LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 13: The List They Tried to Erase

by @hauwajaywrites

Yau tunda garin Allah ya waye duniyar tama Mama zafi ta rasa me ke mata daɗi, abincin da take a gida yau kam hakura tayi dan bata jin zata iya, tunda taga irin Alkhairin da honorable yake da kuma ɗawainiyar shikenan ta rasa sukuni yau kuma da Bappah ke waya da honorable a gabanta cewa magabatan sa zasu zo tambaya da saka rana shikenan ta sake ruɗewa kuma duk yadda ta dinga ma Bappah da ido amma ya kasa bin maganarta balle yayi stopping Honourable, ita kaɗai ke zaune a ɗaki tana ta faman sakawa da warware wa da tunani, hannunta rike da hijab amma har yanzu bata sa ba, wata makwabciyarsu ne ta leƙo siyan Alale ganin ko murhu ba'a kunna ba yasa ta shiga ɗakin Mama da sallama, Mama na kallon ta cike da abin duniya ya mata yawa ta miƙe ta fara magana a zafafe

"Maman ladi wallahi tallahi, idan har aka ce ba za'a fasa zuwa tambaya ba wallahi ko nawa sai na kashe, sai na kashe ko nawa ne nace, dan ba zan iya zama in kwashi bakin ciki ba ina ji ina gani ƴar kishiya ta shiga gidan Hutu" Maman ladi ta sake baki tana kallon ta sai kuma ta ce

"Haba Maman Abdul, dama rabon da Allah ya bawa wani akwai wani mahalukin da zai hana ne? Ni dai shawara ta ki hakura idan ba mijin ta bane ba za'a taba yin aure ba amma muddun mijin ta ne wallahi duk kinki sai an ɗaura" Mama ta katse ta

"Kimin shiru! Kada ki sake min maganar kaddara anan! Me yasa rabon zai fara da Azrah toh? Me yasa Azrah ce kaɗai bayan ina da nawa yaran" Maman ladi kam abin ma mamaki yanzu ya fara bata tana kallon tsantsan kiyayer Umma a idon Mama

Mama ta miƙe tsaye ta fara zaga ɗakin tana huci kafin ta tsaya, har sannan Maman ladi bata daina kallon Mama cike da mamaki ba, Mama ta ce

"Ki barmin kofar ɗaki dama na daɗe da sanin cewa bakin ku ɗaya da ita ai shiyasa zaki zo kina kare ta naga kema ƴaƴa matan gare ki amma ai har yanzu suna zuɓe a gaban ki! Idan ma Ni kaɗai ce toh sai nasan yadda za'a yi a fasa wannan zuwa gaisuwar wlhi, Malamai kuma nawa ne a cikin garin nan"

Maman ladi ta sake labulen ɗakin Mama ta ce "Ni Kinga tafiya ta, Allah ya yaye miki" daga haka ta nufa kofa sai kuma ta tsaya ta juyo tana kallon kofar ɗakin Umma sai akwai ta fita abinta.

Bayan wasu kwanaki

Bayan sun gama candy har saura kwana biyar su fara WAEC, Azrah ta faɗa duniyar karatu sosai dan koda yaushe tana riƙe da littafin ta, tana kuma kokarin kula da kasuwancinta kamar yadda ta saba, sosai honorable ya bata space ganin ta ɗauki karatun first priority ɗinta sannan zuwan ma ya daina sai dai har sannan basu bukatar komai dan yakan kawo musu everything enough. Wata rana yazo kamar kullum ta same sa a motar sa ta gaishe sa dan har sannan bata iya kallonsa balle ta iya magana mai tsayi a gabansa sai dai a waya, nan ma bawai takan yi sosai bane, tana ta sauraronsa wanda rabin Maganan ma shi kaɗan sa yake yi, ya ɗan ja hankalinta da tambaya

"Azrah, please give me Zahra's full name and age da kuma wani aji take yanzu, I want to do something for her" Azrah ta kallesa cike da mamaki sai dai bata ce komai ba

"Sir... Her name is Zahra Muhammad Sulaiman, She's sixteen, she's in Jss3" honorable ya gƴaɗa kai ya ce

