PAGE 16
GANIN IDO 🥀🥀
ADABI WRITER'S ASSOCIATION
AMEENA IBRAHIM
OUM-AMEER
Wattpad:@Ummu-Ameer
ArewaPen:@Oumameer2671
FREE-BOOK
PAGE 16
A bakin titin da ta ajiyeni a nan na ci karo da Yaya Jafaru, jikin shi butu-butu da siminti da alama daga wurin aiki yake.
Shi kuma cike da nuna kulawa yana murmushi ya ce mini.
"Ah! Da alama dai tattaunawar ba mai jimawa ba ce naga har kin dawo."
Murmushin nima na mayar masa ina mai jinjina masa kaina na ce.
"Wallahi kuwa!"
"Miye tace miki? Allah yasa ba zancen komawa aikin ba ne? Naga Ammie ta ɗauki zafi sosai..."
"Hmm! Kai dai bari Ya Jafaru, wata magana ce kuma ta daban ta zo mini da ita..."
Maganar ta wa ce ta yanke jin wani uban horn da ake ta ruga mana tamkar mai motar zai bi ta kanmu ya wuce, hakan yasa ba shiri cike da hanzari muka yi gefe muna masu ƙure motar da kallo. Wani irin mummunan faɗuwar gaba ne na ji ya riskeni lokaci ɗaya bayan na yi tozali da mammalakin motar.
"Ohh! Wai Beenafah ce? Sannum ki"
Da ƙyar na iya ƙaƙalo kalmar Ina wuni daga can ƙasan maƙogwarona na jefa mishi wacce na san zan ɗauki tsawon lokaci ina jimami da baƙin cikin furta ta gareshi domin bai cancance ta ba.
Shi ma ɗin kallona ya yi da wani kalar murmushin mugunta a fuskar sa ya ce.
"Na ga kina mini wani kallo mai kama da harare ko? To ni dai ina fata baku ɓata mini gidana ba? Ya kamata ma na riƙa zuwa jewaya gaskiya."
Cikin nuna fusata Ya Jafaru ya kalle shi ya ce.
"Kai Malam lafiya? Miye haka?"
Wani kallon ya yi wa Ya Jafaru mai nuna alamun gargaɗi sannan ya ce.
"Kai kuma a suwa? Mts!"
Daga haka ya buga motar sa ya wuce.
Kallona Ya Jafaru ya yi fuska cike da alamar tambaya ya ce.
"And shi kuma wannan wane ne shi Beenafah?"
Wata irin nannauyar ajiyar zuciya na sauke a hankali na lumshe idanuna na buɗe su sannan ce.
"Wannan shi ne wanda ya bamu gidan sa yanzu haka muka muke zaune a kyauta..."
"To amma shi ne zai riƙa miki maganganu na cin fuska da tozarci?"
Murmushi na yi ina mai girgiza masa kaina na ce.
"Ba komai Ya Jafaru, wannan ni ba komai ba ne a wurina kada ka damu..."
"Beenafah!"
Ya Jafaru ya kirana sunana a hankali yana mai bina da ido tamkar yau ne ya fara ganina.
Kallonsa nake, nima idona a cikin nasa na ce.
"Na'am Ya Jafaru."
"Shin zan iya sanin su waye ku?"
Wani guntun murmushi ne ya suɓuce mini ba tare da na shirya ba na jinjina masa kai na na ce.
"Mu ɗin nan fa ba wasu bane Ya Jafaru, mahaifinmu ya rasu shekaru biyar da suka gabata, sai muka dawo hannun Wan mahaifinmu sai kuma daga baya ya koma Abuja ya bar mu a nan, daga nan kuma yasa aka koremu daga gidan nasa, sai wannan Uncle Isma'ilan da ka gani ya bamu gida muka zauna."
Cike da nuna tausayi a kalamansa ya ce.
