LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 16: The Weight of Shame

by @hauwajaywrites

Motocin ƴan sanda ne suka faka a daidai kofar gidan Bappah, yaran unguwar duk suka fito harda manya dan ganin meke faruwa, haka ƴan sandan nan maza da mata suka sauka zuwa cikin gidan, banka kofar su da bata da karfi suka yi, Umma dake compound tana alwala ta ɗaga kai tana kallonsu gyara mayafinta tayi tana kallonsu ganin sun nufe ta...

Yara da har sun fesawa Mama cewa ƴan sanda sun cika layinsu kuma jin sun nufi sashin Umma yasa ta fito tana murmushin mugunta tana son taga komai da za'a yi ayi a gabanta

Babu rahama ko alamun wasa a fuskokinsu, ɗaya daga cikin su ya ce

"Wacece Uwani?" Umma da kalli Mama da fitowan ta kenan bata bata ma ji su ba, a hankali tana kallon polisawan ta ce

"Gaskiya ban santa ba" wani tsawa suka daka mata dan they're very sure gidan ne la'akari da cewa Maman Asabe ce ta kawo su, Zahra ce ta fito tana kallonsu sai kuma ta kalli Mama dake murmushin mugunta irin polisawa suna ma Umma tsawa, a hankali ta ce musu

"Sir, gata can wanda kuke neman, itace Uwani" juyawa suka yi, ita dai Umma ta zama speechless, Mama kuma ba jin Zahra ta yi ba kawai gani tayi ƴan sandan sun nufeta kamar ta gudu amma ta dake tsoron kar ace bata da gaskiya ko kuma a harɓe ta, wani kallo suke mata wani ya ce

"Ke ce Uwani?" Mama ta gyaɗa kai zuciyarta na bugawa ta ce

"Eh nice... Ohh A'a bani bace ashe.." wani kallo wata ɗaya daga cikin polisawan kawai ta kama hannun Mama ta dasa mata anƙo, Mama ta fara magana tana cewa

"Wannan wani irin wulakanci ne... Mutum ba tare da yasan laifin da yayi ba sai ku kama sa? To ku jira mana mijina ya dawo" wani kallo Wani police ya mata wanda yasa ta haɗiye maganganunsa janta matar take yi har ta fita da ita waje, ai nan da nan Mama taji wani zufar ya sake gangaro mata sakamakon ido huɗu da tayi da Maman Asabe, cike da kaskanci suka wurga ta cikin motar ga ƴan unguwar duk an taru ana kallonsu.....

Wurin da aka kai su Mama ba wurin da ake kai masu laifi bane kawai, amma wurin da ake ƙoƙarin murkushe mutumtaka ne, Su Mama suna zaune a cikin Naman Asabe harta gaji da tsinewa Mama tayi shiru, wajan banda zarni babu abinda yake yi, Wani ɗan sanda yana tsaye a gabansu da duk da akwai noise mask a fuskar sa amma ya daura hannunsa akan hancinsa kamar wanda yake jin warin, yana kallon su Mama da idanu masu cike da raini ya ce

"Ku ne kuke daukar hoton wata Hajiya ku saka mata fuskar karya, kuna tunanin zaku tsallake hakan ne? Lallai ba ku san waye Honorable ba ne yasa kuka fara wannan jahilcin naku, wannan ba a film bane ko littafi, it's reality ne"

Mama ta sunkuyar da kanta ba don tana jin kunya ba, sai don takaici, tana jin kamar ta tashi ta zazzaga masa zagi jin wai Hajiya ma yake kiran Azrah, amma ta san hakan ba zai kawo mata mafita ba sai ma ta karama kanta wani laifi

Daga nan aka fitar da su zuwa wani ɗakin na daban, can suka wuni. Ba abinci, ba ruwa. Maman Asabe tana tsaye akan Mama ta dinga tsinewa mata tana faɗin

"Ina zaman zamana gashi kun jefa ni cikin ukubar bala'i, yanzu na koma gida nace wa Naman Asabe mene? Yanda yasha zamini kunne da ke idan ya sake Ni ina zan shige Ni asu?"

Mama ba tace komai mata komai ba, tana jin yunwa amma yunwar ba ta tada mata hankali kamar kalmomin tsinuwa da wulakanci da Maman Asabe ke zuba mata ba

Meanwhile..... Umma tana tsaye da rashin natsuwa, Idanunta har jaa yayi saboda tashin hankali tana jin kamar zata yi kuka tana kallon Zahra ta ce

"Zahra je ki kira Bappahn ku" Zahra ta taɓe baki sannan ta ɗauki mayafinta ta nufi hanyar inda Bappah ke zama, tun kafin Zahra ta isa, ta ci karo da shi a hanya, yana dawowa gida, fuskarsa cike da damuwa.

