LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)
Episode 17: The Silent Thunder
Wani babban parlon ne wanda ke ɗauke da duk wata kayan more rayuwa ta duniya, wata mata ce ke zaune a kan wata sofa tana ƙaɗa kafa har sannan zuciyar ta bata daina tafarfasa ba, tana danna wayar hannunta ne ba tare data san me take yi ba, wata mata ce daga cikin wanda ta saka su mata aiki ne ta shigo cikin nutsuwa amma idonta na ɗauke da wani sirri mai nauyi tana murmushi dan tasan Hajiya zata ji daɗin wannan samo dukkanin bayanan akan wannan yarinyar amma kuma ba lallai ta iya jura jin menene ba
"Barka da zuwa" Hajiya ta faɗa cikin kulawa
"Nagode Uwargida a gidan honorable, na samo miki dukkannin bayanan amma... kuma sai kin daure zuciyarki" ta kare maganar tana avoiding eye contact da Hajiya
Hajiya ta ɗaga gira tana kallonta alamun sauraro
Sai matan ta miƙa mata wani envelope dake dauke da wasu pictures na wata yarinya da kuma rubuce da bayanai ta ce
"Sunanta Azrah Matar da aka cewa Honorable yana da niyyar aura kenan Hajiya, amma karyan su tasha karya, na tura ƴan leƙe-leƙe sun binciko min cikakken bayani akanta"
Hajiya ta karɓi takardun tana duba hoton Azrah, lokacin da tayi ido huɗu da hoton nan take jikinta ya ɗaura rawa, numfashinta ya fara seizing, zuciyarta na bugawa da ƙarfi,
Fuskarta ta cika da mamaki da kuma tsoro da lokaci guda ya kamata
"Wannan... irin wannan kyau... balarabiya ce ko?!" Hajiya Maryam tayi tambayar ba tare data san ta furta hakan ba
"A'a duk da dai ance kamar ita mahaifiyar yarinyar ba'a san assalinta ba amma tabbas mahaifinta ɗan nan Katsina ne, mazauniyar kofar Marusa a Ghetto area suke ma Hajiya"
Kusan saura kaɗan Hajiya ta sake fisari a jikinta, da kyar ta miƙe ta nufi ɗakinta ta kasa tsayuwa ta kasa kwanciya, ta kasa zaune zuciyarta na cike da ɓacin rai da mamaki da kuma kishi daya cika shi fam
Kamar wanda aka tsikara sai ta miƙe da sauri ta fara shiri, cikin fushi ta saka kaya ko ɗaura ɗankwali bata yi ba ta fita zuwa compound da sauri wajan motarta ta nufa ta shiga ciki har wani jiri take ji amma ta tada motar ta figa a mugun guje kai tsaye gidan co-wife ɗinta ta nufa
Tana parking ta nufa entrance ɗin ba tare data tsaya ta rufe motar ba ko ta dawo da nutsuwarta ba, tin daga balcony ta fara kwaila mata kira, da sauri Hajiya Rabi ta fito tana kallon kishiyarta da mamaki, tun kafin tayi magana ta katse ta ta ce
"Kin ga wacce Honorable ke shirin aura? Kin san daga ina take? Wallahi wannan ai tozarci ne!" Hajiya Rabi ta tsaya cak yana kallon ta da mamaki sai kuma ta ce
"Babban Macece kenan zai aura?" Hajiya Rabi ma ta mata wani kallo ta ce
"Take this and see" ta kare mata maganar tana miƙa mata hotunan Azrah,wani zaro ido tayi tana kallonta bayan ta karɓi hoton itama tana kallo, murmushin takaici tayi ta ce
"Ai bamu ga ta zama ba, ina mu ina bari ya auro mana wannan? Ai mun shiga uku idan har ya aureta mulakanci kuma sai wanda muka gani" Hajiya Maryam ta ce
"Ke duk ba wannan ba, tashi zakiyi mu je mu tabbatar da gaskiyar lamarin... sannan mu bawa yarinyar concrete warning tunda daga ghetto area take ba abinda zasu iya yi, shi kuma tunda har bazai tsayar da hankalinsa ba munsan wata idan bai sani ba, ita kuma zata gane tsakanin mata akwai ruwan zafi".
