ABUNDA KE 'BOYE...

9

by @surayyahms

ABUNDA KE ƁOYE....

Love And scandal💕

Arewabooks@surayyahms

⏯️9️⃣

Door bell securityn ya danna within 2 mins wata maid sanye da torqouise colour uniform ta buɗe kofar tafito, suna hade ido da ibaad ta tsaya cak tana kallonsa cikin haɗiye yawu a fixge ta dauke idonta a nitse tace ma security "i will take it frm here. kai ya gyada mata baice komi ba yajuya yabarta tare da ibaad din awajen, cikin kare masa kallon rudewa ganin kamanin jini da prof a fuskarsa yasa tace "please come in ure welcome sir.."fuska ba yabo babu fallasa ibaad yace thank you gaba tay yana biye da ita abaya suna shigewa ciki aka rufe kofar gidan kirif.

Katafaren Parlour ne mai wani irin girma da tsari dayaji Lumtsattsun kujeru na royal chairs golden and red colour. labulaye da chandelliers suma golden colour sai baza qyalli suke snn Duk wani abu daya ƙawata Falon ya zamto shima golden nd red colour dinne da wasu irin manyan turkish carpet, manya manyan Airmores da incence burners kusan kowani kusurwa suna aikin bada Dadaddan Qamshin turarruka na alfarma da kuma iska mai sanyi wanda already sanyin ma yakama falon takoina sabida wata irin dukiyace ta musamman aka narkashi acikin wnn falon.

Babu kowa acikin falon tasu ta farko wanda shine zai sadaka da babban falo na biyu wanda ya kasance falon zama daganan kuma har zuwa sashen cin abinci.

Ratsa dogon Falon tayi ibaad na biye a bayanta ta nufi kofar da zai kaita ainihin falon prof zayyanu na musamman tana isa dede wajen kofar ya budu ta tsaya cak anan tamasa alama akan da yakarasa shiga shikaɗai sabida prof already yana ciki, uffan baice mata ba cikin takunsa mai sanyi da aji ahankali yashige ciki ita kuma takoma gef ta tsaya daga nan tana jiran fitowarsa.

Katafaren falone na alfarma an masa kwalliya da dusty rose da wani irin cool black furnishings, wanda shirun da wajen yay tamkar babu kowa aciki banda qamshi da ƙarar ac dake tashi ahankali.

Ajiyar zuciya ibaad yay tareda ta sakin masa nitsatsiyar sallama ayayin da prof ya dago kai yanamai sauƙe ruwan idanuwasa akan ɗan yayan nasa.

Zaune yake cikin shiga ta alfarma jikinshi killace da manyan kaya wanda tuni tay bajintar fallasa siffarsa na kyakkwan namiji mai cikar zati,jarumtacce mai kuma cikar ƙirar halitta da dirarren siffar jiki. Kallon daqiqa biyu yayi ma ibaad din,ganinsa lafiyayyan yaro mecike da tsananin sanyin kyau da cikakkaer kwarjini me rikitarwa zak zak irinna mahaifinsa wanda hakan ya kusan rudasa atake, ji yay aransa inama ace Da Shine Allah ya bashi wnn darajar samun ɗa namiji dakakke irin wann ba babban wansun daya rasu ba.

saurin daidaita kansa yay cikin tattaro makansa nutsuwa da ƙarfin hali yanamai sakin masa murmushi adan dake har ya amsa sallamarsa tare da umartansa akan ya karaso ciki.

ibaad na karasowa ya tsuguna kasa daf cikin

nitsuwa ahnkli yace "ina wuni kawu, fatan na sameka lafiya?

prof ya karemai kallo sama da kasa cikin yanayin kamiya adan tsime yace masa lafya kalau, shiru ne ya dan ratsa kafin yace" Kaine babban ɗan marigayi ko? bayabo ba fallasa ibaad yace eh nine, prof ya gyada kai, but u can see the provocking jelousy nd envy wailing tru his eye balls, dan yafiso ace kowani abu mekyau a duniyan nan shine zai mallaka msmn yadda yaga ibaad yafara girma cikin nitsuwa izuwa hadadden namiji mai kwarjini da aji sai yakeji aransa inama ace danshi na cikinsa ne bana yayansa ba.

