LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)
Episode 8: A Setback
Bayan wasu kwanaki.... Rayuwa ta cigaba da tafiya musu jita iya yau, amma Azrah koda wasa bata taɓa cire hope ba, tana kuma gwagwarmayarta kamar yadda ta saba, da safe makaranta da yamma sana'a da daddare kuma karatu, Bata da hutu amma zuciyarta na ɗauke da burin zama wani a gaba da hoping bright future, Duk sanda take jin kamar ta gaji, sai ta tuna da cewar babu wani wanda zai gina mata gobenta sai ita. Kuma kullum da safe tana saka ₦500-800 a cikin asusunta da take kiyayewa kamar rainta tana fatan zata kai target kafin lokacin candy
Zahra na taimaka mata sosai, ita ke kai kayan sana'ar da Azrah ke sayarwa makarantar su, Zahra ke kai mata snacks data Fara kanti da kuma makarantar ta, Zahra na ɗaukar nauyin kai kaya ko da rana rana ce bata jin ko wahala as per as zasu samu kuɗin da suke tarawa cos basu dogara da kowa ba takan yawan cewa "Ni da Yayata wallahi mun rantse sai mun fita a cikin wahalar rayuwa, wata rana Umma zata yi rayuwar farin ciki"
Wata rana.. bayan sun gama morning assembly a makaranta, Principal ta hau stage da muryarta mai hope da kwanciyar hankali
"Important notice to all students: Registration for the Candy program is closing in three days. Students intending to sit for the WAEC exam this year should complete their registration by 12 PM tomorrow to avoid missing the deadline. After this time, the final list of participants will be submitted to the relevant authorities"
Azrah ta tsaya cak, Saura kwanaki uku? Zuciyarta ta buga, Hannunta ya fara sanyi, idona ya fara tara ruwa, a zuciyarta ta ɗauki ƙudurin Yau saita gayawa Bappah duk abinda zai yi kawai ya karɓa mata kuɗin a wajan Mama dama ai responsibilities dinsa ne
Da ta dawo gida bayan ta huta kaɗan, sannan ta fita zuwa ɗakin Bappah, wanda ke zaune yana karanta wani jarida, da sallama ta shiga ta gaishe sa
"Bappah…" ta furta a hankali, Ya ɗago kai da murmushi ya ce
"Na’am?"
"Bappah dama ina so na roƙeka ne, Ka taimaka min da kuɗin registration na candy, Sauran kuɗin da nake da shi kaɗan ne sannan kuma jibi zasu rufe" Bappah ya ce
"Shine baki yi magana ba sai yau Azrah" tayi kasa da murya ta ce
"Bappah kaine kace ai kana sane lokacin dana taɓa maka magana sannan ai kace ka bawa Mama kuɗi ta juya, siyasa banyi magana ba" Bappah ya ɗan gyara zama
"Toh ni bani da kuɗin, amma zan karɓo daga wajen Mama idan har zata iya bayarwa" Azrah ta ji wani farin ciki ya lulluɓe ta ta ce
"Nagode sosai Bappah" ya miƙe itama miƙewan tayi ya fita tana biye dashi a baya ɗakin Mama ya nufa sai kawai ta tsaya a compound ɗin tana jiransa, can ta fara jiyo muryan Mama tana faɗin
"Ni babu wani kuɗi a wajena yanzu Malam, Kuɗin magani da sayen abinci sun cinye komai, Ka duba wani wuri kawai dan Allah, amma taya kuɗi zasu zauna ne"
Bappah yayi shiru na ɗan lokaci kafin ya fice daga ɗakin da hannunsa a aljihun wandon sa, Bai ce uffan ba har ya wuce Azrah dake tsaye da idonta cike da hawaye
"Bappah…?" ta kira shi da ta kira sa muryan ta kasa kasa, Amma bai tsaya ba balle ya kalle ta
Zuciyarta ta tsinke, tayi ta kallon dakin Mama, sai kawai ta nufi dakin Umma da hawaye suna gangarawa daga idonta
"Umma… shikenan kenan?" ta faɗa cikin kuka
Umma ta nufe ta, ta rungume ta sosai "Ki daina kuka Azrah, Wallahi Allah zai kawo miki mafita, Kuɗi ba shine komai ba, Ni na san irin ƙoƙarin da kike yi, Allah kuma ba zai bar ki ba" Azrah ta girgiza kai
"No Umma, saura 3days fah! Ya zanyi toh?" Umma ta ce
"Ya ku kayi da Bappahn naku kuma?" Ta ce
"Wai bashi da kuɗi, sannan kuma Mama wai ta gama kashe kuɗin akan kayan abinci da magani, just imagine waɗannan makudan kuɗin ne ta kashe su Umma" tana gama magana ta sake fashewa da kuka, Umma taji ranta ya fara tafarfasa ta ce
"Wuce ciki Azrah" daga haka ita kuma tayi ɗakin Bappah ranta a mugun ɓace tana shiga da sallama ya ɗago kai yana kallonta ya ce
"Lafiya kika tsaya min a kai?" Ta ce
"A'a, i doubt much!" With shock Bappah ke kallonta ya ce
"Ina jinki toh tunda ba lafiyar kike son a zauna ba" ta ce
"Gaba ɗaya nawin da Allah ya ɗaura maka ka yarda su, ka bar yaranka mata suna ɗaukar ɗawainiyar kansu, yanzu idan har Azrah ta biya kuɗin nan ai dai ka tambaya aina ta samu amma kai ko a jikin ka, yanzu yarinyar nan so kake ta fara wani tunanin na daban ko me? Ya za'a yi tace maka za'a kulle abu kace baka da kuɗi" yayin saurin katse ta ya ce
"Toh karya nayi ina da kuɗin ne?" Ta ce
"Idan baka da kuɗin ai da lokacin da ka sayar da mashin ɗinka sai ka bani kuɗin na ajiye musu ko ka bani na ja jari amma ka ɗauka ka bawa Matarka yanzu kuma tana cewa ba zata bayar ba saboda ita ai bata san darajar karatun ba"
Muryan Mama suka jiyo wanda tana kan yaye labulen ɗakin Bappahn "Eh bansani ba kam, saboda ke da kike da karatun da shi kansa Malam ɗin duk rayuwa ɗaya muke a gidan nan dan ina jin gwara Ni ma dan duk nafi walwala daku" tana dasa aya ta tuntsere da dariya
Umma ta juyo dan ita bata da lokacin exchanging words da ita ba, dan lokuta da dama tana bata uzuri dan jahilci ke damun ta tayi ficewar ta ba tare da ta sake bi ta kan Bappahn ba.
