12
by @surayyahms
Susum writer:
ABUNDA KE ƁOYE....
Love And scandal💕
Arewabooks@surayyahms
1️⃣2️⃣
tafiya me dan nisa juma yay kafin ya samu ya shigo cikin asalin kauyensu ta majiya, lokcin daf ana neman wajejen karfe goma na safiya kai tsaye gidan da ake saida yar tsame da dan wake ya wuce batare da ɓata lkci ba yabiya aka masa hadin dafa duka na wake da danwake ga kuma yar tsamensa da zazzafar kokonsa agefe yana turiri..
saidai tunda ya zauna akan teburin gabaki daya saiyaji ya kasa taɓa abincin, lura da dabi'un kananan yan matan dake taya aikin saida abincin kawai yaketayi musmn yadda yagansu yara kanana suna magana da maza anyhow babu alamar kunya da kamun kai atattare dasu da kuma yadda suke muamala da duk wanda yazo siyan abinci. har cikin ransa kallon marasa tarbiya dama yake musu, suna giftwa agabansa gaba daya sai yaji hanklinsa na tashi , zantukan dandanko ne suka soma dawowa masa kai batun rayuwar yaransa ayanah da inayah, dan shide yasan acan tudu baisaka musu wani mutum yanamai bincike akan rayuwar taawure da yaransan acan ba sabida gani yay agidan hajy mairo me tuwo suke kuma hajiya ai matsayin goggonta ne sai baikawo wani zargi ko matsala da zai afku da tarbiyansu acan ba, saidai tunda yaji har dandanko ya fara kawo tsegumin ko hala wnn irin rayuwar banzan sukeyi acan saiyafara ji aransa kmr fa biri ne yay kama da mutum da irin ciwon ciki da amai da inayah take dayaki warkewa sam.
gidan hajy mairo gidan jama'a ne kuma yasan dolene hala yaransa suma suna hulɗa da mutane acan sosai, kasa hadiye kunun da ya kurba yay ya zauna shiru cikin tunani, cikin ransa yace toh wayasan ko dagaske ne innari takwaso masa abun kunyane suke raina masa hankali duk atake saiyaji yarasa meke masa dadi.
cin abincin yake tmkr na dole yana Allah Allah ya fita kawai ya fara bincike, can sai ya tuna cewa da akwai wasu fulaninsu nan nan majiya masu saida dabbobinsu acan tudu toh hala zasu iya gaya masa wani abu game da rayuwar yaransa.
bayan kamr minti 20 ya gama cin abincin tare da gudanar da duk wata lissafinsa,ya taso kenan zai fita sai ya lura kame yanayin garin ya fara sauyawa kamar ma haddari ne keson tasowa, hakan yasa bai wani bata lkci ba ya biya masu abinci kudinsu cifff snn ya nufi cikin anguwa agaggauce domin neman masu basa shaidoji
ata fannin taawure kuwa matsanancin damuwa da tausayin yarta inayah sosai ya fara hanata sukuni, dan banda kuka, addua, da wayyo wayyo cikina babu abunda inayahn take kanyi gwanin ban tausayi, ganin halin da inaya take ciki wanda tamkar magungunan data bata gabaki daya basuy aiki ba yasaka taawure tay shahada aranta tayanke wani babban hukunci na zaɓar ran yarta akan aurenta da juma..
wann ba tunanin me sauki bane, bakomi hukunci me dadi bane har a idon Allah
amma tasan in har batakai inaya tudu inda akwai likita sun same taimako ba hala yarta inayah zata mutu anan da ciwo kuma awahale, at same time cikin zuciyarta tasani inhar ta fice agidan taje tudu toh saki uku tabbas ya shiga tsakaninta da juma kenan rabuwa ta har abada..
