LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 2: A glimpse into Azrah's Life

by @hauwajaywrites

Tsane ruwan dake zuba daga kanta tayi, ta ɗaura ɗan karamin towel ɗinta sannan ta sanya hijab a jikinta, ta dauki shower gel ɗinta da shampoo dake kan tagar ban-ɗakin wanda ko plasta babu balle window, tura kofar ban-ɗakin tayi ta fito cikin ɗan matsakaicin compound ɗin nasu, Mama dake kwashe abincin talla tana zuba wa a cikin robar tallan ta ɗaga kai tana mata wani banzan kallo ta ce

"Ace yarinya ƴar gidan talakawa amma ki dage ke lallai sai da wannan sabulun turawan zakiyi wanka ke ga ƴar gold ko? Mu da muke wanka da Omo ai mutuwa muka yi"

A hankali ta buɗe baki ta ce

"Mama bani fah aka yi, bawai nace nafi karfin wanka da Omo bane" Mama ta bita da wani kallo ta ce

"Ai karya zan miki, ba abinda kika iya banda yawon iskanci, yo yawan iskanci mana wai ke gaki ƴar boko ko?"

Azrah ba tare da ta sake kallon direction ɗin Mama ba ta wuce zuwa ɗakin dake kusa dana Mama ta shige ciki

Umma ta ɗaga kai tana kallonta ta ce

"Sai dana ce miki ki daina fita da wannan sabulun ruwan amma baki ji" kallon Umma tayi cike da mamaki sai dai bata ce komai ba ta wuce daki direct dan sanya kaya

Bayan ta gama shafa lotion dinta ta dauki well ironed uniform dinta wanda daga gani kasan ya gama koɗewa ta sanya sannan ta fito rike da jakka a hannun ta, tana kallon Umma ta ce

"Ina Zahra Umma?"

"Na aike ta ta tsiyo sigari" Umma ta mayar mata da amsa

Ta ce "Toh Ni zan wuce makarantar kar na makkara" Umma ta ce

"Toh Allah ya bada sa'a Azrah, ki kula da kanki" ta gyaɗa mata kai daga haka ta nufi compound ta samu Mama da wata makwabciyar su da alama magana suke yi

Mama tayi wani murmushin takaici ta ce

"Wato ke Azrah baki da aiki sai zuwa makaranta saboda baki son aikin gida ko?"

Makwabciyar ta su wanda ake kira da Maman asabe ta ce

"Toh ai sai ku hana ta ai tunda bata isa ce muku A'a ba, dan Ni banga amfanin wani makarantar boko ba" Mama ta ce

"Yo dama me suke koya a makarantar idan banda iskanci? Nawa zaki ga yarinya wai ita boko daga karshe shikenan ta koma karuwar gari"

Tuni Azrah ta fita ba tare da ta sake waiwayosu ba ko tanka musu

Gidan su kawarta Fatima ta tsaya, tana sallama sai gata ta fito itama cikin shirin makaranta daga haka suka wuce zuwa makaranta

Bayan ta dawo daga School babu kowa compound ɗin su ta wuce dakin Ummanta ta shiga da sallama, Zahra dake jikin Umma tana cin abincin ta ɗaga kai tana kallon Azrah ta ce

"Sannu da zuwa Anty Azrah"

Azrah ta gyaɗa mata kai tana kallon Umma ta ce

"Barka da rana Umma" 

Umma ta ce "Yauwa Azrah, ya karatun?" Ta ce

"Alhamdulillah Umma" daga haka ta miƙe ta wuce ta shige dakin da yake nasu bata daɗe ba sai gata ta fito tana sanye da doguwar riga da hijabi Umma na kallon ta ta ce

"Ba zaki ci abinci bane zaki tafi?"

Azrah na Murmushi ta ce "A'a Umma nasan abincin ba yawa idan naje gidan Mummy ba zan rasa abin da zan ci ba, amma wannan na bar muku ke da Zahra"

Umma tayi shiru tana kallon 'yar nata cike da tausayi

Azrah ta yanke mata tunaninta ta ce

"Toh Umma na tafi" Umma ta gyaɗa mata kai ta ce

"Allah ya tsare" Zahra ta miƙe ta raka ta har bakin kofa sannan ta koma

Wani babban gidane wanda ya gaji da kyau a Barhim estate, dake jihar Katsina, a bakin gate ɗin tayi knocking mai gadi ya leƙo ganin ta ya wangale mata gate ɗin ta shiga tana mai gaishe sa ya amsa mata, daga haka ta nufi cikin entrance ɗin gidan, a balcony taga Ya saif na zaune

Ta ce "Ina wuni Ya saif"