cikin kaucar da wann tunanin yace ohh babu shakka, i can see the resembelence, "wai har ku nawa ne ya haifa haka? batare da dago kai ba ibaad yace "mu biyu ne. prof ya kara zuba masa ido da mamaki ayayinda shiru yadan ratsa tsakaninsu sai can snn yace umm well, dats fair amma kuma dukanku maza ne? nasan da babanka bai rasu ba hala da ƴayansa sunfi haka yawa,..baima bar ibaad din ya amsa shi ba cikin yanayin mita yace" babanka shine babbanmu a ahalin nan amma bansan mesa yaje ya auro yarinya karama ba, uwarkun tana raye ko itama tabishi?..

ibaad ya dago kansa ahnkli suka haɗe ido fuskansa adan daƙile yace mishi "she is alive. prof yay dan kwafa a shashance "tou hakan yay dai-dai alhamdullh tunda kuna da wacce zatana ciyar daku kai tashi muje ciki nagaji da wann surutun..ibaad yay shiru kamar baiji shi ba, har saida prof din yamiƙe yafara tafiya snn ibaad din ya mike tsaye shima yafara binsa abaya,

wani katafaren hallway suka ratsa, acikin izza prof yake tafiyarsa yana lallatsa wayarsa kai daga ganinsa kasan ba har cikin ransa yake son wnn yanayin ba, shidai kwata kwata baison yan uwansa na jini suna raɓar gidansa bare arzkinsa wnn karon ma babu yadda ya iya ne rayuwar yarsa tafi mai komi muhimmnci a yanzu

suna shigowa wani katon white hall mai tattare da babban dining area sai ga nan matarsa hajy hamidan tabude wani babban kofa ta fito amugun mugun kasaitance wani irin kwalliya tayi tamkar ɗawisu qamshin hadadden turarenta tuni ya bule wajen da qamshinsa, tana taku dai dai kmar bazata taka kasa ba, tasaka wani ubansun boubou na original shadda lace royal blue colour wuyanta da hannunta sunci uban su da gwalagwalai.

suna hade ido da ibaad ta tsaya turus tanata kallon yaron cikin fallasashen ruɗewa dan acikin ranta batay tsammnin wai harya girma ya ƙara kyau haka ba, tasan dai zainab arifah tana yawan zuzuta kyansa ita a mind inta she expects to see notin but a hungry local boy with no social class, dan rabonta da ganin fuskarsa tun ahoton haihuwarsa datagani awayar anty safeera.

cikin neman wakanta nitsuwa tay gyaran murya me aji tabi ta tsime batako musu sallama ba dake taga mijintan nakan amsa call kai tsaye ta shigo cikin dauke kai tayi kamr batagan ibaad a tsaye ba.

tana zama akan chair ibaad ya daga ido ya kalleta daga tsayen yace"ina wuni ? ranta a harde ta masa wani irin kallon sama da kasa me shaqe da rainin wayo muryanta ciki ciki tace "lafiya. snn ta dauke kai tay banza dashi, shima sai bai kara kallonta ba, shiru ne ya ratsa tsakaninsu dan wani mugun haushin yaron ne ya riketa kamr zai fasa mata kirji irin feeling feeling dinnan najin anrainata dake ta riga ta saba ana yawan mata fadanci ko mutum ya girmeta zakaga yana rusuna mata kai kasa sabida matsayi da dumbin ikonsu, yadda tagama raina ma labarin kyan ibaad wayo sai kuma tazo taga ya ashe ma wuce yadda take tsammani tun daga siffarsa har izuwa kan dressing insa me mugun dauke ido da uwa uba yadda dadin turarensa me aji ya kusa danne nata me matukar tsada.

shi mutum ne wanda iya tsaftarsa ne zai soma dauke maka hankali, he always look so smart nd very neat, shi baya son tula kayan sawa ajikinshi amma kuma sutura me bala'in aji yake yawan sawa.

prof ya gama wayarsa kenan ya kallesu duka ganin kowa ya dauke kai sai yay gyaran murya yace hajiya hamida wann fa shi ne dan gidan marigayi babban yayana late dr almustapha almansur.

