Page 6
by @sanazty
WUTAR ƘAIƘAYI
Wattpad@SaNazdeeyah_
Arewabooks@sanazty
Facebook@SaNaz Deeyah
Youtube: ***
KARAMCI WRITERS ASSOCIATION
[karamci tushen mu'amula ta gari]
Book 1
```🆓Page 6```
"Aunty Sady indai ba korata kike daga gidanki ba to dan Allah kar ki takura kan lallai sai na faɗa miki ko wace ce, ni dai kawai ki tayani addu'a Allah ya sa na manta da ita."
"Shi kenan, Allah ya zaɓa mafi alkhairi"
"Amin ya rabbi."
Ya ɗan taɓa hira da ita kafin daga bisani bacci ya ɗauke sa, dan haka ta ƙara matsar masa da fanka sannan suka fita ita da Ihsan.
***** *****
"Gaskiya bai zo ba tun ɗazu ƙila dai ya yi amfani da sunana ya yi tafiyarsa wani wurin"
"To amma ina zai je bayan fama nake ya daina zaman kaɗaici amma yaƙi"
"To bara na kirawo Sadiya mu ji"
"Kina ganin zai je can kuwa?"
"Ba tabbas amma bari na tambaya."
Tana katsewa ta kira Sadiya.
"Yar halak yanzun nan Najma ta gama ce min wai yaushe zan kawo ta gidanki na ce mata ta bari sai weekend"
"Allah sarki, dan Allah ki kawo su tun friday"
"In sha Allah, ya kike ya gida"
"Lafiya lau, cewa na yi ko Faruq yazo gidan ki ɗazu?"
"Ai yana nan tun safe, yanzu haka ma bacci yake"
"A gidan na ki?"
"Wallahi kuwa, da alama yana da damuwa kuma baya samun isasshen bacci sai anan ne yanzu ya samu ya runtsa"
"Gaskiya na yi mamaki sosai, gidana ya ce zai taho fa"
"Aikam dai yana nan"
"To ba damuwa tunda mun san inda yake ai da sauƙi"
"Hakane"
"Bari na barki haka, zamuyi magana daga baya."
"To shi kenan."
Tana katsewa ta kira Mameey ta sanar da ita, sai a sannan hankalinta ya ɗan kwanta tunda an san inda yake.
*Bayan wata ɗaya*
Ta daɗe a gaban gadon da yake kwance kafin daga bisani ta samu ta zauna akan carpet dake shimfiɗe a ƙasa.
"Ni fa abin har ya fara bani tsoro, ciwo sai gaba yake kuma baya jin magani"
"To ina zai ji magani tunda babbar matsalar shi ne damuwa kuma yaƙi ya fitar da ita a ransa."
"Allah ya ba shi lafiya, Yazid ma ya ce idan ya taso daga kasuwa zai zo ya duba shi"
Saddiqa ta ce "Sadiya ni kin san me nake tunani?"
"A'a sai kin faɗa"
"Kamar damuwar Faruq akan so ne"
"So?"
"Ƙwarai kuwa, saboda idan kin lura sai ya zauna ya ƙurawa guri ɗaya ido, sannan Mameey da Surayya sun sha kama shi da hoto amma daya gansu sai ya ɓoye baya bari su gani"
"To a bincike ɗakin idan baya nan sai mu ga wace yarinya ce."
"Surry da Mameey ba irin laluben da basu yi idan baya nan amma basu gani, na 'yan gida kawai suke gani"
"Ya ilahi, to amma..." Wayar Saddiqa da ta fara ya saka Sadiya gintse sauran maganar.
"Hello Dee!"
"Har yanzu Mameeyn bata dawo ba"
"Ok. To ba damuwa bari na fito tunda Sadiya ma tana nan" Tana gama faɗa ta kalleta.
"Sadiya tunda Mameey har yanzu bata dawo ba bari na tashi na tafi gida na ɗora girki."
"To shi kenan sai kin dawo"
"Ok"
Tana fita Sadiya ta miƙe ta koma jikin gadon da Faruq ke kwance ta zauna gefen gadon ta ƙura masa ido.
"Allah ya baka wannan wadda kake so ɗin, wadda ka kasa faɗa mana ko da sunanta." Tana miƙewa taji ya riƙo hannunta, sai da ta ɗan tsorata dan batayi tunanin idanuwanshi biyu ba.
"Ki zauna a kusa dani kar ki tashi"
Zama tayi tana sake kallonsa, har a lokacin idanuwansa a rufe suke.