Ko kallon ta bai yi ba balle tasa ran zai amsa mata kuma bata yi mamaki ba dan idan da sabo ta saba dama ba gaisuwar ta yake amsawa ba, tana shiga parlorn taga Mummy na zaune ga kuma Suhaila a gefen ta tana shan fruits, duk ɗaga kai suka yi suna kallon ta har ta karasa cikin parlorn ta duka jikin wani kujera ta ce

"Ina wuni Mummy"

Mummy da murmushi shinfiɗe a fuskar ta tace "Lafiya kalau Azrah, ya su Umman ki?" Ta ce

"Alhamdulillah" ta maida kallon ta ga Suhaila ta ce

"Ina wuni Anty Suhaila" itama da murmushi shinfiɗe a fuskarta ta ce

"Lafiya Azrah, kar dai yauma takowa kika yi da ƙafa?" Azrah murmushi kawai tayi, Suhail ta ce

"Ke baki ganin nisan unguwar taku ne? Ace tun daga Kofar Marusa har nan Barhim estate ki tako a ƙafa?" Azrah murmushi kawai tayi dan yanzu har ta daina ganin nisan

Mummy ta ce "Ai yabi jikinta ba zata iya dai nawa ba" Azrah ta miƙe ta fara tattara parlorn da ba wani datti sosai yayi ba tana gamawa ta wuce kitchen

Nan ma ta fara gyara kitchen ɗin bata dau lokaci ba ta gama sannan ta tara kayan wanke wanken a sink ta fara yi cikin kankanin lokaci ta gama ta daura abinci, Mummy ta shigo kitchen ɗin tana bi da kallon, ɗaya daga cikin abin da take son aikin Azrah kenan tana da tsafta yarinyar sannan bata da gandan aiki shiyasa kawai take managing duk da Azrah idan ana School ba da safe take zuwa ba, ta juyo tana kallon Mummy ta ce

"Mummy kina bukatar wani abun ne na kawo miki?" Mummy ta ce

"A'a yi aikin ki kawai, zan dauki abu ne" Azrah ta gyaɗa mata kai kawai ta cigaba da aikin gaban ta

Sai karfe biyar ta gama aikin gidan tass da abincin, ta duka a parlorn tana kallon Mummy ta ce

"Mummy zan tafi gida" Mummy ta ce

"Toh shikenan Azrah, sai gobe ko?" Ta gyaɗa mata kai, Suhaila ta ce

"Gashi nan dubu uku ne, kiyi using ma week din nan kina hawa keke ki daina wannan takowan da ƙafa dan Allah", Azrah ta sa hannu ta karɓa ta ce

"Nagode sosai Anty Suhaila, Allah ya biya ki da Aljanna" ta ce

"Is Okay Azrah, Amin thank you" daga haka Azrah ta bar parlorn

Suhaila ta kalli Mummy ta ce "Wallahi Mummy ina son ganin rayuwar yarinyar nan yayi kyau, Allah bata miji mai kuɗi da zai iya riƙe ta sakani da Allah" Mummy ta ce

"Wallahi Nima ina mata sha'awar gidan Hutu, gata da hankali ga kuma ilimi kamar wacca ba makarantar gomnati take ba" Suhaila ta ce

"Wallahi Nima ilimin ta dai mamaki yake bani, ga kyau kamar wacca ita tayi kanta, kwatakwata bata yi kama da 'yar gidan talakawa ba" Mummy ta ce

"Dan kawai naga Yayanki basu shiri ne amma da wallahi na masa maganar ya aure ta dan banga wani abu na qualities ɗin mace ace bata da shi ba" Suhaila ta ɗan yi frowning face ɗinta ta ce

"Shi ya sani, ai na taɓa masa maganar kamar wadda na kara masa tsanarta a zuciyar sa, wallahi duk macen da zai kawo dakyar ta wuce Azrah da wani quality ɗin wallahi"

Mummy ta miƙe tana hanyar bedroom ɗinta ta ce

"Zan gwada masa magana gaskiya idan har zai yarda" Suhaila ta ce

"Hmm" ta cigaba da danna wayan ta.

A gajiye Azrah ta isa gida, ta shiga dakin Umman su da sallama a bakin ta, Umma dake koyawa Zahra Tauhidi ta ɗaga kai tana kallon ta harta karasa cikin ta zauna tana sauke ajiyar zuciya dan ba karamin gajiya tayi ba, Zahra ta miƙe ta fita daga ɗakin, Azrah ta ce

"Barka da yamma Umma" Umma na kallon ƴar nata cike da tausayin wahalar da take sha ta ce

"Sannu Azrah, Allah miki Albarka ya baki future mai kyau wanda ba zaki sha wahala ba" Azrah ta ce

"Amin Umma"  Zahra ta shigo da ruwa a hannunta ta karasa inda Azrah ke zaune ta miƙa mata ta ce

"Gashi Anty Azrah" karɓa tayi tana faɗin

"Nagode Zahra"

Kafa kofin ruwan tayi a baki bayan ta sha ta sauke tana kallon Umman nasu ta miƙa mata kuɗin da Anty Suhaila ta bata

Umma ta ce "Kuɗin me kuma Azrah?"