" Allah sarki! Allah ya kyauta wannan zamanin da muke ciki. Muddin mutum ya rasa majingina shi ya rasa ba ruwan wani. Idan ana ganin idon wanda ake kunya sai a rasa ma ina za a aza da kai idan kuma ƙasa ta rufe mishi ido shikenan ka zama banza wanda bare ma sai ya fika muhimmanci.... "
Hanya na miƙa kawai na ci gaba da tafiya. Duk abin da Ya Jafarun ke faɗi ina ji amma na kasa amsa masa domin shirun shi ne yafiye mini alheri a yanzu. Wani gefen kuma; takaicin Uncle Isma'ila ne ya dabaibaye mini zuciyata, da a lokacin baya ne ko me zai yi ba zan iya buɗe bakina na gaishe da shi ba. To amma yanzu rayuwa ta ƙara yi mini wani karatun da na ɗauki darasi a cikin sa. Ba ko ina fushi yake yin tasiri ba da hawa dokin zuciya. Da ace a wannan ranar na yi haƙuri da abin da Muhsin ya yi mini kamar yanda na saba da yanzu Daddynsu bai kore ni ba, hakan ya koyar dani cewa ba ko'ina rashin haƙuri yake yin tasiri ba domin gashi na ƙare a matsala. Shiyasa na ɗaukarwa kaina alƙawarin zama mai haƙuri kamar yanda Allah da Manzon sa suka koyar cewa mu riƙa yin afuwa da haƙuri. Hakan yasa dole a yanzu na yi kasa da kaina kada na tunzura Uncle Isma'ila har ya kai ga korarmu kuma ba zan so hakan ba domin idan ya koremu ban san inda zamu nufa ba.
Muna kai wa ƙofar gida Ya Jafaru ya ce mini.
"Kinga bamu ko kai ga tattauna maganar da kuka yi da Hajiya Labiba ba wancan banzan ya zo ya ɓata komai."
"Ya Jafaru ba komai zamu yi shawara da Ammie."
"To ba matsala Allah yasa mu dace."
"Amin."
****
Gefen su Mummy kuwa, suna nan zaune suna ta cin duniyar su da tsinke yayin da arzikin bana ya ci uban na shekarun baya.
Aunty Aysha na gidan har yanzu domin ta ce babu inda za ta sai ta yi shekara ɗaya ta cire marmari da kewarsu da ta kwasa na tsawon lokaci. Dole haka Ahlan ya dawo Abuja ya gaishe da su Mummy Sannan ya juya ya koma London shi ka ɗai.
Ƙaninta Hafiz ma da ke karatu a Australia sau biyu yana dawowa gidan yana komawa. Ga abubuwan magana tana ganin su amma ba ta da ikon yi magana. Haka Hassana ke tara samari kala-kala da sunan ma su neman aurenta wanda har ga Allah ba ya yiwa Aunty Aysha daɗi ita da Husaina kawai dai ba su bakin magana.
Yau ma a fusace Daddy ya dawo gidan
Ya tara su a parlour har Mummy. Wuri ya samu ya zauna yana kallon Mummyn ya ce.
"Wai Hajiya Zaliha miye matsalar Hafiz ne? Na ce miye matsalar?"
Wani kallon ta yi mai tare da ɗan ƙara muskutawa kan kujerar kaɗan, ta ce.
"Kamar ya kenan?"
"Kin san komai Hajiya Zaliha! Dake da ɗan ki so kuke ku mayar dani shashasha! In ba shi ba karatu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa! Sai kuɗi nake tura masa amma ban san inda ya dosa ba, yaushe rabonsa da tura mini sakamakon jarabawarsu idan an fitar? Ni gaba ɗaya ban san ma a wanne aji yake ba kuma ban san semester ɗinda yake ciki ba..."
"Haba Alhaji! Ka fa san sha'anin karatun nan na zamani komai ya dawo na kuɗi..."
"Eh, ai ban musa miki wannan ba, amma ki tuna nima na yi karatun nan ba wai ban yi ba....Ya mayar dani wani hotiho miliyoyan kuɗi kawai yake karɓa to na mene ne?"
Daga haka ya miƙe yana ta wani huci ya fice ya bar musu parlourn.
