CHAPTER 7
ALUURA TA TONO GARMA 7
Karaf! Asabe ta haɗa ido da Malam Hassan, ta sunkuyar da kanta ƙasa da sauri saboda wani irin kwarjini da ta ga ya yi mata. Cikin nutsuwa ya je ya samu wuri mai kyau ya zauna yana kallon shari'ar da Alƙali yake gudanarwa cikin nutsuwa. Ko kaɗan bai kalli inda su Asabe suke zaune ba, duk da ya lura hankalinsu gaba ɗaya yana kansa...
Suna nan zaune har aka yi shari'ar mutum biyar aka zo kansu, bayan magatakarda ya kira Asabe da Malam Hassan sun fito gaban kotu.
Sai Alƙali ya kalli Malam Hassan ya ce,
"Shin Malam Hassan ko ka san a kan wanne dalili matarka Asabe ta yi ƙararka a wannan kotu mai adalci?"
Malam Hassan ya girgiza da sauri ya ce,
"A'a Akramukallahu ban san dalilin da ya sa ta yi ƙara ta ba."
Alƙali ya ce, "Ta yi ƙararka ne a kan wata rana ka fita sana'arka ta adai-daita-sahu da daddare ka dawo da jaririya a hannunka, ka shaida musu cewa a adai-dai-sahunka uwarta ta bar maka ita.. Matarka Asabe ta nuna sam ba ta yarda da wannan maganar taka ba domin babu sha-sha-shar uwar da za ta iya tafiya ta manta ƴarta a abin hawa, kawai dai ka je ka yi zina da wata matar ta haife maka cikinka, ta kawo maka ƴarka ka rasa yadda za ka yi da ita, shi ya sa ka kawo ta gidanka ka faɗi wannan maganar don ka kare kanka, su yarda da abin da ka faɗi. An yi haka?"
Malam Hassan ya ce, "Tabbas an yi haka Akramukallahu! Amma ni tun da nake a rayuwata ban taɓa aikata zina ba, hasalima babu abin da na fi tsana a duniyar nan sama da zina. Ban taɓa sha'awar aikata ta ba, balle har na yi wa wata ciki..." Nan take ya faɗawa Alƙali duk yadda aka yi ya samu jaririyar, a ƙarshe ya ce idan ana so a tabbatar da abin da ya faɗa a kirawo DPO shi ma shaida ne a kan duk abin da ya faru game da jaririyar..."
Alƙali ya yi rubuce-rubucensa sannan ya ɗago ya kalli Malam Hassan da Asabe ya ce, "Kotu ta ɗage wannan shari'ar sai nan da sati biyu masu zuwa, kuma kotu za ta gayyato DPO domin ya bayar da cikakkiyar shaida a kan Malam Hassan...."
***
Da suka dawo gida hankalin Asabe ya tashi sosai, ta kasa tsugun ta kai gwauro ta kai mari ta rasa mafita, domin tana ji a jikinta indai aka gayyato DPO kotun nan to tabbas ƙaryarta ta ƙare domin zai faɗi gaskiya ne, kuma kotu za ta amfani da duk abin ya faɗa..
Tana nan zaune cikin ɗakinta ta rasa yadda za ta yi, can sai wata dabara ta faɗo mata cikin ranta ta ce, "Bari na je wajen ƙawata Rabi na san ba za ta rasa shawarar da za ta ba ni ba.."
Tana gama wannan zancen zucin ta ɗauki hijbinta da sauri ta nufi gidan Rabi.
"Kwata-kwata hankalint ya ƙi kwanciya, gani nake a wannan shari'ar mu za a kai ƙasa.."
Rabi ta ce, "Me ya sa ki ka ce haka?"
Asabe ta cire hijabin ta ajiye a kan gadon Rabi ta dube ta fuskarta ɗauke da tsantsar tashin hankali ta ce, "A jikina nake jin Malam ya fi mu gaskiya tsinto jaririyar nan ya yi, saboda har shaidu ne da shi a kan haka.. Mu wacce shaida za mu nuna a yarda cikin shege ya yi?"