Azrah ta ce "Anty Suhaila ce ta bani wai na daina tafiya da ƙafa shine da zan dawo naki hawan a daidaita nace sai a biya ma Zahra kudin Islamiyyanta sai ta koma ko?"

Umma na kallon ta hawaye yana cikowa daga idon ta dakyar ta maida sa dan bata son yaran nata su fahimci haka amma zuciyar ta cike take da tausayin irin wahalar da Azrah zake ciki ta ce

"A'a Azrah, gaskiya ne ki daina wannan takun kinga wajan da nisa sosai kawai ki ajiye tare da ke sai kina amfani da shi wajan tafiya ko?" Azrah ta girgiza mata kai ta ce

"A'a Umma, har dubu uku ne fah" ta zare dubu ɗaya ta miƙa ma Zahra ta ce

"Gashi gobe ki kai kudin makarantar ki saiki fara zuwa ko?" Zahra ta karɓa ta ce

"Nagode Anty Azrah, Allah ya mayar miki" Azrah ta harareta sai kuma ta mayar da kallon ta ga Umma ta ce

"Ina ga ba zan saka a asusu ba kawai zan nema abin da zan kara na sana'a ko Umma, sai wannan ya zama kamar naki ne" Umma tayi shiru tana kallon ta

Azrah ta mata murmushi ta kalli agogo ganin Magrib ya kusa yasa ta miƙe ta ce

"Bari nayi shara sai na ɗaura abincin dare" daga haka ta wuce cikin compound ɗin na su.

Da daddare bayan sallahn Isha'i sai ga Bappah ya shigo gidan Mama na zaune a tabarma tana lissafin Kuɗi, ga kuma Habiba da bata daɗe da dawowa daga talla ba, ganin Bappah yasa ta tura kuɗin kasanta tana "Sannu da zuwa Malam" Habiba ta ce

"Ina wuni Bappah" Bappah ya karasa ya zauna yana faɗin

"Fatsuma ba zaki daina tura yaran nan talla ba ne?" Tayi kicin kicin da Idanu ta ce

"Haba Malam, ina yanzu tallan ne ke rufa mana asiri, ina daga kai har matar ka duk da shi kuka dogara amma sai kana wani maganar kuma" wani kallo yake mata sai aka doka sallama daga bakin kofar, ya miƙe yana amsawa daga wajen mutumin ya ce

"An kawo gawayi ne, muna sauri zamu yi gaba" Bappah ya kalli Mama data taɓe fuska, sai ga Azrah ta fito Zahra na biye da ita a baya suka yi gate ɗin da sauri tana faɗin

"Ku shigo min da shi, gani zuwa"

Bayan ta karasa fita ta samu suna kokarin shiga da shi, matsa musu tayi har suka shigo mata da shi cikin compound ɗin ta irga kuɗin su ta miƙa masa, karɓa yayi ya irga ganin ya cika ya juya ya ce

"Toh sai da safe" sai sannan ta lura da Bappah dake tsakar gidan da murmushi a fuskarta ta ce

"Sannu da zuwa Bappah" Zahra ma ta juya tana gaishe sa.

Juye gawayin dukka tayi akan wani buhu ta shiga aikin kullawa a laida ita da Zahra, can Mama ta gagara hakuri ta fara masifa

"Gaskiya za'a daina kulla mana gawayi a gida, dubi yadda ake ɓata mana gida da gawayi"

Daga Azrah har Zahra ba wanda ya tanka ta

Suna aikin su cike da nishaɗi, can sai ga Siyama ta shigo tana waka da kayan tallah a hannunta, kamar wata ƴar tasha ta zuɓe akan tabarman tana faɗin

"Gaskiya yau nagaji Mama, dole gobe da safe ki barni nayi bacci gaskiya"

Mama ta ce "Dan uwarki tallan ma kice ba zaki ba daya fi miki" taɓe baki tayi tana kallon Habiba ta ce

"Ke tashi kije ki sako min abinci mana" Habiba ta ce

"Toh shine zaki wani cemin ke sai kace baki san sunana ba" ta karasa maganar cike ta tsiwa, Siyama ta sake baki tana kallon ta zata kai mata duka sai ga Bappah ya fito daga ban ɗakin hakan yasa ta miƙe zuwa ɗebowa da kanta tana faɗi

"Zan kama ki kuwa dan Uwarki"

Azrah har suka gama kulla gawayinsu ba tare da sun kalli direction dinsu ko kulasu ba

Tana shiga ta same Umma na zaune tana jan carɓi har sannan, Umma ta ɗaga kai tana kallon su ta ce

"Sannu da kokari, kuyi hakuri da rayuwar da kuke ciki yanzu, wata rana sai labari In Shaa Allah" Azrah taji hawaye na taruwa mata girgiza mata kai tayi ta ce

"Ki daina cewa haka dan Allah Umma, Ni buri na kawai ki samu lafiya ne" miƙewa tayi tana kallon Zarah ta ce

"Muje mu kwanta ko?" Zahra ta miƙe tana bin bayan ta suka wuce ɗakin su.

