LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 10: When fate opens the right door

by @hauwajaywrites

Washe gari tun asuba'in fari Azrah ta farka, damuwa ce fal a zuciyar Azrah, Ba ta yi baccin kirki ba, she's just pretending saboda Zahra, sosai idanuwanta sun kumbura saboda rashin baccin kirki, salloli ta dinga yi har akayi sallah sannan itama ta daura, tana cikin sallah Zahra ta tashi ta fita itama dan ɗauro alwala, tana starring waje ɗaya tana ƙoƙarin gamsar da kanta cewa yau tana da mafita dan da tunanin Jiya ta kwana kuma da shi ta tashi kuma ta gama making mind ɗinta up

Dan bata da wani sauran lokacin and kuma ba zata hakura ba sai ta gwada trying luck ɗinta, zata rubuta candy, Kuma yau ita ce ranar da ta yanke shawarar tunkarar wajan no matter what zata je

Da ƙarfe takwas da rabi na safe, ta fito cikin tsaffin doguwar riga da mayafinta mai launin Maroon wanda ya sake bayyana tsantsan beautyn ta, amma fuskarta cike take da fargaba dan babu annurin amma hakan bai ɓoye kyaunta ba, ta ɗaura jakarta a kafaɗa, cike da takardun candy, da kuma result ɗinta tun daga JSS1 to SS2 da kuma many awards certificate data samu wasu na spellings wasu kuma na best student wasu kuma na debate ne, Zahra ta fito daga ɗaki tana kallonta da mamaki ta ce

"Ina kuma zuwa da sassafen nan Yaya?" Azrah ta mata murmushi ta ce

"Zan je wani waje ne Zahra... Idan na dawo zan baki labari" ta kare maganar da assurance da kuma murmushi karfin hali, Zahra ta ce

"Allah Ya tsare ki Yaya, ya kuma baki sa'a koma menene na san it's going to be best" Zahra ta karasa maganar amma zuciyarta cike take tambayoyi.

Azrah ta leƙa ɗakin Umma ganin tana bacci kawai ta fita ba tare da ta tashe ta ba

Haka ta dinga tafiya da ƙafa, wasu motar su tsareta amma taki tsayawa wasu kuma su biyo ta amma duk babu wanda ta tanka musu, idan sun gaji dan kansu suke kyaleta a haka harta isa....

A gaban Government House taga wani motar na tsaye amma bata ma kalli inda motar yake ba dan wannan bashi ne a gabanta ba

Securities na wajan suna zaune, sai ga wani a bakin gate yana dube-duben masu shigowa da fita Azrah tana tunkaran sa, tana takawa cikin nutsuwa, sai dai a zuciyarta damuwa da tsoro sun fi yawa

"Ke! Ina zaki?" daya daga cikin securities ɗin ya tsayar da ita da tsawa kamar ba dan adam ba

Azrah ta ɗan ja baya da tsoro amma bata bari yayi affecting ɗinta ba cos yanzu ba tsoro bane a gabanta, ta ce

"Don Allah ina son naga gwamna ko wani Babba a ciki" wani kallo ya mata alamar bai gane ba? Irin is she even Okay? Ta ce

"Dama na zo ne akan maganar taimako, ina son na gan..." Tuntsurewa suka yi da dariya dan ba kaɗan ba ta basu dariya ɗayan yana kallon abokin aikin sa ya ce

"Is she even Alright?" ɗayan ya Kalle sa dan shima abin da mamaki ya ce

"I doubt much" Azrah tayi saurin cewa "I'm much Alright sir, taimako zaku min fah, dama government house ba wajan taimako bane?" Ya ce

"Ke! Koma baya! Bamu da lokacin wannan rubbish ɗin naki"

Azrah ta kafe su da ido, idonta cike da ƙwalla Sai wani ɗayan security mai taushi ya kalle ta sai kuma yayi kasa da murya

"Ke! Wayarki akwai kati?"

Ta ɗaga kai da mamaki take kallon sa ta ce "Eh... me zaka yi da ita?"

