LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 4: Beneath the Surface

by @hauwajaywrites

Mama tabi Azrah da kallo baki buɗe har ta fita, ta fara tafe hannu tana salati ta ce

"Yau Ni Azrah zata ma rashin kunya? Har ina mata magana zata iya tafiya ta barni tsaye? Saboda ganin bani na haifeta bane ko kuma so take ta nuna min cewa ban isa da ita bane" Siyama ta ce

"Ai dama za'a rina, yanzu gani take ai tafi ƙarfin tallah balle tayi, mune dai ya zama mana dole" Mama ta ce

"Wallahi bari Bappahn ku ya dawo, zanyi maganin ta sai dai idan har ta daina cin abincin gidan nan ne" Siyama ta ce

"Toh Kema Mama ai Kinsan ba zata ba kika tsaya ɓata bakin ki a banza, baki ga kalar fatarta bane, ai gani take ita ƴar hutu ce mune dai ƴan wahala" Mama ta tamke fuska ta ce

"Toh me a fatar nata?" Siyama ta ce

"Yanda yake sheki mana, Kema Kinsan Manyan maza ne ke siya mata waɗannan sabulun turawan mai uban tsada, kuma Kinsan maza basu kashewa mata kudi haka kawai wlhi" Mama ta fara dariya ta ce

"Ai kuwa Nima har sannan mamaki baya barina sai na ratsa aina take samun su, Ahap ba sunce ita ƴar boko ba? Muna nan mu zuba da su saita kawo musu abin kunya, waye kuma bai san Matan boko ba?" Siyama ta miƙe tana faɗin

"Ai muna kallon su kuwa".

Ba Azrah ta dawo gida ba sai wajajen karfe 11am a mugun gajiye ta karasa cikin gidan nasu wani almajiri yana biye da ita rike da wani bakko a kofar ɗakinsu ta ajiye na hannunta sannan ta karɓi na hannunsa ta fara kaiwa ciki, ta kuma fitowa ta basa laɗan aikinsa sannan ta karasa ciki ta zauna kan laidar dakinsu tana kallon Umma dake zaune tana karanta wani lissafin musulunci, Umma ta rufe littafin tana kallonta ta ce

"Sannu Azrah, kinsha wahala kam" ɗan murmushi tayi ta ce

"Sannu da hutawa Umma" fara cire kayan bakkon tayi tana nunawa Ummanta kayan da tayi tsari tana faɗa mata kuɗaɗen su Umma ta ce

"Ɗazu naji kamar kun sami matsala da Mama?" Nan da nan annurin fuskarta ya washe tana kallon Umma ta ce

"Kiji fah Umma, wai tallah gareji zata bani na kai mata, nikuma nasan ba zanyi ba shiyasa kawai nayi tafiya ta" Umma ta ce

"Kinyi min daidai dan Banga dalili ba, idan Nima ina son na saki tallan ai da tuni na fara turaki amma dake bana son yarana suna tallan shiyasa ban fara barinku kuna yi ba tun farko, sai dai kawai yadda naga tana masifa na san dole zata haɗa ki da Bappahn kune sai kisan me zaki ce masa" Azrah ta ce

"Toh shikenan" Umma ta ce

"Miƙamin laidan sai na fara kulla busheshshin kayan miyan, kawai ke kije ki shirya ki tafi gidan da kike aiki Karki yi rana tunda yau baki je boko ba, danma suna hakuri ne kawai wlhi" Azrah ta miƙe ta bawa Umma laidar daga haka ta wuce cikin ɗaki ta fara shiryawa, har zata sa wani ƙuncen Abayan Anty Suhaila data bata sai kuma ta fasa tunda aiki zata no need kawai ta sanya wani riga da skirt ta ɗaura hijabinta daya ɗan koke ta fito tama Umma sallama sannan ta fita.

Tunda ta shiga parlorn taga Saif yana zaune babu kowa hakan yasa ko kallon direction ɗinsa bata yi ba ta kama hanyar kitchen ya ce

"Ke kuma haka aka baki tarbiyya baki iya gaisuwa ba?"

