LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 6: A Ray of Hope

by @hauwajaywrites

Da daddare misalin 2:30am Azrah na zaune akan dadduma a gefen gadon da Umma ke kwance, ta shafa fuskarta da tafin hannunta, idanuwanta sun kumbura da kuka hatta gaji, tunaninta duka yana kan Umma da ke kwance cikin rashin lafiya, tana ta mika kuka zuwa ga Allah masu mafita ya kuma bawa Umma lafiya

"Ya Allah... Ka bawa Umma lafiya. Ka ba mu mafita, ko daga inda bamu zata ba..." ta furta a hankali, kamar kada kalmomin su farka da Umma da ke kwance kusa da ita.

Tun da yamma Zahra da Bappah suka koma gida, Azrah ta rage ita kaɗai a asibitin ta rasa ina zata fara neman kudin da zata cika deposit ɗin maganin da likitoci suka bukata kafin su cigaba da duba Umma, a haka take tun lokacin da su Bappah suka koma har sanda take kan sallayan

Tayi shiru ta faɗa duniyar tunani, wani tunani ne ya faɗo mata a zuciyarta, Sai kawai ta tuna da Mummy, ta tuna da aikin da bata je ba a ranar, aikin da ke kawo mata ƙananan kuɗaɗen da take adanawa, A hankali ta fara jin wani hope, hope ɗin da yasan bata da tantama akai, dan she's very sure Mummy ba zata ɓata kunya ba, whispering ta yi

"Idan na roƙi Mummy ta bani kuɗin aikina na wata uku nan gaba, zata iya bani... zan iya amfani da su na cika balance ɗin kuɗin maganin Umma" ta faɗa a ranta, Wannan tunanin ya dan taɓa zuciyarta da fatan cewa watakila mafita na kusa.

Bayan gari ya waye tana zaune amma gaɓa ɗaya she's spaced out, Zahra ce ta shigo ɗauke da ƙaramar kulan abinci, Azrah ta ɗaga kai tana kallonta harta karasa ciki sai kuma ta kalli bayan Zahra kaman tana hoping ganin wani, Zahra ta zauna a kan wani kujera. Bayan sun gaisa, Azrah ta ɗan murmusa kamar tana son tambayar Zahra sai kuma tayi shiru, can ta ce

"Ya Bappah? Ko yana waje ne?"

Zahra tayi ƙwafa tana girgiza ƙafa ta ce

"Dalla ki bar ni da Bappah! Ni wallahi na gaji da halin ko in kulan sa, just imagine bai zo duba Umma ba, balle ya fara maganar clearing bill, shi baya ma tunanin aina kike samun kuɗi balle yaji tsoron tarbiyyar ki" ta karasa maganar cike da takaicin Bappah

Azrah da tunda farko ta tsaya kallon Zahra da shock har sannan bata janye idonta akanta ba cos Zahra na mugun bata mamaki idan sometimes tace wani abu ko kuma ta aikata wani abu, tayi kasa da murya ta ce

"Zahra ki rage zafi, Koda me ya faru Bappah mahaifinmu ne, bai dace mu raina shi ba... mu dai cigaba da roƙon Allah harya gane abinda yake ba daidai bane" Zahra ta taɓe baki ta ɗauke kanta daga Azrah dan bata ji zata iya cigaba da wannan maganar da ita ba

Can kuma sai ga Nurses suka shigo suka duba Umma, bayan ta karya suka mata allura, wani daga Nurse ya kira Azrah ya sake jaddada mata cewa dole sai an cika kudin ko kuma su sallame su zuwa karfe biyu

Azrah ta dafe kanta data ji ya tsara mata , Nurse ɗin ya juya ya fita, ta juya tana kallon Zahra da rinannun idonta, ta roƙeta ta zauna ta kula da Umma, ita kuma ta fice cikin sauri, ta kama hanya a kafa zuwa gidan Mummy, a zuciyarta addu'a da fatan zata Mummy zata yarda ta bata kuɗin aikin nata kamar yadda ta yanke hukuncin tambayarta.

Azrah na tafiya absent-minded jikinta yayi sanyi kamar wadda aka cirewa laƙƙa, tafiya take kamar bata san inda take dosa ba tunaninta na zagaye ne da damuwa, da tunanin yadda zata ceci rayuwar mahaifiyarta idan har Mummy bata yarda ba, Har ta isa gidan Mummy bata ma lura da yanayin hanya ko mutane ba knocking tayi gatekeeper ya buɗe mata

Tana shiga ta tarar da Mummy zaune tare da Suhaila da Saif, suka ɗaga kai suna kallonta harta karasa ciki parlorn ta gaida su, Mummy ta kalle ta ce

"Azrah meyasa baki zo jiya ba?"