"Bappah!" Zahra ta ce da sauri "An kama Mama da Maman Asabe an kaisu station!"

"Me?" Bappah ya tsaya cak yana kallon Zahra da idanu masu cike da tambaya

"Wace irin magana ce haka? Station? Ina ne? Dama da akace polisawa sun taru kofar gida kamasu kenan akayi ko ya? Sai kuma ya kama tafiya da sauri har haɗe kafa yake yi ya isa gida ga Zahra dake binsa a baya

Anan compound yaga Umma na tsaye har sannan ga kuma Azrah dake zaune itama tayi tagumi, anan Muna ta fara sanar da Bappah abinda idanunta suka sani

Suna cikin wannan ruɗanin ne sai ga sallamar wani mutum, Mijin Maman Asabe ne, sau kuma.da Asaben daga bayansa, ya karasa ya mikawa Bappah sannan ya fara masa magana

"Ai wallahi ni banga laifin matarka ba, amma nasan halin Maman Asabe, zata iya shiga rigima fiye da haka, ita dan haka kullum a garin tara mutane suke jefa ta cikin masifa" inji mijin nata

Asabe dai na gefe tana ji tana kallon su, ba ta ce uffan ba sai ga su Siyama da Habibah sun shigo gida da sauri, fuskokinsu cike da damuwa, Asabe ta watsa musu wani banzan kallo cike da tsana sannan ta juya zata koma gidan su

Bappah da Mijin Maman Asabe suka tashi suka kama hanyar station ɗin unguwar su domin su san inda aka kaisu, Amma ba'a kai su station na unguwar tasu ba, Sun zagaya kusan rabin stations ɗin garin amma basu same su a can ba

Daukar washegari da kyar suka samu inda suke da taimakon wani police ɗin, Su Mama suna cikin yanayi mai raɗaɗi ba duka aka musu ba, amma sun sha wahala ba kaɗan ba wulakanci, yunwa, rashin barci, da tsoro Lokacin da Bappah ya tambayi bail, aka ce masa

"Bailing ɗinsu? Haba ku kuwa duk girman laifin nan, toh honorable bai yarda a bada bailing dinsu ga kowa ba" with shock Bappah yake kallon sa ya ce

"Honorable kuma?" Police ɗin ya gyada masa kai yace "Eh shi, yarinyar da zai aura ne suka ɗaura hotonta akan na wata matan banza wanda sun tura masa hakan kuma zai iya ɓata masa kujerar takaransa...

Bayan fitowar Bappah da mijin Maman Asabe daga ofishin 'yan sanda, jikin su babu ƙwari, ya gama sanyi wanda duk basu yi sammanin haka bane abun ya faru, haka suka fito kowannensu na dauke da fuskarsu mai nauyin laifin da suka aikata, Suna ƙoƙarin danne kunya da takaici dan ba kaɗan ba sun dasu kunya...

Bayan su Mama sunyi laushi iya laushi ga abincin kuma kamar yadda kasa ma karamin yaro zaka bada haka suke sako musu, can kusa da Magrib sai ga Honorable da kansa ya iso ofishin 'yan sandan fuskar sa ɗauke da ƙiyayya da mamaki....

"Ina mamakin ku akan me zaku ɗauki hoton mutum ku ɗora masa karyar da bata da tushe? Wannan fa cin mutunci ne! Wannan kuma ɓata wa mutum sunane" Honorable ya faɗa da murya mai ƙarfi

Mama da sauri ta furta "Wallahi sharrin shaiɗan ne ya yi mana tasiri"

Maman Asabe kuwa cikin rawar murya tace

"Ni Mama Abdul ce ta saka ni, ita ce ta ja ni cikin wannan magana da masifar, amma a gafarta mana yallabai"

Garba kam ya zauna ne tamkar ba a kansa ake magana ba ko kallo bai yi ba balle awa ran zai ce wani abun

Honorable ya ce "Me dalilinku na hakan kawai nake so baki? Duk shiru suka yi sun gagara basa amsa

Honorable ya mike fuska a daure ya ce "Na tabbata koma da ƴaƴa kuma yanzu ace ma naku aka yi wa haka zaku ji daɗi?"

