LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)
Episode 14: The Price of a Daughter
"Ke Maman Asabe, yau ba sai kin zauna ba, mu tafi yanzun nan kafin ya fita tunda kince baya zama" cewar Mama tana takawa da sauri cikin riga da zani da mayafi daya rufe mata har kunnenta.
Maman Asabe tayi wani murmushin mugunta "Toh ai ni dama a shirye nake na ɗauka sai kin huta zamu" ta miƙe ta fara bin bayan Mama Wanda har tayi gaba ta ce
"Wannan mutumin da ake kira Garba dai ba wasa bane, ya taɓa jefa wata ‘yar unguwarmu na can zango cikin matsala har iyayenta suka koreta"
Dukkansu suka nufi bakin titi cikin shigarsu na gaggawa dan babu waccan take cikin nutsuwarta, Mama na ta furzar da iskan baki ta ce
"Ni wallahi ba zan bar yarinyar kishiyata ta fi nawa ba, Ai na haifi ‘ya’ya mata har biyu, ko ɗaya cikinsu ba ta taɓa ganin arziki ba sai wannan Azrah ɗin, In banda isa da ɗabi'a irin tata koda wasa bata yarda tayi wanka da Omo Bansan aina take samun waɗannan kuɗin ba gata sai uban saka kaya sai ka rasa aina take samun waɗan nan"
Maman Asabe ta ce
"Ki kwantar da hankalinki, Idan wannan mutumin Garba ya haɗa video ɗin nan da muke so, wallahi Honourable sai ya gudu da ƙafarsa ko sake waiwayo ta ba zai yi ba, wannan fa har tsoronsa nake kamar ba mutum bane sai kace machine ne".....
Bayan sunje sun faɗa masa yadda suke so ya zama, lokacin da suke hanyar komawa gida, Mama sai murna take dan yanzu hankalinta ya gama kwanciya ta ce
"Wallahi na san wannan abun zai yi tasiri, Yanzu sauran kawai mu nemo hoton ta ko wani short video nata kamar yadda ya faɗa"....
Da daddare a ɗakin Bappah, Umma na zaune tare da shi, duk sunyi shiru ba mai magana a cikin su, sai can Bappah ya daga kai yana kallon Umma ya ce
"Bitti, Honourable ya kira, jibi ne zasu zo a saka ranar auren wai,
ya ce komai ya shirya yanzu"
Umma ta dinga kallonsa kamar wanda ya dawo hayyacinsa dan ita bata yarda da changes ɗin nan nasa gareta ba sai sannan ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Allah ya nuna mana, sannan muma Allah ya bamu abinda zamu fita kunya da shi"
ya amsa da Amin, daga haka ta miƙe ta fice daga ɗakin nasa tana jin damuwarta yana dawowa sabo full bata san yaushe zata goge wannan zanen kaddarar ba? Ita yaushe ne zata samu nutsuwa ga ciwon daya sata a gaba tana tsoron ta mutu yanzu ba tare da ta sake waiwaye wannan......
Bappah ma ya miƙe ya nufa kofa yana haska compound ɗin yana dube dube sai ga Abdul ya shigo gidan yana fito kamar wanda bai san sallama ba
Bappah ya daka masa tsawa sannan yana masa wani banzan kallo ya ce
"Ni dai na gaji da halin ka Abdul, kullum baka taɓa abu kamar nagari, ina ka je bana ganin ka kwana biyu a gidan nan?"