"Aunty Sady ai na faɗa miki ba za ta taɓa so na ba"
"Ka faɗa min ko wace ce ni na jarraba"
"Ba za ki iya convincing ɗinta ta so ni ba"
"Saboda me?"
"Saboda ta yi nisa a son wani, har ma an saka ranar aurenta"
"Duk da haka ka bani dama na jarraba..."
Bai bata amsa ba aka turo ƙofa, Mameey da Surayya ne.
"Aunty Sady kin ƙaraso kenan, ina wuni" Cewar Surayya.
"Lafiya lau Surry"
Ta kalli Mameey da ta ɗaga hankalinta ta ce "Ina wuni Mameey" Wani kallon banza ta watsa mata duk sai ta yi sanyi.
"Mene ya kawo ki nan?"
Furucin ya bala'in bata mamaki, ta ƙara jin ta yi sanyi dan ta yi tunanin Mameey ta huce.
"Magana fa nake miki" Ta daka mata tsawar da ba ita ba, hatta Surayya sai da ta tsorata, shi kuma Faruq a lokacin ya buɗe idanunsa.
"Mameey nazo duba Faruq ne"
"Tunda kin duba shi ai sai ki kama hanya ko"
"Mameey kiyi haƙuri"
"Ki riƙe haƙurinki ki tattara ki koma inda kika fito tunda kin yi dubiya.
Ba taji daɗi ba, kuma sam babu ƙwari haka ta ɗauki pause ɗinta ta fita daga asibitin.
Napep ɗin da ta tara kai tsaye gida ta ce ya kaita.
Tun daga nesa ta hango wata baƙar Benz sai sheƙi take. Mamaki sosai take dan ta san akaf 'yan uwan Yazid na kusa dai babu mai kalar motar nan da har zai kawo masa ziyara, bata dai sani ba ko 'yan uwa na nesa. Tana shiga Yazid ya ɗago ya kalleta tare da cewa "Yawwa ga ta ma ta dawo"
Kallon mata biyu dake zaune kan tabarma ta yi, gabaɗaya babu wadda ta sani a cikinsu, sai dai yadda taga ɗaya ta ƙura mata ido har sai da ta tsargu sosai.
"Mommyn Najma ki zauna mana, bari na samo masu lemo da ruwa, yanzu dama nake shirin kiranki domin sun ce min baƙin ki ne."
Mamaki da kuma damuwarta ta yi ƙoƙarin kawarwa wajen ƙirƙiro murmushin dole sannan ta zauna.
"Sannunku da zuwa"
"Yawwa sannu"
Yana ƙoƙarin fita ɗayar ta yi saurin cewa kar ka damu wallahi ba sai ka sayo mana komai ba, daga gida muke a ƙoshe muke"
"Ai ruwa da lemo ba dan yunwa ake shansu ba, kuma ku baƙin madam ne, so dole na girmama ku."
Daga haka ya fice, ita kuma ɗayar ta kalleta.
"Sunana Lawisa, na san baki sanni ba, wannan kuma abokiyar aikina ce sunanta Mansurah.
"Allah sarki sannunku da zuwa"
"Yawwa sannu"
Shiru ya ɗan biyo baya kafin daga bisani Lawisa ta ce "Dama nazo neman wata alfarma ne a gurinki"
"Alfarma kuma? Tame?"
Zama Lawisa ta gyara sannan ta fara da faɗin "Yayana ɗan jarida ne yana aiki da wani gidan radio acan garinmu Yola, mutum ne mai hazaƙa da kuma jajircewa, sai dai a shekara ta uku da fara aikinsa wata gagarumar matsala ta kunne kai, lokacin anyi zaɓe so gaskiya an ɗan rasa rayuka da dama, shi kuma sai ya nemi ya bankaɗo sirrikan wasu 'yan jarida wanda bai kai ga cimmasu ba suka ganoshi kuma suka haddasa masa hatsarin da har sai da ɗansa kwaya ɗaya tilo ya rasa rayuwarsa. Lokacin ana gab da aurensa dan a hanyarsu ta zuwa wajen bikin hatsarin ya faru, ita kuma wadda zai aura ɗin suka bita har garin nasu suka kasheta da bindiga suka harbeta"
"Subhanallahi" Sadiya ta furta tana ɗan dafe goshi.
"Amma idan na fahimta aure na biyu zai yi a lokacin?"
"E, saboda ai na faɗa miki yana da ɗa"
"Hakane! To Allah yajiƙansu da rahama ya sa can tafi musu nan"
"Amin ya rabbi."
