LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 11: A visit that stirred Hearts

by @hauwajaywrites

Tun bayan kiran da Honorable Ibrahim ya yi wa Umma da cike da mutunci, zuciyarsa ta kasa samun nutsuwa, ya zauna a ofishinsa yana tunanin Azrah yadda take magana da nutsuwa, kyakkyawan tarbiyyarta, tausayin da ke cikin idonta duk da irin mawuyacin halin da take ciki. Ba kawai ya ji tausayinta ba ya fara jin wani abu fiye da haka.

Yana komawa gida daren nan, maimakon ya wuce kai tsaye ya shiga gida as usual, ya zauna a cikin motarsa yana kallon hoton daya ɗauka da camera ɗin CCTV lokacin da take zaune a office ɗin

"Wannan yarinya... me ke damunta har haka? Kuma me yasa na kasa mantawa da ita tun jiya?" Yayi maganarsa shi kaɗai kamar yana jiran jin amsan daga garesa kuma.

Zuciyarsa na masa tambayoyi da yawa, A daren ranar bai samu bacci ba cos duk lokacin da ya rufe ido, sai hoton Azrah ya bayyana a zuciyarsa. Yanzu kam ya sani ba iya tausayi ba, zuciyarsa ta fara jan shi zuwa wani sabon yanayi, Ya fara tunanin "Me zai hana in taimaka mata gaba ɗaya? Ko... ko kuwa aure... ?".

Washegari....

Azrah na zaune a kitchen tana girkin abincin rana da misalin karfe 10 na safe, tana so ta kammala ta taje gidansu Fatima dan karɓan wasu takaddun da zasu fara na jarabawar candy wanda yanzu tana hundred percent assurance zata zana both waec da neco saboda ko bata ci candy ba tana da kuɗin da zata biyawa kanta balle ma bata fatan hakan, muryan Maman asabe da Mama taji a compound ɗin suna magana Mama ta ce

"Ke Ni yanzu abin nasu ma ya fara tsorata ni, Ni fah kullum idan aka ga yarana sai ace yaran wancan matar ne masu tarbiyya amma banda nawa dan suna zuwa tallah, amma wallahi Naman Asabe ina faɗa miki lafiyayyan abinci suke ci kuma ba Malam bane ya tsaya musu" Naman asabe ta riƙe haɓa ta ce

"Iko sai Allah, toh daga ina kenan suke samun kuɗin da suke siyan kayan abinci ni Uwani?" Mama na kwashe abincin sana'arta ta ce

"Yanzu ke har sai nace muku gashi? Yarinyar da ake ganin tafi kowa kyau a unguwar mana ita yasan inda take zuwa suke bata kuɗi" Maman asabe ta riƙe haɓa ta ce

"Kice yanzu dai ker take kallon mu?" Mama ta ce

"Tun yaushe kuma, ranan fah haka wani ya kawo mata kaya cikin Ghana, gashi bata wanka sai da sabulun turawan nan, ke baki ganin yadda jikinta yake wani sheki Ni" Maman asabe ta ce

"Bariki, wato shi yasa take jin tafi karfin yaranmu siyasa ko magana bata musu" Mama tayi wani humming,

Zahra ta fito a zuciye ta karasa inda Azrah take zaune ta ce

"Anty Zahra tashi ki shiga ciki zan karasa" Azrah ta Kalleta ta ce

"Ki bari zan karasa kawai, though nagama ai" ta sauke stew ɗin kan wutan tana mikawa Zahra kulan abincin, ta karbi kulan ko kallon su Mama batayi ba balle su sa ran gaishe su, tana hanyar ɗakin Umma ta ce

"Kai jahilci ma bai yi ba, Yaya kiyi sauri kizo ki tafi kinsan baki da lokacin ɓatawa" daga Mama har Maman asabe suka ɗaga kai suna kallon Zahra da har ta shige ɗakin Umma, Mama ta miƙe ta wulwulo wani ashar ta jefa mata ba, ta fara banbamin masifa da ashar

Azrah ta wuce su ko kallon inda suke bata yi ba, dan ita tana mamakin hali irin na Zahra, harta shiga ɗakin Umma bata Kalle su ba, Umma ta ce

"Zahra nace ki fita ki basu hakuri, basu haife ki bane da zaki jefa musu magana?" Zahra ta ɓata fuska ta ce

"Umma kinji na zage su dan Allah? Ko kinji na kira sunan wani? Kawai fa ina magana da Yaya ne nace ta shigo ciki saboda jahilci beyi ba"