Kamar kullum Azrah ta gama duk wani aiki da tasan tana yi, ta kawo duk wani abu da Umma zata bukata ciki, kallon Zahra tayi wanda itama ta fito cikin shirin makaranta ta ce

"Dan Allah Zahra kuna tashi ki dawo gida kar ki tsaya a hanya saboda Umma ko?" Zahra ta gƴaɗa mata kai ta ce

"Toh Anty Azrah, ba zan tsaya ba" Ta na kallon Umma ta ce

"Umma Ni zan tafi, idan ana bukatar gawayi yana waje" Umma ta ce

"Toh Allah bada sa'a, Allah yayi muku Albarka" duk suka amsa da Amin sannan suka fita

Mama dake zaune tana abincin tallan ta ce

"Wallahi yau bari Bappahn naku ya dawo anjima, gaskiya ba waccan zata sake fita a gidan nan da sunan wai zata makaranta, dan Banga dalili ba ace sai nine zanna ciyar da ku" Gaishe ta suka yi, ta bi su da harara basu kuma bi ta kanta ba suka fita, Azrah ta kama hanyar makarantar su haka ma Zahra.

Mummy na kallon sa ta ce

"Magana fah nake maka Saif" Saif ya tamke fuskarsa jin maganar da Mummy ta gama dan ko kaɗan be kawo abinda zata ce masa ba, Suhaila dake danna wayanta ta ɗan saci kallon sa sai data kusan dariya dan ganin reaction ɗinsa, saidai ta ɗauke kanta ta cigaba da danna wayanta, Mummy ta ce

"It's Okay tunda ba zaka iya bani amsa ba, ka mayar dani banza ai" ya tsosa kansa ya ce

"Haba Mummy, how on earth zaki haɗani da wannan low class din, for that matter ma wannan teen ɗin" Sahulai bata san sanda ta fara dariya ba wani kallo ya wurga mata Mummy ta ce

"Ka dai bi duniya a sannu da hankali, dan naga kamar ka ɗauke ta da zafi nikuma dama shawara na kawo maka ganin yarinyar tana da hankali ga tsafta kuma kyakkyawa ce" taɓe bakin sa yayi ya miƙe ya bar parlorn, Suhaila ta ce

"Dan Allah Mummy karki sake ce masa komai, zamu ga kashen classic babe ɗin nasa ai"

"Hmmm" kawai Mummy ta iya cewa.

Yau ma kamar kullum, bayan ta dawo a makaranta ta gama shirin tafiya gidan Mummy ta fito tana sanye da Hijab ɗin ta, Zahra ta ce

"Anty yaushe zaki sake illoka? Kinga yadda ake tambaya a ajin mu kuwa?" Murmushi tayi ta ce

"Maybe idan na dawo yau, dan bana son kashe kuɗin" gƴaɗa mata kai tayi, mayar da kallonta ga Umma tayi ta ce

"Umma bari na tafi ko?" Ta ce

"Sai kin dawo, ki kula da hanya sannan ki kula da kanki dan Allah" kai ta gƴaɗa mata ta ce

"In Shaa Allah Umma" Umma tana miƙa mata ɗari biyu ta ce

"Gashi wannan ki hau abin hawa tunda Kinga jiya sunyi magana" Jim kaɗan tayi tana kallon Umma sai kuma ta miƙe tana faɗin

"A'a rike kuɗin ki Umma, akwai ɗari biyu a waje na" daga haka ta musu sallama ta fito ɗan karamar tsakar gidan na su, sai da gabanta ya faɗi kallon step bro ɗinta Abdul dake tsaye a kofar Mama yana binta da wani mayen kallo, tunda ta Kalle sa sau ɗaya ta ɗauke kai dan bata kuma bukatar ta sake haɗa ido da shi, sai data zo fita ba tare da ta Kalle direction ɗinsa ba ta ce

"Ina wuni" bata jira amsar sa ba tayi fice warta, wani a daidaita data gani yazo zai wuce tayi saurin taran sa da faɗa masa inda zai kaita dan ta gama tsorata da Abdul dukda bata yi niyyar tafiya da keke ba

#Jiddatulkhayr

***