanci taya da degreen ka za'a damfare ka kudadenmu? Gashi ka mana sanadiyar baƙin talaucin da babu ranar fita daga cikinta.."

Yace yana harzukowa

"eh ai gwara ni da degree na ke fa? A sadda ake neman kiyi karatun ƙi kiyayi kika ce aure gashi yanzu uwar miji ta sakoki ba Chas ba ass se tallar doya"

"ahayyeee ai gwara ni ban zama malohuwa sokuwa ba, mace nake kuma ina amsa sunana wasu mazan da suka koma mata fa? Kai da kayi degreen da me ya anfana maka? Gaka nan marabinka da mahaukaci bin bola...!"

Ta kare tana buga kafa kasa cike da masifa, tsabar rama da talauci kana iya ganin ƙura na tashi in tayi wani jijjigan

"ni fa kun ishe ni Haba!"

Surayya dake fitowa daga fallen ɗakin dake gidan bayan wani me ciki da parlor ta faɗa tana saɓan mayafinta a kan igiya.. Tayi gaba

"yawon shashancin da aka saba, tsabar lalacewa ma wai a wurin masu shayi da layin ga ruwa ake ƙarewa"

Cewar Kausar again.

Surayya da har ta fita ta dawo tace

"ai gwara ni ina da abunda zan bayar ɗin in wata ta isa tayi mana..."

Harzukowa Kausar tayi sede tuni Surayya ta fice, Zasu cigaba daga inda suka tsaya da Yusuf umma ta fito sanye da wasu riga da zani da suka ji jiki ta kare kaman ba umma ba, zata yi magana wata sangamemiyar mata ta fito daga daki me ciki da parlorn tace

"kai ya isheka hakanan! Ina cefenen da na ce karka dawo gidan nan babu shi?"

Sosa kai yayi cikin wani irin ladabi yace

"Wallahi wallahi ba aiki yau dako nayi kuma shima ɗari ɗaya kawai na samo"

"kawo ka wuce ka koma...marar zuciya sususu"

Zuwa yayi ya miƙa mata ya juya ya fice.

Kallon tsakar gidan tayi tana kallon umma tace

"ya aka yi kwata kwata wurin ba'a kimtse ba?"

Umma tayi saurin cewa

"eh..eh dama yanzu ne za'a kimtsa..."

Fara tattare gidan tayi tana kallo Kausar ta gama Haɗa doyarta ta fita ko yanka ɗaya bata bar mata ba gashi tun safe babu abunda ya shiga cikinta.

Tunanin rayuwa ta faɗa..

Ashe haka hidayat ke ji a sadda suke azabtar da rayuwarta? Wani irin sakayyah ce wannan me muni? Tun bayan da ƙasa ya rufe idanun Abba ibtila'i yake sauko musu abu na karshe da tayi nadama shine korar kare da tayiwa hidayat da ɗanyen jariri.

Yadda hidayat ta sa kafa ta tsallake kaman ta tafi ne da duk wani sauran rayuwar da suke lallaɓawan, garin wawancin yusuf ya zube dukiyar su duka hannun rikakkun ƴan 419

Sun sayar da Motoci har biyu wurin bin polisawa ko za'a samu clue dukiyar su ta dawo sede a banza.

Bayan tafiyan hidayat Yusuf ya haɗu da wata mata, tunda ta ganshi taji shi take so kuskuren shi daya shine zina da ya fara da ita wadda shine makasudin rayuwar da suke ciki yanzu, saboda ana rade raden cewa muddin  ka kusanceta to zata mallake ka ne da abunda ke kewaye da kai har se in ita ta tafi da kanta amma baka isa guje mata ba.

A yadda yake a hauka hauka saboda kasa sukuni da mafarke mafarken Usman cikin mugun yanayi ta saka shi aurenta, ita ke tura shi ya sato abubuwa masu muhimmanci da su umma suna sayarwa kan umma ta farka wayam, kayan sawa ma be bari ba, karatun Surayya ya tsaya Chak hafiz ya ɓata ɓat kaman walkiya.

Har ta kai ta kawo gidan Abban ya fi karfinsu saboda suna zaune ne kaman a kango tunda gashi a cikin babban gida sede ba abinci, dalilin sayarwan kenan suka dawo suka saya wannan me saukin kuɗi a cikin irin wannan anguwa da da ko wucewa babu ɗayansu da ze iya yi.

Kausar ta gamu da sharrin uwar miji sanadiyar kaninshi da tayiwa ƙage akan ya neme ta wadda kashe ɗan uwanshi ne kawai mijintan be yi ba, daga nan uwar mijin ta sa mata karan zuƙa wata biyar tana gana mata kalolin matsaloli har asirin ta ya tonu kawai tana jin haushin cin arzikin ɗan uwanshi da yake yi ne, nan suka mata jina jina tayi tilis kan suka korota daga ita se kayan jikinta.

Daga karshe taje ta kwashe kayan ta sede a hankali suma aka sayar da komai chanjin ne har yanzu take Juyawa shima da tsiya tsiya.

Fahariyya kuwa mijinta aure yayi ya auro wacce ta maida ta bola, tana zaune ne kawai saboda tsoron irin rayuwar da ake a gidansu amma kwarai tana azabtuwa yadda ya kamata!