duk sai ta rasa abunda ke mata dadi but the more ta kalli yanayin inayah sai taji rauni me tsanani ya kara rufeta
cikin wnn zullumin she waited for a while cikin da nisan tunani, can dai dataga garin ya fara hada hadari jikinta amatukar sanyaye ta miƙe tsaye tabi ta shiga dakinta, kallo daya tay ma dakin ta tuna ranar da aka kawota ciki tun aurensu na danye tana amarya, lokcin mijinta juma na sonta sosai, kai bazaka taɓa tsammanin cewa wani abu na tsana da cin mutunci zai shigo cikin rayuwar aurensu ba. wasu abubuwan inta tuna takejin gwiwarta yay sanyi, cikin rauni ta tsuguna adan wata kusurwa hawaye na zubo mata da tsananin karsashin zafin rusa aurenta da zatay ynxu aranta tayi kuka tay kuka sosai tagode ma Allahnta
dakyar ta iya bushar da zuciyarta tamiƙe tahau tattara duk wani savings inta na kudi da few kayanta na sawa ta sakasu a yar jaka saura ta daure su da tsumma,. tana gamawa ta fito da kominta a jakan snn ta daga ayaanah tadora mata jakan akai tace mata taje maza ta sako takalminta a daki ynxun nan snn ta fito su tafi,
ayaanah bata fahimci komi ba ta shiga dakin sun da kayan akanta tanamai lura da yanayin rauni da taurin rai dake kwance akan fuskar mahaifiynta wanda sosai ya bata tsoro da kuma fargaba. ta shiga ciki bada jimawa tazo ta samu tawuree har ta lallaba ta saɓa inayah abayanta ta daureta da zani kamr ba yar 12yrs ba, nishi me tsanani kawai inayahn takeyi batama hayyacinta banda ma dauriya irinna yaran buzaye da fulanin jeji da bazakace a age intan nan har zata iya daurema azaban zafin ciwon ciki datakeji ajikinta ba.
kafin kace wani abu taawure ta umarce ayaanah akan ta wuce gaba. kai tsaye suka fice agidan suka dau hanyar tudu, dan tsabar wahalan dataji inayahn takesha sai taji ko nauyinta bataji tafiya kawai take da sauri sauri kuma ƙarfin zuciya dukansu ukun suna ambaton Allah yanayinsu cikin rauni har suka isa garin tudu acikin kankanin lokci sai gasu kofar gidan hajy mairo mei tuwo..
lokacin kusan daf ake da karfe sha biyun rana amma dake hadari ya dan rufa sai wajen yay duhu da sanyi, suna isa taawure tay maza ta sauke inayah akan dakalin tsakar gidan dan izuwa ynxu inayahn tama dena yin motsi sai shure shure fuskarta yay fayau yay fari sosai, dan tsaban azaban datakeji acikinta wani dan uban nishi kawai takeyi idanunta sunyi farare soll sun jujjuya tay lagwas kmr lokcin mutuwarta take jira
ayanah tana aje kaya dake kanta tun taawure bata furta mata komi ba tay marmaza ta falfala da gudu ta fice kasuwa domin kira musu hajiya mairo me tuwo, daga nan kuma ko minti biyar da zama a dakalin basuyi ba inaya tafara jin wani irin sanyi sai kawai tafara ririike jikin taawuren tana shigewa jikinta sosai kamar wata mai ciwon nakuda tana nishi ahnkli kuma me nauyin gaske inda yake ciwo acikinta sosai yay tozo agefen dama ya kumbura
acikin matsanancin rauni baƙinta dake bari yahau cewa umma am, umma...ina ganin kamar mutuwa xanyi umma
atake idon taawure ya cika da hawaye tana juyowa idonsu ya sarkafe cikin na juna, ahnkli cikin nishi inayah me sauka tare da wani irin makodan hawaye tace "umma dan girman Allah kiy hkri ki yafemin musmn ma da aurenki da baba ya mutu yau a sanadiyata..umma dan Allah ki yafemin.. umma ki yafe min dan Allah karna mutu da wann shaidar akaina,.. kusan maganartan dakyar yake fita cikin nishi amma kuka take yi sosai taawure dake hawaye bata iya cewa komi ba ta rungumota ajikinta sai a sann ta itama fashe da kuka mai rauni itama inayahn sai ta kara fashewa da kuka sosai, ahnkl cikin lallami taawure tahau shafa mata baya tanacewa" yi ishiru abunki innari, ni bakimin lefin komi ba, ai danabarki ki mutu acan majiya gara auren nawa kawai ya kare..kinga shi mutuwar aure qaddara ne zanyi hakuri dashi, amma idan na barki kika mutu banyi komi akai ba hakan zai zama mini babban ciwo a rayuwata da zuciyata har na mutu baza yafema kaina ba.
kara kankameta inayah tay tanata bata haquri dukansu suka taru sunata kuka sosai...
sunjima ahaka sai can kafin taawure ta share hawayenta tafara ma inayahn nasiha masu ratsa jiki akan tay hqri da ciwon nan jarabawa ce kawai da Allah ya aiko musu.