Azrah ta durƙusa kusa da kujerar da Mummy take, ta sauke ajiyar zuciya tana cewa

"Umma ce Mummy... bata da lafiya sosai har anyi ta dinta a asibiti hakan ne yasa ban samu zuwa ba."

Mummy da Suhaila suka ce

"SubhanAllah," sannan suka fara mata addu’a da fatan sauƙi, amma banda Saif wanda ko kallonta bai yi ba, balle yayi magana, Har lokacin Azrah na duke a gefen kujerar Mummy, kamar wata mara galihu, ganin har sannan tana duke Suhaila tama Mummy magana da ido wanda yasa Mummy ta ce

"Menene Azrah?"

Azrah ta kalli Mummy da idonta cike da hawaye ta ce

 

"Dan Allah Mummy, ina roƙon ki ki bani kuɗin aikina na wata uku gaba… zan yi amfani da su ne wajen cika kudin asibiti na Umma, ba mu da wani mafita sai hakan ne, ki tausayamin"

Wani shiru ya biyo bayan kalamanta Mummy ta zuba mata ido, tana nazarin yanayinta, Azrah harta fara cire hope kawai ta tsinkayi murya Mummy

"To Azrah, Nima yanzu da nake zaune akan kaya ne wlhi, Jibi idan Allah ya kai mu zamu bar ƙasar nan gaba ɗaya" da sauri Azrah ta ɗaga kai ta Kalle ta sai yanzu ma yanayin parlorn da babu wasu kaya ya dawo mata da kuma yadda shekaran Jiya ta kalli wasu curtain changes a gidan

Tana kallon Mummy kamar wadda ke kokarin processing maganarta, sai hawayen da ke makale a cikin idonta suka fara gangara saman kumatunta Kafin ta ce komai, Mummy ta miƙe tana cewa

"Mu shirya mu je mu duba Umman tunda ba wai wani abun muke yanzu ba and it's good ai"

Suhaila ta bi ta a baya, amma Saif ya cigaba da zama kamar bai ji komai ba balle su saka ran zashi

A asibiti ganin yadda Umma ke kwance cikin rauni, ya sa Mummy ta cika duka kuɗin da ya rage suyi balancing na asibiti ba tare da wata tambaya ba, Nurse ɗin suka karɓa suka tabbatar da an biya cikakken kuɗi Azrah da Zahra ba su iya boye farin cikinsu ba Sai godiya suke ta yi kamar rayuwarsu ta ta'allaka a kan hakan ne

Bayan sun gama komai suna dakin da Umma take Azrah ta sanar da Umma, hawaye ya fara sauka idonta ta daga hannunta tana yi musu addu'a

"Allah ya saka da Alkhairi ya biya muku dukkanin bukatunku, Allah muku fiye da yanda kuka faranta mana,

Da zasu tafi Azrah ta raka su har bakin mota, Suhaila ta riƙe hannunta ta ce

"Zaki zo kafin mu tafi ko?"

Azrah ta gyaɗa kai tana murmushi, tana jin tun yanzu ta fara missing ɗinsu"

Washegari da safe, aka sallami Umma daga asibiti bayan an bata magunguna masu ƙarfi. Bayan sun dawo gida, suka zagaye Umma suna kallonta cike da tausayi Umma na kallon Azarh ta ce

"Azrah ki tashi ki je ki yi sallama da Mummy, sai kuma ki sake musu godiya pls, live ina musu fatan Allah kaisu Lafiya" Azrah tayi shiru tana kallon Umma sai kuma ta wuce ciki ta sanya hijab ɗinta ta fito

Sallama tama su Umma, dama tana son zuwa ta sake musu godiya kuma tana son suyi sallama, amma haka kawai take jin kamar wani nauyi ne a zuciyarta da ta kasa sauke tun ranar da Mummy ta sanar mata zasu bar kasar, har ta isa gidan Mummy tunanin da take kenan

A parlour ta same su Mummy, Suhaila da wani mutum da ba ta taɓa ganinsa ba a gidan amma da alama shine Babban su Suhaila dan ga kama ya tabbatar mata da hakan, Fuskar sa cike take da natsuwa da annuri, Yana zaune yana tattaunawa da Mummy a hankali, duk suka ɗaga kai suna kallonta

Suhaila ta miƙe da murmushi ta rungume ta kamar ƴar uwarta,

Bayan ta Gaishe da dukkansu Mummy ta ce

"Azrah ya gida? Ya jikin Umma?"

