LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)
Episode 12: Whispers and Watchful Eyes
Tun bayan tafiyan honorable har bayan kwana biyu bata sake jin motsin sa ba, dama koda yake kira da wayan Umma ne, har taji hankalin ta ya kwanta dan ta mayar da hankalinta sosai akan karatunta da kuma jarabawar da suke yi...
Tana fitowa a exams hall ɗin, ta zauna a jikin wani wall tana maida numfashi saboda zafin da hall din yake da shi, fifita kanta take yi, kamar ance ta ɗaga kanta kawai idonta ya faɗa cikin na Sagir, tana processing ɗin inda ta taɓa kallon face ɗinsa amma ganin ta kasa tunawa kuma har sannan ita shi ma ita yake kallo yasa ta ɗauke kanta zuwa wani direction amma me? Idon ta ya sauka cikin na Sadeeq, nan take taji wani bugawar zuciya, ɗan yamutsa fuska tayi ta ɗauke kallonta daga gare sa, sai yanzu ta tuna inda ta taɓa kallon sa, wani tsaki ta ja ta miƙe daga zauna da take, sake haɗa ido tayi da Sagir wanda yana mata murmushi amma koda wasa bata mayar masa ba, gaba ta kara sai kuma ta jiyo murya Fatima
"Azrah!" Cak ta tsaya ba tare data juyo dan bata bukatar sake haɗa ido da su, Fatima ta karaso ta na cewa
"Okay.. da ban fito ba da tafiya zakiyi ki barni?" Azrah tayi murmushi ta ce
"Ke, I'm moody ne, kuma naji na bar wajan" daga haka suka kama hanyar gida..
Azrah tana isa kofar gidan su ta fara jin hayaniyar Zahra da Habiba, da sauri ta karasa shiga gidan tana kallon Zahra data sha ɗanmara tana zazzaga ma Habiba magana kamar yadda itama Habiban tayi da alama dambe suke shirin yi yasa taje da sauri ta riko Zahra tana cewa
"Zahra kina da hankali? Ki wuce mu shiga ciki" Zahra ta kwace kanta ta ce
"Kinsan me tamin ne Yaya? Daga ajiye kuɗin gawayin da wani ya tsiya a waje na fah ta ɗauke, ina kan zuba masa kayan miya a laidar fa, kuma ina ganin kuɗin a hannunta shine wai ba zata bayar ba, Mamanta kuma wai taci Uwa ta, ce mata aka yi Habiban ta isa min wani abun ne?" Azrah ta ce
"It's Okay, ki barta kawai tunda tace bata ɗauka ba, kina amfani da ilimi not all the times zaki tsaya faɗa" Habibah ta wawulo wani ashar ta jefa ma Azrah ta fara zazzaga mata magana, Zahra ta kwashe da dariya ta ce
"Wallahi sai kin biya wannan kuɗin ko kuma bashi kika ci" daga haka tabi bayan Azrah da sauri, bayan ta shiga ta samu already Azrah harta zauna tayi wani iri ta Zahra tw ce
"Yaya mene ne kuma?" Azrah ta ce
"Wallahi ban faɗi maganar dan nayi hurting dinta ba, sai dana faɗa kuma ya dame Ni" Zahra ta ja tsaki.
Washe gari.... Tunda Ayrah ta tashi yau haka kawai take jinta so tense, idan ta tuna wai Honorable zai zo gidan kuma wajenta zaizo sai taji kamar tayi kuka, tana tunanin wai da kansa zai zo?, ba wai magana a waya ba, ba kuma ‘yan aike ba, at this point bata san ko haduwar ta dashi Alkhairi ne ko akasin hakan ba, Tunanin nan ya ishi Azrah tun tashin ta daga bacci..