Abdul ya ɗan taɓe baki, "Toh ai ba wani abu nake ba sannan ba wani wajan nake zuwa ba..." Bappah ya daka matsa tsawa
"Toh idan ba wani abu kake ba, sai kayi ta yawo? In baka daina ba wallahi zaka bar min gida na rantse dan bana son iskancin banza da shashanci"
Abdul ya wuce ɗakin Mama yana huci, Mama na zaune tana tsince wake ta ɗaga kai ta kalle shi
"Me ya faru kuma?" ta tambaye shi
"Wannan tsohon faɗa faɗa kamar shi kadai ya fi kowa ganin laifi? Ni dai gaskiya na gaji kija masa kunne, tahm" ya fadi yana zama akan wani ruɓeɓɓen kujera
Mama na kallon yaran nata ta ce
"Yauwa ga wani aiki ya samu, hoton Azrah nake so ko kuma video nata, duk wanda ya kawo min yana da dubu goma"
Siyama da Habibah suka haɗa baki wajan cewa "Ni zanyi" wani kallo Abdul ya musu wanda yasa Siyama ɗauke kai tana hararansa yana kallon Umma ya ce
"Umma ba wanda zai yi a cikin su, naga ba waya garesu ba taya zasu fara, kema kin san wannan aikin nawa ne kawai" Umma na Murmushi ta ce
"Toh ka samu ka kawo min zuwa gobe da safe" yan kallon Umma ya ce
"Zan kawo miki kamar yadda kika ce amma ina fatan kuɗi na ba zasu yi ciwon kai ba ko? Kinsan bana wasa da harkan kuɗi" Umma ta ce
"Kana kawo min zan dasa maka kuɗin ka" ya gƴaɗa kai daga haka ya miƙe zuwa ɗakinsa dan kwnaciya
Washe gari da safe, Zahra ta fito cikin sabuwar uniform ɗinta tsaf-tsaf! Farar rigar da Black skirt sun yi mata kyau fiye da zaton mai zato
Azrah dake wanke wanke a sakar gida ta ɗaga kai tana kallonta ta ce
"Zahra ina zaki haka da wuri?" Ta kare maganar cike da zaulaya
Zahra ta yi murmushi,ta ɗaga jaka "Sabuwar makaranta mana, Private school ma kike ji, Allah ya saka ma Honourable, Allah ya ƙara masa fiye da haka"
Azrah ta yi murmushi bata da buri fiye da ganin Zahra na Murmushi ita da Umma, amma Maganar honorable Ibrahim babu wanda ya san me ke cikin zuciyarta, Hope and pain suna fafatawa
Tana gama aikinta ta fara kulla gawayinta ba tare data kalli Mama da Maman Asabe da suke tsakar gidan suna haɗa kayan tallah, tana ji suna jefa mata magana amma sai tayi kamar bata ma fahimce su ba ma dan ta basu uzuri yau ta sake gaskata rashin ilini na haifar da komai but how iyn earth zaka na ma ƴar cikinka habaice
"Wasu suna jin cewa idan sun iya abinci da sana'a sannan sunyi candy, to sun gama rayuwar kunci fah, daɗi ne zai biyo baya, ai muma mun yi fiye da haka" inji Maman Asabe tana kallon Azrah kai tsaye
Azrah ta shige kitchen ba tare da ta ce komai ba, Ta ɗauki gawayi zata hura dan ɗaura wa Umma ruwan wanka
Abdul ne ya shigo kamar zai wuce, tuno deal dinsa da Mama yasa ya tsaya ya ciro wayarsa, ya ɗan juyar da camera
Azrah da bata san komai ba ta zauna tana kan ketta ashana ya ɗauketa ba tare data sani ba, su Mama ganin haka suka wuce ɗaki da sauri suna jiransa fuskokin su cike da murmushi
Yana shiga ɗaki ya ce da Mama
"Na gama nawa, miko min kuɗin"
Mama ta amshi wayar ta ciro dubu goma ta mika masa
"Gashi Allah ya saka"
Daga nan ita da Maman Asabe suka fita zuwa wata shago, suka kira Garba
"Garba! An samu, gashi nan a waya, amma ba ta nawa wayan bane zamu turo maka kafin yamma"