Shiru ne ya ratsa tsakanin su tsawon lokaci wanda kowa da abin da yake saƙawa a cikin ransa musamman Mummy da ta yi zugum! Tana mai nutso cikin tunani. Daga ƙarshe dai ajiyar zuciya ta sauke ba tare da ta yi wa kowa magana ba ta ɗauko wayar ta kamo lambar Hafiz ɗin ta kira.
Sai da wayar ta yi ringing kusan sauka sannan daga ƙarshe ya ɗaga murya sa a ƙasa sosai ya ce.
"Mummy! Whatsap?"
Cikin nuna tsantsar ɓacin rai ta ce.
"Miye kake yi a yanzu na ji muryarka ta yi ƙasa?"
"Ni ɗin wai? Ba abin da nake sai bacci, bacci nake shiyasa."
Jinjina kai ta yi ta ce.
"OK. Ina so in tambayeka, Miye ka gayawa Alhaji?"
"Miye fa, kawai na tambaye shi 2M ne..."
"Wai Hafiz ina so ka faɗa mini miye kake da kuɗi haka?"
Wata dariyar baki san gari ba ya yi mata sannan daga ƙarshe ya ce.
"Mummy wannan wace kalar tambaya ce? Wanda ke karatu a Nigeria ya nemi kuɗi ballantana ni. Kawai dai kin san rayuwar komai ya dawo sai da kuɗi..."
"Ka shiga taitayinka ka ji na faɗa maka. Yanzu ya zo yana faɗa akan cewa bai san halin da karatunka yake ciki ba, saboda haka; ina so ka kira shi ka faɗa masa shekarar da kake da kuma semester ɗinda kake. Kasan halina Hafiz da abinda zan iya yi ba sai na faɗa maka ba."
Daga haka ta yanke kiran sannan ta mayarda wayarta ta ajiye, a hankali ta rausayar da kanta jikin kujerar tana mai ƙara shiga nazari.
Taɓe baki Hassana ta yi tana wani yatsina ta ce.
" Ni fa Mummy kawai ina ganin Daddy rigima yake ji. Idan ba shi ba miye abin tada jijiyar wuya saboda kawai Ya Hafiz ya tambayi 2M, Kuma dai yafi ƙarfin kuɗin nan ballantana ace..."
Kallonta Husaina ta yi ta ce.
"Hey! Ya kamata Ki fahimci magana kafin ki yi sharhi a kai. Don ya tambayi kuɗi ba laifi ya yi ba amma dai faɗan da shi Daddy yake yi shi ne; Wace Year yake? Sannan a wacce Semester yake."
Miƙewa Aunty Aysha ta yi tana faɗin.
"Allah ubangiji ya kyauta yasa mu dace."
Daga haka ta yi shigewarta ta bar su a nan wanda en biyu ne suka yi ta musayar kalamai yayin da Mummy ta yi musu tamkar ba ta wurin har sai da suka gaji don kansu suka watse suka barta ita kaɗai.
****
Ina shiga gida na tarar da Ammie zaune da kuular abincin Bahrain a gabanta tana zubawa za a kai mishi Islamiyya kasancewar yau Asabar ce.
"Wai har kin dawo?"
"Uhm! Na dawo Ammie.."
Na faɗa ina saƙale hijabina a igiya sannan na samu wuri daga gefen ta na zauna.
"To miye ta faɗa miki? Ina fata lafiya?"
Cike da fargabar rashin sanin amsar da za ta bani na kalle ta na ce.
"Wani zance ne dai makamancin wancan."
"Na me kenan?"
"Cewa ta yi wai na zo ta kai ni gidan iyayenta sai na ci gaba da aiki a can..."
Na ƙarashe maganar ina mai ƙure ta da kallo.
"To idan matar ta ci gaba da bibiyar ki fa? Ko kuma idan Mijinta ya ji ba kwa tunanin matsala? Kada ya zo ya gano watarana yasa a yi miki wulaƙanci..."
"Ammie gidan iyayenta fa na ce miki ba gidan ba.."
"Na sani..."
"Ammie Please kada ki hana dan Allah! Dama ce muka samu kada mu yi wasa da ita. Duk abin da ya faru tsakanina da Muhsin magana ta gaskiya ban taɓa sanar mata ba, na san da ace na faɗa mata tun farkon da ya fara shiga harkata da ta ɗauki mataki. Amma yanzu In Sha Allahu zan kula.. "
" To na ji! Amma su ɗin kin san waɗanne irin mutane ne?"