Zaune take a bakin katifarsu ta jingina da bangon ɗakin, tana starring one place, Zahra na gefenta, tana kokarin goge mata hijabin da zata saka, domin Umma ta ce kada ta fita da gyalle tayi using hijab sbd idan mutum kamar Honorable zai zo cikin gidan at least tayi shigan mutunci
"Kina jin tsoro ne ko kunya?" Zahra ta tambaya tana kallon fuskarta
Azrah bata amsa ba, Kamar zata fashe da kuka, amma ta ɗan daure, ta kalli gugan da Zahra ke mata ta ce
"Zahra... bana son wannan attention ɗin"
"To me kike so?" Zahra ta ce da dariyar mugunta
"Karatu ne kike so ko? Toh Mango park uwar karatu sai kin shanye komai a bokon kenan? To ai Kuma ya ce ba zai hana ki karatu ba ai ma yafi Sadeeq ko Saif ne ma?"
Zancen Saif ya tsinka zuciyarta, tana mata wani banzan kallon ta ce
"Waye kuma Sadeeq?" Zahra ta buɗe hannayenta alamun bata sani ba sai ta fara dariya ta ce
"Toh Nima na san sa ne? Kawai naji sunan ne yafito min daga baki" Azrah taja tsaki ta ɗauki littafinta tana forcing kanta da karatu
Can yamma sai ga wasu yara biyu sun shigo gidan da gudu suka yi wajan dakin Umma suna wai wani a waje yace a kira masa Azrah, Zahra tayi saurin cewa
"Okay, je kuce gata nan fitowa" Sai kuma ta mayar da kallon ta kan Azrah tana Murmushin Mugunta, ko da wasa Azrah taki kallon direction dinta kuma bata tashi ba, dan ita tasan yadda zuciyarta yake bugawa da karfi
Ganin bata da niyyar tashi yasa Umma ta ce "Azrah ke baki ji ance ana miki magana bane a waje? Kuma ai kinsan dole honorable ne amma kikayi kamar baki ji ba, ko dan kina ganin yanzu Shikenan zaki iya masa abinda ranki ke so saboda yana son ki" jiki ba ƙwari ta tashi ta wuce ciki bata jima ba sai gata ta fito sanye da Hijabn da Azrah ta goge mata
Tunda ta fita kofar gidan bata gansa ba sai motarsa dake parke hakan ya tabbatar mata yana cikin motar ne amma sai kawai ta tsaya tana kallon wani waje
A wajan honorable kuwa tun fitowanta yake kallonta bai san sanda murmushi tayi escape daga fuskarsa ba, bayan ya kare mata kallo sanin ba zata karasa ba yasa ya buɗe motar ya sauka ya taka har inda take tsaye yayi ƙasa da muryansa ya ce
"Muje cikin motar ranki shi daɗe, cos nan duk wanda yazo wucewa sai ya Kalle mu" ta gagara ce masa A'a haka tabi sa har motar, ta shiga da sallama
"Assalamu alaikum" ta furta muryanta ya soma rawa
"Wa'alaikum salam" Honorable ya amsa da murmushi mai ɗaukan hankali
Yana kallon yadda ta takuren waje guda kana ganinta kasan she's not comfortable da spot ɗin, a hankali ya ce
"Hope kunyi magana da Bappah and kinsan me ya kawo ni wajan ki right?" Kai kawai ta gƴaɗa masa, tana Allah² ya gama maganarsa ta fita dan ji take numfashinta kamar yana seizing ya ce
"Well! Duk da nasan ke ya kamata na farawa magana amma magana da Balpahn ku shine ya fi, and I want you to relax please Karki sa komai a ranki nayi miki alkawarin ba zaki taɓa dana sani ba Azrah" ya kare magana yana kallon ta amma ko making any move da zai nuna zata iya basa amsa bata yi ba, ya kuma cewa
"Karatu Shine burinki?" Ta ɗan Kalle sa sai kuma ta ce a hankali
