5
by @surayyahms
ABUNDA KE 'BOYE....
Love And scandal💕
Arewabooks@surayyahms
⏯️5️⃣lamarin boyayyr soyayya me zafi da zainab Arifah take kumsawa aranta akan ibaad yakan daure ma kowa kai musmn dake ita da kanta ɓoyewa takey sai ya zamana kowa yana dan dauke idonsa akan wasu abubuwan datakeyi, kafin takacika 14yrs duk matayen familyn al-mansur saida suka san da wannan ciwon obsession datakema ibaad wanda ynxu yafi karfin ace masa tsaftacyar soyayya dan wani bin inbata gansa ba iskar datake busan numfashi dashi kamar dauke mata yake a makwogoro, haka ma duk ran da akace tazo gidan ta gaishesa yahade rai ya wuceta be amsata ba haka zatayta kuka da tsananin fushi kamar me fama da aljanu a dakin anty safeera, wani bin har kaga tana zazzabi me tsananin zafi, haka ma inta koma gidansu xata kulle kanta a dakinta tay ta rabza kuka kmr an bugeta tanajan zuciya wai dan ibaad bai amsa gaisuwarta ranan ba,
gabadaya sai ta Ɗaga ma kowa hankalinsa agidansun, saidai duk rintsi duk wuya bazata taɓa iya furta ma kowa cewa ibaad ne matsalarta ba, kuma shine take mutuwar so aranta a fili ba, yanxu haka iya kawayenta na schl ne kawai suka san asalin meyake damunta aranta..
wasa wasa abun har ya fara zame mata kamar wani strange ciwon ODD wato (oppressive defiant disoder), kowadai ya damu, ganin iyayenta sun fara fita hayyacin su wajen bincike akan sabon sabbin bhvrs dinta yasaka tadan fara kamewa,musmn dataji prof dakansa ya farayin tunanin hanata zuwa can family house dinsun kwata kwata, anashi tunanin hala cutar da yarsa akeyi aɓoye dan baya yawan bada kudadensa ma dangi ana bushasha dashi, hjy hamida kuma gani take kamar maita ne kawai ake so alashe mata yarta kwalli daya dashi acan family house hala shiyasa yartan take behaving strangely dan har malamai takira anyi ma zainab din ruqiya da su hayaki basu san damuwar soyayyar ibaad ne kawai aranta ba.
Ganin iyayentan sun fara daukar zafi akan maganan har sun fara batun yanke hukunci akan zasu hanata zuwa family house din ma kwata kwata yasaka marmaza ta hau neman mafita dan bata kaunar wani abunda zai jawo ace bazataje can gidan taga kyakkwayr fuskar ibaad a wknds ba.
Sangartattun Kawayenta na schl Nala bala da rukky hamza sune suka soma bata shawara, sukace since her 14th birthday is coming up soon ai ynxu tawuce ajin ace mata yar karamar yarinya yanzu kawai taje ta samesa kai tsaye ita tafara masa magana akan abunda takeji akansa. abunka da yara kanana kuma sangartattu yan gata cikin iko da rashin tarbiya da nuna tsagwaron manyance
suka zugata sosai kuma ta zugu,ata fannin ibaad din kuwa lokacin anata rububin ganin sakamakon jarabawane na school of medicine nd surgery pre test zai shiga jamiar Bayero na kano, jarabawar ya fito kenan yacinye sosai yanata kkrin tunkarar karatun medicine dinsa daya ke buri, satin saiga zainab arifah tasha wanka tazota weknds as usual taci uban gaye sosai tasaka wasu purple and white english wears masu aji ,hakanan tazo ta hakimce a karamin falo tasaka anty safeera agaba da shagwaba da manyance akan dole dole taje kawai takira matashi tacemai yazo nan shashen ya samete inyaso snn sai tamasa maganan datake tafe dashi, ita sam bata san hakan ma rainin wayo bane. wai in tana da magana da mutum da mutum toh ita bazata daga kafarta taje ba saidan in mutumin yazo har inda take ya sameta koda kuwa ya girmeta sosai.