ayayinda ayaanah taje har kasuwa tana haqi, koda ta shiga shagon hajiya taci neman duniyan nan ma hajy mairon a shagonta amma bata sameta ba, hanklinta ya dada tashi, gata yar yarinya badon ma tanada rare beauty ba da babu wanda zai kula metake cewa, da kyar dai ta samu wata yarinya yar karama kusan age mate din addanta inayah anace mata Ruthy, kallo daya zaka mata kasan chirista ce sabida yanayin shigarta da kuma gashin doki dake kanta, she is like 12yrs old amma tana da girman jiki, ankawo ta shagon ne a matsayin sabuwar mai aikinsu wanda hjy mai tuwo ne taje ta daukota cikin satin nan agidan wata magajiyar karuwai dan kusan sau biyu kenan ana case nakkrin abusing in ruth sexually at dis very young age of 12yrs, sabida angane batada iyaye tsintar ta akayi a kwali anjefarta a kwalbeti, irin yaran nan da karuwai keyin cikinsu su haifa su zubar dasu a kwali..
hajy mairo tunda taji labarin ruth hakanan tay ruwa tay tsaki har saida ta kwato wann yarinyar daga shiga ukubar karuwanci a danyen shekaru a gidan magajiyan ta bata aikin shara da aika a shagonta dan kar acigaba da lalata mata rayuwa.
ruth din ne tazo tafara kula ayaanah sukayi magana harta gaya mata cewa ai hjy nacan police station suna case da mai anguwa yauma wata sabuwar case ne tsakaninta da wasu kidnappers aka bude
,..abunka da yarinta damuwar aayana kawai naga jikin addarta ne, haka ta sako ruth din agaba da magiya har sanda ta mata jagora takaita police station da kyar ma aka barsu suka shiga snn taga hjy mairo wanda suna hade ido rauni ya rufeta tafara panicking tana hawaye tana gaggaya mata cewa har sunzo da ita da mamanta da addanta jikin addanta yaki yay sauki.
ba agama rufe case da su mai anguwan tudu ba hajy tay maza maza taje ciki ta rokesu aka bata daman zuwa da dawowa aka bata 2hrs sabida case din nata da yan kidnappers kusnn babba ne so kawai ake a cimma wata matsaya yau basai ankai gobe ba.
ana basu 2hrs din nan hajya mairo tariko hannun ruth da ayanah wujiga wujiga suka kamo hanyar gida a abun hawa, tun daga zaure ta doka sallama suka samesu a manne da juna taawure ta tungume inayan ajikinta inayah tay lumui ta lumshe idanunta sosai ,
hjy nazuwa tadora idanunta akan yanayin inayah ganin yadda ta dawo wani iri kmr me kanjamau yasa ta fashe da kuka cikin kankanin lkci tafara raki tana salati tana sallamewa tana tambayar taawure meya faru cikin tashin hankli, tun ba amata bayani ba tasaka marmaza aka tada kura aka dauki inayahn abaya kamar yar tsana suka fito wqje wujiga wujiga aka sata abun hawa dukansu su hudun suka wuce da ita dan karamin Primary health care facility dake cikin tudun agaggauce.
suna isa cikin asibitin kuwa ruwa ya fara sauƙa kmr da bakin kwarya, da Allah ma yaso su yau akwai likitan dayazo daga cikin kano, duk dama sauri yake shima zai karkare aikinsa zuwa gobe juma'a zai koma cikin garin kano yanayin jikin inaya dayagani yasaka ya tsaya dan ya taimekesu
gurgura inayan akay a gado mai taya aka kaita har wani daki aka fara saka mata ruwa snn aka ja jininta aka fara mata yan gwaje gwaje ayayinda taawure da hjya mairo da ayaana da ruth suke tsaye likita yana musu tambayoyi,
ayaana ce tafi bada amsarsu sabida kusn komi na alaman ciwon addantan a idanunta ya fara..
bayan likita ya dau duk wani rahotonsu ya tafi dashi ciki nan hajya mairo tafara mita da masifa wa taawure kamar Allah ne ya aikota, akan meyasa tuntuni taawure bata dawo tudu sun nemi waraka ma inayah ba,
saidai koda taji taawure tahau furta mata labarin danbanzan duka da kuma tsauraran kalmomin da juma ya furta akanta tare da jarumtar datay yau na kashe aurenta danta ceto rayuwar inaya sai gabaki daya jikin hajya mairon yay mugun sanyi, atake kuma sao ta koma lallashinta tana bata hakuri.
lokcin ruwa akeyi amma ba sosai ba tunda sukaga likita yanata aiki baice musu komi sai suka dan samu sukuni aransu, har hjy mairo take basu labarin case inta da wasu mutane da aka samu rahoton cewa yan kidnappers ne kuma sunce zasu saceta, shine fa aketa case da ita har da mai anguwa akan zasu kafa vigilante group a kusa da kofar shagonta snn za'a basu daman rike bindiga sabida tsaro..