Girgiza kaina na yi na ce.
" Ban sani ba Ammie, amma dai ina kyautata musu zato. A lokacin da na fara zuwa gidan Aunty Labiba daga ni har ke bamu san wane kalar hali gareta ba, sai gashi ta yi mana kirkin da bamu tsammata ba. To Ammie Mace mai hali irin wannan ya kike tunanin gidan iyayenta ya kasance? Tarbiyya da hali mai kyau fa mafi yawan lokuta daga gidan iyaye yake farawa kamar yanda kika sha faɗa mini."
Matsawa na ƙara yi dab da ita ina mai kamo hannayenta duka biyu na jimƙe a nawa cikin ƙara tausasa murya na ce.
" Ammie! Na ƙara samun wani Ilmi da darasi daga abin da ya faru. In Sha Allahu yanzu zan kiyaye in ƙara yin taka-tsan-tsan fiye da baya."
Ta jima sosai tana nazari sannan daga ƙarshe ta shafe hawayen da suka silalo mata a hankali tana mai jinjina kanta ta ce.
" Ƙwarai kuwa Beenafah, Tarbiyya da hali na gari daga gida yake farawa, duk da cewa ni ban rayu da iyayena ba, ban san ma ya suke ba, ko a ina suke ban sani ba. Amma kuma Alhamdulillah ina alfahari da waɗanda suka raineni har na girma na kawo yanzu. Saboda haka na yarda na kuma amince ki je amma ki kula dan Allah."
" In sha Allahu Ammie. Na gode da yarda dani da kika yi, In Sha Allahu zan kiyaye."
Daga haka na miƙe na haɗa basket ɗin Bahrain na fito gida da nufin kai masa sai ga Yaya Hamza ya zo karɓa yace na koma gida, fita zai yi daga can zai biya ya ba shi.
Yinin ranar gaba ɗaya da tunanin Gidan su Aunty Labiba na yi shi, a raina ina ta saƙe-saƙen ko wane kalar gida ne oho! Har dai Ya Jafaru ya shigo muka ƙara tattaunawa da ni da shi da Ammie daga ƙarshe na ce ya kira mini ita in sanar mata. Ina gama yi mata bayani cikin farin ciki ta ce gobe da safe ƙarfe goma in jira ta in da ta ajiye ni ɗa zu, za ta zo ta ɗauke mu tafi.
Da dare ya yi ma haka na yi ta matse-matsen Ido amma kuma baccin sam ya ƙauracewa Idanuna. Tunani ne ya taru ya yi wa masarrafar tunanina rubdugu. 'Aunty Labiba ta kasance Mace mai matuƙar girma da daraja a gare ni, a gidanta ne na samu 'ƴancin kai wanda zan zauna in yi yanda nake so ba tare da nuna hantara ko ƙyama a gare ni ba, to amma yanzu ina zan dosa? Wane irin gida ne zan je? Su waye zan tarar? Wace kalar rayuwa masu aikatau ke gudanarwa a gidan? Shin akwai 'ƴan ci kamar gidan Aunty Labiba ko kuma gidan mulkin mallaka ne kamar na Mummy Zaliha?'
A haka dai na shafe tsayin dare ina tubka ina warwarewa har kusan Asuba. Da gari ya waye kuma tun da nayi sallah ban sake kwanciya bacci ba. Aikina na yi cikin lokaci kamar yanda na saba, komai sai da na kambala sannan na shirya na cewa Ammie zan shiga gidan Mamansu Fakiha na yi mata bayani sai ta isarwa da maman Abul.
Ina shiga gidan bayan mun gaisa na kalle ta na ce.
"Mama daman cewa na yi ki sanarwa da Maman Abul cewa daga yau na daina yin aiki a gidanta ta nemo wata domin na samu wani aikin wanda yafi na gidanta, aikin wannan watan da na yi mata kuma ta ƙiyasti ta biyani duk abin da tayi niyya..."
