LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 15: A Cry Beneath the veil

by @hauwajaywrites

Tafiya take cikin sauri kamar bata ganin gabanta ko kula yaran dake gaishe ta bata yi damuwarta ta ganta gidan Maman Asabe, zuciyarta banda bugawa babu abinda take kamar waccan ba zata isa gidan ba. Tana isa gidan Maman Asabe, ko kwakkwaran sallama bata yi ba ta shiga

Ta tarar da ita tana shirin yin Sallah, Maman Asabe ta ɗago tana kallonta da mamaki, Mama ta ce

"Maman Asabe wallahi abin da nake tsoro shi ya faru yau!" Ta karasa maganar tsantsan bakin ciki yana bayyana a fuskarta

A mugun razane Maman Asabe ta gwalo ido tana kallonta ta ce

"Ban gane ba? Sun zo kenan kike nufi ko kuma an saka rana ne?" Mama ta sake share zufanta na countless times ta ce

"Su dai sun iso, Motoci sun cika titin mu fah yadda kika san ƴar gidan gomna za'a zo tambaya, ashe sadaki suka kawo, Ni duk ba wannan ba Sadakin ne yafi tsaya min a rai Maman Asabe" ta kare maganar tana share hawayen bakin ciki da suka fara sauka kan kuncinta, Maman asabe ta dafe kirjinta ta ce

"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un!" Mama ta ce

"Mu shiga ciki tsayuwa anan bai kama mu ba, ki kira mana Garba muji me ake ciki yanzu"

Bayan Mama sun kira shi harya katse bai ɗauka ba sai can kuma gashi ya kira back, muryarsa da sauti mai ƙarfi cike da Mugunta ya ce

"Yanzu na karɓi confirmation, video ya tafi hannun sa, Kuma na sa anyi forward zuwa numbern sa kai tsaye"

"Ya ce me?" Mama ta tambaya

"Baice komai ba tukuna... ya karɓa ne kawai, Amma ya ƙara cewa za'a ji daga gare sa da daddare ko gobe da safe"

Mama ta kashe wayar, ta miƙe tana kallon Maman asabe tace zata koma gida. ta nufi gida a hankali kamar wacca kwai ya fashe mata a ciki. Bata karasa ɗaki ba kawai ta tsaya nan sakar gidan ta fara Alwala tana idarwa ta wuce ɗakinta ta kama sallah, tana idarwa ko addu'a bata fara ba sai ga su Siyama sun shigo kamar wanda aka wurgo su haka suka faɗa ɗakin, fuskokinsu kamar wanda basu taɓa sanin wani abu wai shi murmushi ba

"Mama... gaskiya ne wai motoci sun cika kofar gidan nan? Sunce har Governor ya zo? Kuma akan maganar Azrah ce ko?" Habibah tayi maganar cike da damuwar da ya bayyana ƙarara a fuskanta

Mama ta kalle su, idonta ya cika da hawaye, tayi ajiyar zuciya sannan tace

"Toh ku zauna mana zan gaya muku amma kun tsaya min a ka"

Duk zama sukayi Siyama so kawai take taji ance mata A'a, duk Idanu suka zuba mata, Mama ta ce

"Wannan abinda kuka ji gaskiya ne, sun zo, kuma sun bada sadaki Naira na dukan Naira har miliyoyin ɗaya fah, biki kuma tana gama jarabawa za'a yi"

Kafin ta ƙarasa Habibah ta fashe da kuka, Siyama ta rike kanta tana fadin

"Ya Allah! Amma meyasa haka? Me yasa Bappah zai yarda bayan yasan na girme ta, har Habibah ta girme ta amma sai ya fara aurar da ita kuma?"

Mama ta share hawayenta, ta dafe kirjinta

"Ku kyaleni mana... wallahi yau ɗin nan zuciyata ta yi nauyi, kar ku kara min wata damuwan kuma... Allah ya zabar mana mafita".

Daren ranar, Azrah bata iya rintsawa ba, ta juya daga hagu zuwa dama, daga dama zuwa hagu aikin kenan, zuciyarta cike da rikice-rikicen da basu da suna, ta rike pillow ɗinta kamar zai ba ta amsa, tana starring waje guda

"Yaya zan zauna a matsayin mata ta uku? Ni da ko fiye da 18 ban yi ba? Yaya makomata zata kasance a gidan cikin manyan Mata? Umma, Zahra, Bappah... duk suna mafarkin jin dadina, Amma me zai faru da ni?"

