LABULEN SIRRI (BEYOND THE VEIL)

Episode 18: The Breaking Spell

by @hauwajaywrites

Kamar yadda yanda rana ke fitowa ba tare da izinin kowa ba, haka ne ma rayuwa ta ci gaba da juyawa tsakanin su Azrah da Honourable ba tare da wani communication ba, dan tun daga wancan ranar bai sake zuwa ba sai dai yakan kirata lokacin zuwa lokacin wanda kwata kwata ya kasa gane kan Azrahn, kana ganinsa kuwa kasan yana cikin damuwa wanda hakan bai fasa bayyana a fuskarsa ba

Kamar koda yaushe Hajiya Maryam ta fito cikin ƙasaita da izza irin nata, makullin motar ta a hannunta sannan ɗayan hannun nata tana riƙe da fashion designer bag, tana sanye da sun glasses, ta wuce inda Mijinta ke yawan zama a backyard dan wajan shan iskansa kenan, ɗan taɓe baki tayi tana kallonsa tana ayyana damuwar daya sama kansa saboda wata banza can, ta karasa inda yake ta ce

"Darling" a ɗan firgice ya juyo alamun ta yanke masa tunaninsa ya ce

"Azrah!" Ɗan dakata wa tayi tana kallonsa da mugun mamaki, wani murmushin takaici da kuma bama kanta tabbacin hanyar da zasu bi yanzu shine best way out, dan tana da tabbacin cewa idan har ya auri Azrah, zata ɗauke musu matsayin su gaba ɗaya a zuciyar Honourable, Zuciyarta taji ya buga cike da tsoro, kishi da fargaba, Honorable kuwa shi bai san ya ce Azrah ba kallon yadda ta faɗa duniyar tunani yake ya ce "Maryam zaki fita ne?" Sai sannan ta ɗan kalle sa sai kuma ta ɗauke kai ta juya ta bar shi zaune baki buɗe haka ya bita da kallo sai kuma ya ɗauke kansa daga kallonta ya jingina kansa a resting chair dake zaune akaj

Tana parking a kofar gidan ko kashe motar bata yi ba ta ɗauki handbag ɗinta, wayanta ta ciro a Jakkan sannan tayi dialing numbernta tana ɗaga wa ta ce

"Ina bakin gate ɗinki" daga haka ta katse kiran tayi cilli da wayar a wajan mai zaman banza ta kifa kanta da steering motar tana jin wani zafi a ranta, Allah ya gani dan co-wife ɗinta ma ba yanda zata yi ne amma da zata zauna da kishiya ne? Balle mace irin Azrah, ɗan tsaki ta jaa, can sai ga Hajiya Rabi'a ta fito tana karasowa ta buɗe front seat ta zauna tana kallon Hajiya Maryam ta ce

"Shine ba zaki shigo ba?" wani kallo ta mata sai kuma ta ɗauke kai ta ce

"Bamu da lokacin ɓata wa, kuma Kinsan kauyen nisa gare sa amma kike wasting mana time da nasan wajen da tuni nayi gama abuna ai" Hajiya Rabia ta gyara zamanta ita kuma Hajiya Maryam ta tada motar suka bar unguwar..

suka tafi wani kauye a can cikin wani gari dake cikin jihar Katsina can wani tsohon daji suka nufa, wanda ba kowa ke iya shiga ba sai wanda suke shawara da shaidan ko suke bin huɗubar shaidan, bayan sun yi parking suka sauka suka fara nufa wani hanyar da zai sada su da fadan Mutumin wanda ba zaiyu su shiga da mota ba dole sai da ƙafa, Suna isa wajen wani dattijo mai murya katti wanda kallo ɗaya da zai yi ma mutum zai karanta zuciyarsa, kallonsu yayi ya kwashe da wata kalan muguwar dariya irin ta bosawa sannan ya nuna musu inda zasu zauna, Hajiya Rabia ta fara magana

"Mun zo ne domin wata yarinya me suna Azrah, tana bamu sleepless night.. yarinyar kyakkyawar ce, kuma harga Allah muna son a nisanta ta da Mijinmu, dan ya kwallafa rai a kanta yana son aurenta mu kuma gaskiya ba zamu iya juren wannan bakin cikin ba"

Dattijon ya yi dariyar da ke tsoratarwa ya ce

"Wannan yarinyar ba mai sauƙi bace, ta gina kanta da addu'o'i da azkar, sannan kuma tun daga can garinsu an dafa naman su da magungunan kariya, toh kunga ba wani tsafi da zai yi tasiri a kanta idan kuma kuna so za'a iya mata wani aiki amma aikin zai yi wahala sosai sbd Akwai hatsari ana samun matsala kaɗan zai juyawa kanku" yana kare maganar ya sake shekewa da dariya mai tsoratarwa, kallon juna suka yi sannan suka sake maida kallon su ga Mutumin,yana wani irin abu tare da bubbuga kasa ya ce

"Idan kuma kuna so tunda ita akwai hatsari akan ta, Amma mijinku fah? Nan da nan aikin zai kamasa"

Nan take suka yarda, suka bada kuɗi masu yawan gaske sannan sun bi dukkan umarnin da aka dinga ya musu, ya ce

"Za'a fara da cire Azrah daga tunanin Mijinku ? Za'a rufe zuciyarsa da rashin sha'awar ta balle tunaninta kuma, za'a mayar da tunaninsa bisa ga abubuwan daban-daban sannan za'a saka masa ƙiyayyarta mara adadi a zuciyarsa......"