"Perfect! I like her courage... remind me to send someone" Azrah bata fahimce shi ba amma saboda bata iya masa magana yasa tayi shiru kawai

Mama tayi sallama a gidan Maman asabe, Maman asabe ta fito daga ɗakinta tana gyara zanin jikinta ta ce

"A'a Maman Siyama kece a gidan namu, toh karaso mana" Mama ta karasa ta zauna tayi tagumi tana kallon Maman asabe ta ce

"Kinga ba zama ya kawo ni ba, yanzu so nake ki taimaka min ki bani shawara mai zan aikata wanda zai sa a fasa auren yarinyar nan" Maman asabe tayi shiru dan ita bata san me zata ce ba can ta ce

"A'a ga shawara nan, ina kince mutumin ɗan siyasa ne ko? Kawai a ɗauki fuskarta a ɗaura akan video ƴan iskan mata sai a kai masa Kinga ba zai so ace zai haɗa iri da ita ba ko dan kar a ɓata masa kujerar mulkinsa" Umma tayi wani shewa harda miƙewa tsaye ba tare data san tayi hakan ba tana kallon Maman Asabe ta ce

"Toh ai har kin fini tunani, yanzu wa zamu samu su mana wannan aikin ne? Nifa a shirye nake dana kashe ko nawa ne?" Maman Asabe ta ce

"Zan kira Garba naji ya za'a yi dan nasan ba zai rasa sanin masu yi ba" Mama ta fara dariya ta ce

"Kinga kuwa yadda ƴa unguwar nan suke kallonsu kamar gold zasu fara kyamar su suma".....

Umma da yaranta suna zaune suna hirar su cike da sha'awa da ban sha'awa, sai ga wayan Azrah ya fara ringing, Azrah ta ce

"Dan Allah Zahra ɗauka kice ina bacci"  Umma ta kalleta Zahra ta ɗauki wayan bayan sun gaisa ta isar masa da sakon da Azrah ta bata ya ce

"It's Okay, dama ke nake son gani Zahra, ki fito ina kofar gida" daga haka ya katse kiran Zahra na kallonsu ta ce

"Yace wai dama da Ni yake son magana" Umma ta ce

"Toh ki tafi" daga haka Zahra ta ɗauki hijab ɗinta ta fita

Tana isa jikin motarsa ya sauke glass ɗin yana kallonta, murmushi tayi ta ce

"Sannu da zuwa Sir" honorable Ibrahim ya ce

"Sannu Zahra, kin kammala homework ɗinki kenan?" Zahra tayi murmushi ta ce

"Na gama tun ɗazu Sir" Ya ce

"Ma Shaa Allah" wani envelope ya ɗauka a dashboard ɗinsa ya mika mata ya ce

"Take this, naki ne idan kin shiga ciki sai ki duba ko?" Ta karba tana masa godiya, daga haka ya tafi

Da sauri ta shiga dan tana son kallon menene a ciki, Umma da Azrah sai kallonta suke bayan ta Ciro da papers ɗin envelope ɗin Azrah ta karba da sauri dan ganin kamar admission letter ne, sake baki tayi tana kallon papers ɗin, One of the best school ya mayar da Zahra sannan ga receipt na biya mata school fees tun daga SS1 to 3, ga kuma sauran receipts na other stuff, sanin wane shi shiyasa ko maganar interview ba'a nema a mata ba aka gama mata komai, Azrah taji hawaye ta mikawa Umma takaddun ganin yan kashe wajan 1.5M, lokacin da Zahra tayi tozali da sunan makarantar bata san sanda ta miƙe tsaye tana ihu da salle salle...