Matar Yusuf ba ginin da za'a taka a hau bace hakan yasa komai na gidan su suke yi, sau daya Kausar ta gwada Haɗa  ƙashi da ita Seda aka mata ɗauri, har yusuf ɗin in ta ganshi yana kallon wata haka zata saka shi a gaba ta zane tsab! Har Seda ya fara dana sanin zina a rayuwar shi.

Gabaɗaya rayuwarsu ta taɓarɓare wadda a shekarun baya ko a mafarki basu taɓa Tunanin kasancewa cikin irin wannan rayuwa ba.

(Ni ko nace ai wadda ya ƙi Sharan masallaci dole ze yi na kasuwa!)

PARIS

Zaune take riƙe da waya a kunne

"Daadida! Don Allah ki kwantar da hankalinki a bi komai a sannu, a gaskiya taɓon da Baba bukar yayiwa rayuwar yallaɓai me matukar girma ne wadda bana Tunanin ze gogu sede watakila idan addininshi yayi zurfi zuciyar musulunci tasa ya iya gyara alakarshi da Mahaifinshi, karki manta ba iyaye bane kaɗai ke da hakki a kan yara, ƴaƴa ma suna da hakki a kan iyaye.. Mu yi ta Adu'a Allah ya dubi lamarin se kiga komai ya zo ya wuce"

Daadida ta share hawayen fuskanta tace

"bana so in mutu in bar su haka Hidayat, kullum ƙara tsufa nake rayuwar bukar ta riga ta gama taɓarɓarewa saboda abunda ni na san hakki ne...! Ciki harda laifi mafi girma shine na saɓawa iyaye, A hakan ma kullum ina rokar mishi gafara sede Allah babu ruwanshi abunda kayi shi za'a maka... Jiya ya bar nan cikin tashin hankali saboda wani mummunar faɗa da Badi'ah da Zara suka yi wadda yayi sanadiyar jefa ƴaƴan su rijiya, ya ce kullum gidanshi kaman gidan kaji ko na ƴan dambe, ko allura ya ajiye za'a nema a rasa saboda sata gashi har yau bayan Raed be da wani ɗa namiji... Yara mata ne cikinsu babu abunda babu, har da ƴar daba wacce yace tayi ikirarin yanka wuyanshi ya sake ɗaga mata murya gidanshi kuma dole ta shiga... Hidayat abunda ya ɗaure min kai har yanzu be yarda hakki ne ke binshi ba ya kasa neman yafiyata ya nemi albarka... Ya kasa neman ɗan shi ya nemi ɗauki wani irin azabtar da kai ne wannan?"

Hawaye hidayat ta share tace

"Ki cigaba da Adu'a da sadaka Daadida in shaa Allah komai ze yi sauƙi... Watakila Allah ne ya ɓatar dashi ya kuma mantar dashi Tunanin da ya kamata yayi wurin gyaran kuskuren shi saboda ya girbi abunda ya shuka, muyi fata Allah ya tsayar dashi iya haka"

Dukda hidayat bata taɓa ganin Daadida ba sede akwai wani shakuwa da ya shiga tsakaninsu ta waya, saboda matsaloli Raed Dukda har yanzu ba shiga harkar ta yake kaman da farko ba, iyakar su karatu wadda yana gamawa ze fice,  ya fi maida hankalinshi kan sana'arshi yana kuma azabtar da kanshi da motsa jiki a ko wani lokaci.

Sallama suka yi da Daadida tana sauke wayan hamza na kira.

Ɗagawa tayi yace

"Hidayat da wa kike waya tun ɗazu layinki busy?"

"Da grandmother ɗin boss ɗina muna tattauna wani batu ne da ya shafe shi..!"

Ta faɗa kanta tsaye da iyakar gaskiyar ta.

A zafafe yace

"kina so ki kashe ni ne hidayat? Wallahi hangen kwanana nake kusa...! Rayuwata na shirin taɓarɓarewa na kiraki ko zan samu sanyi ta wurinki shine kike gayamin maganan wani boss?"

Dafe goshinta tayi tace

"ya ilahi! Ya Hamza wani furuci nayi da ze harzukaka haka? Tambaya ta kayi na kuma baka amsa.. Me ke faruwa ne?"

Runtse idanunshi yayi yace

"Hidayat hajiya ta ƙi tsayawa ta saurareni zainab ta rigani a wurinta, a sanina yadda hajiya ke so na a matsayin tilon ɗan ta komai nake so yi min take amma yanzu tana shirin juyamin baya"

"ya hamza ka san me ya fara burgeni da kai?" Ba tare da ta jira amsar shi ba ta cigaba.

"Kaifin basirarka da natsuwarka amma yanzu duk kana nema ka rasa, ni ba gudu zan yi ba ina nan ka bi komai a sannu har mu samu albarkarta kaji don Allah?"

"Hidayat companies ɗin Abba na na rawa wadda sanadiyar abubuwan dake faruwa dasu na bar aikin soja na dawo don in kula dasu amma na kasa focusing don Allah in zo a ɗaura mana aure daga baya se mu nemi yafiyar hajiyar ko zan samu in mai da hankalina kan abu guda.."

Kasake hidayat tayi, Wai me ke faruwa ne?.ta tambayi kanta.. Wani irin possession ne wannan?

(Nima nace ku tayani gani)

Don Allah wa ya san wani magani na ciwon kunne? Wallahi nayi yawon Asibiti na gaji

#like

#share

#comment

                  🖤Gureenjo🖤