Rabi ta yi murmushi ta dafa kafaɗar Asabe ta ce,
"Haba Asabe wallahi kin ba ni mamaki, gaba ɗaya kanki ba ya ja...wannan ƙaramin abun ya daina ɗaga miki hankali.."
Asabe ta ce, "Rabi dole hankalina ya tashi, tun jiya na kasa bacci tunanin mafita kawai nake amma na rasa, ba na so wannan shari'ar ta ka da mu, idan haka ya faru da wanne ido zan kalli Malam?"
Asabe ta ce, "Akwai mafita.."
"Wacce mafita ce?"
"Ƙwararren lauya za mu ɗauka, na tabbata ba zai ba mu kunya ba.."
Asabe ta yi shiru tana nazarin maganar cikin ƙwaƙwalwarta daga bisani ta dubi Rabi ta ce,
"Kuma kin zo da shawara mai kyau. Amma ta wacce hanya za mu samu lauyan cikin sauri kafin sati biyun?"
Rabi ta ce, "Ki bar komai a hannuna, ke dai kawai ki tanadi kuɗi masu kauri waɗanda za mu ba shi.."
"Indai kuɗi ne ba ni da matsalarsu, domin kuɗin gadona har yanzu suna nan a ajiye ban taɓa ba.."
"To shikenan ki kwantar da hankalinki, na yi miki alƙawarin lauyan da zan samo mana ba zai taɓa ba mu kunya ba.."
Asabe ta ji hankalinta ya kwanta sosai, ta yi wa Rabi godiya ta bar gidan ranta ya yi fes, ta samu nutsuwa.
Kwanci tashi babu wuya a wurin Allah ranar zaman kotun ta sake kewayowa, kowa ya hallara har da DPO da kotu ta gayyato shi ya zo ya bayar da shaida..
Wannan karon Malam Hassan tare da Hauwa'u da jaririyar suka zo kotun, bayan Alƙali ya shigo Lauyan su Asabe ya tashi tsaye ya yi gaisuwa ga Alƙali sannan ya ce, "Sunana Barrister Tahir. Ni ne lauyan Asabe.."
Bayan ya zauna Alƙali ya dubi Malam Hassan ya ce, "Kai ka samo lauya?"
Malam Hassan ya girgiza kai ya ce,
"A'a! Ni ban samo lauya ba."
Alƙali ya girgiza kai ya ce, "To za mu ba ka lauyan gwamnati idan kana buƙata."
Malam Hassan ya ce, "A'a! Nagode Akramukallahu ba na buƙata."
Sannan Alƙali ya buƙaci DPO ya fito gaban kotu ya bayar da cikakkiyar shaida a kan jaririyar da Malam Hassan ya ce an bar ta a cikin napep ɗinsa..
Da ƙwarin gwiwarsa ya fito ya tsaya a gaban kotu, sannan aka saka shi ya yi rantsuwar zai faɗi iyakar gaskiyar da ya sani... Alƙali ya buƙaci ya faɗi iyakar gaskiyarsa a kan jaririyar da Malam Hassan...
Nan take DPO ya yi bayani dalla-dalla kamar yadda Malam Hassan ya yi a ƙarshe ya ƙare da cewa,
"Har yanzu muna kan bincike, amma har zuwa yanzu ba mu gano inda matar take ba. Amma muna daɗa ci gaba da zurfafa bincike. Wannan jaririyar va ƴar Malam Hassan ba ce, tsintar ta ya yi ba cikin shege ya yi wa wata ta haif..."
Da sauri Asabe ta tashi tsaye kamar an tsikare ta, cikin ɗaga murya mai bayyanar da ɓacin rai ta ce,
"Wallahi kar ka yarda da wannan maganar ya maigirma mai shari'a, kawai Malam ya ba shi cin hanci ne don ya kare shi....
HUSSAIN YUSUF