dake tariga tasaba komi tace musu tana so ana mata haba haba, kawai yau sai taji mugun mamaki dataga anty safeera takekeshe ido tace mata bazata iya zuwa sashen ammi karama dan ta kira mata ibaad nan ba saidai in ita taje ta samesa dakan ta, a wasa ta dauki maganan dake ba'a saba ce mata "no" ba can kuma sai taji haushin hakan sosai, saidai duk a tunaninta na yaranta ta dauka hala kawai tsoronsa suma manyan matan gidan sukeji, mugun yarda dakanta datayi yasaka tamike tana mao gyara zaman kayan jikinta cikin jan tsaki kai tsaye tajeta har sashen ammi karama tana takunta ahnkli kuma ayangace kamar bazata taka kasa ba.
cikin cin sa'a kuwa sai ta samesa tun a babban falon gidan da laptop agabansa yana kan kkrin registering kansa for clearance dan shi babban likitan zuciya (cardiologist) yake da burin yaga ya xamo dan haka karatu ne meyawa agabansa, lkcin kansa yadau zafi yanata cike cike sqi ganan zainab arifah ta doso, tsayuwar cak tay daga samar stairs tana kallonsa dan duk dama tana mutuwar sonsa babu karya dakakken kwarjininsa yana mugun girgizata, tafiya take kirjinta na tsananin bugawa amma data doso kasa ta falon tadan kare mai kallo duk sai taji takara mucewa da sonsa a tsaye, he was wearing this very clean plain cream shirt da yaji karin guga haɗe da plain coffe brown trousers, tsaftarsa da kwarjinin sa sosai yakara cike mata ido gashi bao saka turare me karfi saidai me sanyi wanda daga ka doso sa zakaji kamar a fatar jikinsa qamshin yake tashi.
jin kirjinta na bugawa fat fat kamar zai ballo waje taji tsoro yadan kara rufeta, dacan har zata hakura takoma dakin anty safeera ta kara shiri sai kuma ta tuna cewa iyayenta zasu iya hanata zuwa gidan kwata kwata in har batay wani abu akan abunda takeji akan ibaad ba, nan da nan kuwa sai ta cije ta danne tsoron, gashi dama bayan gaisuwa sama sama basu taɓa yin wani maganan 2 scnds dashi ba all this years is like baisan ma tana existing ba dan ya jima da tsanar behviours inta na raini da sangarta.
kwas kwas ta karaso cikin rangwadi da yadda da kai batay mai sallama ba iyaka qamshinta ne ya bule wajen tabi ta kuresa da manyan idanunta tanaji aranta kamar zata haɗiyeshi, idanun sa stiff suke akan system dinsa ko daga kansa baiyi ba haka zalika baice komi ba har tanemi waje daf da chair dinsa ta dan zauna ta kuresa da ido., shiru ne ya dauke wajen ganin bazai kulata ba aftr like 10 min cikin rollng idanu tace amm hi, can i have ur attention here. yay shiru kamr badashi takeyi ba
tweeking fingers dinta tay ayagance gaban screen din laptop din suna hade ido tace "hey, bakaji abunda nace bane ?? fusknsa a mugun harde yace "what? tace "you" i just talke to u .cikin katseta yace ohhhh "sallamar ki kenan?
"my bad"..assalamu alaikum.
dauke kansa yay saida yaja kamar 3 min snn ya amsata ciki ciki.. tace "can i talk now.. irin kallon ohonkin dataga ya mata yasata dan kyabe baki cikin sauke ajiyan zuciya tace "anyways.You should probably calm down before I actually admit I’ve been crushing on you. maybe your ego won’t survive it. ina so in gaya maka cewa ive been thinking about u, i think i am in love with you ibaad.. ina so..wani irin dakakken kallo yamata tunkan ta karasa ba cikin datsar numfashinta yace "i have heard enuf kitashi kibarnan.
karamin murmushin ko inkula tay snn tazuba masa manyn idanunta masu cike da tsagwaron rashin kunya atakaice tace
"excuse me?? iya abunda zaka ce kenan? Ugh i cant belive this, I don’t even know why I’m saying this, but I’ve kinda had a thing for you, wai ko baka gane me nake nufi bane...