jin abun babba ne yasaka tawuree tace mata tunda jikin inayan ma da alaman sauki kawai takoma station agama case din in yaso in tagama ta dawo, da kyar dai hajy mairo ta amince da haka, koda zata tafi ita dayanta taje har ta dakin da aka kwantar da inayahn ta sameta wanda suna hade ido hawaye ya cika idonta tazo tadan rungumeta tayita mata adduoin samun sauki masu yawa tasaka mata albarka sosai.
itadai inaya sai cewa take ayafeta takuma gode tagode da irin kulawar da suka bata sai kuma tay murmushi me cike da hawaye me rauni.
ahaka dai da wann kalman har suka rabu da hajy maituwo dukansu suna zubar da hawaye ma juna at same time suna murmushi ma juna. hjy tana ficewa a asibitin tabi ta aje ruth a shago snn ta koma station agurguje da gunjin tausayin inayahn a zuciyarta
bayan tafiyar hajy maituwo ba da jimawa taawure tay zamanta a reception daga ita sai ayanah, sallahn azhar ne kadai ya dagasu lokcin kuma already ruwan saman yadan lafa sosai saidai wani sabuwar haddarin ne yake kan sake tasowa gashi har yanxu likita baice musu komi ba.
Dagata dayan bangaren at around 3:40pm na yamma ibaad ya bar school of medicine ya dawo gida agaggauce dan kansa har wani irin ciwo yake masa tsabar practical activities da yay a club dinsun yau.
tun 11am na safe ya gama normal school lectures, frm 12-3.30pm dinnan duk acikin club practical lab dinsu ya kareshi sun dukufa sunata practical kala kala akan major field dinsa na cardiology at an introductory level.
yana isa gida kai tsaye yahaura sama dama kuma dakinsa is always neat, wankansa kawai yay sharply yasan dake maheer bai dawo ba so baida wanda zai iya bata mai lkci, within few minute ya fito ya kintsa kansa anitse yasaka kananan kaya ajikin sa farin rigan raymond T shirt original cotton me dogon hannu da bakin wando suade da wata sleek sneakers yabi ya saka wata original black baseball face cap data masa mugun mahaukacin kyau kagansa kamar balabe except that he had this glowing yellowish body tone. shigarsa simple yet classy nd smart, bakaramin kyau yayi ba musmn da ya toshe idanunsa da fararen rayban spec da shirin zuwa anguwar tudu agaggauce dan yana so ya samu yajeshi ayau din nan dan komin dare yay makansa alkwari yaudin zai dawo gida dan yanada abubuwan yi a lab dinsun gobe sosai.
bayan ya gama shirinsa tsaf ya fetsa turarensa original dior souvage me sanyi snn ya fito ya dau jakar bayansa da wayansa yana tafiya anitse har ya same ammi babba a falo tana kallon indian wani series..
qamshin turarensa me aji ya saka ta tafara daga ido ta kalleshi itade duk ta kallesa kyaun fuskar uwarsa take gani dan haka takejin ta tsanesa kamar mutuwarta.
kallon tsana take masa har ya karaso ciki ya dan rusuna ya gaisheta ta amsashi ciki, snn ya sanar da ita inda zaije nanma tay kamar batajishi ba, after few scnds of silence dan kansa yagaji da attitude inta yamiƙe shiru ya fice agidan yanaji tana binshi da tsaki tare da cewa Allah yasaka mutuwarka ce ta kiraka a tudun mayen yaro kawai Allah yasa gawanka ne zai dawo bakaiba.
..koda ya dauki mota ya fice haka maganan nan nata yarinka masa yawo akai cikin wata karamar toyota jeep da bappa zaidu ya bar masa zaiy tafiyar dashi, yana tukin ahnkli ya kira bappan zaidun awaya suka fara magana ya sanar da shi cewa ynxu zai wuce tudu wajen hajy mai tuwo, hira sukeyi har ya isa cikin anguwar rijiyar zaki inda family house dinsu yake dan ya amsho wasu sakonin da za'a kaiwa hjy mai tuwo daga wajen mahaifiyarsa ammi karama, kusan kaf gidan babu karya ammi karaman tafi samun karbuwa awajen uwar mijinta, dake ita tasan wani abu waishi nitsuwa, dattako, gata da biyayya da sanyin hali, tunda taji uncle moh yasanar da cewa ibaad kawai zasu tura wajen hajiya ayau din taje kasuwa tasiyo dukkan wasu abubuwan masu kyau datasan hajy mairon tana mugun so snn ta dafa mata abinci me rai da lafiya tay packaging insa a close basket dan yawuce mata dashi.