Azrah na karbar notice daga wani student, dake itace headgirl sai ga wani student ya zo yana kallon ta ya ce

"Senior Azrah principal na kiran ki a office, wai kije" Azrah ta kafe sa da kallo kamar bata gane ba sai kuma ta ce

"Where is he kace?" Ya ce

"Yana office ɗinsa ne" kai ta gƴaɗa masa ta sallame ɗalibin gabanta, Kalle Kalle ta fara ko zata ga Fatima dan ita tun wancan maganar daya gwada mata taji ta tsane sa kuma bata son zuwa office ɗinsa ita kaɗai ganin bata ga Fatima ba kawai ta nufa jiki ba ƙwari

Da sallama ta shiga ta same tare da wani Malami ta ce

"Sir, gani" ko kallonta bai yi ba ya cigaba da magana da ɗayan Malamin har ya gama masa bayanan sannan ya fita, Azrah dake kallon wani waje taji muryan sa

"Azrah look I want to help you, But I can't fight government for a stubborn girl like you" Azrah cikin nutsuwa

"Thank you Sir, amma I'll be fine" Principal ya tsaya kallon ta da mamaki dan bai taɓa expecting haka daga gareta ba, ya ce

"Okay! Out of my office! Since you feel big!" Ta juya ta fita ba tare da taji ɗar ko wani tashin hankali ba dan hundred percent sure honorable ya gama saka sunanta and he has nothing to do sai ya karata da iskancinsa

Da kallo baki buɗe ya bita with lots astonishment, yafi some secs yana processing sai kuma yayi dariyar mugunta ya jawo wani long book da aka saka result ɗinsu na candy a ciki,  cire sunanta daga cikin jerin sunayen da gwamnati zata biya musu WAEC yayi, yana dariyan mugunta ya ce "Zanga me tsaya miki kuwa, zanga karshen rashin kunya ai"

Azrah na fita ta duba bata ga Fatima ba kawai tayi tafiyarta tana mamakin hali irin nasa, tsaki tayi tana sake godewa Allah daya haɗata da honorable sai yanzu ma take sake ganin honorable Ibrahim a matsayin wani wall a gareta...

Zahra na wanke wanke while Azrah na kitchen tana tuka abincin dare, ta gama kwashe abincin a kula ta kai ɗakin Umma sannan ta kwashe waste dishes takai ma Zahra daga haka ta wuce ɗakin Umma ta zauna,  Zahra dake wanke wanke kamar daga sama taji shigowan Abdul wanda da fito ma ya shigo gidan ɗan kallonsa tayi ta ɗauke kai ta cigaba da abinda take yi, ɗan tsayawa yayi ya Kalleta ya ce

"Ke dan Uwarki baki ganni bane da ba zaki gaishe Ni ba?" Tayi kamar bata jisa ba, ya gƴaɗa kansa ya ɗauki buta ya nufa hanyar banɗaki, ajiye kayansa yayi a wajan sannan ya shiga

Zahra ta kai sauran kayan data wanke ta fito tana kallon hanyar toilet inda ya ajiye kayan a kasa, taka wa tayi a hankali harta isa wajan kallon wayansa da tayi a ajiye tare da wasu stuff ɗinsa ne yasa bata san sanda murmushi ya ƙuɓuce mata ba ta ɗauka da gudu tayi ɗakin Umma ta shiga tana haki, Umma na kallonta ta ce

"Wani rashin gaskiyan kika aikata Zahra?" Azrah ta kalleta sai kuma ta cigaba da abinda take yi, Zahra ta zauna tana murmushi

Umma ta kalli wayan hannun Zarah ɗin ta ce

"Zahra wannan wayan waye kuma? Sannan Meyasa zaki shigo a guje?" Ta kare maganar tana tamke fuskan ta, Zahra ta ce

"Dama nayi rantsuwa ai Umma, wayan Abdul ne kuma nace sai ya biya kuɗin daya ɗauka, so yanzu ne right time, ya biya ba tare daya sani ba kamar yadda ya ɗauka ba tare daya tambaye mu ba" Umma ta ɓata rai ta ce

"Zahra bana son wannan halin naki, bana son kina ɗauke abun mutane da sunan kina rama abin da suka miki, how sure shi ya ɗauka" Zahra ta ɓata rai ta ce

"Bayan Yaya ta kama sa" Umma ta ce

"Ki mayar masa nace, obey before complain Zahra" Zahra ta turo baki tana kallon Azrah irin tasa bakin nan amma Azrah yi tayi kamar bata ma san meke faruwa a wajan ba, Zahra ta ce

"Ai naga shi ya fara sace kuɗin candy ɗin Yaya Azrah ranan, Da ba dan Allah ya turo Honorable ba, da ai har yanzu muna kuka"....