"Ki kira wanda kika zo nema, idan har da izini kika zo, zai fito ya shiga dake ko kuma ya kira waya ya ce a barki ki shiga"

Azrah ta yi shiru, toh waya ai bata da ita, ace tana da waya ai ba zata ma tsaya a wajan ba da tuni ta sayar, kuma ko da akwai wayan wa zata kira a ciki? Wa ta sani? Sai kawai ta ce "Ban da waya, banzo da ita ba"

"Eh toh, idan baki da waya, kuma baki da wanda zai fito ya shigar dake ko ayi waya, ya kike so mu miki?, wannan ma ai raini ne"

Azrah ta saki ajiyar zuciya

"Wallahi ba raini bane, dama... na zo ne akan maganar candy jarabawar sakandire, Ina nema ne a taimaka min da kuɗin rijista, Ban da wanda zai taimaka min ne sai nayi tunanin nan zan samu mafita tunda ai nan kowa zai iya kawo kukansa kuma a share masa"

"Ke! Ki juya! Bamu da lokacin sauraran karatun novel ɗinnan naki"

Amma kafin ta juya, wannan motar da ta gani tun ɗazu a wajan mai plate no ɗin gwamnati ta kuso kai zata shiga ciki, Azrah ta matsa gefe da sauri tana gyara mayafinta. Da sauri security ya buɗe musu gate, Matar cikin motar ta hango Azrah tana kade hannunta kuma duk tayi abin tausayi, kuma taji Convo ɗinsu, sai ta leƙa ta ce

"Wannan yarinyar fa?"

"Wani matsiyaciya ce da take cewa wai tana son a taimaka mata da kuɗin jarabawa" Matar ta ce da sanyin muryarta

"Ku bari ta shigo, muna buƙatar jin irin waɗannan yaran and she looks serious and responsible"

Security ya harareta amma ya ce

"Ke! Shigo"

Azrah ta kafe shi da idanu na godiya amma bata ce komai ba Tayi shigarta ciki, zuciyarta cike da fargaba da fatan Alkhairi

A cikin ginin Government House...

An kaita wani ofis na musamman a sashin kula da harkokin jama'a wato Public affairs Unit, banda addu'a babu abinda take yi, fatan Allah bata Sa'a kawai take duk da yanzu taji hankalin ta ya kwanta

Bayan ta zauna na mintuna wani mutum mai kamala kuma alamar girma ya shigo Shine Honorable Ibrahim Yusuf ɗaya daga cikin ‘yan siyasan da suka fi riƙewa a jihar da taimako ga al'umma, kallo ɗaya yama Azrah ya ɗauke kansa, Yana magana in very calm way kamar ba wani Babba bane a jihar yana kallon matar dake kofa ya ce

"Who is this girl?" Ta ɗan risina ta ce

"She came for help concerning education, sir" ya ce

"Let me speak to her, bring her in" daga haka ya shige ofis ɗin dake cikin wannan, Matar ta shiga da ita ciki sai kuma ta fito

"Assalamu alaikum" ta faɗa kanta a kasa ya ce

"Wa’alaikumus Salam" ya amsa mata ya ce

"Have a seat" ta ce

"thank you sir" sai sannan ta zauna

"An ce kina da matsala ne akan candy right?"

"Eh ranka shi dade, Sun ce za'a rufe rijista saura kwanaki biyu yau, kuma kuɗin jarabawar wanda na tara da kuɗin sana'ata an sace kuma babu enough time it's already late balle na sake tarawa, kuma a gida ma bamu da su... Na zo ne don neman taimako"

Ya zauna yana kallonta da mamaki

"Kin zo Government House ke kaɗai? Ba tare da rubutaccen wasiƙa ba? Ko wakili ba?"

Azrah ta girgiza kai "Eh... I follow my heart ne na taho Ina ganin idan akwai inda zasu saurare ni to nan ne"

Honorable Ibrahim ya gyara zaman sa dan banda mamaki ta babu abinda yake yi, kuma iyakar gaskiyar ta yake gani a kwayar idonta, maganar kuma itake tara kuɗin sana'ar ya tsaya masa a rai ya ce

"You mena you hustle and still go to school? Sannan ke kika tara kuɗin registern da farko?"

Ta gƴaɗa masa kai ta ce

Yes sir, Ina sayar da kayan miya, ina ƙulla gawayi da daddare, Zahra kanwata tana taimaka min da kai kaya makarantar su, and other stuffs Mun kai rabin kuɗin da ake nema sai aka sace su"

Kawai ya tsaya kallon ta ita kuma ta ɗauka bai yarda bane yasa ta ciro file daga jakkanta ta miƙa masa ya karɓa yana mamakin ganin results dinta, ba kaɗanba ta basa tausayi yasan tasa karatunne a rai shiyasa ya ce

"Me yasa kika cigaba da ƙoƙari duk da wannan wahala?"