cikin rolling ido ta juyo tanamaiyin kamar tuntuni bata ganesa ba, da wani irin yaken makirci tace ohhhhh ayya, Allah sarki ashe dan marigayi ne, gashi kuwa ya girma da kamannin mahaifinsa, gosh jishi duk ya zama abun tausayi toh Allah dai ya jikan babankan, ran ibaad yafara baci bt still ya kwantar da hanklinsa yace Amin. ido ta zuba masa ta kara kallonsa ita dai gaba ki daya ji tay kmr taƙi jinin yaron dan daga ganinsa tasan zaiyi girman kai yadda taga ya hade ransa baya ko murmushi, saida ta gama kare masa tanaɗi aranta sann tace Alhaji sai ku karasa dinning din i am sure we are all famished.. prof yace aa hajiya kinsan ni bawani son cin abnci da yamma nakeyi ba amma dai tou bakomi muje dai zan taɓa.

tay murmushi yawwa my darling ai kuwa dazance kar kayi haka

ta kalli ibaad da rainin wayo a kwayar idonta cikin rage murya kasa kasa inda tasan ibaad din zaiji tace "ohh ni hamida dama haka yaron yake abun tausayi, alhaj ya naga duk yunwa ne ajikinsa kasan me? kuje kawai kan dinning din zan sameku acan i need to check on our princess,

prof baice komi ba ya gyada mata kai tana barin wajen ya kalle ibaad wanda already zuciyar yarinta na raya masa akan kawai yaqi cin abincin ya tafi sai kuma yay wni tunanin kawai sai ya danne zcyrsa yabishi suka zauna akan dinning table din kusan atare.

nan ma shiru ne ya ratsa tsakaninsu har saida hajya hamidan ta dawo ganin ita daya ta fito babu zainab arifah yasaka tun bata zauna ba prof ya fara tambayatta inq yarsan take, fuska ba yabo ba fallasa tace "alhaj ka kwantar da hankalinka she is coming kasan dai yarkan sarauniya ce mai son kwalliya da tsafta, so she will be here in few minutes dai tacemin, cikin jin dadin hakan yace its awryt let her take her time she will alwys be the prize, atare sukayi dariya. shide ibaad baice musu uffan ba,

daga kan long luxurious table din ido kawai bazai iya kirga abincin da ake jera masa agabansa duk dan a nunasa nasa bambamcinsa da su.

abincin gargjiya har tuwon biski ta saka anyi wai a tunaninta ko yaron baisaba cin na yan gayu irrinasu ba, itafa komin arzikn ka inhar ajinku ba daya bane to A talaka kawai take kallonka.

sunfi 10min suna zaune ba ataɓa komi na abincin ba sabida suna jiran yarsu yar gata zainab arifa ta gama duk abunda takey snn ta karaso.

hirar business suka faray sama sama tsakaninsu ganin ibaad bamai son magana ba yasaka basuma tsomasa aciki ba.

after like 10 more mins tahowa zainab Arifah takeyi akan golden steps cikin shan qamshi tana taku kamar bazatay ba domin itakanta qamshin turaren data fetsa ajikin nata tsabar yawansu da karfin qamshinsu ji take kmr suna bugar da ita, daya bayan daya take dora kafafuwanta akan step, cikin tattalin kai

can saiga ta bullo ta wajen inda suke wanda tundaga sama ta zubawa ibaad dake zaune akan luxurious dining table din da aka kawatashi da ababen tabawa ido tanajin kamar mafarki takeyi, wani irin sabuwar farinciki takeji mai yawa na mamayarta har kwakwalwa data gansa.

Kasaitaccen sautin takunta shi yadan janyo hanklin iyayen nata bisa gareta dan tay masifar kyaune na kure hankli saide duk gigin zumudintan nan kuwa bata wani tula kayar tashin hankli ajikinta ba, doguwar riga slay queens gown styles marar hayaniya sosai tasaka ajikinta na babban atamfa original engila red colour snn ta cakkara dauri tare da zubo da sumarta kafadunta, cos at this young age already ta fara saka irinsu nails da curtex da gashin doki duk dama babu laefi itama din tana da dogon suma., cikin nitsuwa ta sauko cos she rmbers clearly cewa babanta yace mata kar tay rawan kai agaban ibaad, dan haka tay balain kkri wajen danne abubuwa dayawa na zumudin ganinsa dake yawo cikin ranta da zucyarta.

