LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 3: Ghetto, But not broken

by @hauwajaywrites

Knocking babban gate ɗin tayi, gatekeeper ya leƙo ganin ta yasa ya buɗe mata, ta shiga tana

"Ina wuni Baba" ya ce

"Lafiya lau Azrah" daga haka ta shige

A daidai kofar shiga parlorn taci karo da Saif da shima yake ƙoƙarin fita daga parlorn littattafan hannunsa yayi watsi a ƙasa, da sauri taja baya tana zara ido dan bata san yana fitowa ba, ganin papers ɗinsa a kasa yasa da sauri ta duka ƙasa tana faɗi

"Dan girman Allah kayi hakuri Ya saif, wallahi ban sani bane"

Shi kam Saif with shock har sannan yake kallonta har ta gama tattara masa sannan ta miƙe cike da ladabi ta miƙa masa ganin bai karɓa ba yasa ta ɗaga kanta for the first time bayan incident ɗinsu ta Kalle sa, ganin wani irin kallo da yake mata yasa ta sake furta

"Dan Allah kayi hakuri, wallahi bansan kana fitowa bane" cike da izza sannan da tsansan kyama ya ce

"Are you doing this just to seek attention? So, ki cire ranki idan har wannan ne ke knocking a kwakwalwar ki, saboda ba zan taɓa cewa ina sonki ba, Stupid" ya ciro Handkerchief a aljihun sa sannan yayi wrapping hannunsa kafin ya karɓi papers da take miƙa masa ya bar wajan

Azrah tafi minti 2 kamar tana processing maganar sa, sai kuma ta juya ta bi inda ya bi da kallo sannan ta harare wajan sai yanzu maganarsa yake jiƙa mata dan ita ko kaɗan yadda ya nuna kyamarsa gareta bata damu ba ɗan karamin tsaki ta'ja sannan ta karasa cikin parlorn da sallama Suhaila ta gani zaune tana danna system ɗinta da murmushi a fuskarta ta karasa ciki ta duka ta ce

"Barka da warhaka Anty" sai sannan Suhaila ta ɗaga kanta tana kallon ta amma har sannan wannan murmushin beyi fading daga fuskarta ba ta ce

"Sannu Azrah, ya hanya da su Umma kuma?" A hankali ta ce

"Lafiya klau, duk Alhamdu Lillah" Suhaila ta ce

"Ma Shaa Allah" Azrah zata miƙe Suhaila tayi saurin cewa

"Wait.. ke da waye ne? naji kina bada hakuri?" Azrah ta Kalle ta sai kuma ta ce

"Ya Saif ne, ban sani bane na buge sa" Suhaila ta jinjina kai daga haka Azrah ta wuce kitchen dan ganin aikin da zata fara Suhaila ta bita da kallo tana cigaba da murmushi dan tasan dole Saif zai ɗauka da wata manufa tunda ɗazu Mummy ta gama masa maganar Azrahn.

Har Azrah ta gama aikinta tana jinta moody kuma tasan definitely abinda ya faru tsakanin ta da Ya Saifuddeen ne ya canza mata yanayi haka ta karasa aikinta sannan ba tare da walwala ba, bayan ta fito daga kitchen yayi daidai da shigowar Mummy, Azrah ta karasa tana karɓan kayan hannun Mummy meanwhile tana gaishe ta, Mummy ta amsa da fara'arta tana tambayar ta ya aiki.

Bayan ta gama ajesu a position ɗinsu ta koma parlorn tana kallon Mummy ta ce

"Mummy zan wuce gida" Mummy ta ce

"Miƙomin wayata akan Centre table na kira Suhaila ta kaiki naga garin da hadari sosai ne" Azrah ta wuce inda wayar Mummy yake ta ɗauka ta kai mata, Mummy na karɓa tayi dialing numbern Suhaila tana ɗauka ta faɗa mata tana neman ta a parlorn, ba'a ɗau lokaci ba sai ga Suhaila ta fito daga ɗakinta tana kallon Mummy ta ce

"Gani Mummy" Mummy ta ce

"Dama wai ko zaki kai Azrah gida ne naga garin da hadari" Suhaila tayi shiru ta ce

"Why not Yaya Deen Mummy? Kar na fita kuma ruwa ya sauko kuma Kinsan jikina baya son sanyi" Mummy ta ce

"Eh kuma fah haka ne" tun kafin ta karasa rufe baki Azrah ta katse ta da

"Mummy ina fita zan samu abin hawa Karki damu" Mummy ta ce

"Toh shikenan, Allah ya tsare" da Amin ta amsa sannan ta musu sallama ta fita.