wayar chagersa kawai ya cire a wuta ya miƙe tsaye har zatai mai magana cikin daka mata tsawa yace kee bance miki kibar nan wajen ba? sai zuttt zutt taji saukar bulalan ajikinta..
within mins akaji ihunta yana tashi agidan..
ahhh, wayyooo,wayyo daddy, daddy, daddy naaa, mummy wayyo Allah ibaad kayi hakuri..daddy kazo ka cece ni wayyo ihu kawai take zubawa me kara tana daka tsalle a mugun rude tana kuka me kara
kusan babu wanda bai razana da ihunta ba, kaf matayen gidan suka firfito duk akayo falon ammi karama arude dan basu taɓa jin zainab arifah na wann ihun ba, nan aka samu Ibaad ne ya rike hannayenta biyu yana cauda mata wayar chargensa ajikinta yana kuma tmbayarta "ko shi sa'arta ne? kiris ya rage ta sume masa dan tunda aka haifeta ko tsawa ba ataɓa mata na bare duka.
yaa maheer ne yay sauri ya karɓeta a hannunsa dan wani irin razannen kukan takey a mugun mugun tsorace jikinta na rawa rawa kamr ba ita ba, wanda hakan yasaka tuni idanun mujaheed ya tara ruwa dan yana da tausayi sosai, atake kowa yafara daga hanklinsa ana ta tuhumar ibaad ko me zainab arifah tayi masa, ammi babba da anty safeera duk sun dau zafi suna kiran sunan sa ana tuhumarsa falon ya kacame da hayaniya sosai.
baice musu komi ba yahaɗe ransa ya koma yazauna snn ya dauke kansa ya cigaba da latsa computersa anata surutu ko ajikin sa face saida uncle moh dakansa ya shigo wajen yafara tambayarsa, agaban kowa ya mike tsaye snn ya maida musu abunda zainab arifah tace mai nawai tana sonshi bla bla bla, ibaad ya nuna bacin ransa sosai, ya hada harda sauran cousins dinsa matan duka wato (kulthum da sultana) yace karda wata yarinya ta kara masa wann wasan shi baison hauka yaushe ma sukakai da su furta ma namiji batun soyayya tun suna early teenagers???
daga uncle moh sai maheer ne kawai suka nuna sun fahimce shi, mj kam baice komi ba saboda kukan balai da zainab arifahn tayi sosai ya jefasa cikin tausayi da rauni gashi dama suna dan shiri sabida shi yaron anty safeera ne kuma age mate dinta kenan dama agidan they are both going to tru the same age.
sauran yaran gidan ma sosai suka dada firgita da tsorota da fushin ibaad, sanin cewa babu mahalukin dayake da ikon taɓa zainab arifah ko ɓata mata rai agidan yadda ake mugun daukarta yar gwal saigashi ibaad ya zane yar banza ciki da bai kamr baisan waye ubanta ba.
duk dama dattijan matayen sun san cewa dagaske ne Zainab arifah tanason ibaad amma haka suka haƙikance suka bi suka dora masa lefin komi duk sukace ai kawai gigin yaranta ne yake damun zainab ibaad bai kyauta ba yayi over reacting yaci zalin yarinya baida haquri,..
kai wasa wasa wasu bakaken maganganun da ammi babba ta hau furtawa ma zaka dauka wani babban zunubi ya aikata, har cewa take zainab arifa din ma aitafi karfinsa a batun soyayya sabida ita tanada bright future ahead na gadon dumbin arziki daga kawu babba shikuma ibaad din yananan ba'asan ma yazai kare anashi rayuwar ba. tanayi kuma tana soka zagi ma uwarsa asakaye itadai ammi karama hakuri kawai ta bayar ma kowa sai bata kara cewa uffan ba ta koma daki.
haka matayen sukayi ta kananan magana a gidan ranan babu kalar rarrashi da kwalemar kwainane wanda ba ama zainab arifah ranar agidan ba,
ammi babba anty safeera Da mj duk suka taru akanta suna ta lallashinta a daki.
