LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)
Episode 7: Pathways to Hope
Da yamma saboda hadarin daya haɗu yasa garin ɗaukar zafi hakan yasa Umma na zaune a bakin ƙofar dakin, tana shan iska tana jingine da bango Azrah da Zahra suma sun fito suka zauna kusa da ita, amma ba wanda ke magana a cikin su kowa da tunaninsa a zuciya, sai dai lokaci-lokaci su kanyi magana a gefe
Can sai ga Bappah ya buɗe kofar gidan yana tunkaro harabar gidan Zahra ce ta fara hangonsa, idonta ya ciko da hawaye dan tunda aka sallame Umma bata sake saka idonta a nasa ba, ta miƙe tsaye da sauri kamar wacce aka sikara tana kallon Bappah daya kusa zuwa inda suke dama ganinsu yasa zai karaso, tana taɓe baki tana ɓata fuska Umma da Azrah sai kallonta suke dan basu ma lura da Bappahn ba sai data miƙe
Bappah ya ƙaraso, idonsa na kan Zahra da yake yawan ce mata 'Mamana' Amma yanzu Zahra ta riga da taji bata wani son Bappah duba da yadda ya maida Mama a gidan, taji ta washe sa Kamar dai yadda tayi alkawarin duk wanda zai zubar da darajar Umma ba zata lamunta ba
Ganin da gaske inda suke zaune Bappah zai karaso yasa Zahra guduwa cikin ɗakinsu, Bappah with shock written all over him yake kallonta ganin zata shige yayi saurin cewa
"Mai namiki uwata?" Ya tambaye ta da ɗan faɗa a muryarsa, yana kallonta cikin rashin fahimta
Zahra ta tsaya cak, ta juyo da hawaye a fuskarta ta ce
"Ni bana sonka Bappah, Tunda kai ka nuna baka son Umma, to nima haka"
Zuciyarta cike da takaici da ciwon da ta sha ganin Umma na kwance a asibiti yayin da Bappah bai taɓa bada ko sisi ba balle ya nuna damuwarsa akan Umma ba wato ma idan ta mutu asarar su, Ta juya da sauri ta shige cikin ɗakin Umma tana sharan hawayenta
Bappah ya tsaya cak, kamar wanda aka zuba masa ruwan sanyi, Bai taɓa tsammanin Zahra zata iya furta hakan a garesa ba Daga cikin duka yaransa Zahra ce wanda yafi nuna mata tsantsan So a fili kuma itace wanda baya ganin laifinta sannan itace wanda idan ya ajiya kaya ko bece ta wanke ba zata kwashe ta wanke masa shiyasa ya fi sonta, amma yau maganarta ya basa mamaki dan bai taɓa sammani ba
Azrah ta sauke ajiyar zuciya, tana kallon yadda Bappah ya kasa cewa uffan, kamar wanda ya sara dukkan thought ɗinsa, ta kalli Umma wanda itama daga gani she's speechless ne, a ranta tana mamakin hali irin na Zahra kamar bata mata magana a asibiti ba, but koma me Bappah zai yi su barsa da halinsa kawai
Mama ce ta fito tana share hannunta da ɗan guntun zanin dake ɗaure a jikinta tana wani murmushi makirci tana kallon Bappah dake tsaye kamar gunki ta tamke fuska ta ce
"Lafiya Malam?"