Shigowar Yazid ne ya saka bata yi magana ba sai amsa sallamar da tayi tare da miƙewa ta karɓi ledar hannunsa, shi kuma ya shiga ɗaki. Kitchen ta shiga ta saka ruwa da lemo a plate sannan ta ɗauki cups ta fita, a gabansu ta ajiye tare da zama.
"Ina jinku, mene alaqata da labarin da kika bayar?"
"Alaqarki da labarin shi ne kamar da kuke yi da Nashwa"
"Nashwa!" Ta maimaita sunan.
"E, itace wadda aka kashe"
Zaro ido Sadiya tayi, ita kuma Lawisa ta janyo waya ta buɗe hotunan Nashwa tare da nunawa Sadiya. Karɓa ta yi tana kalla ɗaya bayan ɗaya, "Tabbas muna kama sosai, sai dai ni bani da ɓular hanci ai, kuma bani da fashin goshi"
Murmushi Lawisa ta yi sannan ta ce "Nima ba wai na ce kece Nashwa ba, na san Nashawa ta rasu, amma kamar da kike da ita yasa nazo gareki"
Miƙewa Sadiya ta yi cikin tashin hankali ta haɗe hannayenta. "Dan Allah ku rufa min asiri idan dan muna kama da ita ne wallahi bani da alaqa da ita, ban san Yola ba ban taɓa zuwa ba, ban san komai daga siyasar Yola ba, dan Allah karku kashe ni ina da yara ƙanana"
Cikin tashin hankali Yazid ya fito daga ɗaki jin abinda take faɗa, da sauri ta ƙarasa gabansa tare da riƙesa "Abban yara turo su aka yi, suna da alaqa da 'yan siyasar kuma ni ban san komai ba."
Lawisa da Mansura gabaɗaya suka miƙe tsaye.
"Ki fahimce mu, wallahi nazo ne onbehalf of my brother, he is in critical condition dan Allah ki saurareni, ni Likita ce bani da haɗi da siyasa, ta faɗa tana fito da ID card ɗin ta. A sanyaye suka zauna, Lawisa ta sake maimaita buƙatarta, sai a sannan Yazid ya ce "To yanzu mene abin yi? Sadiya matar aure ce, kuma kin tabbatar ba ita ce wadda kuke nema ba"
"Hakane kuma na san hoton Sadiya tun kafin Nashwa ta rasu, lokacin na saka hotonta a story na whatsapp sai wata ta ce min tana kama da ƙawarta har ta turo min hotonki"
"Wace ce?"
"Gaskiya ba zan faɗa miki ba, saboda na mata alkawarin ba zan yi haka"
Leɓe Sadiya ta cije sannan ta ce "Hmmm!"
"Sadiya dan Allah kiyi min taimakon nan, har yanzu Yaya ba sai Nashwa ta rasu ba"
"Ya kamata ku gaggauta faɗa masa saboda bani da alaqa da Yayanki kuma ni matar aure ce babu abin da zai sa naje ga Yayanki a matsayin wata wadda bani bace, dan Allah kiyi haƙuri " Tana gama faɗa ta miƙe da sauri ta shige ɗaki.
"Buƙatarku ba mai yuwuwa bace, ku yi haƙuri" Yazid ya faɗa yana miƙewa.
******* *******
Tana kwashe tuwo ya shigo gidan. "Yau tuwo ake mana kenan"
"E, amma fa saboda Faruq na yi dan na san yana son tuwo miyar egusi shi ne favorite ɗinsa."
Kujera ya ja ya zauna gabanta, tana zubawa yana ƙulle ledar.
"Sadiya nifa ina ji a jikina daga wannan shekarar wahalarmu ta ƙare"
"Allah yasa"
"Amin, amma shawararki ta noman attarahu da kuma gudunmawar kuɗi da kika bayar ina ji a jikina bana tarhu zai yi kyau kuma zamu samu alheri"
"Allah yasa"
"Amin Sadiya, gaskiya zai yi wuya a samu mace kamarki"
Murmushi ta yi sannan ta ce "Ai kai ma samun jajirtaccen namiji kamarka sai an tona"
"Sadiya"
"Na'am"
"Kina ganin idan naje duba Faruq ba za a samu matsala ba?"
