🌻🌻MATSALAR GIDAN MIJI🌻🌻(GIDAN AURENA) BOOK 1.
page 16
🌻🌻MATSALAR GIDAN MIJI🌻🌻
(GIDAN AURENA)
STORY AND WRITTEN BY
GIMBIYA AYSHU💞💞💞
ELEGANT ONLINE WRITER'S📚
BOOK 1:CHAPTER 31&32
____________________________Mai ya shafa da sauri,ya shafa body roller,drawer shi ya bude ya dau wani jan riga mai gajeren hannu da wani black chinus jeans,kulle wannan bangaran yayi ya bude wani,boxer's da singlet ne kawai a nan,daukan wani jan boxer's yayi da farin singlet ya kulle wurin,cikin minti biyu ya gama shiri,comb ya dauka ya gyara gashin shi da sauri-sauri dan an fara kiran sallah,tulare ya dauka ya kara fesawa,daukan wayar shi dake bed side yayi ya nufi shoe track wani black Pam ya dauka ya fice daga dakin.
Hannu yasa zai bude kofa aka turo kofar,ji kake "gummmm!".
Jada baya yayi ya dafe goshin shi yana cizan lips yace"wai baki gani ne,sai kina yin abu babu natsuwa,haba dan Allah",ya karasa maganar shi yana jan gajeren tsaki.
"Am srry baby bansan kana wurin kofar ba",ta fada tana kokarin kwantowa a kirjin shi.
Tsaurin jada baya yayi yace"meh haka,ba kiga alamar masallaci zani ba,ko so kike ki karya min alwala".
"Ki tabbatar kinyi sallah kafin na dawo".
I da zumudin ta ta amsa mishi tana murna tace"zamu fita ne,
Harara ya dalla mata yace"sai zamu fita zance kiyi sallah"ya karasa maganar shi yana jan karamin tsaki.
Tayar da sallah da yaji an farayi a masallaci yasa shi yayi gaba ya barta nan ba tare da ya saurari mai take cewa ba.
Bayan kaman minti ashirin ya dawo.
Zaune ya tadda Jameela a parlor taci uban kwalliya kamar wacce za taje gasar kyau.
Tana ganin shi tace"yauwa na gama shiri kai nake jira tun dazu fahhh!",ta karasa maganar ta da dan shagwaba.
Dariya Jalal ya kwashe da shi ya fada kan kushin,nan ma bai mai ba ya fado kasa ya cigaba da kwasan dariya.
Sai da yayi mai isar shi sannan ya zauna ya jingina da kujera yana sauke ajiyar zuciya idan shi ya tara hawaye.
"Gaskiya kinyi kyau kin hadu sossai,anya tunda kike kin taba kyau kamar yau kuwa?",ya fada yana fashewa da dariya.
"Sossai Jameela ta cika tayi famm!,jira kawai take a tabata ta fashe".
Dakatar da dariyar da yake yayi yace"yauwa yanzu ki tashi ki rage kayan jikin ki sabida ki ji dadin aikin da za kiyi",ya fada yana kashe mata ido daya.
"Bangane mai kake cewa ba,naji kana maganar aiki,aiki kamar ya dai yi min bayani".
"Kamar dai yanda kikaji nace,ya fada yana gintse fuska kamar ba shi ya gama kwasar dariya yanzu ba".
"Nifa ban gane mai kake nufi da aiki ba fahhh!",ta karasa maganar ta a zafafe.
Wani irin mugun kallon ki shiga taitayin ki Jalal ya aika mata da shi yace"aikin da nake nufi shine yanzu ki tashi ki shiga kitchen ki dafa mana abinci mai rai da lafiya a kalla kala three(3) kuma ki tabbatar kinyi shi da kyau,kuma ko da wasa naci naji ba dadi sai kin sani,wlh za kiji a jikin ki".
Mikewa tayi tace"whattttttt!" da karaji,ni zanyi girki,akan meh zan shiga kitchen,mai anfanin masu aiki.
Wait wait wai!!!. Ina wannan yar kauyan yarinyar nan mai kama da ragon lay..........
"Ji kake fauuuuu! ya dauke ta da wani gigitatcan marin daya kaita zaune"
Dafe kuncin ta tayi tana kallan shi a razane tace"ni ka mara?".
Yatsa yasa ya nuna ta da shi yace"a ke na mara ko kina neman kari ne?".
"Yanzu akan yar iskan yarin".......
"Ji kake tasssssss! ya kara diban ta da wani mari ta hagu".
Hannu biyu tasa ta dafe kuncin ta da shi tace"yanzu akan wata ka mare ni?".
"Ehhh! na mare ki,ki kara fadar wani abinda bai dace ba ki gani",kuma kika kara maganar daya shafi wannan sai na antaya miki wani marin.
"Tasan halin shi sarai hakan yasa tayi shiru da bakin ta tana hawayen bakin ciki,wai akan mace,macen ma wata kazamar yarinya mara aji da class,wai akan ta mijinta ya mare ta".