A haka Hajiya ta sake sa aka kawo mata wani info wanda yayi daidai dana farkon, tana gama karantawa ta mikawa co-wife dinta ta ce
"To yanzu kin ga da idonki ko? Nace miki komai haka ne ba wata tantama, ta shi mu je, yau zasu gane akwai banbanci tsakanin mai power da wanda bai san ma me powern ba"
Hajiya da co-wife ɗinta ba su yi wata-wata ba suka nufi unguwar Kofar Marusa, Motarsu mai tsadan gaske na karaya ƙasa a cikin layin ghetto, wanda ba kasafai ake ganin irinta ba a wannan unguwar, wanda tun shigowar su layin yara suka fara bin motar da gudu suna kallon motar
A bakin ƙofar gidansu Azrah suka parka motar, Hajiya ta fara sauka sannan Hajiya Rabi karewa layin suke da kallo, kallon ma kallon kƴama
Kamar wanda ba zasu taka kasa ba suka nufi kofar gidan da kakkausar murya Hajiya ta fara sallama
"Assalamu Alaikum!"
Zahra ce ta fito tana daure da darduma a kafaɗa, alamar ta idar da sallah kenan, ta zare ido ganin manyan mata biyu cikin shigar masu hali da izza, tana kallon su ta ce
"Wa'alaikumus Salam Ina wuni?" Duk kallon Zahra suke wanda itama ba maraba da Azrah sai dai Azrah ta fita haske sannan ta fi tsayi
"Yauwa, Ina ɗakin Maman Azrah?" Cewar Hajiya ba tare da murmushi ba saima wani kallo data ke bin compound ɗin da shi
Zahra ta nuna musu ɗakin da hannu, ba tare da wani jinkiri ba suka shiga
Umma ce ta tarbe su da murmushi duk da bata san su ba
"Sannu da zuwa, ga waje ku zauna" ta yi maganar tana shimfiɗa musu dadduma, Umma ta ɗago ganin ta basu wajan zama amma basu zauna ba, cike da wulakanci Hajiya ta ce
"Barkanmu dai, amma ba zaman lafiya ya kawo mu ba, mun zo ne kashedi ma ƴarki Azrah" Hajiya Rabi ta karɓe ta
"Mun samu labari cewa diyarki Azrah na da alaƙa da mijinmu Honorable, har Office ɗinsa take binsa, toh muna baki kashedi da gargaɗi ta rabu da shi tun kafin lamari ya lalace muku, Kuma ku gaya mata cewa mu ba sa'anninta ba ne, ba zata iya shiga cikin rayuwar mu ba balle har ta fara tunanin kishi da mu" har suka kai aya Umma na kallonsu
Jikinta yayi sanyi Zahra wacce ta tsaya a bakin ƙofa da ruwa a kofi, bata san sanda ta tsaya cak ba idanu ta zuba musu itama
Azrah kuwa daga cikin ɗaki ta ji komai jikinta yayi mugun sanyi Zuciyarta ta cika da fargaba da nauyin abin da ke faruwa ga kuma wani tsoro da lokaci guda ya dira zuciyarta
Ba tare da jiran ko tsammani ba matan suka juya suka fita, da suka kai bakin ƙofa suka ci karo da Mama da tun shigowar su ta fito jin abin da ya kawo su ta nufi bakin kofa da sauri shine zasu fita suka ci karo
Mama ta ja su gefe cikin rawar murya, amma tana kokarin yin magana da ladabi, wani kallo suke mata wanda a cike yake da wulakanci, ta ce
"Kuyi hakuri ku saurare ni... Ni ma lokacin da aka kawo ita mahaifiyar Azrahn sai da nayi kusan barin gida, saboda kwatakwata ko kallo ban ishe Malam ba, gani yake ya dauko mace mai karatu sannan kyakkyawa kuma yadda zai iya nunata a kamfafoninsa, amma haka na tashi na fara neman mafita har daga karshe na samu mafita har zuwa yanzu... yanzu idan har kuna da ƙarfin hali, ba wai na kuɗi ba dan nasan kunfi karfin wannan toh kuyi iya kokarinku ku hana auren, kafin komai ya wuce gona da iri ko kuma a ɗaura auren ku shiga uku dan asiri baya cin su"
Amma Hajiya da co-wife ɗinta suna kallonta da wani irin kallo na kyama da wulakanci Kamar dai "wacece ke da zaki bamu shawara?"