"Tura min kafin karfe biyu dai" Garba ya fada da murya mai sanyi amma mai cike da mugunta
Mama ta yanke kira tana kallon Maman Asabe ta ce
"Yanzu ya zamu yi gashi dai kuma kema wayar naki karama ce kuma yace kafin karfe biyu"
Maman Asabe ta ce
"Sai muyi amfani da wayar asabe na kawai"
Da daddare bayan Mama ta tura masa 50k yace zata kara masa ita bata san kuma ya zata yi ba amma damuwar ta ba anan yake ba tunda aiki za'a mata
Sake kiranta yayi ta ɗaga ya ce
"Na tura ma babban namu videon, yanzu zaki cika da sauran kuɗin ko?" Mama ta ce
"Naji wannan ba matsala bane, shi ogan naku me yace?" Ya ce
"Yace a basa 24 hours, zai gama aiwatar da komai"
Mama tamiƙe tana hamada ta ce
"Toh Ni yanzu damuwata gobe zasu kawo gaisuwar nan ne fah ina so tun kafin su zo ya kalli videon nan" Garba ya ce
"Kina da gaggawa ne matsala ta dake wannan harkan ba yanzu muka fara ba amma sai ki bi kiyi ta harzuka mu idan kuma ba'a yi daidai bafa" Mama zata yi magana ya katse kiran abin sa
Washe gari da yamma misalin 4:30pm
Unguwar Kofar Marusa ta cika da SUVs gwanin ban mamaki Black Prado, Range Rover, har da wasu manyan Hilux. Yara suka cika titi suna tsalle da dariya ganin motoci a arean su, mutane suna ta leƙowa ta window ganin meke faruwa
Bayan Abokin Bappah ya shigo dasu cikin compound ɗin da aka gyara ba zaka taba cewa gidan bane, duk suka zazzauna aka fara gaisawa cike da mutunta juna..
Mama daga cikin dakin ta ji hankalinta ya kasa samun sukuni ta tafi jikin labulen ta yaye labulen tana leƙansu... "Na shiga uku Ni Uwani!" Ta furta a hankali ganin manyan mutane da ke cikin gidan
Zahra ma leƙawan tayi ta ce
"Laaah! Wallahi manyan mutane ne Yaya... ga su can suna zazzaune" ko kallonta Azrah bata yi ba tana fama da zazzabin da take ji kamar zai rufeta ne
A tsakar gidan duk suka gama introducing kansu da kuma abun da yake tafe da su
"Munzo tambaye da kuma saka rana gaba ki ɗaya"
Bayan duk sun saka baki Bappah yace a bari sai bayan ta gama exams ɗin ta sannan da sati sai ayi bikin wanda duk sun tafi a akan hakan
Anan ake faɗawa Bappah Honorable Matan sa biyu
Bappah yayi shiru sannan ya ce Allah ya haɗa kansu shi kuma ya basa ikon yin adalci a tsakanin su
Sannan wani dattijo ya mika envelope yana cewa
"Ga Sadakin mu 1 million naira"
Gaba ɗaya wajen ya ɗauki silent gasp
Wani abokin Bappah ne yayi breaking silence ɗin da cewa
"Amma bai yi yawa ba? Kaɗan mai albarka ake so ai" wani dattijo ya ce
"Hakan ma ba laifi bane Babban fatan shine Allah ya basu zaman lafiya"
Da zasu tafi Bappah da abokansa suka raka su har bakin mota suna godiya
Bayan tafiyan su Bappah suka ɗanyi magana da abokansa sannan suma ya raka su kafin ya dawo cikin gida dakin Umma direct ya shiga
Bayan ya zauna ya gama musu bayanin abinda ya faru sannan ya miƙa ma Umma kuɗin ya ce
"Ga Sadakin ta nan sun bada" ya fada yana kallon Umma da Zahra
"Na wa ne?" Zahra ta tambaya da karamin muryan ta
"Million daya"
Umma da Zahra suka zaro ido, "Miliyan ɗaya!?" Bappah ya gƴaɗa masu kai
Bappah ya kuma cewa:
"Amma fa... akwai wata magana da suka faɗa min"
Umma ta dago da sauri ta ce
"Wace magana?"