shikuwa ibaad ko ajikinsa har yanxu ma mamakin tsaurin idon zainab arifah din yakeji aransa yadda tazo masa gatsau ta samesa babu wani dandanin tarbiya ko kunya ajikinta tamasa maganar soyayya da dumbin tsaurin ido da shegen manyance kamar wata yar shekaru talatin, mugun hade ransa yay da kowa agidan shima, bai kuma bawa uban kowa haquri ba face saida mahaifyrsa takirasa daki snn ta masa faɗa tacemai da baidake zainab din ba da faɗa kawai yayi mata, nn ne ma ya sassauto ya ba da mum dinsa hakuri har yace mata bazai kara dukan musu ƴa ba tunda bataso. da kyar da wahala dai wann maganar tay sanyi ranar ma da dumbin zazzabi zainab arifah tawuce gida, taki sam iyayenta suga shatin zanan dukan ajikinta.
shiru shiru har ana zaton komi ya lafa washe gari da yamma ammi babba dataga alamar maganar zai mutu abanza aikuwa nan tadau waya takira gidan prof zayyanu wanda da kyarma aka samu aka haɗata da hajy hamidar suka dan gaisa babu ɓata lokaci tahau zuba zance cikin sigar makirci harta sanar da ita komi da ke faruwa bata rage ko aya aciki ba saima gishiri da maggi data zuzzuba dan labari yayi zaƙi ita kuma ta samu karbuwa.
bazan iya fayyace kalar tashin hanklin data ballo ranar ba, dan ranar gidan prof ko xama basuyi ba, hjy hamida tana gama aje waya jikinta yafara ɓari da tsananin bacin rai, nan da nan takira mijinta tacemai duk inda yake kawai yazo gida yanxun nan za'a kashe musu yarsu da duka, yana can airpot kano amma jin anfurta batun yarsa hakanan ya mance komi ya dawo, yazo gidansa ga samu matarsa cirko cirko duk ta birkice tana huci kamar zakanya tanakuma safa da marwa a wargagejen falonsu da hadadden wayarta a hannu dan tagama qudirawa aranta kawai sojoji zata tura aje har family house a zane kowa dake wajen ciki da bai snn akama shi ibaad din akaisa military gurd room amasa lilis sabida dukan yarsu dayayi
sosai abun yayi ma prof ciwo aransa bana wasa ba, danko shi bai taɓa yin tsawa wa yarsa ba bare duka, saidai harga Allah yasan bazai taɓa iya kama ibaad yakaisa gurdroom akan haka ba yasan za'aje ne akashe shi, kuma haryau yana dan girmama babban wansun aransa wato marigayi dr almustafa mahaifin ibaad, dake shine kawai adangi bai taɓa guje masa ba duk mugun halinsan nan yana tolerating dinsa har ya rasu.
hakanan dai yay masifa yay bori yay bambami snn yabi ya danne xuciyar matarsa aka bar maganan sojoji agefe, nan sukaje har dakin zainab Arifah suka tasota agaba da maganan ibaad, dacan taki sam ta gaya musu amma suma nace mata da nuna bacin rai da lallashi dai har saida ta hakura ta gaya musu dukkan abunda takeji na matsanancin soyayya akan ibaad.
lamarin ya matukar daure musu kai, ya saka musu tsananin baqin ciki tare da dumbin mamakin yadda at this young age soyayya me tsananin zafi ya kama zuciyar yarsu, tunda suke da ita bata taɓa musu kuka irin nayau ba, sai rokonsu take akan kar su masa komi har cewa take zata mutu in sukasa ibaad yakara tsanarta itade tana sonshi. it was pretty serious nd obsessive, amma dake suna matsanancin so ta kawai sai suka bar maganan, suka mata fake promises suka lallasheta sosai cikin nuna mata dumbin soyayya da kuma matsanancin gata, a tunaninsu duk yarinta ne sunaji aransu maybe tsabar kyau da kuma kwarjinin ibaad din ne kawai yake dan rudinta inta girma ma zata manceshi sabida matsayin rayuwarsa ma aiba daya bane.