Dariyar Fakiha na jiyo a bayana tana faɗin.
" Gaskiya Beenafah in dai akan maganar kuɗi ce baki da wasa. Yanzu ma har aikin wannan watan duk da kin canza gida sai ta biya ki ba za ki yafe mata ba? "
Jinjina kaina na yi ina dariyar nima na ce.
" Eh, ba zan iya yafe mata ba gaskiya. Sana'a tafi maula, aiki na yi mata akan zata biyani, ba roƙonta na yi ba, saboda haka dole ta biyani ko aikin kwana ɗaya ne."
Kallona Maman ta su ta yi ta ce.
"Ƙyaleta Beenafah. In sha Allahu zan sanar mata kuma zan amso miki kuɗinki. Halan ina kika samu wani aikin?"
"Gidan iyayen Aunty Labibar ne."
"Eyyah! Allah sarki, wato dai duk tsawon lokacin nan bata manta dake ba tana can tana neman mafita. Allah ubangiji ya saka mata da mafificin alheri ya bada lada. Sai ki kula wannan karon Beenafah. Ki yi ta haƙuri ki kuma zama mai kauda kai ga wasu abubuwan. "
Jinjina kaina na yi cike da jin daɗin maganganun ta na ce.
" In sha Allahu Mama zan kiyaye na gode sosai, sai na dawo.... Bye Fakiha sai na dawo."
Na ƙarashe maganar ina mai ɗaga mata hannu na nufi ƙofa.
"To ya yi, sai kin dawo. Ni ma yanzu ai Islamiyya zan wuce duk da dai na buga uban latti yau."
****
Ban fi minti ashirin da tsayuwa ba sai ga ta tazo ta parker a gabana tare da buɗe mini gaban motar tace na shiga.
Ina shiga na kalle ta na ce.
" Ina kwana Aunty Labiba."
"Lafiya lau Beenafah....kin shirya?"
Kallon jikina na yi a ɗan kaikaice domin in ƙara tabbatarwa sannan daga ƙarshe na gyaɗa mata kaina na ce.
"Eh."
Murmushi kawai ta yi tare da jinjina kanta sannan ta tayar da motar muka fara tafiya.
Kallona tayi a kaikaice ta ce.
"Naga duk kin wani shige gashi Beenafah. Kada ki damu, gidanmu yafi gidana daɗin zama..."
Wani kallon na jefa mata ba tare da na shirya ba, jin wani labari mai kama da ƙanzon kurege. Ta ina gidan su zai fi mini gidanta? Abin da ma ba zai yiyu ba kenan duk da dai banje na gani ba.
Dariya ta yi tana mai jinjina mini kanta ta ce.
" Da gaske nake miki Beenafah, gidanmu yafi gidana domin ni daga ni sai ku, gidanmu kuma gidan mutane ne da yawa..."
Haka dai ta yi ta bani baki domin ta samu na kwantar da hankalina, amma kuma nima abin da yake raina daban.
Ina nan ina baza IDO tamkar wata baƙauyiya duk da ta wani fannin zan iya kiran kaina da hakan, har dai muka iso ƙofar wani katafaren gida abin da ake kira gida wanda masu tsaron ƙofar kaɗai sun isa su sa ka gane cewa ba a ƙaramin wuri kake ba. Bayan mai gadi ya wangale mana gate ɗin gidan mun shiga, nan na ƙara tabbatar da cewa lallai wata jar Miyar sai a maƙota. Duk yanda nake ganin girma da faɗin gidan Aunty Labiba da kuma gidan Daddy, wannan yaci uban na su nesa ba kusa ba. Domin dai it was masterpiece of class and elegance, gidan da duk hassadarka idan ka shigo shi sai ka tsaya kallon sa tsabar burgewa.
Gidan yana da manya-manyan gate guda uku, ɗayan shine gaba ɗaya mai kallon babban titi wanda through nan ake shigowa gidan, sai ɗayan kuma wanda sai ka ƙetareshi sannan zaka kai ga mutanen gidan sai na ukun wanda yake ta baya.