Tayi kamar bata ji sa ba, cos kawai dan tana aiki a gidansu ne kuma yaron Mummy ne amma da sai ta faɗa masa bakar magana akan bakar maganar daya gaya mata jiya dan sai yanzu abin ke kara jiƙa mata kuma ta ɗau alwashin koda wasa ba zata kara Gaishe sa ba balle ya sake cewa tana son jan hankalin sa ne gareta, attention ɗinsa take nema, harta shige kitchen bata Jiyo ba ya bita da kallo baki buɗe, sai kuma yaji takaicin magana da yayi dan wannan raini ne ma gashi baya so wani abun ya sake haɗasa da ita, yayi dana sanin maganar da ya mata yafi cikin ƙwando

Harta gama girki ta fitar kan dinning bata ga Mummy da Suhaila ba, hakan yasa kawai ta girka abinda tayi kwana biyu bata dafa musu ba, tana gama duk wani activities dinta na gidan ta fito parlorn da niyyar tafiya, idonta akan na Saif dake dining ɗin yana cin abinci ya faɗa, da sauri ta ɗauke kanta daga haka ta fita a Parlorn tana mamakin ai kyankyaminsa na banza ne, idan har yana kyamarta akan meyasa zaina cin girkinta ita wannan abin ne yafi bata dariya da tasa kalar saftan.

Tafiya kawai take abinta ba tare da komai ba, sai dai kawai tunanin yaushe zasu gama wannan wahalar a duniya? Few houses da gidan Mummy ta kalli wani mota na parke shima gidan ba karya ya haɗu fiye da tunanin me tunani maza uku na jikin motar da alama dai hira suke, ita dai kullum ta shigo unguwar nan sai tayi fatan suma Allah ya basu koda ƙwatan waɗannan ɗinne.

Kamar ance ɗaga ido kawai idonta ya sauka a cikin nasa, ta gane sa clearly, dan babu ko wani doubt tasan shine tamke fuskanta tayi zata ɗauke kai sai kuma ya sauka a cikin idon Sagir, wanda shima clearly ya gane ta, da sauri ya taɓa Sadeeq ya ce

"Be guided please, gata can" sai kuma ya kwashe da dariya dan shi abin na mugun basa dariya dan duk duniya babu me iya faɗawa Sadeeq magana sai Mami, amma sai gashi ƴar yarinya ta faɗa masa, kuma babu shakku balle nadama saima lots of confidence da take dashi

A fusace Sadeeq ya zuya yana ma Sagir wani kallo ya ce

"Enough please, wait... Do I have any business with her? Ko dai kana neman hanyar da za'a haɗa ka da ita ne?" Sagir kallonsa kawai yake ganin How serious he is

Al'amin ya ce

"She's beautiful, girlfriend dinka ne Sadeeq?" ya kare maganar in very calm tongue, Dan shi bai san abinda ke wakana ba, a mugun fusace Sadeeq ya shige motarsa ya kunna motar wanda kawai figarta yayi da gudu har sai da Al'amin ya matsa masa ganin zai iya buge su, ya bisa da kallo sannan ya maida kallon sa kan Sagir ya ce

"Me amfanin hakan da yayi?" Sagir ya ce

"Alakanta sa da ita da kayi ne ya basa haushi, baka ji yana tambaya yana da business ne da ita ba?" Al'amin ya taɓe baki ya ce

"So? And isn't she beautiful ko dan nayi admiring ne yaji haushi? Sagir ya ce

"Nace maka dan ka haɗasa da ita ne fah yaji haushi" taɓe baki Al'amin yayi ya ce

"Then, shi yaji wajan, amma ai wannan tafi ƙarfin sa".

Azrah dake tafiya taga wucewar motarsa kamar wanda zai tashi sama dan bata san sanda ta koma gefe da gudu ba, sai kuma ta bisa da harara tana taɓe baki.

Da yamma tana karatun babu kowa a ɗakinsu dan Ummar da Zahra sun fita, a cewar su tana ɗan zaga unguwar kar zaman gida kullum kuma ya jawo mata wani ciwon gwara tana excerses

Muryan Mama taji ita da Bappah ga Habiba ma dake sa baki, amma ta gagara sanin akan me suke magana, haka kawai yaji hankalin ta bai kwanta da wannan maganar nasu ba saboda yadda tasan yau kuma ita da Mama sai Allah, rufe littafin tayi ta maida hankalinta tana sauraron su, Bappah ya ce

"Toh ke Fatsuma ai shikenan tunda taki tallan kawai ki kyaleta" Mama tayi wani ashar ta ce

"Kana nufin duk iskancin data min da nuna min ban isa da ita a ya tafi a banza kenan? Harda buga ɗan karamin kofar mu da muƙe managing ɗinsa fah, ace ai ko bata sanni ba bai kamata ina mata magana tayi wucewarta ta barni tsaye ba, Ni kayan takaicin ma yadda ta gaggayamin magane yafi komai ɓata min rai" Bappah ya ce