"Wai Honorable yana da Mata, Mata biyu ma"
Zahra ta zaro ido ta ce "Ya Salam!" Umma kam ma ta gagara magana dan bata san me zata ce ba at this point, Mata bama Mata ɗaya ba har biyu? Hakan na nufin Azrah zata je ta uku Inaaa bata san sanda ta girgiza kai ba ta kalli kofar ɗakinsu Azrah, nan da nan fuskar ta ya cika da damuwa ta, rayuwarta ne yayi flashing a brain ɗinta nan da nan jikinta yayi sanyi tana kallon Bappah ta ce
"Allah ya zabar mata mafi alkhairi, amma wallahi jikina yayi sanyi da wannan maganar"
Bappah ya ce "Ni kaina sai da jikina yayi sanyi ba kaɗan ba" Zahra ta ce
"Gaskiya duk son hutuna ba zan so Yaya Azrah ta shiga kan kishiyoyi har biyu ba, dan Yaya ba magana take ba dama nice nasan yadda zan kwace ƴanci na" Umma ma tunanin da take kenan sai gashi Zahra na faɗa
Meanwhile... Mama
Mama tun lokacin data lekasu ɗin nan tana daki tana share zufa Tana jin tafiyarsu Bappah ya dawo, ta fito da sauri.
"Me ke faruwa a gida? Su waye su din ne?"
"Sun zo tambayar auren Azrah ne har sun bada sadaki" Bappah ya amsa mata a takaice, Umma ta zaro ido waje abinda bata son ji ke nan
"Sadaki?!" ta faɗa da karfi Bappah ya ce
"Eh" Mama a na kallonsa ta ce
"Na wa?"
Bappah ya ce cikin sanyi murya
"Million daya"
Mama ta durƙusa, ta dafe ƙirjinta, nan da nan idonta har ya cika da hawaye "Na shiga uku! Azrah zata shiga gidan hutu? Har an sayar da rana ga sadaki million daya?" Bappah ya ce
"Ki tashi ki gode wa Allah, ki kuma tsanya mata Albarka sai Kiga Allah ya kawo wa su Siyama ma" wani bad look ta masa ta ce
"To kuɗin fa?"
"Na bawa Ummanta itace uwarta ai"
Mama tayi shiru, sannan ta wuce daki tana gyara zaninta daya kusa faduwa, ba tare da bata lokaci ba ta sanya hijab ta fita waje, bata ko damu da cewa Maghrib ya kusa ba, gidan Maman Asabe ta nufa dan bata jin zata iya hakura dan yanzu ma ita kaɗai tasan me take ji
Da daddare.. Umma na zaune a ɗakin su tana yanka fruits, Azrah na kusa da ita tana gyara notes ɗinta wanda tun ɗazu take avoiding magana da Zahra dan bata son jin komai game da saka rananta Umma ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Azrah ina son ki bani hankalin wani abu zan fada miki... "
Azrah ta dago kanta, ta ajiye pen ɗin hannunta tana kallon Umman
"Sun zo tambayar aurenki ɗin sannan an basu... sun bada sadaki... million daya..."
Azrah ta janye hannunta daga Umma, ta rufe book ɗin gabanta Idonta ya yi jajir lokaci guda, Umma ta sake gyaran murya ta ce
"Amma... akwai wata magana, sun ce yana da mata har biyu fah Azrah" Azrah tayi shiru tana ta kallon Umma cike da mamaki kamar bata fahimci me take cewa ba
Sai kuma ta kalli kasa tana jin zuciyarta na bugawa kamar wanda ake controlling bugawan
Umma ta kalli yarinyar nata cike da tausayawa ta ce
"Allah ya zabar miki mafi alkhairi Azrah, Amma wallahi jikina yayi sanyi, sai dai ba hakan yake nufin bashi ne mafi Alkhairi ba, zan cigaba da miki addu'a" sai sannan Azrah taji hawayen idonta ya soma zuwa ta ɗan kalli Umma sai kuma ta sauke idon ta kasa dama tun farko taga ya mata kama da mai mata, kuma tun farko ya mata girma yanzu kuma ga wata maganar mata har biyu ta share hawayen daya gangaro mata ta miƙe ta fita ba tare data kalli Umma ba...