Wani daddaɗan ƙamshi ne ke tashi ta ko'ina na Imported roses and jasmine, ta dalilin flowers ɗinda aka shuka cikin harabar gidan wanda a cikinsu akwai na na'ura masu zaman kan su da suke bada ƙamshi na musamman tare da kaɗa iska mai ɗauke da ƙamshin turaren Oud.
Gidan gaba ɗaya kewaye yake da CCTV Cameras, smart lighting system, da Kuma automatic gate sensors Wanda Idan dare ya yi hasken gidan shi ke kunna kansa idan gari ya waye kuma ya kashe kansa.
A nan harabar first gate parking lot yake inda Aunty Labiba ta wuce kai tsaye ta yi parking. A farfajiyar parking lot ɗin kaɗai;ƙasan shi an yi shi ne da Italian interlock stones, ash and champagne gold, sai wani irin sheƙi suke tamkar glass aka shimfiɗa, Wanda a ƙarshen Layin ginin parking lot ɗin,akwai electric car charger Wanda aka saka don motar BMW i8 hybrid, Sannan akwai motion sensor camera mai lura da duk wanda ya shigo. Hakan kuwa nasan baya rasa nasaba da jibga-jibgan motocin da aka ajiye a harabar ajiye motocin wanda bahaushe ya ce tsaron kaya yafi ban cigiya. Sannan a bangon gefe kuma akwai garden lights da stone bench, inda yawanci suke shan coffee da safe Ko dare a duk sanda suka yi ra'ayi.
A farfajiyar gate na biyu kuma;akwai artificial fountain da ruwa ke ɓuɓɓuga sannu a hankali yana bada wani soothing sound gwanin burgewa.
A hankali nake bin bayanta tamkar wani raƙumi da akala har muka tsallako second gate inda yake ɗauke da manya-manyan mansion guda biyu, ɗaya flat ɗayan kuma Upstairs ne mai hawa uku, sai wa su ƙananun flat a can nesa da su. A hankali na ji na jefa ƙafata ƙasan polished marble tile ɗinda aka yi pathway zuwa main door ɗin babban flat Mansion ɗin Wanda kuma a gefe-gefe akwai automatic lamp posts masu haske da solar sensors suna tsaye a layi wanda suke kunna kansu da zarar hasken rana ya fara gushewa.
Muna jefa ƙafa cikin katafaren parlourn... Oh my God! Lokaci ɗaya naji bugawar zuciyata ya sauya, sanadiyyar wani irin sanyi da ƙamshin daɗinda suka buga ƙofofin hancina zuwa ƙwaƙwalwata. A ƙasan parlourn, Persian rug ne gold and brown yana wani irin sheƙi tamkar an shafe shi da mai. Ceiling ɗin saman ɗakin kuwa, Gypsum ne wanda aka zagaye shi da blue and white LED Light suna wani walƙiya suna shining tamkar taurari a sararin samaniya.
Italian Sofas ne jere a parlourn, beige and gold colour waɗanda aka ƙawata su da adon pillows manya-manya masu kyau da tsari. A tsakiyar parlourn, akwai crystal glass centre table Wanda a ciki akwai Dubai fresh flowers masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali.
Wani Babban photo frame ne jingine a bangon yamma na wani kyakkyawan matashi wanda ke sanye a cikin shigar kaki da ban san ko na miye ba. Sai kuma art painting daban masu kyau da ɗaukar ido na manyan masu kuɗi.
A gefe guda kuma, akwai 85-inc smart TV da home theater system daban.
Sai wani kewayayyen wuri wanda akwai mini coffee bar, Inda akwai Coffee machine da Turkish teapots, da Kuma flask masu kyaun gaske. Sai wani katafaren wurin Gym daban wanda babu abinda babu na motsa jiki.
Haka muka ratsa muka shige wani babban parlourn, sai dai shi wannan parlourn bai yi tarkacen wancan na farkon ba amma kuma akwai wani wuri da aka zagaye shi tamkar masallaci inda akwai wata ƙaramar show glass Mai ɗauke da kwalaben humra da kuma litattafan addini a jere wuri ɗaya, sai babbar prayer Mat da aka malale wurin da ita.