Zuciyarta tayi mata nawi sosai gashi bata son ko da wasa ta daga ma Umma ciwonta, A hankali ta miƙe, tsakar gidan nasu ta fita ta ɗauro alwala sannan ta koma daki ta shimfiɗa sallaya ta fara sallah tana faɗa wa Ubangijinta damuwarta.

Bayan ya dawo gida very late ɗakinsa ya wuce direct, ajiye expensive phones ɗinsa yayi a bed side sannan ya cire kayan jikinsa ya wuce toilet dan fresh up, yana fitowa ya ɗaura sleep wear ɗinsa, ya haɗa tea yana sha wayansa yayi kara alamar shigowan message kallon wayan yayi sai kuma ya ɗauke kansa baya son wani damuwa shiyasa kawai ya tsaya a bangarensa saboda yana bukatan rest and probably bazai wuce first wife ɗinsa bace ta turo da sakon, miƙewa yayi ya ajiye cup ɗin sannan ya koma kan gado yayi sliding wayan new number ya gani amma sai ya share ya shiga searching numbern Azrah magana ya mata a Whatsapp ganin bata online kawai sai ya sauka har zai fita a Whatsapp kuma sai ya danna ya shiga wannan numbern, videos ya gani haka kawai yaji gabansa ya faɗi saboda yadda message ɗin ya shigo ba sallama balle wani content kuma private line ɗinsa ne ya daure ya danna download na video ɗin, nan take ya buɗe, playing video din yayi bai san sanda ya tashi daga kan gadon ba ba shiri yana zaro ido meanwhile yana girgiza kai trying all positive kar ya yarda da wannan videon.

Fita yayi a Whatsapp ɗin ya zauna speechless ganin hakan ba mafita bane kawai ya ɗauki ɗayan wayansa wani number yayi dialing ana ɗaga wa ya ce

"Ka duba DM ɗinka na tura maka abu, Find out who sent the video, Get me everything, names, locations, the sender's intent, I want to know who is trying to ruin this.." Bai karasa ba kawai ya katse kiran jin wani tsarawan da kansa ke masa

Honorable ya sake kallon fuskar Azrah da ke cikin video ɗin, yana jin wani abu mai wuyar fassara, tsakanin so, ƙiyayya da rudani, amma abu guda ya bayyana a zuciyarsa "She will be mine. No matter what" but yanzu yana son ya san dalilin hakan da gaske ne ko kuma sharri ne.

Washe gari da safe Mama ta tashi da mugun zazzaɓi wanda har hakan yasa ta gagara ɗaura abincin tallah, Zahra tunda sassafe ta gama shirin school ɗinta ta tafi, Azrah da itama ta tashi da zazzaɓin ta ɗaura breakfast ta kama aikin gidan saboda in few days zasu fara waec yasa bata zuwa makaranta tana cikin wanke wanke sai ga Siyama ta shigo gidan ko kallon ta Azrah bata yi ba, Siyama ta ce

"Sannu Malama, ai yanzu kina ji da kanki shiyasa ko magana baki ma mutane saboda kina jin Yanzu kinfi karfin mu ko? Toh ki sani gwara ki daina murna dan wannan ba inda zai kai ki kina nan cikin gidan nan"

ko da wasa Azrah bata kalli direction dinta ba ta kwashe kayan data wanke ta kai kitchen ta fito zata share compound ɗin ta kalle ta har sannan tana tsaye rike da kugunta ta taɓe baki, wani ashar ta jefa mata, sai sannan Azrah ta kalleta ta ce

"Look! Ki kama kanki please, kiyi maintaining wannan respect bond ɗinda ke tsakanin mu, Kinga nace wani abun ne? Balle kiyi tunanin saboda gaisuwar da aka kawo har zai sa na canza?"