Kura ake yi ga garin ya fara duhu sakamakon hadarin, a haka ta dinga tafiya tsoron kar ayi ruwa yasa kawai ta tsare keke ta shiga, tana isa unguwarsu ta samu already su har an idar da ruwan da aka musu, ta shiga cikin gidan nasu babu kowa a sakar gidan haka yasa ta wuce ɗakin Ummanta kawai, da sallama ta shiga ta samu Ummar na kwance Zahra na zaune gefen ta tana karatu da sauri ta karasa ciki tana faɗin

"Umma baki da lafiya ne?" Murmushi kawai ta mata ta ce

"A'a Azrah, kawai dai mura ne yake damuna Maybe saboda ruwan da akayi ne" Ayrah na kallon Zahra ta ce

"Zahra ko zaki tsiro mata magani ne?"

Zahra ta ajiye littafinta a gefe ta miƙe zata zo karɓa kuɗin sai kuma Ayrah ta ce

"Barshi ma kawai bari naje da kaina dama ranan da na tsiyama Umma magani ina binsa canci" Umma ta ɗaga kai tana kallon Azrah da har ta miƙe ta ce

"A'a Azrah ke da ko hutawa baki yi ba kuma ace zaki sake fita? Ki bari nace miki sanyin garin ne ya sake tado min da muran' Ayrah bata ji zata iya ba gaskiya kallon Umma kawai take yi.

Tunda hanya ta biyo da su wani ghetto area dake Kofar Marusa yake ta masifa yadda kasan wanda ke driving ɗin ne ya lalata hanyar can wanda ke driving ya ɗan juya ya Kalle sa ya ce

"Dan Allah Karka isheni da jarabarka, sai kace Ni na ɓata hanyar"

Sadeeq a ƙufule ya ce "Amma kuma ai kaika biyu da mu hanyar ko? Babu wani hanyar da zamu bi ne sai wannan for that matter?"

Sagir ya ce "Enough please, Ina kace kana sauri shi yasa na biyu da kai ta shortcut amma ji yadda kake ɗaga jijiyan wuya sai kace wanda na maka laifi" tsaki Sadeeq yaja ganin yadda motar nasu ke wani hawa da sauka suna wani rawa a motar sabar yadda suke bin ɓacaccen hanyar, can motar su ta kafe taƙi tafiya, Sagir ya juya yana kallon Sadeeq ya ce

"What is it?" Wani banzan kallon Sadeeq yama Sagir jin banzan tambayar da yake masa

Sagir yayi murmushi ya ce

"Ina ji motar gaskiya ba zata iya tafiya ba sai mun sauka a ga menene ne"

Sadeeq yayi humming kawai ba tare da ya Kalle Sagir ba sai ma danna wayan sa da yake yi, ganin haka yasa Sagir shima ƙwafa ya gƴara zaman sa a motar ya ciro wayansa yana ayyana a ransa yau zai gwada ma Sadeeq bashi kaɗai keda miskilanci da izza ba, they were like that for almost 10 mins

Can Sadeeq ya ɗaga kansa yana kallon Sagir ya ce

"Let me have the key tunda baka ga damar kaimu ba" Sagir ya masa wani kallo yana danne dariyarsa ya ce

"So, dama ka iya magana ne? Lokacin da nake tambayen ka ya zamu yi ai shareni kayi" ɗan kallon sa Sadeeq yayi ya ɗauke kai, jin ana shirin tada sallahr Magrib yasa ya Kalle Sagir ya ce

"Idan zaka iya sauka muje muyi sallah sai mu san matsalar motar toh" daga haka ya buɗe kofar ya fita ba tare da ya san ko Sagir ɗin zai sauko ba, Chemist dake gabansu ya nufa dan tsiya musu pure water da zasu yi alwala dan they're not sure ko masallacin da ruwa.

Azrah tafiyanta take a hankali tana bitan haddan da zata bada ran Saturday, hanyan Chemist ɗin ta nufa dan tsiyama Umma magani, gaba ɗaya she's out of thoughts dan can kasan zuciyarta tana tuna mata next year zata shiga SS3 ya zata yi idan kudin WAEC da NECO ɗinta bai cika ba, wani mota ne da yayi kanta horn ɗin da ya danna ne yasa ta yin tsalle dan kaucewa motar saidai ta faɗa cikin wani ruwa da-ya taru a kasa sakamakon ruwan saman da aka musu, ruwan yayi salle ya fesu a jikin Sagir, da sauri ya ja baya yana me buɗe baki yana kallon ta da mamaki ganin yadda ta ɓata masa kaya, Sadeeq ya taɓe baki ya ce