Azrah ta gyaɗa kai, tana ƙoƙarin hana kanta kukan da ke shirin zuba Amma kafin ta iya cewa komai Mummy ta nuna mata kujera

"Zauna mana, me ke damunki Azrah? Kin yi wani iri..."

Azrah ta zauna tana jinta wani iri, ta buɗe baki zata mata godiya sai  kawai kukan da ta ke riƙewa ya kubuce, tana sharar hawaye tana cewa

"Mummy… nagode… ban san yanda zan saka muku ba…amma zan cigaba da muku addu'a har karshen rayuwa ta, Allah ya saka da Alkhairi…"

Mummy ta rungume ta, tana shafa kanta amma itama she's speechless dan ba kaɗan Azrah ke bata tausayi ba, Har Baban Suhaila wato Daddy ya ce

"Young lady keep on praying kinji? Kuma no matter how no matter what karki bar makaranta,  amma ki daina godiya sbd dan Allah suka taimaka miki"

Suhaila ta tashi ta shige ɗakinta tana cewa

"I'm coming Azrah" daga haka ta shige bata ɗau lokaci ba sai gata ta fito tana rike da wani ɗan ƙaramin Ghana Must-Go cike da kaya ta ce

"Ga wasu kayan sawa da ban so Azrah, sabbi ne sai kuma turaruka da shower gel... Nasa zaki bukace su"

Azrah ta rufe bakinta da hannunta, tana kallon ghanan dake gabanta, ta ɗaga kai tana kallonta da thank you face ɗinta amma ta gagara cewa komai, tana tunanin me ta musu data cancanci irin wannan kulawa daga waɗanda ba su da alaƙa ta jinin, ta duka ta fara mata godiya Suhaila ta tamke fuska ta ce

"Mention not, please"

Da zata koma gida Daddy ma ya zaro kuɗi daga aljihunsa wanda ko irgasu baiyi ba ya miƙa mata

"Ga wannan ki ƙara da duk abin da kike buƙata Allah ya ba Umma lafiya" wanda hakan yasa take tunanin Mummy ta masa maganar ta kenan

Wannan karimcin ya gama karya Azrah, hawaye ta fara yi, tana sharewa ta miƙe ta ɗauki ghanan tana kallon su

"Mummy… Daddy… Suhaila… na gode Allah rufa muku asiri duniya da Lahira"

Suhaila ta ƙara rungume ta ta ce

"Zanyi missing dinki Azrah gashi baki da way"

Azrah ta gyaɗa kai cikin hawaye, tana jin wani abu mai zafi da daɗi a zuciyarta abu da bata taɓa ji ba tun lokacin da rayuwa ta haɗa ta da su

A haka ta bar gidan, Ghana Must-Go ɗinta a hannu, zuciyarta cike da sabbin tunani da sabuwar rayuwar da zata fara babu aiki

Da Ghana Must-Go ɗinta a hannu, Azrah ta shiga cikin gidan su cikin nutsuwa as Azrah dinta, ta tarar da Mama zaune a tsakar gida tare da ‘yaƴanta uku Habibah, Siyama da Abdul da alama akwai abinda suke yi

duk suka ɗaga kai suka kalle ta

Azrah ta ce da ladabi tayi sallama

"Assalamu alaikum."

Mama ta amsa da da wani irin murya tana dariya

"Wa'alaikumus salam ƴar boko" sai kuma tayi shiru tana kallon ganan hannunta ɗin

Habibah ta kwaɓe fuska, tana faɗin

"Wato kaya ta samu ko me? Ta wani shigo mana da ghana must-go kamar wacce ta dawo daga hutu ko jihar Ni Habibah?