Wani haɗaɗɗen matashi ne muka tarar a parlour wanda ya so ya yi mini kama da Guy ɗinda muka baro frame ɗinsa a parlourn farko. Zaune yake tare da wata kyakkyawar Mace wacce ke zaune dab da shi a Kujera ɗaya. Ga abinci nan kala-kala tuttule a gabansu da alama wani bukin ake a gidan. Domin har fruit ga su nan kala-kala da kuma lemukan kwalba.
Murmushi suka sakarwa juna sannan namijin yace.
"Hajiya Aunty Labibatu..!"
Dariya tayi tana mai samun wuri ta zauna a wata kujerar ta ce.
"Ai kai ne Alhaji, ranka ya daɗe."
"Aunty Labiba Ina kwana?"
"Lafiya ƙalau Ziza, ya gidan? Ya jiki-jiki kuma?"
Ɗan sosa bayan ƙeyarsa yayi yana mai yiwa wadda aka kira Ziza wani kallo ya ce.
"Ku daina ce mata ya jikin nan please! Ziza ta hana mini zaman lafiya tun farkon samuwar cikin nan har yau...kullum yanzu ita bata son wannan abun, ita wannan abun take so, idan na dawo don na Huta to ba hutu nake ba because she's always suffering my life all over."
Dariya dukkan su suka fashe da ita sannan Aunty Labiba ta ce.
" Zamowa Baba is not easy at all! So you better shine your eyes. Dukkan iyaye a haka suka fara. Allah ya inganta ya saukar lafiya ya bada kuma rayayye mai albarka."
Ɗan yatsina fuska ya yi kamar wata Macce sannan ya ce.
"To amin, amma please, tell her to stop suffering me. Yanzu haka daga ANC muke, ko yanzu scanning ɗinda muka yi ya nuna akwai kusan two month ahead kafin haihuwar nan amma gata nan sai ta riƙa yin wani abu kamar yanzu za ta haihu..."
Wata dariyar suka sake kwashewa da ita sannan daga baya Ziza ta tsahirta tana mai riƙo hannun sa ta ce.
" Cool down Habibi nima fa ba laifina ba ne... "
Fisge hannun nashi ya yi yana mai canja kujera yace.
" Abeg leave my hand. Kullum ai haka kike cewa."
"To yanzu ni dai duk ba wannan ba. Ina Hajiya...?"
Ta yi tambayar tana mai kallo inda nake tsaye cike da mamaki tace.
"Aa! Wai daman baki zauna ba Beenafah? Dan Allah ki zauna mana."
A hankali na zame daga gefen kujerar da nake tsaye na zauna a ƙasa, Murya a ƙasa sosai na ce.
"Ina kwanan ku?"
"Lafiya."
Wacce aka kira da Ziza ta amsa tana mai bina da kallo yayin da shi kuma mijin nata bai amsa ba bai kuma kalle ni, ban sani ba ko bai ji ni bane oho!
"Ina Hajiya na ce?"
"Hajiya has a visitor fa, but ta ce tana zuwa yanzu."
Cewar Ziza tana mai ɗauke ƙafafunta a hankali ta ɗora su akan gefen kujerar da take zaune.
Fira suka ci gaba da yi sama-sama har lokacin da hajiyar ta fito sannan suka tsahirta, bayan sun gaisa nima na gaishe ta sannan daga baya Aunty Labiba ta kalleni ta ce.
"Hajiya, ga yarinyar da muka yi magana jiya a waya. Sunan ta Beenafah, za ta riƙa yin shara da goge-goge a gidan nan. Idan kinga aikin ya yi kaɗan su biyu, Munira za ta iya joining su Haula a kitchen, idan kuma ya yi miki, sai su riƙa yi a tare, ko kuma a juya mata zuwa wani aikin...."
Sai yanzu ya ajiye wayar hannun sa akan handle ɗin kujerar da yake zaune ya waro idanunsa a kaina ya kalle ni yana murmushi ya ce.
" Wow! Gaskiya Hajiya Labiba wannan kam ba 'ƴar aiki kika kawo ba, matar aure kika kawo min har gida"
✍️ OUM-AMEER ✍️