"This is just a glimpse of what the ghetto girls do, that’s why I hate interacting with them" (wannan kaɗan daga cikin abinda ƴan matan ghetto zasu maka kenan, shiyasa na tsani abinda zai haɗani da su kenan)

Azrah ta ɗaga kai tana kallonsa cike da ɓacin rai, dan ba kaɗan ba maganganun sa sun daketa ta ce

"Wait... Don't insult anyone, because not everyone would do such a thing, Poverty is not madness pls, Even me, it was a mistake and I only did it to save life not intentionally, Be guided, please"(Dakata... Kada ka zagi mutumin da baka sani ba, domin ba kowa ne zai aikata irin hakan ba, Dan talauci ba hauka bane, don Allah, Ni ma kuskure ne kawai nayi, kuma nayi shi ne don ceton raina ba da gangan ba, kasan me zaka faɗa gaba) sai kuma ta kalli Sagir dake tsaye shock clearly written all over his face ta ce

"Dan Allah kayi hakuri, bansani bane nayi hakan ne danna kaucewa motar ne" kai kawai ya gƴaɗa mata dan ya rasa ma me zai ce sai kuma ya kalli Sadeeq wanda yake tsaye har sannan shock dinta bai barsa ba ya kyalkyale da dariya ya ce

"Be guided please" sai kuma ya sake kwashewa da dariya, Sadeeq ya tamke fuskarsa ko alamar wasa bai bari ba, yana kallon mai shagon ya ce

"Ka bamu ruwan mana kar sallah ya barmu" Mai shagon da shima dramar su ya masa daɗi dukda cewa shi ma kame-kamen turancin yake amma saf ya fahimci duk abinda ke faruwa kuma yaji daɗin amsar da ta mayar masa ya ce

"Ai ranka shi daɗe kaff unguwar nan babu wanda ya kai yarinyar nan ilimi da iya turanci dukda a makarantar gwamnati take amma wallahi daban take, kar kayi mamaki dan kaga ta mayar maka amsan da Turanci" Sadeeq ya juya zai bar wajan mai Chemist ɗin yayi saurin cewa

"Yi hakuri Alhaji, ga ruwan abin duk bai kai ga haka ba" Har sannan Sagir bai daina dariya ba dan shima bai ɗauka tana jin turanci har haka ba, dukda ma shi akama laifi amma shi yanzu incident ɗin dariya yake basa ya sake kallon Azrah sannan yayi wajan mai Chemist ɗin ya karɓi ruwan yabi bayan Sadeeq da sauri dan ganin har an kusan ruku'u.

Azrah ta karasa wajan mai Chemist ta ce

"Maganin mura zaka ɓani da canci na da nake binka kwanaki" yana kallonta ya ce

"Nawa ne ma? Sannan wani irin maganin mura?".

A hanyar su ta komawa gida duk kalan masifan da Sadeeq yake ma Sagir akan yadda ya dinga ɓare baki yana dariya kamar wawa shine yafi bashi takaice, yana masa fighting right dinsa amma jibi yadda at long last ya basa kunya

Sagir ya ce "Like seriously yarinyar bata burgeka ba?" Wani kallo Sadeeq ya wurga ma Sagir wanda shi hakan dariya ma yake kara basa, dakyar ya sauya kansa meanwhile yana tuki ya ce

"And she's so beautiful ya Allah" Sai sannan Sadeeq ya Kalle sa ya ce

"Toh ai ba muyi nisa ba zamu iya komawa wajan mai Chemist ɗin sai ya kaimu gidan su yarinyar ko?" Sagir ya ce

"Wallahi zan so fah, da gaske na juya kan motar zuwa wajan?" Wani kallo da Sadeeq ya sake jefa masa yasa ya fara dariya ya cigaba da driving ɗinsa kawai.

Tun daga bakin kofar gida Bappahn ya fara doka sallama har ya shiga cikin ƴar sakar gidan nasu wanda duk sanda ya shigo yana doka sallama sunsan wani abu ne ya faru

"Fatsuma!" Ya daka ma Mama kira wanda hakan yasa ta fito da sauri tana kallonsa ta ce

"Lafiya Malam?" Wani kallo yake mata ya ce

"Ina Abdul yake?" Ta buɗe masa hannu alamar bata sani ba ta ce

"Kaga Malam rabona da shi fah tun da safe"

Bappah ya ce "Toh ki sani ki jama ɗanki kunne idan ba zai natsu ba zai barmin gida gaskiya, ace kullum idan aka tashi kwatancen yaran unguwar nan marasa jin magana toh Abdul na ciki, yanzu ace wai Jiya da daddare ashe sunyi kokarin shiga gidan wani fah? Hakan ya dace ne Ni shikenan bani da ƙima balle daraja a idon duniya?" Mama dake masa wani kallon sha tara ta ce

"Haba Malam sai ka gama tiririn ɗan naka ne a duniya kafin ka rufa masa asiri?" Ya ce

"Toh shikenan, ki cigaba da zancen rufa masa asiri wallahi Karki sa baki a mummunan matakin da zan ɗauka a kansa" daga haka ya wuce fuuu sai ɗakin sa.