ganin hakan datakey na kyautatawa yasaka sumtimes har anty safeeran ma take gani tana daukar darasi, dan anty safeera is a calm young nd wise lady, a shekaru dai bazata wuce 35-36yrs ba duk dama babanta yana da kudi itama tana gama secndry din ta aure uncle mohd har suka samu first son insu mujaheed dayake sa'a da zainab arifah, sai yar autarta kulthum bayan nan ne ta koma karatu, she is curently studying msc micro biology amma a private university., duk duniya babu abunda take mutuwar kauna kamar mijinta uncle moh, shi mutum ne meison jin dadin rayuwa, he is all about this flashy rich guy life, kominsa is loud, tun daga way of life insa me aji, har sutura, kominsa me tsada kawai yake sawa, he is the finest nd the youngest engineer of the almansur's elders, ryt in his early 40s, shi farine sosai dogo mijin novel, mai cute red lips da kwantaccen saje, gashi da saurin fara'a, mutane suna yawan cewa dansa mujaheed yagado farin fatarsa ne sosai.
anty safeera can do anything to please him, wani irin soyayya na amana take masa, ganin ibaad agidan yasa sai itama tajeta sashenta tadan tarkato turaruka masu kyau da tsada ta bashi danta burge mijinta, agabansa tace asaka ma hjyn kayan nata tsarabar aciki.
lafiya lafiya ibaad yay musu sallama, uncle moh ya rakosa har gaban motar jeep in yanamai dada jadadda masa cewa in har ruwan sama ya tsaresa a tudu karyace zai dawo sabida akwai fatake masu kidnaping da barayi kawai yayi haquri ya kwana agidan hajy mairo inyaso gobe da sassafe sai ya dawo
sude babban burinsu shine ibaad ya samu yaje tudun ya gano musu asalin menene ke faruwa da mahaifyar sun acan, snn ya lallaba musu ita taji aranta cewa zata iya barin wajen ta dawo cikin kano ta zauna tare da su a gida.
gabaki daya tabi tahana yayan cikinta binta can tudu sukuma anan cikin kano hanklinsu sam baya kwanciya, sai tace sam za'a sace matasu in sukazo, saidai kawai ayi waya tsakanin ta da bappa zaidu da uncle moh akai akai, dake suna yawan tura mata kudi kowani wata ko cikin sati, prof zayyanu kam dama tun tuni ya dena nemanta kuma bata wani damu da baqin halin sa ba dan abune data saba dashi tun bai kai ma haka ba, ko surukanyenta da jikokinta ma knsu bata fiye kiransu ba sabida tsaro.
at around past 5 ibaad ya kammala duk wata maganansa da uncle mohd snn ya shiga jeep din yakama hanyar anguwar tudu dake wata bangare ne me nisan gaske acikin kano wajen tafiyar awa uku ne da rabi sabida hanyar shiga garin babu kyau ko kadan
tun kafin ibaad ya dauko hanya, ata can bangaren juma kamr dai kullum, zuwansa wajen fulani jin labarin rayuwar da taawure takey a tudu bai kare masa ta dadi ba.
dan kuwa daga isarsa majalisan dattijai ya tarar da su kaca kaca anata raha, toh yay dasu aje gefe suyi magana amma sukaki suka bige da tsokanansa kamar yadda suka saba kullum. dakyar da wahala suka dan sauraresa suka koma gefen kai tsaye ya fara musu tambyar dake tafe dashi, dayan bafulatanin ana cemai sajo shi yafara ce masa ai wnn tsohon zance ne, yaran sa kam dama cikakkun yan barikine dan sun mugun shahara a anguwar tudu msmn ma inayah itace ma ake cewa gwarzuwar tudu.
hanklin juma sosai ya tashi da jin wann furuci, saida suka ganema cewa bada saninsa yaran suke karatu ba aikuwa su suka hau fede mai biri har wutsiya na batun karatun da su inayah da ayaana sukey, komi da komi saida aka gayama juma abaibai wanda tun bai bar wajen ba mazan dake wajen aka fara yaɗa labari nacewa juma cikakken lusari ne baida gindin haifan yaya maza gashinan ashema matarsa taawure tafi krfinsa akan harkan gidansa da yaransa taje tudu ta saka yaransa a makarantar kafuraye batare da izininsa.
ranar kamar kan juma zai fashe da feshin wuta haka ya kamo hanyar gidansa da gudu idanunsa sunyi jajizir ruwan saman nan da aka fara sabo kaf akansa ya kare...