faduwa gabanta ya dingay har ta iso tana satar kallonsa, iyayen atake suka hau yaba kyanta kamar yadda suka saba, itakuma tana fmr shagwabe musu fuska, ibaad yadago kai kenan suka hade ido da ita, gabanta ne ya mugun fadi saikuma taji takasa motsi tabi takafe shi da kallo mai sanyi kamar bata taba ganin kyakkawa irinsa a duniya ba.

ganin ya dauke kansa a kallo daya yasaka itama ta dauke kantan ahnkli cos she was lost in her tots for a moment dan batama jin me iyayen nata suke cewa kawai satar kallonsa ta dingayi harta karaso gefen baban nata ta nanike ata gefensa yarike mata hannu cikin tsantsan nuna mata soyayya da gata a fili, a shagwabe ta zauna daf dashi batace ma iyayenta uffan ba, tay cunen baki tanajin kanta a matsayin yar gata sangartacciya kuma ƴa guda awajen iyayentan wanda tasan zasu iyayin komi akanta a duniyan nan, yau yadda kasan danyen tuwo haka take narkewa jikin babanta. Tun data nemi waje tazauna acikin yanayin shagwaba batace uffan ba bare tay gaisuwa daga ta turo musu baki, sai tay rau da idanunta cikin tsinannen rigima.

hanklin ibaad gabaki daya baikansu jin yadda iyayen suka fara jajayya da ita wajen gaisuwa dan tun safe bata gaishe da iyayen nata ba.

yau sosai yakara lura da cewa zainab arifah din sangartacciya na kure hankali da tunani kalar wanda tsarin rayuwar banza ya riga yashige musu jikinsu sosai.

da kyar dai suka sakata tay gaisuwar harta gaishesa ya amsa atakaice kafin nan baban nata dakan sa ya bada oda masu aikin gidan dake akansu suka fara aikin serving dinsu abinci wanda gabaki daya wajen ya gamutsu da wani irin qamshi me shegen dadi ga nan dadadan aroma na garnished soups da gasashun namar kaji.

sama sama ake hira akan table din..shide ibaad sam ya kasa fahimtar kalar rainin wayo irin tasu cos all this traditional food tagabansa kawai ake tarawa hakama idan za'a samai abu a plate dinsa sai ancika plate din kamar sun ga mayunwaci ko mabaraci. shide tun da ya rike spoon yana jujjiya wa bai isa yace yayi loma yakai uku ma abincin ba..

prof ne yake magana time time yana kushe kokari, ilimi, da arzikin kowa cikin familyn su al-mansur, at same time yana dan sako labarin mahaifin ibaad din dake duk zuria shine kawai bai taɓa yin zuciya dashi ko ya rokesa kudi, ko wani taimako ba. hasalima badon shegen son zumunci irinna mahaifin ibaad ba da tuni prof ya raba kansa da zuriarsa sabida bappa zaidu da uncle moh sai suyi shekara fiye da hudu ma basu kulashi ba.

shi bawani cin abincin yqke ba kallon ibaad kawai yake yana cewa..."babanka mutum ne mai mutunci duk zuria shine kawai be taɓa nunamin baqin cikinsa ba,shi yasa nake jin kamar ba zaidace mubari zumuncin daya kulla da gidan nan ya yanke gaba ɗaya..

duk da prof baison zumuni bt he try to pursuade ibaad dan yaji aransa cewa zai iya amsarsa agidansa a mtsayin ɗa kodan albarkacin mutuncin mahaifinsa.

hajy hamida kuma tafi matsuwa datasan educational level din ibaad bawai dan zai mata amfani ba saidan ta samu wani makafar ci masa mutunci da kaskantar dashi in the future, she was highly expecting to hear some mediocre course. saidai tun ya ce musu medicine mbbs yake karantawa a jamiar Ado Bayero sai taji ranta ya baçi wann karon batama iya boye tsanar da take masa a fili ba..,

cikin furucinta na rainin wayo sai nuna mai take kamar bai kai ya karanta wann course din ba. sai tambayar ya uwaka tay ta haifeka take masa akan karatun. tanamai nuna masa karara cewa medicine yafi karfin brain insa like he cant just afford to be a doctor. tafara masa suggesting su hospitality managmnt, zoology, french, islamic, political science, library science, history, hausa e.t.c..shide ibaad bai iya raina babba amma tunda ya gane salonta na rainin wayone sai ya zamana da daddaya yake bata amsa me kaifi da nauyi wanda yasan hakan yana mata ciwo aranta sosai. duk courses din data kirasu mediocre saida ya gaya mata relevance insu a real life. ta dage masa wai saidai yabar medicine ya karanta wani course dede dashi. shima ya dage da ce mata aiwann dinne ma kawai dede dashi.