Sai Azrah ta kalle shi da idanuwa masu ɗauke da tarihi ta ce

"Saboda bana son zama kamar wasu mata da suka saida mutuncinsu saboda jarabawa Ina da burin zama likita Ina son taimakon mutane... kamar yadda bani da wanda ya taimake ni"

Ya lumshe idanu yana sauraren kalamanta kamar yana karanta littafi mai sutsar da zuciya ya buɗe idon yana kallon ta ya ce

"Ki ba ni tarihin rayuwarki... daga farko, Ina son jin wane irin yara ne ke fuskantar irin wannan rayuwar "

Azrah ta sauke ajiyar zuciya sannan ta fara... ta faɗa masa yadda rayuwa ta canza bayan lokacin da karayar arziki ta samu Bappah, Yadda take aikatau a gidan mutane da irin sana'ar data yi wanda ba zata iya irgasu ba, da yadda Umman ta take fama da lalura har yasa ta bata kuɗin data tara, yadda suke fama dan ita ke ɗaukan nawin kanta da mahaifiyarta sai kanwarta, Bata ɓoye komai ba

Ya ɗaga kansa cike da tausayi ya ce

"Alright... I will help you In Shaa Allah Amma before that give me your number"

Azrah ta kalli ƙasa ta ce

"I don't have a phone sir" ya ce

"No phone? Hmm… Okay, give me your mother's number then"

Ta fara furta masa numbern Umman yana typing a wayan sa ya ce

"Where do you live?"

Ta faɗa masa sunan unguwarsu da kwatancin gidan su

Ya ɗan yi shiru sai can kuma ya ce

"You're brave Azrah, You could've ended up in something else, but you're still focused" ta ce

"Na zaɓi mutunci sir, Ko da wahala ta min yawa, nasan one day definitely zanji daɗin hakan" Ya murmusa

"I respect that! From today, I'll personally support your education in shaa Allah, But I also want you to report back after your exams kunji?" Idanunta cike da hawaye ta ce

"Nagode sosai sir, Allah ya saka da Alkhairi, ya kare ka"

Ya miƙa mata kuɗi

"This is for your Tp"

Ta karɓa da duka hannayenta biyu tana jin babu irin kalmomin da zata iya masa godiya da shi, tana share hawayenta

Ya miƙe tsaye yana kallonta "Ill call your mom, Take care"

Tunda Azrah ta fito daga ciki gani tayi kamar a mafarki ne dan she never expect this, bata taɓa kawo hakan ba balle harta shiga ciki, ta sake share hawayen ta for the countless times ta fito, tana fita ta kalli wani taxi ganin kuɗin da ya bata dayawa ne kawai ta tsare sa ta faɗa masa inda zai kaita sannan ta shiga, har suka isa unguwarsu bata san sun iso ba sbd yadda ta faɗa tunani.

Ko da kuwa bata samu kuɗin candy kai tsaye ba, amma yadda Honorable Ibrahim ya saurareta da mutunci da kuma yadda ya karɓi lambar Umma ya tabbatar mata da cewa akwai hope

Tana shiga cikin layin su Zahra ce ta fara ganinta daga bakin titi wacca ta fita mikawa wani yaro gawayin daya tsaya, da gudu ta nufe ta

"Yaya Azrah! Sannu da zuwa! Ya akayi? Ina kika je? Naga is like your happy" duk ta jero mata waɗannan tambayoyin lokaci guda

Azrah ta janye mayafinta ya ɗan koma kafaɗarta, tana sauke ajiyar zuciya ta ce

"Bari mu shiga cikin gida mana na huta kadan, sai na faɗa miki" Azrah na gaba Zahra na Binta a baya suka shiga

Zuciyar Umma cike da tuhuma da mamaki tana kallon Azrah daga jikin kofa data fito daga ban ɗaki, zuciyarta na bugawa ta wuce ɗaki alamar bata so suyi maganar a tsakar gidan hakan yasa su Azrah binta a baya tana shiga ta juyo tana kallon Azrah ta ce

"Ina kika je Azrah?" Azrah ta zauna tana sauke numfashi tana kallon Umma cike da nutsuwa ta gaishe da Umma ta amsa

"Azrah daga ina kike haka?" Umma ta kuma jefa mata tambayar, Azrah ta ce

"Umma daga Government house nake" ta karasa maganar tana ciro bunch of money da yana bata, a take Zahra da Umma suka haɗa bakin cewa

"Daga Government house kuma?" Abin yaso bata dariya ta ce "Eh daga can nake"