yana dawowa gidan ya shiga turakarsa ya dau wata igiya ya cusa a wandonsa snn ya dau wata addansa mai kaifi akan yau xaima tawure dukan mutuwa snn ya sare kafafunta dashi..
hakanan yaci nemansu agidan har wajajen daya saura na rana bai samesu ba kuma kwata kwata bai kawo aransa cewa har taawure zatay tsaurin idon kashe aurensu akan ciwon inayah ba, adan dolensa yaje jejo ya nemo kasurkurmin magulmacin nan dandanko, sabida yasan duk tsiya abakinsa kawai zaiji labarin inda taawure takai masa yayansa,
haka ya bazama jejin kmr mahaukaci da kyar ya sameshi, dandanko dayaga juma wujiga wujiga sai yaki sam ya gayamai komi saida ya sha cikinsa yaji labarin asalin meke faruwa tukuna.
bayan yagama jin komi sann yahau kara masa wuta yana cewa aidazu ance masa anga matarsa taawure ta goyi innari sun wuce tudu da kayansu, snn yabi yace ma juma toh tabbas cikin shege ne inayah take dashi sukaje zubarwa a tudu awajen likitocin kafuraye, inba hakama ba, wani irin ciwo ne haka inayah takeyinsa da amai da rashin cin abinci da kuma ciwon ciki me tsanani..snn kuma ace duk saiwoin kauyensun nan ya kasa magancewa...
yace ma juma kawai dai cikin shege innari taje ta kwaso taawure take kokarin boyewa kawai yaje ya dau mataki sabida kar martabansa da kimansa ya kara zubewa a garin majiya.
hakanan ya kara pumpa zuciyar juma da zugi da kuma zargi harsaida yasaka ta karayin baqi qirin da mummunan fushi da kuma bacin rai, daga nan babu wani jira juma ya saɓi sandan sa da addarsa ya wuce garin tudu acikin yayyafi, ya iso around 2pm dede na rana lokcin jikin inayan yafara rikicewa
likita ya fito yana kkrin ceto ranta da taimako da ake bayarwa na emergncy sabida sun riga sun gano cewa chronic appendix ne yake damunta gashi bayan ya girma harma yafara ruɓewa acikintan dolene kawai amata tiyata aciresa agaggauce.
tun bayan sallahn azahr suke cikin wann tashin hankli anata kkrin stablizing din inayah kafin ace zaa nemo motar da zai kaisu cikin birnin kano dan amata tiyatar nan agagguce gashi lkcin ana wani irin kwaxa ruwan sama me yawa da kuma tsawa
duk da zafin ciwo wasiyar hakuri da neman yafiya kawai inayah take nema awajen taawure da ayanah dan ciwon ciki takeji mei tsananin ciwo da bazata iya fasalta azabansa ba,
anata rububin nan ashema kudin tiyatan nasu bai cika ba, gashi taawure bata da waya haka tafita tabar ayana ajikin inayah ruwa na dukanta duk abun hawa sundauke da kafa ta dinga tafiya cikin sauri tay hanyar police station neman hajy mairo dan tabata aron sauran kudin tiyatan agaggauce..
ficewarta a asibitin bada jimawa ba Allah yay ma mijinta juma isowa har cikin asibitn da taimakon wasu matasa dake yawan zama daf da kofar gidan hajya mai tuwo dake zaman saka ido dama suke sune suka dada tabbatar masa cewa tabbas taawure da yayanta suxo amma sunbi hjy mairo sunje asibiti tun da jimawa
ransa a matukar dagule ya farabibiyar kwatancen asibitin tun abakin matasan dayake tambaya yaji kusab kowa ana cewa inayah gwarzuwan tudu, shi duk ya dauka gwarzancintan nan a karuwanci ne da tsabar iya bin maza baisan gwarzuwan karatun qur'ani suke nufi ba.
zcyarsa baki kirin ya diro cikin asibiti, daf lokci ciwon cikin nata ya tsananta sai nasiha take ma ayaanah akan karda tay rauni koda ta mutu bata duniyan nan ta tabbata ta tashi tsaye tazama wata jajirtcciyar mace snn ta mata alkwarin zata cika ma mahaifyarssu taawure bban burinta naganin sunyi ilimi sun zama mutanen kwarai.
tsabar kukan da sukeyi rikeda hannun junansu in an intense emotional state basuma san sanda juma ya shigo kansu ba.