"Bansan sau nawa kuma zance kiyi hakuri ba, maganar tallah kuma tunda tun farko Uwar bata so shikenan, amma dole zan ɗau mataki akan yadda tayi miki ai" Mama ta masa wani kallo ta ce

"Toh gaskiya Malam sai dai Matar ka da yaranka su fara girkin su amma Ni gaskiya nagaji, Ni nawa yaran ba sonsu nake ba da nake tura su tallah ai, wato nata yaran ne ƴaƴan gata ko? Wallahi na daina saka musu abinci daga yau ɗin nan" Bappah ya ce

"Haba ke kuwa Fatsuma, ai abin duk bai kai haka ba, tallah kuma tunda kince sai sun fara zuwa ai wannan dole ne, dole ne sai sunje amma sai dai kar ana shiga hakkin lokacin karatun su tunda suna zuwa makaranta" sai kuma ya shiga ƙwalawa Azrah kira

"Ke Azrah! Kina ina ne ina magana ba zaki fito ba" Azrah dake sauraron su ta ajiye littafin hannunta ta share hawayen daya gangaro mata she wish Umma na nan, ta miƙe jiki babu ƙwari, jin ya sake doka mata kira yasa ta ce

"Na'am Bappah gani fitowa" Muryan Mama ne ya biyo bayan nata tun kan ta rufe bakin nata ta ce

"Dan uban ki ana magana ba zaki fito bane ko sai na shigo na fito dake" buɗe labulen kofar tayi ta fito koda wasa bata kalli direction ɗin Mama ba tana kallon Bappah ta ce

"Bappah gani" Bappah ya ce

"Kema yanzu kin canza hali ko? Akan wani dalili zata na faɗa miki magana kice mata A'a sannan tana miki magana kawai sai ki tafi ki barta a tsaye? Haka ake yi ko kuma Uwarku ce ta koya miki" Azrah ta share hawayen daya gangaro mata tana kallon Bappah ta ce

"Bappah nifa ban mayar mata da magana bafa, kawai nace Ni ba zani tallah bane kuma wai tallan a gareji ba zan iya zuwa bane Bappah shiyasa nace A'a , amma kuyi hakuri dan Allah" Bappah na mata wani kallo ya ce

"Kin kyauta ma kanki, yanzu daga yau zaki fara tallan kema kinji? sai kar kuyi nisa"

"Babu tallan da zata yi dan Banga wanda zai ɗaurawa Azrah tallah ina da rai ba" Murya Umma ya dake kunnuwan su wanda basu lura da shigowa nata ba ga kuma Zahra a gefenta, karasa cikin sakar gidan tayi tana kallon Bappah da mamaki dan tasan shima baya son tallan nan amma ji lokacin guda ya yarda, Mama ta katse mata tunanin ta

"Ai ita take ɓata yaran Malam, ba'a isa a ɗau mataki akan su ba sai tace ita kaza, ga ita mai ƴara ba" Mama ta kalli Zahra dake gefen Azrah ganin yayarta na kuka yasa itama farawa ta ce

"Azrah kama hannun kanwarki ku wuce ciki" Azrah ta juya Zahra na biye da ita a baya

Umma tana kallon Habiba dake zaune sai washe baki take tana dariya ta ce

"Kema Habiba tashi ki wuce ciki" Habiba ganin Bappah yasa ta ɗan ɓata rai ta wuce ciki tana gunaguni

Mama na kallon Bappah ta ce

"Malam kayi hakuri amma gaskiya I'm very disappointed in you, ace har zaka yarda a tura yaranka tallah? Idan har ina son suyi tallah da tuni na fara ɗaura musu, ko Azrah dake sana'a iri da kala naga a gida take yi sai dai wasu lokutan a fitar kofar gida amma rana tsaka kace zata fara fita tallah" Mama ta riƙe kugu tana kallon Umma ta ce

"Toh sannu Uwar Agwagwa, ai ta gwada bata so ina Kema zaki so" Umma ta ce

"Tabbas kuwa ba zan so ba" Bappah yana kallon dukkan su ya daka musu tsawa, Mama ta ce

"Shikenan Malam tunda har abin haka ne, Ni kuma daga yau na daina abinci dasu, su koma girka abincinsu su daina dogara da Ni" Bappah zai yi magana Umma ta rika sa