Bappah ya juyo gareta ya mata one look ya wuce ba tare da ya ce uffan ba,
Azrah ta juyo ta kalli Umma, wacce ke kallon samata ce
"Umma Allah ya sa hakan ya ishe shi darasi Thank God Zahra ce ba wata bace ta faɗa masa maganar"
Umma ta yi shiru na wani lokaci, sannan ta ce ƙasa-ƙasa
"Ƙwata kwata banji daɗin abinda Zahra ta aikata ba, amma bansan ya zanyi da ita ba"
Mama dake tsaye jikin ɗakin ta tayi wani dariya ta ce
"Ni dai dama tun farko nace yaran nan basu da tarbiyya! Ashe dai ba kawai yarinya ce mai tsegumi ba, har da rashin kunya! Wannan shi ne ilimin boko kenan? Allah ya kiyaye da ace yaran Alhaji Lado ne, wallahi ba haka zasu tashi ba! Amma Malama ya zuba muku ido yana kashe kuɗin mu akanku amma sai rashin kunya da rashin ɗa'a da kuka koyo, yanzu kuma har shi kansa Malam baku bari ba"
Ta kalli Azrah da ke gefe kamar ba ta ma jin mitan, idonta na kan Umma kamar tana jiran ta mayar mata da martani amma sai Umma bata ce uffan ba, Zahra kuwa ta fito daga ɗakin da taga mitar Mama bata da iyaka Bappahn ma baice komai ba amma tana cika musu kunne da magana
Tana rike da kugunta ta karasa cikin gidan tana takawa kamar ba zata taka kasan ba, ta tsaya a kusa da inda sun Umma ke zaune ta zuba mata kallo ɗaya mai cike da raini da rashin jin tsoro, Sannan ta juya kamar ba ta bukatar ɓata lokaci akanta kuma, zauna kan tabarman da Umma da Azrah ke zaune
Mama ta ɗan zaro ido da mamaki, amma tunda ba wanda ya tanka mata sai ta taɓe baki ta juya da jin haushi ta shige ciki tana banbami musamman yadda Bappah ko magana ya kasa
Bayan an ɗan yi shiru, Umma ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce da kakkausar murya
"Zahra, Azrah… ni ba wai ina son halin da Bappah ke nuna mana bane, amma fa ku sani, kowane hali da yayi, Bappah mahaifinku ne Kuma rashin girmama uba ko da ya yi kuskure.. kuskure ne iri ɗaya, gaskiya ba zan lamunci haka daga gare ku ba musamman ke Zahra dan ke ce baki jin magana" Azrah ta lumshe ido ta ce
"Umma kin faɗi gaskiya"
Zahra ta kalli Azrah sai kuma ta kalli Umma sai kuma ta kwanta a cinyarsa ta ce
"To Umma idan shi mahaifine, Mayasa baya adalci ko nuna muku soyayya? Ai tunda ya daina ganin mu a matsayinsa, to mu ma zamu daina ganin sa as Bappahn mu na baya"
Umma ta girgiza kai, zuciyarta na ƙuna amma ta san halin Zahr idan ta kuɗirci abu a zuciyarta, sai Allah kuma
Washegari...
Azrah na zaune a aji amma gaba ɗaya hankalinta baya jikinta Malamar da ke karatu a ajin tana musu bayanin salla dalla yadda zasu gane amma Azrah bata jin komai cos tayi nisa sosai a duniyar tunaninta, abin daya dame ta yanzu shine maganar candy kuma
Tunda ta shiga makaranta da safe, taji wasu 'yan ajinsu suna tattauna cewa an sake fitar da sabuwar candy sannan an saka dateline shikenan kuma hankalin ta ya kara tashi zuciyar ta kuwa ta buga da ƙarfi
"Mummy..."Ta faɗa a ranta, "Allah sarki! Maybe sun manta da maganar candy name amma da nasan kila zasu taimaka"
Kuma yanzu da ba a san lokacin dawowarsu ba, sai taji komai ya sake birkice mata. Damuwa ta shige zuciyarta har tana jin kamar ana sara mata kanta sabar lokaci guda da kanta ya fara ciwo, Tayi kokarin kame kanta ganin bata yi kuka ba amma idanunta suka cika da hawaye
Fatima kawarta ta lura da yanayin Azrah tun bayan shigansu ajin, ta matsa kusa da ita a hankali ta ce
"Azrah lafiya? Me ke damunki ne? Kin yi shiru tun safe fah"
Azrah ta girgiza kai kamar bata da bakin magana ganin kallon da Fatima take mata yasa ta ce
"Fatima... I'm lost, Mummy ta bar kasar nan, Kinsan da kuɗin da take bani karshen wata nake tarawa kuma nake jari, yanzu kuma ina zan samu aiki? Ga kuma maganar candy data tsakanin a rai"
Fatima ta kamo hannunta cike da rarrashi ta ce
"Karki damu Azrah, Allah yana tare da ke zai finding miji wani way out, just trust him In Shaa Allah komai zai wuce"
Azrah ta gyaɗa kai, hawaye na gangarowa a gefen fuskarta ta kwanta tana jin hope
Ko da Azrah ta dawo daga makaranta, ta shiga gidar da sallama amma babu kowa hakan yasa ta wuce ɗakin su, ganin Zahra bata nan yasa kawai ta ɗaura girki kamar yadda ta saba ta dafa tuwo da miyan kuka sbd fav ɗin Imma ne tana gama wa ta kama shara, share dukka gidan harda ɗan compound ɗinsu haka kawai take jin wani iri sbd yanzu da ace Mummy na nan da tana can gidanta, babu aikin data manta batayi ba amma kallo ɗaya zaka mata ka fahimci cewa ba ta cikin hayyacinta
Umma tana kallonta tun daga lokacin da ta shigo, tana lura da yadda Azrah ke tafiya kamar wadda aka zarewa laƙƙa, tana aikin ne amma babu walwala tattare da ita, balle annuri
Bayan sunci abinci, Umma ta juyo da kallonta kanta
"Azrah lafiya dai ko?" Ta tambaya cikin taushi da kulawar Uwa
Azrah ta ɗaga kai tana ƙoƙarin yin murmushi amma hakan ya gagara ta dake ta ce "Lafiya kau Umma, babu komai"
Amma me? Yadda tayi maganar ya sake bayyana yadda take cikin damuwa cos kasan daurewa take, Umma ta kura mata ido tana cigaba da kallon ta da tausayi
"Zo nan ki zauna kusa dani" Umma ta faɗa a hankali.