duk wadatar da bappa zaidu yake dashi na kudi da rufin asiri still zaginsa takeyi tana cewa wai aibazai iya ilimantar da yaransa snn yazo yq ilimantar da ibaad dake maraya ba. yanayin datake sakayawa tay zagin hakanan shima ibaad yake sakayawa ya cakka mata amsa tare da mata tambayar ko ta taɓajin bappa zaidun yazo gabanta ya durkusa yana nemam taimakone akan harkan iliminsu

it was so clear dat jinin hajy hamida sam bai hadu dana ibaad ba.

ganin hirar tasu is bcming a bit awkward yasaka prof ya fara kawo batun karatun zainab arifah, ryt in d midst of their heated conversation yafara yaɓa ilimin yarsa yana nuna cewa itama yar baiwace, kuma business kawai zata karanta infact sai takai matsayin higher doctorate, yace yarsa bata bukatar dagewa sabida ilimin gidansu ta gada, amma shi fa ibaad din nuna masa sukeyi baida wann gadon ilminin dolensa sai yadage. duk dai yabi ya rasa menene takamamen abunda yasaka mutanen nan suka kirawoshi gidan su dan banda baqar magana da cin fuska baiga abunda yake karba a hannunsu ba.

har saida suka gama kammala cin abincin snn prof ya fito fili ya fara masa magana akan alakar sa da zainab arifah cikin sakayawa, sai yake nuna masa tunda yafi aminta dashi yana buktarsa da yadinga sake fuska wa yarsa zainab arifah dan tadada sanin danginta with his supervision. wasu kalamai, da karairaye da cin fuskar daya gaggaya ma ibaad akan familynsu ma hankli bazai dauke ba, its obvious gani yakeyi kamar kowa ne yake masa baqin ciki akan daukakar da Allah ya basa kuma kudinsa akeso ba shi ba.

ibaad yay shiruuu harsaida prof ya gama kushe kowa adangi ya koshi snn yabashi baki....

nan ne kuma hajiy hamida ta fara kawo nata surutun cikin irin hikimarnan na mata dan ita haryau bata yafe dukan dayay ma yarta ba, kai tsaye ta fara kawo masa batun dukan dayay ma zainab Arifah kai tsaye tafara cak cakka masa magana wai "sun yafe masa ne sabida sungane ba lefinsa bane lefin uwarsane data tarbiyantar da namiji kamrsa me dukan mata tun yanada danyen shekaru.

wann maganan sosai yamasa zafi aransa musmn yadda prof ma kansa yake cewa ai ammi karama a danyen shekaru aka aurota bata da wayo hala ma mahaifin ibaad dayake raye dukanta yakeyi agaban ibaad shiyasa itama bata san yadda zatay ta tarbiyantar da danta namiji ya dawo ɗa na gari ba.

ganin ibaad yadena cin abinci yay shiru baice musu komi ba, jikinsu yafara basu hala ransa ya baci ne,

sai kawai suka wanye cikin hira suka ce ma zainab arifahn wai ta bashi hakuri agaban su dansu tabbata cewa komi ya wuce tsakaninsu. dakyar zainab din ta amince tacemai yay hakuri wanda dashi da babu kusan duk dayane dan abune anayi ana masa iyeyi, gashi tsabar iya manyance da shagwaba irintata wani bin intana magana ma basajin metake cewa.

ibaad sosai yagama gane yanayninsu, mutane ne marasa mutunci, ya lura so kawai suke sukulla wata friendly alaka tsakaninsa da yarsu zainab arifah amma bawai dan son ransu suka nemeshi ba. they want him to blindly tolerate zainab arifahs spoilt brat behaviour, ace kome tace masa kar yay mata tsawa, fada, bare duka, he can clearly read what is behind their selfish fabricated gestures and intensed fake smiles amma dake shi yarone duk sai ya danne abun aransa ya biye musu har suka gama surutansu bai musu rashin kunya ba duk da zagin uwarsa da sukayi wanda duk shi yafi masa ciwo aransa sosai.