Azrah ta zauna ta ce "it's okay Umma, yanzu idan ta fita maganar kuma zai dawo sabo saboda kinsan ba zasu kyaleta ba"

Zahra ta miƙe ta wuce ciki, ba tare data kalli Umma ba dan wallahi Umma ne ke taka mata burki

Kamar yadda kwana biyu honorable ya kasa manta Azrah haka yau ma har ya isa ofis, amma ba zai iya aiki yadda ya saba ba, yana jinsa very weak, kawai ya ɗauki waya ya kira wani amininsa a Education Board, yana ɗaga wa bayan sun gaisa ya ce

"Please idan yarinyar nan ta sake zuwa akan cika scholarship ɗin da nace a bata pls a sanar dani, Kuma ku tabbatar bata shiga wata matsala ko cin mutunci a kowanne mataki, sannan bana bukatar wani daga cikin staff ya nema mata magana idan ba abinda ya shafi cika maganar scholarship ɗin bane"

Mutumin ya yi mamaki, sai dai baice komai ba a haka suka yi sallama.

Kwana biyu bayan haka...

Rayuwa na tafiya musu yadda suke so, Alhamdulillah yanzu ba zasu ce ga wani abu da suke bukata ba, sun bunƙasa sana'ar su ba tare da sun dogara da Bappah ba.

Azrah  tana can jikin katifa tana gyara jaridun da suka tsufa na Bappah tare da wasu old books ɗinsa da sometimes take karantawa, Zahra ta shigo tana kallon Azrah ta ce

"Aunt Azrah! Umma na kiran ki"

Tayi saurin mike wa, zuciyarta na tafi ya fara bugu da karfi dan haka kawai taji wannan kiran bata yarda da shi ba

A cikin ɗakin Umma, ta tarar da Umma tana riƙe da wayarta a kunne, Azrah yanayin data ga Umma na waya ta fahimci da Honorable take waya, ta sake baki tana kallon Umma da zuciyata take jin yana kara sannanta bugawa, Umma ta miƙa mata hannu alamar ta zauna sai kuma tayi sallama da honorable, Umma na kallon Azrah ta ce

"Azrah mutumin nan ne Honorable, ya ce zai zo gidan nan gobe"

Azrah ta buɗe baki amma ta kasa cewa komai sai kallon Umma da take ba ko kiftawa, Umma ta cigaba

"Ya ce yana so ya zo ya gana da mahaifinki"

Kamar saukan a rasu haka Azrah taji a kunnuwanta, jikinta yayi sanyi, Me zai ce? Me zai nema? Ta rasa abin cewa sai kallon Umma kawai take yi.

Da yamma bayan Bappah ya dawo daga Majalisar sa, Umma ganin Mama bata nan yasa kawai ta miƙe ta nufa hanyar ɗakinsa da sallama ta shiga ya ɗaga kai yana kallon ta ya ce

"Allah sa lafiya dai, dan bana son tashin hankali Bitti" Umma ta dinga kallon sa sai kuma ta daure ta zauna tunda ba abinda ya kawota ba kenan ta ce

"Malam dama honorable Ibrahim ne yace zai zo gidan nan gobe, toh yace yana son magana da kai ne" Bappah ya dinga kallon ta kamar bai fahimci me take nufi ba ya ce

"Ban gane ba? Me kuma haɗi na dashi? Sannan ina kika sansa?" Umma ta ce

"Shine wanda ya biyawa ƴarka kuɗin candy, yanzu kuma yana bukatar haɗuwa da mahaifinta ya ce, shiyasa na maka magana" sai sannan Bappah ya sake fuskansa ya washe baki ya ce

'Toh..toh.. ai sai kiyi bayani tun farko, shikenan Allah kawo sa goben, Allah yasa kuma Alkhairi ne zai kawo sa" Umma ta taɓe baki ta miƙe ta fita daga ɗakin Bappah

Bayan ta koma ɗakinta a'a usual kamar yadda ko wani garin Allah ya waye rana ɗaɗɗaya ne bata ɓuya tayi kuka haka yanzu ma tana shiga ɗaki ta wuce ta zauna a bakin katifar ta ta zauna ta rufe fuskanta da ɗankwalin ta tana share hawayen daya fara gangaro mata, tana jin zuciyarta na kuna bata san yaushe zata daina wannan kukan nata ba, bata san yaushe zata jita at ease ba, sometimes takan yi dana sani amma it's already late balle ta gƴara, jin motsin Zahra yasa ta goge fuskarta ta kwanta kamar mai bacci....