Azrah ta zauna, ta ajiye jakkanta sannan ta fara bayani, Cikakken bayani, tun daga shigarta Government House, drama da securities, zuwa taronta da Honorable Ibrahim, Sai da ta kai karshe sannan ta ce

"Shine ya tambaye ni tarihin rayuwata, ya karɓi lambar ki... ya ce zai kira, idan Allah Ya yarda, zai taimaka"

Umma ta zuba mata ido, tana mamakin yadda ‘yar cikin cikinta ke da wannan ƙarfin hali da hikima, Kafin tace komai Zahra ta ce

"Yaya Azrah... Gaskiya I salute ur courage, yanzu kenan zakiyi waec da necon cikin kwanciyar hankali, Allah saka masa"

Azrah ta ce "Ba mu tabbata ba har yanzu... amma ko bai bani ba ace ma bai kira ba ai kuɗin daya bani na mota dashi zan yi amfani dan wallahi nasan nan ya kusa 80k"

Umma ta zuba mata idanu, ba don tayi shakkar Honorable ɗin ba, sai dai fargabar yadda duniya take a lalalce ta ce

"Allah Ya kawo mafita, idan har da manufa ɗaya yake son taimaka miki Allah basa iko, Amma ina fatan babu wani abu da kikayi wanda zai kawo mana matsala...?

Azrah ta girgiza kai "Wallahi babu Umma"

Umma ta sauke ajiyar zuciya "To Allah Ya saka masa, ke kuma Allah miki Albarka"

A bangaren Honorable Faruq...

Bayan tafiyar Azrah da yamma Honorable ya kira lambar da aka bashi, Umma ce ta ɗauki wayan ta kai kunne

"Assalamu Alaikum, ni Honorable Ibrahim ne daga Government House. Ina magana ne akan ‘yar ku Azrah"

Umma ta ce cikin girmamawa "Wa'alaikumus Salam, eh ranka shi dade, Allah ya saka da Alkhairi, ta dawo gida ai tun ɗazu"

"Na kira ne in tabbatar muku da cewa za mu taimaka mata da kuɗin candy. Ba za mu bari irin azamar da take da ita ta tafi a banza ba, sannan zanyi kokarin ganin sunanta ya shiga cikin wanda zasu samu scholarship da yarda Ubangiji"

Umma ta ji kamar ta saki ihu dan murna, idonta ya fara tara kwalla, tana fara masa godiya ya katse ta da wuri

Ya ce "Ku ci gaba da tarbiyyarta yadda kuke yi, sannan ku barta akan dream ɗinta, Karku hanata tunda har ta iya neman na kanta kuma ta iya ɗaukan karatun ta"

Bayan sun gama magana yace su turo da acc details wanda ba ɓata lokaci suka tura amma sai da suka sha mamaki ganin ya turo 500k instead 50k da suke nema.

Da daddare... acikin ɗaki Zahra da Azrah suna zaune a saman katifar su, Azrah ta jingina da bango Zahra na kallonta kamar zata yi tambaya can ta kasa daurewa ta ce

"Yaya... kina tunanin yanzu rayuwarmu zata fara sauyawa ne?'

Azrah ta ce da sanyin muryarta

"Zahra wallahi ni ma haka nake tunani kuma nake fata, Amma ba zan sa rai sosai"

Zahra ta langwabar da kanta, tana murmushin da ke nuna kwanciyar hankali

Washegari da safe...

Duk suna zaune bayan sun gama breakfast suna lissafin yadda zasu yi, Azrah kuma tana so su gama ta shirya zuwa makaranta kawai wayan Umma yayi ringing, Zahra ta daga da sauri tana mikawa Umma ta ce "Umma honorable ne"

Umma ta ɗauka ta gashe sa ya amsa cike da girmamawa yace

"Mun tura details ɗinta zuwa Government Education Board. Zata iya zuwa ta cike form ɗinta da gaggawa idan waec ko neco ya fito zata kai musu anan ne scholarship dinta zasu bata, amma zata jana Jamb da farko"

Umma ta fashe da kukan, su Azrah suna jira ta gama ta basu bayani saboda su basu jin komai amma yanayin umma kuma sun san wani abunne

Wani mako bayan nan...

Azrah ta kammala rijistar candy da taimakon honorable Kamar mafarki, amma gaskiya ce Haka rayuwarta ta fara ɗan buɗewa as not expected.

#Jiddatulkhayr

***