Wani shewa Siyama tayi duk da bata fahimci wasu daga cikin maganganun Azrahn ba, tayi kamar zata kamata da faɗa dama jira take ta tanka mata sai ga Bappah ya fito daga ɗakinsa ya ce

"Siyama Karki kuskura, ke yanzu ba abin kunya bane a gareki kina neman tsokanan Kanwar ki? Just imagine fah? Ke waya hana ki fito da mijin da har kike wasu maganganun" Siyama ta kalle Bappah sai kuma ta fashe da kuka ta wuce ɗakin su tana jin haushin abin da Bappah ya mata

Azrah na shiga ɗakin Umma ta ce

"Azrah no matter what kar ki ce zaki na biye musu, harda rashin ilimi ke damun su, amma mutum me ilimi ai ba zai yi haka ba" Azrah ta ce

"Umma I'm always avoiding their dirty words, always pretending banji ba, yi nake kamar bansan suna yi ba ɗazun ma banyi niyyar kulata ba amma yadda naga take juya maganar wani iri shiyasa nace tayi respecting kanta" Umma ta sauke ajiyar zuciya ba tare data sake magana ba.

Yau tunda honorable ya tashi Matansa basu gane kansa ba babu wannan murmushin da ya saba musu balle wasa da dariya, kuma sun tambaye sa bashi da lafiya ne yace Lafiyan sa kalau, haka kawai yake avoiding mutane dan jiya ya kasa ma baccin kirki shiyasa gaba ɗaya ya tashi moody ganin ba zasu kyalesa ba duk da baiyi niyyar fita office ba kawai ya shirya ya gwammace ya tafi can inda babu wanda zai takura sa.

Yana zaune a office yayi nisa cikin tunani yaji wayansa ya fara ringing ɗauka yayi tare da kaiwa kunne ba tare da yayi magana ba, wanda ya kira sa ya ce

"Sir, mun samu information game da sender ɗin yanzu haka na tura maka everything a DM ɗinka" sai sannan ya sauke ajiyan zuciya ya ce

"Mind you, bana son jin wannan magana ya fito daga gare ka and ina son ganinsa, make sure kun kawo min shi but Everything should be done secretly please" Mutumin ya amsa da toh cike da ladabi, bayan ya katse kiran sai yanzu yaji wani kwanciyar hankali, a hankali ya miƙe ya fita.

Umma data shiga cikin gidan zuwanta kenan daga gidan Maman Azizah ta kalle Mama na zaune ta ce

"Barka da Rana Maman Abdul" wani kallo Mama ta mata cike da tsana ta ce

"Wani munafurcin ne kuma harda wani gaishe Ni? Dama magana kike min ? Ko kuma so kike ki gwaɗamin ƴarki zata shiga gidan daula ne? Toh ta shiga mu gani mana" Umma tayi murmushi ta girgiza kanta ta ce

"Allah ya baki hakuri, miji kuma wallahi duk ina musu addu'a Allah basu nagari wanda zai riƙe su da mutunci ban cire su siyama ba dan duk kallon 'ya'ya na nake musu" Mama ta ja wani dogon tsaki ta ce

"Aikin banza, Uban waya ce toh ki musu idan duniya da gaskiya ai sai kice tunda Siyama ta girme su a basa ita amma ai baki yi hakan ba, sannan kuma naga har wani tsiya kuka tsiro daga ke har 'ya'yan naki" Umma bata kara ko Uffan ba ta wuce ciki abinta

Zahra dake cin abinci ta ɗaga kai tana kallon Umma cike da takaici ta ce

"Allah Umma da baki kula wancan matar ba, bata da hankali bata iya magana ba, ji fah wata mugun fatan da take wai ayi auren a gani? Lallai ma wallahi" har ta karasa maganar Umma bata daina kallon ta cike da mamaki ba ta ce

"Sannu Zahra, ita ba Uwar ki bace da zaki ce wai wancar matan? Toh kar naji kar na gani kin sake faɗin haka, kinji?" Zahra ta ɗauke kai ta cigaba da cin abinci ta.