bayan kamar awa guda da zuwansa yace musu zai tafi gida..wani irin murna sukaji dayace hakan acikin ransu, amma a fili har wani ɓata rai prof yay yahaushi da masifa "haba haba kai kuma sai kace wanda ake korarka...cike da makirci hajy hamida tafara fada" hmm alhaj ainni gani nayi kamar be wani sake jikinsa da mu ba, he barely eats kuma nace amasa packging din abincin nan yace min a'a, karshensa sai dai azubar kenan kasan dai mu bama cin irin wann local abincin, yo ko maganan kirki fa basu zayna sunyi da yar uwansa ba gashi yanace mana wai zai tafi..

atake zainab arifa tafara hararar mum dintan dan duk wani surutun cin fuska da suka masa yasa ita bata wani ji dadin haka ba. yadda take mutuwar son ibaad ko kadan batason taga ransa ya baci.

cikin katse mitar mum inta da muryan shagwaba tace mummy pls nidai kidena masa fada kibarshi ya tafi hala dai ya dan gaji ne kmr fa daga schll fa ya taho he need to go and rest.

ammkance hajya hamidan tace nd who told u daga schl ya fito da duk wann uban kwalliyar ke kuma yar azarbabi...

ckin rolling idanu ahnkli tace kai mummy haka fa shi yake dressing, nd i have my ways mum

kinsan elder bro na kawata nala kin tunashi? ayatsine hjy hamidan tace eh, tace toh ai ajinsu daya da ibaad so dazu muna chat da nalan ita tacemin a schl suka wuni yau so pls just let him go..okay?

murmushin yake kawai prof yay ganin yadda zainab din take ta kkrin kare ibaad wajen mahaifyarta

shide ibaad baice musu komi ba yama juya kansa gefe kmr baya wajen,can prof yadan kallesa yace toh bakomi sai Ka maida hankali sosai, shi zumunci da karatu kusan shi ne abin da mahaifinka ya fi so arayuwarsa, saika dage snn idan kasamu lokaci ka dinga zuwa kana taimakawa yar uwarka zainab arifah da karatu agidan nan, i know my princess is smart amma ai tana buƙatar kwarin guiwar daga yan uwanta.

babu yabo babu fallasa ibaad yace toh bakomi kawu. ni zan wuce. Nagode sosai da kulawarka. hajya hamida ta ɓata rai ganin har zai juya baice mata uffan ba..

prof ya ma zainab Arifah ido akan tabishi waje, duk dai burinsa baifi yasa zainab taji cewa yana tare da ita akan ibaad ba, dan hakan ne kawai zaisa tay tunanin zata same soyayyarsa harma ta cire damuwar soyayyn aranta ta warke snn tamaida hankli wajen karatunta sosai.

tunda taga babanta ya bata go ahead da rawar jiki ta kama bin ibaad abaya wanda tun basu gama ficewa a hallway din ba suka fara jiyo muryan hajy hamida datake fmr mita da masifa "alhaj kaga rainin yaran nan ko? waima "hajiya" fa yake cemin kamr ni bankai na haifesa ba nide next time yazo gidana nd he stands to greet me wallhi zanci masa mutunci inhaka yake gaida uwarsa atsaye agida toyasani nide nafi karfin yaro kmrsa ya gaida ni a tsaye masifa take ta inda take shiga bata nan take fita ba..

ibaad kuwa tunda ya saka kansa bai kara juyowa ba barema surutunsu ya damesa dan already ransa ya baci sosai. har me aiki tabude musu kofa duhu duhu yake gani bai daga ido ya kara kallon kowa ba, yana ficewa harabar waje zainab Arifa ta karaso da sauri harta jikin motarsa tana haki da wani irin rangwada tace hey ..ibaad, please wait..

Miskillalliyar Ajiyar zuciya ya saki snn ya juyo adan takaice Suna hade ido ta dan sakar masa murmushi maisanyi, sai snn ta tuna zcyarsa a kusa yake baison magana musmn ma na raini so da wurwuri tace mai "salam alaikum, Hi .

kallo ɗaya yamata ya amsa sallamartan a dakile tare da dauke kansa yanamai kawar da idanunsa can gefe.