Da daddare bayan Isha'i Zahra ta dawo daga aika, idonta akan roban sauran awara da ya rage a cikin roban da ake fita da shi talla, bin compound ɗin tayi da kallo ganin babu kowa yasa ta tafi da ɗan sauri amma tana yi dan karta making any sounds, buɗe robar tayi ta juye sauran awara da akalla zaiyi na 2k a kasar hannunta dan kamar zai zuɓe ma saboda laidar ya masa kaɗa, jin motsi daga bayi yasa tayi sauri ta shige ɗakinsu tana ɗan leka ta jikin labulen taga Siyama ce ta fito, karasa cikin ɗakin tayi tana dariyar mugunta ta zauna tana miƙawa Umma katin data tsiyo mata

Azrah dake kallon ta da mamaki ta ce

"Aina kika samu wannan uban awaran Zahra?" Zahra ta jawo plate da Azrah ta gama cin abinci ta juye a ciki tana cewa

"Gidan su kawata na biya na karba, kinsan dama jita muka haɗa kuɗi shine yau ta mana" Zariya ɗiba ta koma gefe ta fara ci, Umma ta ɗauki guda biyu ta kai baki, Zahra ta ce

"Umma kara mana" Umma ta girgiza kai ta ce

"A'a Zahra wannan ma ya min" wani ashar suka biyo daga can compound, Zahra ta fara jin awaran da sauri kamar wacca take da ciwon yunwa, jin kalmar da Siyama ta faɗa ga kuma Mama ta fito itama tana masifa yasa Umma da Azrah kallon Zahra data ki haɗa ido da su, Siyama ta ce

"Wallahi Mama na shigo da awarar nan, kawai daga shiga bayi shine fa aka ɗauke"

Umma na kallon Zahra ta ce

"Zahra mayasa zaki yi haka? Baki san sata bane hakan?" Zahra ta taɓe baki ta ce

"A cikin kuɗin Yaya da suka ɗauka ne na cira" Umma ta ce

"A'a bana son haka Zahra, wannan ba hali mai kyau bane, wanda ya maka mara kyau ka saka masa da Alkhairi haka rayuwa take sai Kiga rayuwar ka yana kyau" Zahra ta taɓe baki ta juya taki kallon su Umma, Azrah ta ce

"Umma ɓata bakin ki kike da Zahra, amma Zahra bata jin magana wallahi" Umma ta ce

"ɗauki awarar ki mayar musu, sannan sai ki biya su kuɗin wanda kika ci" Zahra ta miƙe a zuciye ta fita compound ɗin ko kallon su Siyasa da suke zabe zage da tsinuwa bata yi ba, direct waje ta nufa tayi ɗan gaba da gidan su ta tara almajirai tana musu sadaqa.

Washegari...

Tunda suka tashi suka gyara gidan, Umma take gidan Maman Aziza ta karɓi aron dadduma mai kyau wanda idan at least honorable yazo zai iya zama akai, suka gƴara gidan suka share tas.

Kusan ƙarfe huɗu na yamma, wata mota ce ɗalleliya ta shigo cikin unguwar ta su,  Kowa sai kuskus ɗin magana ake yi, wata babbar mota ce me tinted glass ta tsaya a gaban gidan su Azrah wanda har yaran unguwar sun fara taruwa suna kallon motar

Zahra ce ta fara leƙa kofar gidan dan ganin menene bayan ta samu labari daga yaran unguwar da suka shiga suka shafa musu, tana leƙa wa ganin motar ta koma ciki da sauri ta ce

"Aunt Azrah Motar Honorable ce wallahi!"

Azrah ta kalli kanta a madubi Zuciyarta na cike da ruɗani, ta shafa ƙirjinta a hankali, tana jin kamar numfashinta yana tsayawa ta ce

"Ya aka yi kika san shine?" Zahra ta ce

"A kofar gidan nan fah naga ya tsaya, kuma waye yace zai zo idan  bashi ba, hala ma sonki ya ke wallahi" Azrah ta wurga mata wani kallo daya sa ta zanye bakinta tayi shiru

Can sai ga wayan Umma ya fara ringing, bayan sunyi magana ta wuce ɗakin Bappah ta sanar da shi akan ya iso