ji kawai sukayi ana huci daga bayan su ankuma zaro katon sanda kmr za'a je yaqi a mugun zuciye yana huci yadaga sandan sama zai bugashi akan nurses din dake tsaye duk suka saka ihu suka bar dakin aguje ganin sa gabjeje babu wacce tay gigin taresa. dayaga haka sai girman kansa ya kara hautsina yafara dirin masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba yabi ya haukata asibitin da zage zage
ayanah ta mugun tsorota, yadda kasan zucyarta zai fice daga kirjinta ya fice, amma haka ta cije ta ki sam tatashi ajikin inayahn tabi ta rungumeta tana kuka mai mugub karsashi wanda hakanne kawai yasaka bai kai musu dukan atare ba.
muryansa kamr zai tada asbitin yake kiran taawure kamr wani tabbabe yanamai zaginsu yanamai cewa inayahn karuwa tsinanniya kawai, yar bariki irin uwarta, yace wallh kinyi asara innari Ashe dama cikin shege kikayi kuke boyemin keda uwarki?? da yaren buzanci da fulatanci duk ya hada yana tsine mata dashi.
itade inayah kuka takey tana furta innalillah wa inna ilaihi rajiun....idonta a lumshe taki tace masa komi taki ta masa bayani bare ta bashi haquri..
..duk wani xafin xagi me tafe da amon muryansa dayake saukewa aknsu ji take kmr ranta yake zarewa dan zafi.
ayanah da tsabar tsoronsa ma bata iya masa magana ido da ido amma yau babu irin tsaurin ido da yaren da bata masa rantsuwa da bayani dashi ba.
tabi ta rungume inayah sosai tana kareta dagashi cikin kuka mai rauni, tanacewa baba ciwon appendix ne yake damun adda inayah ba cikin shege ba
hargagi yake ko ajikin sa kamar baijinta tanakan maganan ma ya ficokota ya tureta ya faffala mata maruka masu karfi, yaki sam yaji komi, shide yanaso ne ma yaga kawai ya gwada ma inayahn sandansa ya kashe ta,
dakyar likitan da wasu maza suka shigo suka samu suka rirrikesa snn aka kwace sandan daga hannunsa, ahakama sai zagin yaransan yakeyi kamar bashi ya haifesu, anfi minti ashirin ana wann hayaniyar da juma...
ayaanah ce ta fara jin daukewar numfashin inayah, ta mike da sauri jikinta na bari tayo kanta tun bata bude baki ba ahankli tajiyo kalmar shahadarta daya kufce mata abaki very faintly.,
akace wai duk inda malaikar mutuwa yazo sai iskan wajen yayi daban wani irin dimmm taji wajen ya dauke mata cakkkk, dan tunda tajiyo wnn numfashin ta na karshen taji kirjinta da jijiyon zuciyatta duka sun tsinke jikinta na wani irin rawa atake ta juyo sai kuma tazube aragwabe ajikin inayah tafara wani irin kuka mekara tana jijjigata tana kiran sunanta kamar tabbabiya..
da gudu likitan ya sake juma ya karaso wajen aka dudduba aka samu rai yay halinsa kowa yana furta innalillah aayana ta zube kasa tana kuka kamar ranta zai fita amma juma ko gizau baiji ba dan ya mugun tsanar asbiti da duk mutanen dake cikinta, anata batun yarsa ta rasu amma masifa yakeyi yana cewa sam cikin shege akazo zube mata tay mutuwar kafirci.
ran kowa saida ya baci a asibitin ko ajikinsa, shi mutuwar inayahn ma dadi ya masa gani yake data haifi shege agidan sa gara ta mutu, hakanan ya fizgo aayana waje, lkcin ana yayyafi sosai ya tsare adedeta ko ciniki baiyi ba ya cusata ciki yaciro igiyansa daga aljihunsa ya daure mata hannunta biyu da igiyan ajikin karfe ta cikin keke, snn ya koma ciki yanamai kara saukar musu da jakar balai yabi har kan gadon ya dauki gawan inayan akafadarsa, itama ya saka acikin keken, duka dashi da yaransa ya debosu agabansa suka kama hanyar garin majiya aganinsa sai ynxune ya cika namiji, snn zai nuna ma kowa tsananin jarumtarsa for once dai zaiyi abunda ya dace akan yaransa bisa tsarin al'adarsu ta kaka da kakanni dan martaban sa da kimarsa ya dawo.