Siyama ce ta shigo da sallama kamar mara gaskiya tana bin gurin da kallo ganin baya nan ta ce

"Mama ina Bappahn?" Mama ta taɓe baki ta ce

"Ke kuma me na wani abu kamar mara gaskiya" ta ce

"A'a nikam ki kyale Ni, bana son jaraban Bappah" daga haka ta wuce ciki ta bar Mama da bakin cikin abinda Bappah ya gama mata kuma tasan definitely Umma ta ji su, wani dogon tsaki taja sannan ta wuce cikin dakin ta.

Har kofar gida Sagir ya sauke Sadeeq wanda har suka je inda zasu suka dawo bai sake kula Sagir ba, bayan ya sauka zai kulle car door din Sagir ya ce

"Good night Aboki, please be guided" Sadeeq ya tsaya yana kallonsa sai kuma ya ce

"Look! Idan har ba zaka daina shirmen nan naka ba wallahi ba zan sake haɗa hanya da kai ba balle wani aiki ya sake haɗa mu" Tun kafin Sagir yayi magana ya wuce zuwa babban gate ɗinsu wanda gidan sai ka ɗauka a wata kasar take.

Umma sai kallon Azrah take wanda tun ɗazu tayi tagumi, kana ganin ta kasan yau tana moody, Umma ta ce

"Damuwar me kike saka ma kanku Azrah? Kina bukatar wani abu ne?" Azrah ta sauke hannunta da tayi tagumi tana kallon Umma ta ce

"Nothing fah Umma, kawai dai na gaji ne" Umma ta ce

"Toh tashi kije ki kwanta, Kinga ƴar uwarki kam ai ta kwanta kuma ke kike bukatar hutu" ta girgiza mata kai ta ce

"Idan na kwanta kuma aka zo siyan abu kuma fah Umma?" Umma ta ce

"Sai na fita na bayar" Azrah tayi murmushi dan ita a kalan tausayin Umma da take ji ba zata bari tana aikin wahala ba saboda kar kanta ya fara ciwo balle har taje ta fama ma kanta matsala, ga kuɗin aiki wajan 30Mil ta'ina zasu fara, kamar Umma tasan tunanin da take yi ta ce

"Ai ba zan yi hayaniya ba balle har kan ya fara ciwo Azrah, balle ma kwanan nan ma ai kan yana ɗan ciwo amma ai yana tafiya kuma ba tare da ciwon ya ta shi ba" Azrah ta ce

"Toh Allah kara miki lafiya Umma, burina nayi karatu na samu kuɗi da za'a rabaki da wannan ciwon ne" Umma ta ce

"Amin, Allah cika miki buri".

Har Azrah ta kwanta amma kuma sai ta kasa manta da maganar wannan strangern ga kuma Ya Saif, haka kawai taji ta tsane su with passion, wato talaka bashi da wani ƙima ko daraja kenan? Wato talaka bashi da aiki sai zama mutumin banza? Wannan ne babban burinta na son cinma buri a karatu saboda ko dan kujewa irin wannan wulakanci, tasa hannu ta share hawayen fuskanta sannan ta miƙe zaune tayi addu'an bacci ta gama shafe jikinta ta kwanta.

Washe gari tun safe Mama ta ɗaurawa Habiba tallah, wanda Siyama na gefenta suna dafa abinci da itama zata fitar tallah.

Azrah dake kallon Umma ta ce

"Umma toh barin tafi kasuwan ko da wani abun da kuma zaki bukata?" Umma ta ce

"A'a babu Azrah! Allah tsare min ke" ta amsa da

"Amin" a compound taga Mama da Siyama suna ta girki suna magana, a hankali ta ɗaga kai tana kallon Mama ta ce

"Ina kwana" Mama ta ɗago tana mata wani kallon banza ta ce

"Karki fita ko ina, ki dawo dan yau dake za'a je tallah gareji sai dai ki mutu amma sai kinje"

Azrah taji hawaye yana shirin taruwa mata, amma ta hana kanta haka, tayi wucewar ta kofa ba tare da ta sake kallon Mama ba dan tana jin wallahi ko dukan mutuwa za'a mata ba zata tallah gareji ba, sai kace ƴar iska mara kunya.

#Jiddatulkhayr

***