Bappah ya fito cikin shadda mai kyau, ya karasa har kofar gidan ya shigo da shi, suka zauna anan compound akan dadduman da aka shimfiɗa, ko kaɗan bai nuna ma kyama ko wani abu ba

"Barka da yamma Honourable" Bappah ya ce cikin ladabi

"Lafiya lau Baba, Na gode da damar da ka bani"

Honorable ya sake gaishe da Sallah cike da girmamawa, ya kawo maganar yadda za'a duba lamarin su Azrah game da scholarship akan dan Allah Bappah ya barta idan ta samu, ya ce

"Na sha mamakin yarinyar nan, Tana da ilimi, nutsuwa, da burin rayuwa"

Bappah ya ɗago kai ya kalle shi.ya ce "Haka ne sun gado hakan ne daga mahaifiyar su" sai kuma Bappah yayi shiru jin wani bakon yanayi da lokaci guda ya ziyarci jikinsa

Honourable yayi shiru kamar mai nazari sai kuma ya dake ya ce

"Dama na zo neman Alfarma ne ina kuma fatan zaku taimaka min" Bappah ya dinga kallonsa toh me suke da shi da har zasu iya ba sa, can Bappah ya ce

"Allah yasa muna dashi ma tukun" Honorable ya numfasa ya ce

"Idan har ba'a ma Azrah miji ma ina neman Alfarman a bani aurenta dan Allah" Bappah yaji tambayar a ba zata dan this is the least da zai kawo ran sa, ganin shirun Bappah yasa ya ce

"Nayi maka alkawarin ba zan hanata karatu ba, sannan zan gina mata future mai kyau da yardan Allah, dan Allah ka taimaka min"

Bappah ya sake yin shiru, sai daga bisani ya ce

"Zan tambayi iyalina, Amma ba zan hana ƴata cika burinta ba... in har hakan ba zai rusa rayuwarta ba"

Honorable ya ce

"Nagode kwarai, Allah ya saka maka ya tabbatar mana da Alkhairin sa" daga haka Bappah ya raka honorable har waje wanda ƴaran unguwar sun taru jikin motar suna kallo

Bayan tafiyan honorable Bappah ya shiga ɗakin Umma direct inda ya tarar da su zaune duk suma sun kosa suji make faruwa

Bappah yayi gyaran murya ya ce

"Toh abinda ya kawo sa wai yana so a basa auren Azrah ne idan ba'a mata miji ba"

Daga Umma har Azrah da wani expression suke kallon Bappah wanda ba zaka iya tantance what exactly fuskar su ke nunawa ba, Azrah ta fara girgiza kai, Umma ta ce

"Amma Malam ai Azrah tayi karama, ko gama secondary school bata yi bafa"

Bappah ya ce "Toh ai ba yanzu bane Bitti, dole zamu ce amsa sai ta gama secondary school, kuma yace ba zai hana ta karatu ba, zai barta ta cika burinta"

Zahra ta ce "Ahtoh, dama nasan mutum irin honorable ba zai hanata karatu ba" Umma ta ɗauki pillon gefenta ta wurga mata ta ce "ta shi ki bani waje mara kunya" Zahra na dariya ta miƙe ta koma ɗaki

Azrah da har idonta ya cika da hawaye, umma ta riko hannunta cike da lallashi, Bappah yana kallon Azrah ya ce

"Na san wannan ba burinki bane Azrah, Amma idan har zai bar ki ki cigaba da karatu, ya dace mu karɓa, amma think first"

Zahra ta sake lekowa

"Ina ganin ki yarda wlh Yaya, Kema ai kin san irin wahalar da muke ciki, Kuma ya ce ba zai hana ki komai ba"

Azrah bata iya cewa komai ba sai hawaye, can ta ce

"Na yarda... amma fa... ban san me rayuwa zata bani gaba ba, I'm just scared" tunanin ciwon Umma data yi kawai yasa taji ta amince masa.

Daren ranar...

Azrah na kwance, idonta biyu tana kallon sama, tana jin zuciyarta ya mata nawi, tayi addu'a da fatan hakan ba zai zama kuskure ba a rayuwar ta, dukda tana jin tsoro, but duk sanda ta tuna Umma kuma sai tayi calming kanta down"

A bangaren honorable kuwa..

Honorable yana kwance a kan gadonsa, Hoton Azrah da ya ɗauka a government house yana kwance a fuskar wayar, kuma tun ɗazu yake kallo, Yayi murmushi

"She's different Ya Allah" ya faɗa a hankali.

This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to ***.