Hmmmmm! wlh sai ta sani,mu zuba ni da ita.
"Katse mata tunanin da take yayi da fadin yanzu ki tashi ki shiga kitchen,kuma ko da wasa naji bakin ki sai kin sani".
Mikewa tayi sim-sim ta nufi kitchen dan tasan halin kayan ta,ba duka ba zagi amman zataji a jikin ta wanda gwara dukan ma a wurin ta.
Daura apron tayi ta fara girki,ba ita ta gama ba sai hudu saura.
Abinci kala uku tayi kamar yanda yace"shinkafa da stew yaji naman kaza zuka-zuka,tuwon semo da miyan taushe sai pounded yam da egusi soup yaji stock fish da naman rago.
Jera coolers din tayi akan dining ta koma ta wanke duk abinda ta bata.
"Tana kammalawa ta nufi upstairs gudu-gudu sauri-sauri sabida tsabar zafin dake addabar ta,ji take kamar an daura ta akan gas".
Kwance ta sami Jalal akan gado yayi ruf da ciki yana charting,dauke kai tayi kaman bata ganshi ba ta tube kayanta ta shige bayi.
Bayan kaman minti goma ta fito daure da towel.
"Mai ta shafa ta shirya cikin material na dogon riga ta danyi light make up".
"Kallan ta Jalal yake ta gefen ido,tsaftar ta da kwalliyar ta yana daya daga cikin abinda yake so a tare da ita".
Bayan ta gama ta feshe jikin ta da tulare,karasawa tayi kusa dashi ta zauna tace"Baby na gama",ta fada muryar ta a shagwabe.
Ajiye wayar yayi yace"sannu da aiki,ina fatan kinyi girkin da kyau?".
Girgiza mishi kai tayi alamun ehhhh!.
Murmushi yayi yace"yauwa Beauty na,kinyi kokari",yanzu ki tashi muje shakatawa.
Murmushi Jameela tayi tace"okh".
"Allah ya sani tana mutuwar san mijinta,bata son wani abu da zai raba su ko kadan,koya kankantar abin yake bata so".
Gyara zaman gyalan jikin ta tayi tace"Bby na gama".
Daukan car key yayi ya riko hannun ta suka fice daga dakin.
Haka ya rike mata hannu har wurin motar da zasu fita da shi,bude bangaran mai zaman banza yayi yace"ranki shi dade have ur seat"ya fada yana nuna mata kujerar.
"Murmushi Jameela tayi ta karasa ta zauna".
"Kulle kofar motar yayi ya zagaya driver seat ya zauna".tada motar yayi suka fice daga gidan bayan Baba ya bude musu gate.
Sai shida saura Mami ta dawo.
Tana tura kofar parlor straight dining ta kalla.
Murmushi Mami tayi tace"Allah ya taimake ki yarinya,da yau kin kwanan gidan ubanki".
Ba su suka dawo yawon shakatawar su ba sai bayan sallah magrib.
Ko da suka shigo babu kowa a parlor.
Dakin su Jameela ta nufa shi kum ya nufi na Mamin shi yayi sallama ya shiga bayan ta bashi izini.
Zama yayi kusa da ita yace"ina wuni Mamina,sannu da zuwa,ya Dada take da Mutanan gidan?".
Lfy su lau sunce ma na gaishe ka,Dada kuma tace"yaushe za kazo gaida ta,wai tunda kayi Aure ka manta da ita".
Dariya Jalal yayi yace"ayyyahhh Dadana zanje ko in gaishe ta jibi jum'atu babban rana".
Yauwa ina da magana da kai,yaushe zaka koma aiki,ko zaka ce min har yanzu baka gama hutu ba.
Murmushi Jalal yayi yana sosa kai yace"Mami ran Monday zan koma insha Allah".
"Toh shikenan Allah ya kaimu rai da lafiya,ina matar taka?".
"Ameen,tana daki za tazo ta gaishe ki".
Tabe baki Mami tayi tace"ni ba sai tazo bama".
"Murmushi kawai Jalal yayi bai ce komi ba".
*****MONDAY *****
Tun da Hauwa ta tashi sallah bata koma ba,bayan ta gama aikin daya kamata tayi wanka ta shirya tsaf.
"Shida da minti goma sha uku ta bar gidan,shida da talatin da biyu ta isa".
Bayan ta biya mai napep ta shigo gate,da Baba ta fara cin karo.
"Dukawa tayi har kasa ta gaida shi"
Amsawa Baba yayi da kulawa yana mata ya jiki tare da sa mata albarka.
Murmushi Hauwa tayi tace"jiki Alhmd Baba na warware sossai,ya gida ya kwana biyu da iyali".
"Alhmd lfy lau suke diyata,Allah ya kareki daga dukkan sharri".
"Ameeen Ameen Baba bari na shiga daga ciki",ta fada tana mikewa tsaye.
Shida da Minti Talatin Jalal ya bar gida bayan ya gama shiri hannun shi rike da jakan laptop....................................
By Gimbiya Ayshu💞💞💞.