Abdul yana fitowa a banɗaki yazo kwashe kayansa sai baiga wayansa ba da sauri ya zazzaga kayan nan ma baiga komai ba, wani ashar ya yi, sake duba kayan yayi da bai gani ba ya fara ihu

"Mutum daga dawowansa sai sata! Wallahi idan ban ga waya ta ba yau za'a ga abinda zanyi a gidan nan ashe baku Sanni bama kenan" Umma tana kallon Zahra da suke jin ihun Abdul da zage zagensa ta ce

"Zahra bani wayan idan ba zaki maida masa ba" Zahra ta ja baya da sauri ta ce

"Umma nayi rantsuwa fah" wani kallo ta mata wanda yasa ta miƙe ba shiri.

Bayan kwana biyu..

An manna sunayen waɗanda gwamnati zata ɗauki nauyin WAEC dinsu, Principal ya ƙaraso da takarda a hannun sa zai manna a notice board saboda kowa ya gani, ya ɗaga hannunsa zai manna sai gani yayi...

"Azrah Muhammad... number one?" With shock written all over him yake kallo

Yayi shiru, ya tsaya, ya kasa motsi, while ga students duk shi suke jira ya manna ɗin su gani hankalin su ya kwanta amma principal ya kasa koda ce uffan ne, kamar me whispering ma kansa ya ce

"Amma.... I removed it myself"...

Bayan kwana biyu..

Zahra ta fara sabuwar rayuwa a private school da honorable ya maida ta, Azrah na cigaba da karatu da kasuwanci sannan har sannan bata barin ibada.

Wata rana ta shiga school saboda research Principal ya kirata bayan ta tafi office ɗinsa ya sassauta nuryansa ya ce

"Azrah..Kin cancanta everything and more, Sorry for before"

Ta kalle sa sai kuma ta rasa me zata ce masa ta ɗan kalle sa taga ita yake kallo sai kuma ta mike ta fita a office ɗin ba tare data ce masa kala ba, principal ya bita da kallo yana mamakin yaushe tazo tana masa kuka akan ya taimaka mata amma yanzu wai yaze a cire sunan ta akan mistake ne sai kawai aka masa warning cewa idan beyi hankali ba zai iya rasa aikinsa.

Da yamma Azrah na tsakar gida tana kulla gawayinta sai ga Siyama da Habibah sun shigo ko da wasa bata ɗaga kai ta lalle su ba, sai kawai taji dariyarsu Siyama ta ce

"Kin ji ‘yar masu baiwa ko?A yanzu ma ita ce first name a list ko?" Habibah ta ce

"Ƴar gayu mana, ai yanzu jin kanta take ita wata shegiyar ce"

Azrah ba ta ce musu komai ba, sai ga Zahra ta fito

"Eh mana, ai dole taji da kanta ko kunga tayi kama da kalarku ce? Ai duk wanda ya ganta yasan ba ƴar gidan wahala bane, balle ta tsaya biyewa jahilai" Azrah ta juya tana kallon Zahra

Siyama da Habibah suka yi kanta da gudu suna zaginta amma ina tuni ta wuce ɗakin su ta window ta sa bakinta tana zagin su

Siyama ta ce "idan ba tsoro ba ki fito mana" Zahra ta ce

"Idan ba girma ya faɗi ba ina ke ina faɗa da Kanwar bayan ki? Ai shine maraban jahili da mai ilimin kenan, yanzu kun taɓa ganin Anty Azrah na cacan baki da ku"

Saukan mari taji da sauri ta juya tana kallon Umma sai kuma ta fara kuka, Umma ta ce

"Zahra ki shiga hankalin ki, bana son Wannan neman maganar naki"

Har sannan su Siyama basu fasa zage zage da suke ba daga karshe Azrah ta koma ɗaki.

Da daddare Mama na zaune a ɗakinta ga yaranta kewaye da ita can ita kadai ta furta

"Auren nan dole sai an fasa dan ba zan yarda ina ganin ƴaƴan Bitti suji daɗin rayuwa ba"...

Few Free pages ya rage, better ku biya kafin labari ya fara ɗaukan zafi

This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to ***.