"Baki san abinda nake addu'a akai ba kenan? Dama taya idan banda zalunci ace kece zaki na girki sai kinga dama ki tsokara mana sannan kuma ki haɗa da gori, wallahi tafi Nono fari a waje na" Bappah ya ce

"Yanzu ke da kike murnan an raba girkin ya zakiyi, kin samu ana rufa miki asiri shine kike da bakin magana ko?" Ta ce

"A'a ta rufa maka asiri dai, sannan ai dama cinmu da shanmu a kanka yake Malam, dan haka sai ka fara providing mana muma" Mama da shock take kallonta dan bata ɗauka hakan daga gare ta ba, taso ta bata hakuri ne

Ita kuwa daga haka ta juya ta wuce ciki, tana shiga Azrah tayi kanta da sauri tana faɗin

"Umma kiyi alwala ki zauna da shirin ki ana magrib sai ki kwanta ki huta Kinga kinyi magana dayawa Ni tsoro na ma kar ciwonki ya tashi ne" Umma na Murmushin karfin hali ta ce

"Karki damu Azrah, ba zai tashi ba In Shaa Allah" daga haka ta wuce ta kwanta akan dadduman dake shimfiɗe a Parlorn.

Har dare yayi Mama bata kawo musu abinci ba, Azrah dake zaune ta kalli Zahra ta ce

"Zahra zo ki raka Ni" Zahra ta mike tare suka wuce kitchen ɗin, tuba tsohuwar mukubur ɗinsu sukayi suka fito dashi fili, Azrah ta ɗauki gawayi a wanda take sayarwa ta hura wutan, ta wuce ɗaki bata daɗe sosai ba ta fito tana mika ma Zahra kuɗi ta ce

"Zahra je ki tsoho mana taliya laida ɗaya sai a sa miki mangyaɗa gwangwani ɗaya kinji? Kiyi sauri dan Allah" Zahra ta amsa da "toh" ita kuma ta zauna nata cigaba da fifita wutan.

Bayan sun gama girkinsu suka shiga ciki da shi, mikawa Umma suka yi, Umma ta ce

"Amma mayasa kika tsaya Azrah? Azrah ta ce

"Toh haka zamu kwana da yunwa Umma? Ai abinci dole ne" Umma ta ce

"Toh ai naga a cikin kudin kine Azrah, kuma bana son kina taɓawa saboda gaba" Azrah ta ce

"By then, Allah zai kawo mana wani In Shaa Allah" Umma tayi shiru tana kallonta, suna kan cin abincin sai ga Bappah ya shigo, Umma ta ce

"Sannu da zuwa" ya amsa da "yauwa" yana kallon su Azrah ya ce

"Ku shiga ciki ko?" Ta shi sukayi suka wuce ciki, ya maida hankalinsa ga Umma ya ce

"Amma mayasa zaki ce kina son zakuna girkin ku?" Wani murmushin takaici Umma tayi ta ce "Toh dama ai ba zamanta nake ba, kuma ai ba ita ya kamata ta ciyar da mu ba" Bappah ya ce

"Toh ai zamana kike kuma Ni na tsara hakan" Umma ta ce

"Yanzun saboda gudun karka na tsiyo mana kayan abinci ne yasa kake son naje na bawa matarka hakuri Malam? Lokacin da ka dauki kuɗin da ka siyar da machine dinka ka bata da niyyar tana juyawa ana samun wanda za'a ci Ni ka tambayi shawara balle kuma ka bani Nima ina juyawa? Amma ai gashi kullum gori da kuma gadara da akan ita take ciyar damu ya ishe Ni, kaima sai kayi hakuri akwai ka cigaba da siya mana namu muna yin sa daban" Bappah yayi shiru yana kallonta.

Duk kallon Daddy dake bayani suke, a hankali Saif ya ce

"Amma ai Daddy Suhaila ya kamata ama magana saboda Normally mata na riga maza aure amma tana her late 20s sai ni kaɗai" wani kallo Daddy ya masa, Mummy ta ce

"Deen yaushe zaka daina haɗa kanka da kanwar ka ne wai?"

Daddy ya ce "Saboda ita macace idan miji bai zo ba ba ita zata je ta nema ba, kai kuma na miji ne, a haka ne kake son na ɗaura ka akan business Dina ba tare da kana da aure ba? Ai hankali na ba zai kwanta ba ina turawaka different countries" ya ɗan kalli Daddy shi ya tsane anything pertaining wannan so called company, ya fiso independent life ne amma ba zasu gane ba.

#Jiddatulkhayr

***