Suka fara basa hakuri da neman afuwa amma ko kallo bai sake yi musu ba, ya juya ya bar wurin cike da taimacinsu

Da yamma Bappah ya fito daga ɗakinsa yana bin compound ɗin da kallo wanda yana son tabbatar da babu kowa, bakin kofa ya nuna yayi dialing ana honorable yana sake kaka cikin gida to be sure babu wanda zaiji wyan, Honorable na ɗaukawa cikin sigar natsuwa da tawali’u, ya fara da bashi hakuri

"Alhaji ina neman Alfarman mana" Honorable ya ce

"Ina jin ka Baba, menene? Bqppah ya ce

"Wannan matan da kasa aka kama da ɗayan Mata ta ce ka tausaya mata ka sake su, in shaa Allah hakan ba zai kara faruwa ba"

Honorable ya yi shiru na ɗan wani lokaci sannan ya ce

"Shikenan Bqppah zan sa a sake su amma saboda kai, kuma ban yaɓa dauka ai ɗayan matar ka bace" bayan gama.wayansu har sannan honorable bai daina jinjina wannan labarin ba...

Bayan wayar Honorable ya kira ofishin ‘yan sanda, ya bada umarni da a sako su Mama da Maman Asabe, amma kafin hakan, sai da suka sha masifa da gargaɗi mai tsanani daga hannun jami'an tsaro, an sake su ne kawai saboda girmamawar da Honorable ke wa Bappah, ba don suna da wani cancanta ba.

Rayuwar da suka yi a ɗan wannan wajan banda faɗa babu abinda suke yi kamar basu san junansu ba haka suka koma

Da suka dawo gida, Bqppah ya ɗaga kai yana ma Mama wani kallon tsana ya fara mata masifa kamar zai dake ta, ga taikaicinsa su Habibah da Siyama da yanzu sun ma daina zaman gidan, yana kallon Mama wani one look ta masa wanda ba shiri yayi sitt

Bayan magariba, jama'a suka fara shiga yin ja je, wannan yana fita wani zai shigo kamar wanda suke zuwa karɓan sadaqa tsabar gulma

Habibah da Siyama ne suka kulle ƙofar gidan suna masiyan gadon

"Gulma za ta kashe m

su, kai Allah wadaran naka ya lalace"

A bangaren Maman Asabe kuwa tunda tasa kafarta a cikin gidan mijinta ya fusata ƙwarai, har sai da ya kusa duka ta saboda fadan da yake mata

"Sau nawa nake ce muku bana son kallon matar nan kuma mu'amala amma bakya ji ko? Ga irinta ai nan, Kin jawo mini kunya!" Cewar mijinta

A gidan honorable komai na tafiya lafiya a ido, amma a zuciyar uwargidan nasa kamar wacca ake hura wuta. Uwargidan Honorable Hajiya Maryam,

ta saba ganin Mijinta a cikin natsuwa da kamun kai, A.amma kwanan nan tana jin canji wani abu da bata iya fassara ba

A daren ranan, matarsa ta biyu, Hajiya Rabi, ta shigo dakin uwargida da fuskar da ke ɗauke da wani nauyin magana. Ta zauna a gefen katifa, tana kallon uwargida da murmushin karya

"Anty... wallahi ban san ko zan faɗa miki ba, amma zuciyata ba ta barni lafiya, sau na huta brain ɗina zai dawo

Hajiya Maryam ta ɗago kai

"Me ke damunki haka Rabi?"

Rabi ta saki ajiyar zuciya. "Wallahi naji wata magana ce da ban jin ya kamata ki zauna baki sani ba, Sun ce mijinmu yana shirin sake aure shi yasa kwana biyu yake diverting zama gida ga kuma changes da suke ganinsa da shi,

Maryam ta ɗan yi dariya mai taushi

"Wannan magana ba sabuwa bace Miji namiji ne, ai..."

Sai Rabi ta katseta da gaggawa. "A'a Anty ba kamar sauran zance ba Wannan karon gaskiya ne,.kuma yarinyar kamar ita tayi kanta

Fuskar Maryam ta sauya. Wannan karon zancen ya ɗan dame ta "Yanzu ke faɗin haka? Wato magana ce da har take da tushe?"

"Eh kuma yarinyar kamar ita tayi kanta, Ni wallahi duk na tsorata"

Daga nan Hajiya Maryam tasa masa ido sosai nan taga yadda maganar Rabi gaskiya ne

Ba tare da ɓata lokaci ba, sai ta kira wata amintacciyar kawarta da ke da alaƙa da wani jami’in bincike, ta roƙe ta da a taimaka a gano wacece wannan yarinyar da ake danganta da mijinta, tace a tantance komai: asali, danginta, makarantar ta, da inda take zuwa.

"Ni ba zan zauna a raina ni ba dole kuma kowa ya bani respect Dina kuma ya gama aure a duniya" cewar Hajiya Maryam,

"Ko aure zai yi, dole na san wa zai aura"

A haka aka fara bincike cikin sirri, aka sa ido, ana bibiyar yarinyar da aka ji ana ambata. Zancen ya fara ɗaukar zafi, yayinda masu bincike suna yara duk wata information suna adana musu