"Yes, sir" ya ce
"Zan taimaka miki ki cika wannan burin naki, amma bana so ki ji tsoro, wannan ba abu ne da zai hana miki karatu ba, Rather, I want to support you even if you want to become a professor ne Azrah"
Ta ɗan Kalle sa, sai kuma ta fara jin nutsuwa ta ce
"Amma aiki fah? Zaka barni nayi? Cos ina son taimakawa Umma na da kanwata" ya ce
"Bazan hana ki ba, In Shaa Allah" ta gƴaɗa masa kai ya ce
"Kince baki da waya ko?" Nan ma kai ta gƴaɗa masa ya ce
"Okay" wani ɗan karamin paper ya miƙa mata ya ce
"My private line, sai kiyi saving da shi zaki na kira na" ta karɓa daga haka ya sauka ya buɗe bayan motar ya Ciro wani laida sai kuma ya koma motar har sannan laidar na hannunsa
Siyama da Habibah da suka taso daga tallan su duk a gajiye suke kamar wanda aka musu duka lis, tafiyan ma dakyar suke yin ta, ko hirar da suka saba ma babu dan duk shiru suka yi suna tafiyar su, Sai kwatsam suka hangi wata mota mai haske da sheki 'black Lexus SUV', na tsaye a bakin ƙofar gidansu
Habibah ta tsaya cak tana karewa mota kallo, sannan ta runtse ido tana ƙoƙarin processing ɗin fuskar data hango duk da ta ganta amma bata son believing cewa ita ce
"Kai Habibah... kamar Azrah nake gani daga motar can fah!" Siyama ta faɗa a daƙile
"Wallahi nima dai kamar ita nake gani... ko da yake sai dai mu je ciki mu tambayi Mama ko kuma idan muka je kusa ai zamu gani wacece"
Da sauri suka nufo gida cike da ƙudurci, da kuma tabbatarwa idonsu cewa ba ita ɗin ba ce.
Honorable ya ɓata rai ganin yana miƙa mata laidan tana ce masa ta gode ya ce
"Ba zaki karɓa ba ko? Roƙa kika yi da zaki ce A'a ina kyauta na baki? So, babu kyau maida hannun kyauta baya" da kyar Azrah tasa hannu ta karɓa tana masa godiya
Lokacin da suka iso kofar gidan yayi daidai da sanda Azarh ta juyo tana kallon Honorable cike da kunya tana karban laidan tana masa godiya, suka kalli juna ai basu san sanda suka yi hanyar cikin gidan da gudu ba
Suna shiga gida, kai tsaye suka nufi dakin Mama da zuciyarsu ke ƙuna da tafarfasa cike da hassada
"Mama! Wallahi mun ga wata a mota a kofar gida, kuma kamar Azrah muka gani a ciki!" Mama ta tafe kirjinta ta miƙe tsaye a secs sannan ta zaro idanu ta ce
"Azrah? Wace mota? Me kuka gani?"
Siyama ta zayyano duk yadda suka gani, Habibah kuma na gyara mata inda ta kauce
Mama ta nufi kofar gida a hanzarce tana leƙa, amma tuni motar ta fice
Azrah tana ganin reactions ɗinsu taga sun shiga da gudu tasan definitely Gulma zasu kaiwa Mama shi yasa ta fara Allah² ya tafi bata son draman su Mama su fara nunawa a gaban bako, yana cewa
"Toh sai an jima, sai munyi waya ko?" Ai bata san sanda ta gƴaɗa kai ta sauka da sauri ba tana gyara laidar hannunta ta nufa cikin gidan da sauri
Ya bita da kallo harta shige cikin gidan sannan ya shafa fuskan sa ya tada motar ya bar unguwar nasu.
Mama ganin babu mota wajan wayam yasa ta koma ciki da sauri wanda a lokacin har siyama da Habibah suma sun fito ɗan su sake kallo ganin Mama na musu wani kallo yasa suka leka waje da sauri suka ga babu wata mota a wajan.