lokacin ruwa aka farayi sabo kamar da bakin kwarya wanda shine yasaka har taawure bata samu abun hawan dawowa da cikaton kudin tiyatar data amso wajen haj mai tuwo akan lokaci ba
ko cikakken minti biyar juma baiyi da dauke yaransa ba ta iso asbitin wujiga wuijga kusab agigice jikinta yay jagwab da ruwa tazo musu da cikaton kudin tiyatar cass har tana haqi, tsabar tausayin data basu da kyar aka samu wata dattijuwar health worker data gaya mata cewa Allah yay ma inayahnta rasuwa snn gadai jahilci da haukar da ubansu yazo yay asibitin kuma ya tafi da duka yaransa gida ynxu
tunda aka fara mayar da maganan kusan kangare taawure ta suma daga tsaye har saida sukaga bata motsi snn aka bambamreta daga sudden shock din data shiga ciki aka samu itama bata ko motsi dan mummunn bugawa zuciyarta yay atake kuma ta suma aka bata gado ana kkrin reviving inta dan karta samu sudden heart attack due to shock.
tundaga hanya ayaanah take rabza kuka mai kara da karsashi, keken yana sauke su juma ya taso keyanta da haryanzu take rabza kuka kamar ranta zai fita wanda duk yawan ruwan nan da akeyi duk jejin saida ya dauka da karar kukanta, tanajin matsanancin tsoron abunda ke faruwa ga tsananin baqin cikin mutuwar addanta na dada gigita mata kwakwala tare da tsinka mata jijiyoyin zuciya..
sun iso gidansu babu takalmi akafara bare dankwali, haka juma ya turata akasa yabi ya kulleta adaki tareda gawan inayan snn ya fito waje ya wuce gari yakirawo mutane dan a masa shaidan binne yarsa da zaiyi bisa hukuncin al'adansu na kauyen, gashinan ruwa fa akeyi sama sama dake la'asr ya riga ya shigo ana neman kusan 4;45pm on dot amma hakannan magulmata da yan son ganin kwaf kwaf suka bazama yana bude kofar ya samu aayana tayita kuka harta sume tay karau ajikin gawar inayah dake dauke da fuskar murmushi.
wani irin shure aayanan yay gefe ta fadi akasa snn ya iyo ma maza biyu suka shigo, cikin masu fidda gawan inayahn dum mamaki ya rufesu ganin ynyin fuskarta da murmushi har suna tsammanin cewa ko ba mutuwa tay ba sabida wnnn hasken da fuskarta yay sosai kamar ba ita ba.
al'adace ya zamo basu yin jana iza wa wacce tay cikin shege agarin, dan haka juma ya sanar ya kuma nuna ma shaidunsa cewa yana Allah wadai da abunda ya faru da yarsa snn a shirye yake amata binnewar al'ada tunda cikin shege taje zubarwa.,
dakyar aka samu mata wanda suka mata wanka aka suturtata, ko kabari ba akaita ba kawai aka haƙa rami a bayan gidansan ta cikin jeji
normally bisa koyarwan addini ladubba ake bi ma saka gawa a rami ahnkli snn ta hannun dama amma koda sukazo saka inayah anata kabarin gungurata kawai sukayi sai suka shushhure mata kasa akanta har saida kabarin nata ya rufe......
(muna rokon Allah ya kare musulmi daga sharrin jahilcin wasunmu musulaman a duk inda suke, true life story, wata sabuwar makwafcyrmu christace baikai ko wata biyu haka ba data tataɓa furta min cewa ita babu abunda zai sakata taso musulunci ko tayishi harta mutu sabida musulmai mugaye ne, dalilinta nafarko shine babban yarta tabar christanci 2yrs back ta musulunta ta aure wani musulmi amma tunda ta shiga hannsa bakaramin tozarci da walaknci me tsanani takesha ba ga duka ga horon yunwa ga zagin cin mutunci, na biyu kuma awani kauyensu a jos tace mana da idonta tagan anyi ma wani mutum bawan Allah irin wannan walakntaccn binnewan da akay ma inayah, wai lefinsa shine shi tubabbe ne ba a musulnci aka haifesa ba, tace sanadiyar wann incident din mutane dayawa sunbar addinin. it was a sad reality in that remote villlage, it took alot of convincing kafin matar nan tazo ta fahimce mu harma tagane cewa ba haka musuluncin fa yake ba, snn zatama iya kaiwa kara kotun sharia dan akarbawa yarta yanci..kalubale garemu ne musulmai, addinimu bawai sai a fuska ko a baki bane. yakamata ace kyawawan halinka ko halinki shine zai fara bayyana kyawun addininki a duk inda ake, lets all make sure we set a good example of our religion no matter whom we are dealing with...bissalam)
a saurare sabon Update ranar monday in sha Allah
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
AREWABOOKS
@SURAYYAHMS
WATTPAD @SURAYYAHMS
WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025