Mama dai bata damu ba ta juya ta shiga cikin gidan, tana girgiza kai kamar wacce ta bata san komai ba
Bayan tafiyar su Hajiya da Hajiya Rabi Umma ta zauna dirshen a ɗakinta, zuciyarta cike da raɗaɗi ta dade a wajan ba tare da ta ce uffan ba, kafin ta kalli Zahra da ke tsaye gefe tana kallonta tuntubi ta ce
"Har ga Allah wannan abin kunya ne, toh me su kuma na zuwa da kansu? Ashe haka auren mai mata yake jawo wa? Wataƙila ba mu yi tunanin daidai ba tun farko..." Ta faɗa cikin tausayin ƴar uwarta
Azrah ta fito a daga ɗakin duk tayi kalar tausayi idonta har yayi mugun ja, Bata kalli kowa ba ta zauna kusa da Umma, sannan a hankali ta ce
"Umma ni bazan ci gaba da wannan ba, Zuciyata ba za ta iya jure irin wannan wulakanci ba Idan har auren Honorable ke nufin raini da tozarci daga matansa to ni na hakura ko da kuwa me zai bani ne"
Umma ta kalleta da idanu masu cike da ƙauna da tausayi amma gaskiyar magana kenan itama hakan ne a zuciyarta tun farko, amma bata so ta hana ‘yarta farin ciki dan bata san ko tana son Honourable ɗin ba, kawai ta ɗan dafa kafaɗar Azrah da murmushin amma dan bata san me zata ce mata bane cos she's speechless....
Bayan Magrib kamar yadda honorable ya saba zuwa haka yau ɗin ma yazo kamar koda yaushe, yayi parking motar sa ya sauka sannan ya karasa zauren gidansu ya kirata a waya
Azrahn dake gefen Umma har sannan babu wanda yace wani abu cikinsu taji wayanta yana ringing kallon Umma da Zahra ta yi, Umma ta mata alama data yi picking, bayan su ɗanyi magana sai kuma ta wuce ɗaki ta saka Hijab ɗinta sannan ta fita
Bayan sun gaisa ta kasa haɗa ido da shi har sai daya ce yau lafiya? Tana kallonsa sai kuma ta sauke ido ta ce
"Alhaji don Allah ka gafarce ni Na yanke shawara… bazan iya cigaba ba, ka hakura da Ni dan Allah" ya dinga kallonta da mamaki duk yadda yaso ta faɗa masa dalilin haka ki tayi daga baya ganin ba zai hakura ba yasa ta faɗa masa cikin tsoro.... Ta karasa ta ce "kuma gaskiya tsoro nake ji, Ni ba zan iya zama cikin matanka ba harga Allah"
Honorable ya tsaya yana kallonta da mamaki da kuma tausayi ya ce
"Azrah… listen to me, duk abinda suka aikata sunyi shi ne without my knowledge... I've been trying to protect you shiyasa banma taɓa faɗa musu wani abu game da ke ba"
Amma kafin ya gama magana ta fara girgiza kai hawaye na gangarowa daga idonta ta ce
"Bazan iya ba wlhi ni yarinya ce ba zan iya zama da manyan mata ba... Zuciyata ta gaji kuma Please… just let me go"
Wani irin shiru ne Honorable yayi ya tsaya yana kallon ta kamar yana neman kalmomin da zasu sauya zuciyarta… amma babu wata da zata shige zuciyarta a lokacin
Azrah ta share hawaye a hankali, sannan ta kalli Honorable da ido masu ɗauke da tsoro