Tun bayan da suka dawo daga wannan ƙauyen nan, kamar ranan aka fara musu aiki dan tun daga wannan ranan honorable ya daina kiran Azrah, da farko ta ɗauka ko yawan aiki ne na office sai kuma taga shirun yayi yawa, duk da bata son sa amma sai kuma haka kawai ta fara jin wani iri kuma da shirun nasa..

Azrah ta fara jin zafi a ranta.

Tun abin na damu ta har ta mayar da hankalinta ga karatunta da kasuwancinta, ta fara rubuta WAEC ɗinta cikin natsuwa, tana kuma aikace-aikacen gida sbd yadda Zahra ma ta mayar da hankalinta ga karatunta,  Mama da yaranta kuma basu fasa ci gaba da wurga masu Umma da Azrah habaici habaicen da suke musu ba...

Wata rana da yamma Bappah ya dawo daga inda yake zama ya shiga compound ɗin da sallama Azrah ce kaɗai ke tuka abinci ta gaishe shi ya amsa har yayi gaba sai kuma ya tsaya ya ce

"Azrah idan kin gama inason ganin ki ko?" Ta ce "Toh Bappah" bayan ta gama komai ta ɗauki abinci ta kai cikin ɗaki tana kallon Umma ta ce

"Umma barin je Bappah na kirana" Umma ta amsa mata da 'Toh'

Tana shiga ɗakin Bappah tayi sallama ya amsa mata ta shiga ciki ta zauna ta ce

"Bappah gani" ya ce

"Azrah me ke faruwa tsakaninki da Honourable ne? Ban sake jin labarinsa ba daga gare ku, kuma yanzu na daina kallon sa yana zuwa wajan ki lafiya?"

Azrah ta dan yi murmushi mara sauti ta tsunkuyar da kanta kasa sai kuma tana wasa da fingers ɗinta ta ce

"Bappah Inaga ba Alkhairi ne shiyasa, dan yanzu ya daina kirana kuma Nima na mayar da hankalina ga karatuna siyasa banma bi ta kansa ba, kuma yama daina kiran at all"

Bappah ya girgiza kai "To cire shi a zuciyarki, Allah zai kawo wanda yafi shi, sannan zan kirasa muyi magana idan har ya fasa ne sai ya janya a maida masa sadakinsa dan ba'a nema akan nema, Kada ki damu zamu taya ki addu'a Ni da Umman ku"

Azrah ta amsa da "Amin" kanta a kasa har Sannan...

Rayuwa ta ci gaba da tafiya, Azrah ta ƙuduri niyya ta tabbatar da cewa ba aure ne rayuwa kaɗai ba, Duk wata mafarkin da take da shi game da Honourable dama akan Umma ne sbd lafiyarta

Ta mayar da hankali sosai wajen ganin karatunta ya tafi successful tana komawa gida kullum cikin gajiya amma hakan baya karya mata gwiwa ba, Azrah ta daina jiran sakon Honourable, ta mayar da gaba ɗaya hankalinta wajen nasara ne wanda dama tun tasowanta takan dage kan karatu da kuma sana'a

A bangaren Honourable kuwa, tun daga wannan lokacin duk sanda ya fara tunanin Azrah haka kawai tsoro ke kama sa, duk sai yaji kamar a birkice yake, duk da cikin duhun da yake, amma can ƙasan zuciyarsa bata daina tunanin ta ba kuma baya iya kiran ta duk da wata tsanarta da yake ji a ransa, amma bai san dalili ba, haka kawai ya fice daga hayyacinsa..

Kamar kullum yau ma ta taso daga makaranta tana hanyar gida kamar yadda ta saba tun tana karama kanta a kasa yake idan har tana tafiya, tazo zata tsallake babban titin wajan kamar ance ta kalli gefenta kawai ta kalli Ya Saif ya fito a motar sa yana tsayan abu, nan da nan murnan ta ya dawo ta ma manta cewa ta gaji ashe da gudu ta karasa jikin motar ganin kamar komawa motar zai yi tana isa ta sake masa murmushi ta ce

"Barka da Rana Ya Deen" Saif ya juya yana mata wani irin kallon sannan ya bita da kallo ya ce

"Ke lafiya zaki wani zo min jikin motar?" Ta ɗan kallesa sai kuma ta dake ta ce

"I'm Azrah sir, baka gane Ni bane halan, please numbern Mummy da Anty suhaila zaka taimaka ka bani lokacin bani da waya amma yanzu an tsiya min

Dakata wa yayi daga shiga motar yana mata wani irin banzan kallo ya ce

"Malam lafiya? Ko dai kina Bara ne ban sani ba?" Azrah ta tsaya kallonsa with shock sai kuma a hankali ta ce