suka mata wayo suka nuna sun fahimceta, hardai ta amince tay shiru, likitansu na musmmn aka kirawo yazo ya dudduba jikinta musmn wajen shatin bulalan aka bata wasu special pain relievers da kuma underage antidepresant drugs tasha sabida yadda ta bi ta galabaice sosai.
dan kawai hankalinta ya kwanta haka iyayen suka nuna mata cewa zasu mata dukkan abunda take so din, bazasu taɓa ibaad ba tunda ma bata so ataɓashi. amma fa sosai abun yayi ma mahaifyarta ciwo aranta bana wasa ba dan tabalain so ace taci mutuncin kowa agidan akan wann abun da akama yarta. shikuma prof zayyanu
ji yake ko a mafarki bazai taɓa aura wa yarsa talaka ba bare kuma har ajega batun auren dangi. dukkn su iyaye ransu bai musu dadi da lamarin nan ba. they just try to numbed it a fuskarsu, acting all fine nd supportive while they are not dan kawai kar zainab arifah ta gane basaso ta shiga wani mummunan hali gashi
dakyar Allah ya basu ita.
arana ranar da daddare bayan likita ya gama dubata nan danan prof yasaka hajy hamida ta shirya tawuce da zainab Arifah din izuwa kasar sydney on a 5 days daddys girl petting break waidan kawai hanklinta ya kwanta
ahakama prof bai daddara ba, suna wucewa sydneyn maza maza ya kira uncle moh a waya, ko sallamarsa bai amsa bare gaisuwa yahau sauke masa buhun masifa ta inda yake shiga batanan yake fita ba, kai tsaye babu sakayawa ya masa ihu ihu ya zazzagesa sosai yace musu da shi da bappa zaidu sune suke daure ma ibaad gindi dan ya kashe masa yarsa kwalli daya, yace dama can yasani bason suga ya haihu sukeyi ba kawai so suke ya mutu a dau dumbin dukiyarsa abasu,.
babu irin zage zagen da zarge zargen da baiyi ba. tun uncle moh yana shiru har kirjinsa ya fara zafi tsabar fushi kawai sai ya kashe wayarsa..
yana katse wayar yazo gida yahau sauke fushin akan ibaad tareda sakamai dokan cewa karya sake dukan kowacce yarinya agidan inba hakaba kuma shi gskiya zai kai kararsa wajen bappa zaidu.
har yagama masa fadar Ibaad dai baice masa komi ba san already ya riga yay ma mum dinsa ma alkwari.
daga fannin ammi babba kuma duk ta kasa zanne ta kasa tsaye tana Allah Allah washe gari yay taga anzo har gidan an ci mummunan mutuncin ammi karama tareda danta ibaad amma sai shiru kakeji, ita bata karajin bayani daga wajen hajy hamida ba hakazalika nan ma bataga anzo anyi hatsayina ba, kai hanklinta bai kwanta saida ta kira anty safeerah toh abakinta taji cewa ai prof ne kawai ya kira ya zazzage su uncle moh. ranta baiso ba duk dai ba haka taso aranta ba.
bayan kusan sati biyu da faruwar haka da kyar iyayen zainab Arifah suka barta ta dawo tana zuwa gidan duk weeknds, saidai wnn karon ta dan shiga hanklinta bata fiye wulgawa ta inda ibaad yake ba dake ma yanxu baya zama yana kan kkrin shiga jami'a ne abunsa. da mujaheed kawai suke dan magana sama sama intazo gidan dake shine sa'arta, shikansa Mjn wani irin mamakinta yake dada sha musmn yadda yaga duk ta sauya salo tanata kkri taga lallai tasaka hanklin ibaad ya dawo kanta, dan kamar ma kara hura mata wutan son ibaad din aka ɗadayi aranta kwana biyun nan..
ANGUWAR TUDU ...