Siyama ta ɗora da dariyar rainin hankali ta ce 

"Dalla malama, saurayinta ne ya bata kaya mana, Kin san haka suke, wannan kayan da take sawa a banza ne aka ce miki, kwadayin duniya kawai yake kaita"

Azrah ta lumshe ido, bata ce uffan ba tayi kamar bata ji ba, ta ɗauki hanyar ɗakin Umma

A ɗakin Umma na kwance amma idonta a buɗe tana kallon sama kana ganinta kasan tana nazari ne Azrah ta shiga da sallama tana kallon Umma

"Umma ya jikin?" ta tambaya cikin damuwa

"Alhamdulillah Kin dawo? Lafiya?" Umma ta ce tana ƙoƙarin tashi daga kwanciyarta

Azrah ta zauna kusa da ita, ta bude ghana must-go ɗin a hankali, ta nuna mata kayan Suhaila ta bata da turaruka da sabbin kayan wanka Umma ta kasa boye mamakinta

"Subhanallah… daga ina duk wannan?" ta tambaya cike da fargaba

"Su Mummy ne suka bani Umma" ta ciro kuɗin tana mika mata ta ce

"Babansu kuma ya bani wannan kuɗin Umma"

Umma ta jinjina kai tana mamakin hali irin nasu Mummy ko kaɗan basu kyamar Azrah kamar yadda wasu masu aiki kema housegirl dinsu

Azrah ta bar ɗakin ta koma nasu har sannan tana jin muryar su Siyama a tsakar gida tana suna cewa

"Yanzu haka ba kowa zata dinga kulawa ba, ita gata sai wani ji take da kanta saboda fatar jikinta take ji da shi, duk dai mun sani wallahi bilicinne"

Azrah ta share hawayenta ta sani ba kowa zai fahimci gaskiyar al'amuranta ba amma ta san cewa zata ci gaba da aikinta domin rayuwa, ba zata tsaya jira jin ra'ayin kowa ba

Bayan Azrah ta gama shirya kayan a daki, tana kokarin jera su a cikin ɗan karamin wardrobe ɗinsu dake mane a bango sai ga Zahra ta shigo dakin da sauri

"Yaa salam! Azrah! Wannan kayan kuma fah?" ta tambaya tana duban jakar da mamaki

Azrah ta yi murmushi kaɗan "Su Mummy ne suka bani, Kayan Suhaila ne da wasu sabbi ne ma… har da turaruka da sabulun wanka"

Zahra ta kalleta ta buɗabaki

"Kayan nan duka daga can?" Ta zauna kusa da jakar, tana buɗewa a hankali.

Tana ɗaukar kaya ɗaya bayan ɗaya tana dubawa, sai ta girgiza kai "Subhanallah…Anty Azrah wannan kayan fa masu kyau ne sosai wlhi ga su masu tsada kayan da ba kowa ke iya samu ba"

Azrah ta ce da ƙasa-ƙasa

"Wallahi nima ban yi tsammani haka ba, hmm kawai daga na roƙi Mummy ta bani kuɗin aikina na wata uku nan gaba zan yi amfani da shi wajan maganin Umma, sai kawai suka bani komai… har da clearing bill ɗin asibitin Allah Sarki, Alhamdulillah my perfect Rabb"

Zahra ta daina kallon kayan tayi tagumi tana kallon Azrah cike da tausayawa

"Allah ya saka mu da Alkhairi, Anty Allah na kallon wahalar da kike sha, shiyasa yake dafa miki a komai" Azrah tayi murmushi ta ce

"Amin… da fatan Umma zata samu sauƙi in Shaa Allah " Zahra ta koma kan kayan ta cigaba da kallo ta ce

"Wannan kayan zan ara wani lokaci fa gaskiya" suka yi dariya tare Azrah ta miƙe ta koma wajan wanda ɗazu ta ware su

"Zahra! ta kira ta a hankali

Zahra ta ɗago kai "Naam?"

Azrah ta ɗauko wasu kaya daga ciki riguna, hijabai da sabulun wanka ta miƙa mata

"Ga waɗannan tun ɗazu dama na ware miki baki ne"

Zahra ta zaro idanu "Ni kuma fa? Wallahi ba zan karɓa ba! Ai naki ne"

Azrah ta girgiza kai tana dariya "ashe zan miki duka kuwa idan kika ce A'a, munsha wuya tare Zahra, wait what are sisters for? Kuma nayi niyyar rabawa tun kafin na shigo gida, Ki karɓa don Allah ko kuma naci kaniyan ki"

Zahra ta tsaya kallonta na ɗan lokaci, idonta cike da hawaye a karshe ta karɓa a hankali

"Nagode Anty Azrah, Allah ya saka miki da Alkhairi"

"Ke... Zanci jam'iyar ki" Azrah ta faɗa da tana murmushi

Sai suka ci gaba da rarrabe kayan, suna dariya da tsokana a tsakaninsu.

Dama a weekdays ne kawai zamu ke update banda weekend amma saboda week daya wuce an samu issues shiyasa zamu yi update yau, thank you darlns