"Ina fatan haka insha Allah"
"To Allah yasa"
"Amin"
*Asibiti*
Koda suka shiga ana ta yi masa faɗa baya son cin abinci. Sadiya ta gaida Mameey sannan ta ajiye ledar abinci, Yazid ma ya gaishe ta, sai dai yau anci sa'a ta amsa gaisuwar babu yabo babu fallasa. Saddiqa ta gaida shi sannan ya ƙarasa gaban gadon ya duba Faruq, bai ko zauna ba ya tafi, dama ba su taho da yara ba.
"Aunty Sady me kika kawo min?" Faruq ya tambaya yana kallonta.
"Tuwo ne, ko za ka ci yanzu na zuba maka? Dan Allah Faruq ka riƙa cin abinci, jinya ba zata yuwu babu abinci ba."
"Kema kya faɗa masa, kowa mitar da yake masa kenan amma ya yi kunnen uwar shegu damu."
"Zan ci!" Ya furta a sanyaye, murmushi Sadiya ta yi sannan ta miƙe ta zuba masa.
"Da kaina ma zan baka" Ta faɗa tana zama gefen gadon. Babu wanda baiyi mamakin yadda Sadiya ta lallaɓa shi ya ci tuwo da yawa, sannan aka ba shi yoghurt ya sha kaɗan.
"Dada ma tana tafe ai, bata ƙasar kuma wai ticket ya mata wahalar samu amma insha Allah zuwa next week za ta shigo Nigeria"
"Allah ya kaimu, ƙila ita zai faɗa mata abinda ke damunsa"
"Taɓ! To Allah ya sa"
"Amin."
***** ******
Cikin tashin hankali yake kallonsu. "Mommy amma meyasa baku faɗa min ba"
"Saboda baka cikin hayyacinka Affan"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, amma ita Nashwa mene lafinta da za su rabata da duniya"
"Tare kuka ga sirrinsu ka ga kuwa dole itama su yi tunanin za ta iya tona asirinsu"
"Mommy ni ina so na koma Yola ina so na fallasa wani sirri da zai girgiza al'umma"
"Kayi haƙuri Affan amma koda ka koma Yola babu wanda zai karɓeka, saboda zasuyi tunanin fatalwa ce"
Bai yi magana ba, sai dai yanayin fuskarsa kaɗai zai tabbatar maka da yana buƙatar ƙarin bayani amma bai samu ba sai ma cewa ta yi. "Anan zamu cigaba da rayuwa kuma za ka nemi aiki amma ba jarida ba domin ka gama aikin jarida." Tana gama maganar ta miƙe ta bar ɗakin.
Lawisa ta taso daga kan sofa ta koma gadon ta zauna a gefe.
"Yaya sai haƙuri amma abubuwa da yawa marassa daɗi sun faru, sannan kuma ina da wani albishir da zai saka ka farin ciki"
"Lawisa shi ke nan na rasa Nashwa?"
"Addu'a za mu cigaba da yi mata Allah ya gafarta mata ya san can tafi mata nan"
Idanuwansa tuni sun kaɗa sun yi jajir.
"Babu Nashwa sannan babu ɗana"
"Yaya ka yi haƙuri"
"Itama Badriyya an raba ni da ita"
"Na san ita kanta a duk inda take hankalinta yana gareka, kuma dole su neme mu su dawo maka da matarka tunda ba sakinta ka yi ba. Kuma ka san mene?"
"A'a sai kin faɗa"
"Na haɗu da mai kama da Nashwa sosai"
"Da gaske?"
"Wallahi da gaske nake kuma abin daɗi ma a garin nan take"
Miƙewa tsaye ya yi sai kuma ya koma ya zauna saboda jiri da ya ji.
"Lawisa tashi muje gareta babu mamaki Nashwa ta ce ta yi ɓadda kama."
"Yaya ba ita bace"
"Karki manta Nashwa marainiya ce, a gidan marayuwa ta girma kafin daga bisani wata mata ta ɗauketa, baki tunanin dama 'yan biyu ne?"
"Gaskiya ba twins bane, saboda ita wannan tana da dangi da kowa da marainiya ce ba za a ƙi faɗa mata ba."
"Lawisa akwai wanda suke riƙe yara kuma har yaran su koma ga Allah basu san cewa ba waɗannan ne asalin iyayensu ba"
Shiru ta yi sannan ta ce "Haka ne amma...."
"A'a Lawisa, koma dai mene ina son ganinta"
"Shi kenan"
"Ayau nake son na ganta"
"Yaya kayi haƙuri za ka ganta amma mu bi komai a sannu"
"Ban gane ba, ganinta wani big deal ne?"