Azrah ta masa ta zauna a kusa da ita, Sai dai ba ta iya jurewa ba kamar dama jira take hawaye suka fara gangarowa daga idonta tayi ƙoƙarin ɓoye su amma ta kasa
"Azrah!" Umma ta ce cikin tsoro tana dafe kafadarta
"Me ya faru? Kin min bayani, Karki tsorata Ni dan Allah, wani abunne ya same ki ko aka miji?"
Azrah ta share hawayen da sauri
"Umma Mummy ta tafi sun bar ƙasar... bana jin kuma nan kusa zasu dawo, bansan wani aiki zanyi na samu aikin da zanna samun kuɗi irin aiki wa Mummy ba, ga maganar candy na matsowa Umma, wannan sana'ar dana ke yi kuma babu wani riba Kema kin sani"
Umma ta dafa kanta, tana shafa gashinta kamar yadda zata lallashi yaro
"Azrah idan kina magana haka sai naga kamar baki godewa Allah, yadda kike da riƙon addini da karatun Alkur'anin ki ba zai tafi a banza ba, In Shaa Allah, Allah zai baki wata mafitan sa saboda masu zuciya irin taki Allah ba zai bari haka nan ba, balle ma kuɗin a jinyar mahaifiyarki kika kashe kuma ai kuɗin Candyn ki na wajan Mama dole Bappah ya baki dan ba zan bari ki fara biya ba har sai shi Bappahn yaki, dan wannan ai responsibilities dinsa ne"
Azrah ta kwanta kan cinyar Umma tana jin nawin zuciyarta na sauya wa zuwa wani sanyi haka kawai taji wani hope yana zuwa mata dan ba kaɗan ba kalaman Umma sunyi tasiri a kanta, ido ta kurawa ceiling kamar tana karanta wani abu daga cikin ceiling ɗin
"Umma…" ta faɗa a hankali
"Kina ganin... idan na fara yin wasu handmade stuffs zan iya samun kuɗi da kaina? Kamar zasu fi kawo kuɗi akan su gawayin nan da kayan mita ko?" Umma ta kalleta da mamaki
"Wane irin stuffs kike nufi?" Azrah ta ɗan murmusa da
"Kamar accessories, scented oils, ko natural soaps, Na koya wasu tun lokacin da aka taɓa kawo tallafin koyar da handmade stuffs, sannan ga tutorials akan YouTube da na rubuta a littafina, kuma ai Mummy har ta fara koya min tun kafin su tafi..."
Umma ta gyara zama cikin kulawa da damuwa ta ce
"To ki fara kinji ƴar Albarka, Kin daɗe kina ƙoƙari Azrah Allah ya saka miki albarka"
Azrah ta ɗan sake numfashin hope
"I guess this is the time, I want to do something that will remind me of Mummy, kuma idan na samu kuɗi zan riƙa taimaka miki da kaina ba sai sai jiran albashi ko Alkhairi daga mutane ba"
Umma ta dafa hannunta "Ina alfahari da ke Azrah, Allah Ya taimaka miki, Ya saka albarka a abin da kika sa a gaba"
From that moment, hope started to plant itself again in Azrah’s chest, Duk da cewar zuciyarta tana cike da kewar Mummy, amma hakan bai hana ta ganin cewa watakila, this is the beginning of her own story her own path
Da dare, Azrah ta zauna a ɗakin su, hannunta rike da karamin diary dinta littafin da take rubuta tunani, mafarkai da ideas nata, Ta buda littafin tana kallon rubutunta
"Brand name: Azrah Scents & Naturals. Handmade soaps. Lip balms. Oils. Goal: Start small. Grow slow. Stay pure."
Tayi murmushi a hankali, zuciyarta cike da fatan Alkhairi Sai dai tana cire kudi a jaka domin ta fara tantancewa sai ta tsaya cak, Kudin da Daddyn su Suhaila ya bata ya kusa raguwa, Bata ma tsaya lissafa ba, ta san ba zai isa ta fara business da shi ba ganin amount ɗin da zata fara
Ta sauke ajiyar zuciya tana kallon ceiling, zuciyarta cike da tambayoyi
"Ya zan yi yanzu? I was ready… but maybe ba yanzu ba, Maybe this dream has to wait."