"Bara kuma akan me? Ko kaga na maka kama da mai raba ce ban sani ba?" Wani kallo yake binta da shi ya ce

"Zaki matsa min ne da kazantar ki ko sai na hanɓare ki kin faɗi tukun nan?" Ja da baya tayi tana kallonsa sai kuma tayi murmushin takaici a ranta tana ayyana cewa da badan Mummy bace Mahaifiyarsa ba, ba abin da zai sa ba tafa faɗan masa bakar magana ba, ko sake kallon direction ɗinsa bata yi ba tayi gaba abinta

Da daddare ta fito daga ɗakin Umma tana haɗa kayan wanke wanken da zata yi and gobe tana da exams da safe, bayan ta ɗibo ruwa ta fara kenan sai ga Mama ta fito daga ɗakinta, Azrah ta ɗan Kalle ta sai kuma ta mayar da hankalinta ga abinda take yi ta ce

"Barka da dare Mama" Mama dake murmushi ta karasa har wajan da take ta ce

"Yauwa Azrah, wanke wanke kike yi kenan? Ba zaki bari da safe ba"

Azrah ta ɗan tsaya tana kallonta saboda sai taji wani iri da yadda Mama ta mata response sbd gaisuwar su ma is hardly ta amsa balle harta nuna wani concern akan su, a hankali ta sauke idon ta kasa ta ce

"Eh da safe ina da jarabawa ne Zahra ma itama tana da makaranta shiyasa" ta gyaɗa mata kai ta ce

"Ayyah, ai naga dare yayi ne shiyasa nace da kin hakura, amma tunda zaku fita da safe gwara kiyi abinki yanzun" Azrah tayi murmushi dan Allah² take Mama ta bar wajan dan kawai ta samu kanta not comfortable, Mama ta gyara tsayuwarta ta ce

"Nikam yaushe ne ma bikin naki? Ko da shike ance kina gama Wannan jarabawar da sati ko? Saura mako nawa yanzu kenan?' Azrah ta sauke idon ta kasa ta ce

"A'a ina ga yanzu ba zai yiwu ba" Mama ta zaro ido irin with much concern ta ce

"Ban gane ba? Wani abu ya faru ne? Ko kuma canza ra'ayinki kika yi?" Azrah tayi shiru dan bata san me zata ce mata ba dan basu saba magana da Mama cikin lumana ba balle har su ɗauki more than a minute suna magana, Mama ta ce

"Kinyi shiru Azrah"

"A'a Inaga ya fasa ne, kuma Nima na fasa shiyasa" Azrah ta bata amsan a takaice, Mama tayi wani murmushi tana ta bin Bappah ya gaya mata yaki gashi yanzu cikin ruwan sanyi ta samu amsar tambayarta, wani murmushin ta sake yi tunawa da shawarar data bawa Matan honorable wanda yanzu ta fara tunanin sune suka bi, daga haka ba tare data sake ce mata komai ba ta wuce ɗakin ta murna fal ranta sai yanzu taji watse

A kwana a tashi a sarar mai rai.. har ta gama rubuta exams ɗinta successful, sanan an saka graduation date wanda yanzu gobe za'a yi....

Ana gobe graduation ɗinsu gida ya dauki salo na dabam, duk yadda Umma da Zahra suka so ta ɗanyi wani abu ki tayi amma daga karshe haka Zahra ta haɗa mata wasu abu ba tare data bari Azrahn ta sani ba, Umma ma gani take atleast ta ɗanyi wani abu tunda abu ne na once in a lifetime, Sannan kuma tana so taga kullum tana cikin walwala ne

Da daddare suna zaune kana ganin Azrah kasan tana cikin farin ciki, Zahra ta ce

"Umma dan Allah ki je tare da mu gobe!" Umma ta mata wani kallo ta ce "Yau naga ikon Allah" ɗaukan wani kayan Umma tayi daga cikin kayanta mai kyau tana warwarewa ta ce

"Umma sai fah kinje Kinga yanzu ma zan saka miki kayan ki a kabbasa tare dana Yaya" Umma ta ce

"Toh Uwata Zahra'u" Azrah dai murmushi tayi tana kallon draman Umma da Zahra

Zahra ta gyaɗa kai ta ce "Yauwa koke fah Umma, ai hakan yafi"

Azrah ta fito da dukkan kayan da Anty Suhaila ta bata ta ce

"Zahra wannan yayi ko?" Zahra ta mata wani kallo ta ce

"Ke kike sa a raina ki, me na ɗaukan wannan, sai kinje an kira ki cikin taro aji kunya" ta fizge wannan kayan ta ajiye a gefe wani haɗeɗɗen lace daga kayan da Aunty Suhaila ta ɗauka tana warwarewa ta ce

"Wannan ya fi" Azrah ta dinga kallonta ganin ɗan gyallen sa karami ne ta ce

"Ke Zahra veil ɗin kayan ɗan karami ne sosai" Zahra ta ce

"And so?" Umma tayi murmushi tana kallon yaran nata