Da yamma ne lis gari yay sanyi yara suncike kan tituna da hayaniya da alamun lokacine na sakosu daga babban makarantar higher islam na yara dake anguwar dake mashi kadaine a anguwar duk wani yaro ko yarinya dake zuwa schl a wann yankin nan duk ake zuwa karatu.
daga cikin rububin yara yan mata inayah da ayanah suka fito suna tafe manne da junansu, yanayinsu na nuna dumbin soyayya na yan uwantaka da dumbin shakuwa a fili take nunawa, duk dama wuni sukeyi makarantar amma tsaf tsaf zakagan uniform dinsu, rigarsu fari kal ne sai hijab da wandon kuma dark green colour kowacce da yar jakar littafanta
ta saƙa akafadarta.
Fasalin jikinsu da kuma kamaninsu dake saurin fallasa mixed tsatsonsu na asalin jinin buzaye haɗe dana fulanin daji ya saka sukayi masifar kyau atare, yanayinsu gwanin ban sha'awa suke tahowa duk jikin su akillace yake acikin green hijab dinsu..
kalar bakaramin yi musu balain kyau tayi ba saboda yadda ta amshe kyakkwan tsarin fuskarsu da yanayin su na yan mata masu fallin tasowa, gaban su gadi suke takawarsu cikin nitsuwa da sanyin jiki dan inda sabo yanzu sun saba da yanayin yadda idanun kowa ke satan kallonsu msmn ma ayaanah datake da wani irin rare calming beauty ita ba fara sol ba ita ba baƙa ba ita ba cokolate ba, tana dai tsaka tsakiyar hasken fulani dana buzaye duk ta hada kamannin biyu, ita kuma inayahr akwai kyan ta dake nuna na fullo haƙƙ babu mix da kuma tsayin ƙafa na mahaifyarsu taawure data gada, duk da kankantansu kallo daya zaka musu kasan cewa tabbas wayann yaran zasu zuba dirin jiki me daukar hankali, kai daga nan ma zaka san sudin nadaban ne acikin mata.
Kamar yadda suka saba kullum adaidai hanyar da yabi kwanan gidan sarkin kasuwa sukeyin sallama da sauran yaran schl dinsu nan bayan sun rabu sai kowacce tanufi cikin gidar iyayen ta.
lokacin yamma ne liss masu zuwa kai haraji da reports gidan sarkin kasuwa anata kkrin kai da komawa yawanci zaka ga kofar gidansun da matasa sosai da yamma
tunda suka doso inayah ta sauke kanta kasa cikin sauri sauri sanin bamai yin lokacin kula gaisuwar su saidai ayita comparing kyanta dana yar uwarta, ayanah kuma mugun tsoron maza takeji dan haka tun kan su iso ta wajen ta fara ɓari ɓari ta kuma kara tantame hannun addanta inaya.
tafiya sukeyi cikin sauri sunajin yadda kananan zunde da gulma kala kala yake tashi ako wani tsirkon taro dake kofar gidan
nasu ,tabbas mafi yawan matunen dake zuba musu ido kullum ba dan Allah bane sai dan gulma munafurci da nuna hassadar su a fili dan kaf anguwa an ririta zancen cewa yayan tàawure me saida nono da suke ɓakunta a anguwar sune masu dumbin kwaxo a makarntar tudu gabaki daya gasu kuma da balain kyau har ana kafa caftersu agidajen mutane.
kamar kullum ido ne ratata akansu, inayah ce me karfin xuciyar kanta akasa sai jan hannun kanwarta take da sauri, suna kaiwa
kofa tsabar ɓari kawai sai jakar ayanahn ya subuce a kafadarta ya faɗi. da sauri inayah ta saketa ta tsuguna kasa zata dauka jaƙar tana tsugunawa kuwa a mugun gigice kuma abazata ta riƙe gefen cikinta da sauri tanamai furta innalillahi wa inna ilaihi rajiun.....da karfi
tun kan ayaanah ta dago kai gabaki daya sai sukaga idanun matasa da dumbin mata dake kofar gidan sarkin kasuwa sun dawo da idanunsu kan inayahn atake da wani irin mummunan kallon zargi....
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻
AREWABOOKS
@SURAYYAHMS
WATTAPAD @SURAYYAHMS
WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025