Kafin ta rufe diary ɗin sai zuciyarta ta kuma faɗi, Tana tuna halin da suke ciki, kayan abinci sun kusa karewa, babu wake, babu su manda balle albasa, ta leƙa Amma dake nata ɗakin sai ta dafe zuciya da hawaye a idanunta, tana mugun tausayawa Umma
"Toh idan kuwa ba zaki iya business yanzu ba, ki yi abu mafi alkhairi" kamar me whispering haka tayi maganar
Washegari, Azrah ta tashi da sassafe ta shirya, bata tafi makaranta ba, kasuwa ta wuce, duk kudin da ya rage a hannunta ta siyo kayan miya: albasa, attarugu, tumatur, su wake, kuka da daddawa, wanda zata na kullawa a gida, sauran kuɗin kuma ta wuce ta siya musu kayan abinci kawai, a gajiye ta dawo gidan ta zauna tana nunawa Umma siyayyar da tayi Umma ta ce
"Da nasan zaki kashe kuɗin nan dukka da ban barki kin shiga da shi kasuwa ba Azrah, da ko deposit kika kai na candyn ki" Azrah ta ɗan bata fuska ta ce
"Toh Umma haka zamu ta zama babu abinci? Kuma ai naga ke kika kwantar min da hankali" Umma ta ce
"Shikenan, Allah miki Albarka, sai duk cinikin da kika yi ki dage da sawa a asusu" ta gƴaɗa mata kai
Umma ta ce "Allah Ya sanya albarka Azrah"
Azrah ta share zufa daga goshinta tana murmushi.
"
Na fara daga nan Umma, Even if I couldn’t start the big dream today… I can feed my family, And that’s enough for now" .
Baya sallama Isha'i, iska mai sanyi na kadawa kadan-kadan, a harabar gidan, Azrah na tsugunne ita da Zahra suna kulla gawayi, suna ajiyewa a gefe
Gaba ɗaya gida shiru ne dan da alama ma babu s siyama, sai muryoyin su dan suna sana'ar nema da shaawa
Can sai ƙofar ɗakin Mama ta bude da karfi! Mama ta fito ta tsaya tana musu wani kallo cike da kiyaye ta ce
"Yanzu har dare ba zaku ƙyale gidan nan ya huta ba?! Wannan gawayin nan naku ya hanani numfashi saboda ƙura, gidan nan ya zama kamar kasuwa sbd jama'ar ku da kuke tara mana"
Azrah ta yi shiru bata ce uffan ba tana ƙoƙarin kammala na hannunta su shiga ciki
Zahra ce ta dago kai, tana magana kasa-kasq
"Mama ai kullum naga ana sayar da tuwo a gidan nan, ba wanda ya taba cewa kuna bata gida da tara Matan unguwa ma, su taru suyi ta dariya da gulma a nan gidan amma ba'a taɓa magana ba sai wanda zai siya gawayi a bakin kofar gida shine za'a ce muna tara mutane" Azrah ta sake baki tana kallonta with shock, ita kuwa ta fusge kamar ba itace ta gama magana kasa kasa ba
Mama ta daga hannu da sauri tana yi musu ashar
"Ni kike wa magana da rashin kunya ke?! Uwarki zanci shegiya fitsararri ƴar tasha mara tarbiyya kawai"
Zahra ta gyara zama, amma bata ƙara cewa komai ba saima karatu data Fara, Azrah ma tayi kamar ba ta jiyo ba dan bata son fitinan Mama ga Zahra kuma bata iya shiru ba
A nan ne Bappah ya shigo daga waje yana bubbuga takalmi
"Me ke faruwa ne kuma da daddare haka?"
Mama ta nufo shi tana cewa da ƙara
"Ka rabani da waɗan nan yaranka, wallahi ba su da tarbiyya! Azrah da Zahra sun gaji halin Uwarsu, harni zasu faɗawa magana dan nace suna ɓata mana gida dagawayi shine zasu zageni"
Bappah ya tsaya yana kallonsu Kallo guda ya yi wa Azrah, sannan ya kai ga Zahra, ya sauke ajiyar zuciya bai ce komai ba
Ya juya ya wuce ɗakinsa bayan gaishe sa da suka yi wanda ko amsa bai basu ba, Azrah ta gyara buhun gawayin ta shiga ciki a hankali, ba tare da ta kalli Mama ba, amma tana jin zafin kalamanta
We're just trying to survive, Mama.