"A'a" ta ce cikin murya mai sanyi "Ni ba zan iya zama da matanka ba Sun fi ƙarfi na, Rayuwarsu da tawa ba iri ɗaya bane, Wayon su da salon su sun sha banban da ni, Bazan iya rayuwa a cikinsu ba, kayi hakuri kawai ka kyaleni ko dan saboda Umma ta"
Honorable ya langwabar da kai yana kallonta ya ce
"Azrah please, give me a chance to explain bazan bar ki haka ba saboda ina ƙaunarki, and I promise you, zan kare ki"
"Ka riga ka kasa kare ni!" Ta katsesa cikin sanyin muryanta da kuma wani confidence ɗin magana "Ka gani fa! Sun zo har gida, Ina laifina anan da nayi har hakan ya shafeni pls? Why not su fara maka magana tunda ai kai kace kana so na"
Sai ta fashe da kuka ta juya tana kokarin shiga ciki Honorable ya tsaya cak, zuciyarsa na kuna, amma ya kasa cewa komai. Ya sauka daga matakin kofar, ya rigata shiga cikin gidan zuciyarsa a matuƙar ɓace
Yana shiga ciki, ya hangi Zahra na alwala, ya dakatar da ita a hankali
"Zahra jagoranceni zuwa dakin Umma mana"
Zahra ta kalle shi da damuwa bayan ta gaishe sa sannan ta tafi cikin zuwa ta faɗa wa Umma. Bayan ƴan mintuna ta fito ta ce
"Zaka iya shigowa"
Honorable ya shiga ya gaishe da Umma cikin ladabi sannan ya zauna
"Wallahi Umma, ban san abinda ya faru ba sai da naji, Ina neman afuwa a madadin matana, nasan bai dace hakan ba it's sign of disrespect nayi alkawarin kuma hukunta su"
Umma ta gyara zama tana dubansa cikin natsuwa ta ce "Ba komai Honourable, wlhi komai ya wuce sannan dan Allah Karka musu magana balle wai hukunci" yayi shiru yana kallon wani waje haka kawai yaji ya kasa maganar da yayi niyyar mata kawai ya miƙe ya fita daga ɗakin
Yana wucewa bakin kofa, yaga Azrah tsaye har yanzu tana bakin kofa, idonta jajir. Bai tsaya ba, ya wuce kai tsaye zuwa motarsa, ya shiga ya tada motar zuciyarsa cike da haushi da damuwa
Azrah ta juya jiki a sanyaye, ta shige ɗakin Umma. Umma ta bita da kallo na tausayi, sannan ta sauke ajiyar zuciya Zahra tana gefe ta ce
"Allah sarki shi. Wallahi yana da hali na mutanen kirki, amma matansa... Allah dai ya kyauta"
Umma ta ɗan murmusa "Zahra, har yanzu ke yarinya ce ba zaki fahimci komai yanzu ba"
Yana isa gida, Honorable bai zauna ba ya nufi ɗakin uwargidansa rai ɓace
"Big shame on you, idan banda jahilci da rashin sanin menene hankali ina ku ina zuwa gidansu yarinyar? Ni na kai kaina shine laifi ya zama nata? I'm warning you idan bakuyi hankali ba wallahi You will definitely regret"
Uwargidansa ta zabura tana kallon sa da mamaki "sbd ita har zaka iya gaya mana magana Alhaji? Yanzu sbd wata banza"
"Sure! And mind you, wallahi hakan bai isa yasa na fasa ba, sannan rashin hankalin ku zai iyasa ku tunzura su" murmushin takaici yayi kawai yabar ɗakin zuciyarsa cike da takaicin su.