Haka Azrah ta zauna banda kuka babu abin da take yi ko abinci ta kasa ci, tun Amma na rarrashinta harta hakura ta kyale ta.
Bayan Magrib tana zaune a bakin katifarsu ta ce "Saura kwana uku kawai…" ta faɗa a hankali "Me zan ce wa kaina idan na rasa damar nan? Sai dai kawai in ci gaba da sayar da kayan miya kenan? Bani da wata mafita kenan?"
Zahra ta zauna gefenta ta riƙe hannunta "Yaya ki daina kuka please, Allah yana tare da mai haƙuri Ki duba irin wahalar da kika sha,kina da buri, Allah ba zai barki haka ba, keep on positive mindset"
Azrah bata iya magana ba Kukanta ta cigaba, A haka har ta gaji da kukan har bacci ya ɗauketa.
Around 2:45 na dare Umma na zaune akan darduma, tana jan carbi, tun ɗazu ta tashi tayi ta salloli tana ma Azrah addu'a sannan Allah ya cire su a wannan wahalar da su ciki
"Ya Allah ka gani, Ba mu da kowa sai Kai, ka yaye wa ‘yata damuwarta, Ya Rabbi ka bata wata mafitan wanda zata ɓullowa wannan lamarin ka tabbatar mata da abinda yake Alkhairi"
Meanwhile a ɗakin su Azrah, Zahra ma sallan take yi tana taya 'yar uwarta addu'a Allah ya kawo musu wata mafitan
"Allah Ka amsa addu'ar Azrah, Ka sa tana da rabo a wannan candyn, Ka duba irin ƙoƙarinta ka bamu wata hanyar da za'a biya mata kuɗin" a haka suka yi ta mata addu'a har asuba tayi wanda Azrah bata ma san sun mata addu'ar ba
Da safe bayan sun idar da Sallah sun gama azkar ɗinsu Azrah ta fita ta fara aikin tattare gidan tana gamawa ta kama wanke wanke sannan ta ɗaura breakfast
Umma dake kallon Zahra ta ce
"Zahra je ki kira min Azrah" bayan Zahra ta fita ko kallon Mama da Yaranta dake bakin murhu suna abincin tallan batayi ba dan yanzu taji ta tsane Mama with passion dan da tana gida abin nan ya faru da tana ji zata iya gaya mata magana, ta wuce su ta wuce inda Azrah take jefa ɗan wake
Siyama ta sake baki tana kallon Zahra da mamaki ganin ta wuce su ba magana ta ce
"Toh yarinyar nan rashin kunya ta karo kenan?" Mama tayi dariya ta ce
"Kyale shegiya suna cikin tashin hankali ne ai yanzu"
Zahra na kallon Azrah ta ce
"Anty Azrah inji Umma idan kin gama ki zo tana neman ki" Azrah ta gyaɗa mata kai kawai.
Umma na kwallon Azrah bayan sun gama breakfast ta ce
"Azrah jeki ɗauko asusun nan ki fasa muga nawa ne kuɗin sai mu san nawa zamu cika" Azrah ta miƙe jiki ba ƙwari duk da yanzu ta hakura ta dai na kukan
Bayan sun fasa asusun suka irga kuɗin suka ga ₦21,000 ne sauran wajan ₦16,000 Umma ta numfasa ta ce
"Zanje gidan su Aziza anjima, koda rance ne zan karɓo, sai ku shirya ku tafi makarantar Azrah dan ba zan barki a gida ba balle ki cigaba da kukan nan"
Murmushi kawai Azrah tayi, ta tattara kuɗin tasa a fos ɗin Umma sannan ta kai cikin ɗakin Umma ta ajiye akan mirror.
Wajajen 12:20pm Abdul ya dawo gidan tun daga bakin kofar yake ta doka sallama amma yaji gidan shiru, ya shiga ya kalli direction ɗin Mama yasan cewa su Siyama suna can wajan tallansu Mama kuma yasan ta shiga wajan Naman asabe ɗakin Umma ya kalla kamar zai fita sai kuma ya karasa ya shiga
Kalle kallen cikin ɗakin su Azrah ya fara sai kuma ya shiga ɗakin Umma idon sa akan fos ɗin ya sauka da murmushi ya karasa ya buɗe fos ɗin ai kuwa yayi tozali da kuɗin dake ciki da sauri har hannunsa yana rawa ya ciro kuɗin ya saka a aljihun sa da sauri ya fito, Azrah da ta taso a makaranta ta shigo gidan da mamaki take kallon Abdul daya fito daga ɗakinsu ta sake baki tana kallonsa ko kallonta bai yarda yayi ba ya fice daga gidan gaba ɗaya
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to ***.
#Jiddatulkhayr
***