Honorable ya shiga ɗakin da aka ajiye Garba a ciki, fuskansa ba yabo ba fallasa ya shiga ciki ya zauna akan kujerar dake opposite da wanda Garba ke zaune amma kansa a kasa, Honorable yafi minti biyar yana kallon sa sannan yayi gyaran murya, Garba ya ɗan ɗaga kansa kaɗan ya ɗan kallesa dan yana avoiding eye contact da honorable

Honorable ya ce "Waye kai?" Garba ganin Honorable ba mutumin da zai ce zai kawo masa wasa bane yasa ya ce "Sunana Sadiq" wani murmushi honorable yayi ya ce

"Ina son sanin komai game da wanan videon da ka turomin" Garba ya ɗan kalle sa sai kuma ya sauke kansa ya ce

"Duk abinda yake ciki ba faking bane, ita ce" Honorable ya gyaɗa kai ya ce

"Are you sure?" Garba ya gyaɗa masa kai ya ce

"Eh babu tantama" Honorable ya ce

"Ina son pure gaskiyar abin nace maka? Zan iya baka kuɗin da baka yi expecting ba" Garba ya ce

"Gaskiyar kenan, yarinyar ce kowa ya santa da wannan halin" honorable ya ce

"Then Meyasa katuramin? Did I request?" Ya girgiza masa kai ya ce

"But I'm trying to protect you ne bana son ka faɗa tarkonta" wani murmushi mai wuyar fassarawa yayi sannan ya miƙe ya ce

"Good for you, Weldon" daga haka honorable ya fita a wajan a bakin kofar ga sojoji suna tsaye tare da wasu police, ganin Honorable suka ja baya cike da girmamawa, yana kallonsu ya ce

"Zaku iya aikin ku, make sure har sai ya faɗi komai, dan naga yana son playing ɗina" daga haka ya wuce motarsa yana kara jinjina alamarin a ransa, fuskan kam nata ne amma yadda yaga body ɗin ko kaɗan baiyi kama da nata ba dan wancan jikin fat ne hakan ya tabbatar masa ba ita bane dan yasan Azrah bata da wani kiɓa.

Duk yadda sojojin nan suko so ya faɗa musu gaskiya ki yayi daga karshe suka hau dukansa babu ji babu gani, ganin akan ɗan 50k ɗin da yayi aiki wanda karshe ma bashi kaɗai ya ci kuɗin ba har wanda ya haɗa masa videon suka raba amma gashi akan sa ana neman a halakasa yasa ya fara ihu yana zai faɗa, suka tsaya da dukansa suna kallon sa suka ce

"Waya sa ka? Kuma videon waye wannan" yana haki ya fara magana ga hawayen daya ke sintiri ya ce "Ba videon ta bane haɗawa aka yi" wani soja ya haɗe rai ya ce

"Who?" Garba ya fara girgiza kai alamar suyi hakuri, ganin zasu cigaba da jibgansa yasa ya fara ihuun zai yi magana, nan take ya faɗa musu plan ɗin wanda suka saka sa aiki, wani police ya fita waje nan ya sanar da Honorable, honorable ya ce ayi arresting ɗinsu suma

Police station suka wuce nan suka ɗebo rundunar polisawa wanda sai ka ɗauka yaki za'a tafi ganin su ma kaɗai sai ya tsinkar maka da zuciya, harda polisawa Mata suka ɗauka, duk suka shiga motar suka kama hanyar gidan su Mama..

Maman Asabe dake tsakar gidanta tana daka ga kuma Yaranta suna gefe suna wanki suka ji an baka kofar gidan da sauri ta ɗago kai tana kallon polisawan da bata san adadin su ba suka cuso kai kai tsaye, ta fara ja da baya Yaranta ma duk cike da tsoro suke kallonsu wani police yayi magana da tsawa ana tambayar waye Maman Asabe, nan duk matan gidan suka dinga fitowa daga dakin su abinka da gidan yawa, ana kallon abinda yake faruwa, wani police ya shigo da Garba wanda duk jikinsa a fashe bakinsa jini ganin haka zuciyarta ya tsinke, nuna musu ita yayi wanda take aka saka mata ankwa tana kuka tana rokon su ba ita bace wallahi Mama ne wata police ta ɗauke ta da mari wanda sai data ga stars ba shiri tayi shiru Yaranta suka fara kuka, cikin unguwarsu duk aka fito ana son ganin meke faruwa suka fito da ita suka wurga ta bayan motar cike da kaskanci kuma da rashin tausayi, Asabe ta fita da gudu tayi hanyar wajan sana'an Baban su, su kuma suka ja motarsu suka bar unguwar wanda tuni an fara magana kasa kasa, Maman Asabe banda kuka mai tsuma rai babu abinda take yi, ta tsinewa Mama yafi a kirga...