Azrah na shiga ɗakinsu Umma da Zahra suna zaune har lokacin suna jiran shigowanta duk kallon ta suke harta ajiye laidan hannunta a gaban Umma
"Wannan fa, daga ina?" Umma tayi tambayar
Azrah ta sunkuyar da kai "Honorable ne ya ce in karɓa, har da wannan..." ta miƙa wani envelope, sannan ta ɗaura
"Kuma wallahi Umma naki karɓa shine ya matsa min"
Zahra ta matso kusa tana buɗe laidar ta ce
"Toh a dalilin me ba zaki karba ba? Naga ai ba roka kika yi ba sannan kuma...." maganar ne ya maƙale a bakinta sakamakon ido huɗu da tayi da wani babban waya a cikin kwalinta ta saka wani ihuuu ta tashi tana tsalle sai kuma ta rungume Azrah tana
"Wallahi dalleliyar waya ya tsiyo miki Yaya duba ki gani, ai wallahi kin more, chap kuma shine zaki tsaya kina nuku nuku da irin wannan mutumin" Azrah ta turata daga jikinta tana hararan ta
Umma ta ce "Sannu Zahra, wato idan kene karɓa ma zakiyi har kike ce mata a dalilin me zai sa taki karɓa ko?" Tana dariya ta cigaba da buɗe laidar wasu haɗaɗɗun Abaya ta ciro tana zara ido
"Kalli Yaya! Egyptian Abaya ce wallahi" Azrah ta mike tayi hanyar ɗakin su, Zahra ta taɓe baki ta cigaba da buɗe laidan ganin ɗayan laidan, laidan chocolates ne yasa ta miƙe ta ce
"Nayi nan, dama anan nafi karfi" Umma ta ce
"A'a karki taɓa komai Zahra ki tsaya har Bappahn ku ya dawo ya gani tukun nan" Zahra taki kallon, Umma itama tayi ɗakin.
Zahra na shiga ciki ta ce
"Wayyo chocolate, lallai dan siyasan nan ya sha kwana, ya iya soyayya wallahi, yasa yadda zai sace zuciyar mutum" Azrah ta ɗauke kai kamar bata san tana wajan ba.
Siyama da Habibah dake tsaye a tsakar gida duk suna jin abin da ke faruwa and yadda Zahra ke magana da karfi da kuma ihun ta suka juya suka koma cikin ɗakin Mama suna faɗa mata
Mama data yi tagumi ta wurga musu wata ashar ɗin ta ce
"Yanzu sai ku ɗaga min hankali ai, ina zan samu nayi bacci yau kince min kunga Azrah a mota? Wato ma har saurayi tayi? Na shiga uku Ni Uwani" ta karasa maganar tana kuma sake wani tagumi
Siyama ta ce "kila wanda take yawo da sune fah Mama, amma Ni nasan ba zai so ta ba"
Mama ta ce "Ai ina fatan hakan kuwa, yadda ƴan unguwa zasu sako ta gaba, ace ma ciki tayi Shegiya sai naga idon Uwar tata ai"
Washegari wata babbar motar kaya ce ta sauke kaya a kofar gidansu Azrah, Mai motar ya ce kayan abinci ne daga Honorable buhunan su shinkafa, cartons ɗin spaghetti da macaroni, kaza frozen, indomie, sugar, da sauransu.
Gaba ɗaya layi ya cika da surutu.
Mama ta fito da sauri tana kallo zuciyarta na tafarfasa, ga kawarta Maman asabe ma data shigo tana taya ta aiki
Ta koma cikin gida ta kwalla wa Bappah kira, bayan Bappah ya dawo daga nuna musu ɗakin Umma suka fara shiga dashi dan shima ya rasa bakin magana, Mama na kallonsa ta ce
"Wannan wane irin abu ne? Me ke faruwa? Don Allah ka faɗa min gaskiya!"
Bappah ya cije lebensa, ya ɗan ɗago ido yana kallon ta, a hankali ya furta
"Honorable ne dai ya ce yana son tallafa musu... kuma yana da wani niyyar Alkhairi ne"
Mama ta goge zufa "bangane tallafa musu ba? Toh kai ba zaka ce musu ba'a bukata ba, tsayama Malam wani Alkhairin kake magana kuma akai?"
Yayi kasa da murya "Ina ji kamar dai Azrah yake so"
Mama tayi wani ashar da sai da Bappah yaja baya
"Wato ƴar kishiya ce za'a ce ana so? Kai ba zaka nuna musu Siyama ko Habibah ba? Amma sai kayi shiru?"
Magana da suke wa Bappah yasa yayi waje danjin me zasu ce, Mama ta wuce ɗakin ta hankali tashe, Maman Asabe na binta a baya danjin meke faruwa.