"Sosai ma"
"Yi min bayani"
"Yaya just be calm please"
"Lawisa so kike ki sosa min rai?"
"Ba haka bane Yaya, amma ka san idan a haka ka je ba zata karɓeka ba, dole zamuje ka yi aski and kana buƙatar waya ma"
"Wannan duk zamu iya ayau kafin muje"
"Yamma tayi so dole mu bi komai step by step kuma Mommy ma bata sani ba har yanzu sannan kuma ba za ta taɓa yarda mu fita at this hour ba, ni kaina idan ba night duty nake ba bata yarda fa"
"It's ok Allah ya kaimu gobe"
"Amin ya rabbi."
****** ******
A bakin ƙofar ta gansu sun yi cirko-cirko, lokacin Surayya ta shigo dan har da ita ta gani. Gaban Saddiqa ta ƙarasa da ledar magunguna da ta tafi karɓowa ta kalleta "Lafiya kuwa?"
"Wai daga ɗan surutun da mukayi har jininsa ya hau, shi ne aka saka muka fito yanzu haka Likitoci biyu ne a ciki"
"Subhanallahi. To ai naga ba wata magana ya yi da yawa ba"
"Ke da kika san dama ba lafiya ne da shi ba, kuma fa abin har ya fara taɓa zuciyar shi"
"Gaskiya Faruq baya kyautawa, ya faɗa mana amma yaƙi faɗa mana ko wace ce bare mu san abin yi"
"Mun yi magana da shi jiya, yake ce min faɗar ma bata da amfani na takura masa shi ne yake cewa ai tayi aure"
"Matar aure?" Sadiya ta faɗa da mamaki.
"Yi ƙasa da murya kar Mameey ta ji, ya ce dan Allah kar na sanar mata"
"Tashin hankali" Ta furta tare da dafe goshi.
Fitowar likita ya saka suka yi shiru.
"Dr Allah ya sa dai jikin na shi da sauƙi"
"E, da sauƙi alhamdulillah, ina magungunan?"
Da sauri Sadiya ta miƙe ta ba shi sannan ta koma ta zauna.
Ya shiga ya ɗan juma a ciki sannan ya sake fitowa. "Wace ce Sadiya?"
"Ni ce" Ta furta tana miƙewa.
"To zo mana" Ya furta yana komawa ciki.
A sanyaye ta turo ƙofar yana zaune ma ya jingina bayanshi da bangon gadon.
"Wannan ce?" Dr ya tambaya yana nuna Sadiya, shi kuma Faruq ya gyaɗa kai.
"Sadiya bismilla zauna mana"
Zama ta yi sannan ta ce "Jikin na shi da sauƙi?"
"E, ku san haka"
Ɗayan Dr ya faɗa tare da jan kujera ya zauna gabanta.
"Sadiya ko?"
"E, ni ce"
Shiru ya yi sannan ya ce "Kin san kece sanadin ciwon ɗan uwanki?"
"Ni kuma? Meyasa na zama sanadi?"
"Saboda kece wadda yake so kuma ya kasa furta mata"
Cikin tsananin tashin hankali ta miƙe tsaye, ta kai dubanta ga Faruq ta ga ya sauke kai ƙasa.
Littafin nan na kuɗi ne tare da tagwayensa, zaku iya sayen ɗaya, biyu, uku ko kuma gabaɗaya huɗu, zaku iya biyan kuɗin karatu a yanzu domin ku samu damar shiga cikin group ɗin da za a riƙa yi muku posting.
VIP na littafin WUTAR ƘAIƘAYI ga wanda basu son shiga group za a tura masu ta PC a farashin ₦1000 a maimakon regular da yake ₦500 ga kuma yadda tsarin biya yake:
Guda 1: ₦500
Guda 2: ₦900
Guda 3: ₦1400
Guda 4: ₦ 1800
Za'a turo kuɗin ta wannan account.
Acct no: 6370370016
Acct name: Halima Salahu Adamu
Bank name: Fidelity Bank
Sai a yi screenshoot a turo shaidar biya ta wannan wannan number ***
Idan kuma VTU ne ko katin waya za'a turo ta wannan number ***.
Shaidar biya ta wannan wannan number ***
lLITTAFAN SUNE:
1-WUTAR ƘAIƘAYI
2-WA'ADI.
3-A CIKIN IDO..
4-TAZARAR SO
#FITATTUHUƊU2025
#WUTARƘAIƘAYI
#SaNaz_deeyah