"i just want to say thank you for coming..

kallonta kawai yay baice komi, da sauri tace "toh ya su anty safeera agida? tun be amsa ba tace ohhh just forget them.. uhm u know, i have been hospitalized. jiya da darema aka dawo dani gida bakaga na canza ba.. i have this..

ganin zata cikasa da surutu banza cikin datsar numfashinta yace toh its okay, saiki koma kije ki huta Allah ya kara sauki..

sounding childish and desperate ta rolling masa ido tace okay, "thank you, thank you soo much for seeing me,wont u like to knw daf ciwon damuwa ne kawao likitta yace yake damuna, nd i have...

ibaad ya mata wani irin dakakken kallo kmr na wanda ake sakashi tsyuwar dole yace ciwon damuwa kusan kowa na fama dashi nd am sure u u ave a therapist by now so why are u telling me?..

ɗan shiru tayi tanata kallonsa kafin can tace mishi umm notin, kawai so nake kasani, kasan ba kowa bane yake iya mantawa da wani abun dake yawo acikin ransa.

kai tsaye cikin datsar numfashinta yace 'toh ke Ki koya mana, Zai taimaka miki fiye da tunaninki. dede nan yabuɗe ƙofar motarsa agajiye takasa cewa komi tanata kallonsa har yashiga motar ya zauna snn takuma cewa thanks for ur time ibaad, it means alot..

..da emotionles face nasa ya dubeta yace "Allah ya kara sauki

..daga haka ya daga glass dinsa ya kunna motar cikin kankanin lokaci ya doshi gate aka bude mai yafita.

zainab arifa ta jima a tsaye anan kafin can ta koma ciki tana jin wani irin sanyi a ranta dan baitaɓa tsayawa tayi magana me tsayi da shi kamar nayau ba, da wani dan uban murna ta koma gida ta rungume babanta tana masa godiya

fannin ibaad kuwa tun be bar titin anguwar ba abubuwan da yafaru agidan ya dinga dawo masa akai sai yanaji kamar zucyarsa na mugun tafarfasa waima ahakama bappa zaidu ya bashi key dib babban mota da kudin sayan sabbin kaya kenan da baisan wani irin mugun cin fuska za'a masa ba, can dai wayarsa yafara ruri ganin sunan maheer ne akan screen babu bata lkci ya jawo ya dauka ya duba sakon dake kai daga nan bai bata lkci ba yakara ma motar wuta tareda shan kwana yanufi anguwan abokinsu abdl gaffar, anan ya samesu dede sunfito gate suna tsaye suna jiransa, sama sama suka gaisa tsakaninsu maheer yabude motar ya shiga suka kama hanyar gida..

tunda suka hau titi ibaad wasnt looking fine at all kawai tuki yakeyi duk kalaman cin fuskar da akama uwarsa tafi masa zafi, wani irin nadama yakeji aransa dan daya san dukan zainab arifah dayay ranar zai iya jawowa har azagi mahaifyarsa comfortbly agabansa ba dabai fara ba

maheer nata shan mamaki ganin yay shiru baice masa uffan akan zuwansa gidan kawu babba ba har suka isa gida kuma baice masa uffan ba.

yana gama parking ya bawa maheer din keys na motar snn yakai kayansa daki baijima ba ya fito agurguje sukayi alwala awaje atare, as usual shiyaja su sallan magrib da ishai a masallincsu na kofar gida, har yanxu kuma baice ma kowa komi akan ziyarar da yakai gidan prof ba suma kuma basu tambyesa ba sabida yanayin fuskarsa.

bayan sun idar da sallanne yaje ya gaya ma bappa zaidu akan zasuje can family house shida maheer wajen maman sa dan tun safe tace tana son ganinsa.. kai kawai bappa zaidu ya gyada musu, kowa jikinsa na bashi wani abu, har suka kama hanya suna hirar ball sama sama har suka kai kwanan anguwar rijiyn zaki maheer baiwani gane kansa ba...

#surayyahms

idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻

AREWABOOKS

@SURAYYAHMS

WATTAPAD @SURAYYAHMS

WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED

#SURAYYAHMS

#COMEBACK SERIES

2024/2025