GUDUN AURE

5

by @bintaumarabbale

Masu tsaron wurin ba su bari mun shiga kai tsaye ba sai da ta yi musu bayani ta fito da takardu ta nuna musu tukkuna suka bari muka shiga. Wurin ya yi sosai an kawata shi ga ko'ina a tsaftace ma'aikata na ta shawagi tare da tashin sautin injina. Sai dibi dibi take yi tana zare Ido. Na ce." To Sahura ina zamu nufa ne yanzu?" A rikice ta ce." Bari na kira Abban Anisa a waya." Na yi shiru ina kallonta ta d'auko wayarta ta kira shi bai daga ba har sau biyu. Jiki a sanyaye ta ce." Kin ga bai daga ba." Na ce.'' Na ji, wata'kila ko yana wani uzurin ne, kin ga yanzu lokacin shiga massalaci ne. Mu bari an jima kad'an sai ki sake kiransa." Muka je muka samu wani wuri muka zauna muna tattaunawa. Wani ma'aikaci da uniform ajikinsa irin na tsaro ya zo ya tsaya akanmu fuska a daure Ya ce.'' Me kuke yi anan?" Da sauri ta ce." Form din da aka ba ni na cike shine na kawo, ina neman Sulaiman sha'abu ja'in." Ya yi jim na minti biyu kafin ya ce." Ba anan yake dindin din ba. Amma yana iya zuwa da kowane lokaci. Ku tashi ku shiga cikin nan akwai wad'andasu a ciki irinku." Yadda ya fadi maganar cikin izgili shine ya bata mini rai. Na ce." Ranka ya dad'e. Ubangiji shi ya karrama dan'adam, ya kuma fifita shi akan kowace hallita. Kaga kuwa wani mahalu'ki bai isa ya 'kas'kantar dashi ba. Ba mu zo wurin nan a matsayin wulakantattu ba face neman dogaro da kai." Ya yi jim Yana kallona kafin ya furta." Kada ki yi mini rashin kunya ko kin ji na fa'di mummunar magana akanku ne?" Na ce." Ba ka fad'a ba Yallabai." Sahura ta ri'ke hannuna muka tashi. Ya ja tsaki tare da nuna mana inda za mu shiga da hannuna. Muka kama hanya muna tafiya raina duk a 'bace. Ba na son raini ko kad'an. Kuma dai d'abi'ata ce rashin yin shiru idan an ta'bo ni. Shiyasa wasu suke yi mini kallon mara kunya tunda gaskiya ba na iya bari, duk girmanka ka nemi ka takani na kan nuna ban yarda ba. Dalilin da ya sanya kenan matan gidanmu suka tsaneni tunda kuruciya. Ba wai Ina yi musu fitsara ba ne, kawai dai ba na yarda da son zuciya. Mun zo shiga manager wurin zai fito a gurguje muka gaisa da alama massalaci zai je. Ya ce mu shiga mu jira shi. Mata hud'u muka samu a zaune a kan kujera. Uku duk da 'kwarinsu. Dayar kuma dattijuwa ce sosai shekarun girma sun cimmata. Muka gaisa kafin mu nemi wuri mu zauna. Wurin tsaf da sanyin Ac ga tibi falasma nan k'atuwa a bango tana aiki. Wajejan biyu da rabi wani ma'aikaci ya shigo ya dube mu kafin ya ce." Ga Yallabai nan zai shigo." Bai jira wata magana ba ya fice da gaggawa. Dattijuwar nan fadi take 'Alhamdullahi' bakinta ya gaza rufuwa. Sahura ta kalleni itama da farinciki a tare da ita ta ce." Lallai mun shigo da kafar dama 'kawata." Shiru na yi ban ce komai ba kawai dai na zubawa hanya ido. Ina mamakin yadda gabad'ayansu suka rud'e. Mutum uku ne suka fara shigowa kafin shi din ya shigo da masu tsaronsa a baya. Hakan ya nuna akwai masu kula dashi a gaba da bayansa. 'Kamshin turaransa ya gauraye wurin. Farin bafulatani ne mai madaidaincin jiki da manyan idanu kamar dai yadda hotonsa yake a kalanda Yana da kyau da fuskar salihai. Yanayin jikinsa shi ya b'oye shekarunsa. Amma dai da shekarun tunda ga tsalli tsallin furfura nan a gashin da yake kewaye da matsakaicin bakinsa, yana sanye da farar shadda babbar riga da 'yar ciki, da jar dara tare da farin gilashi a idonsa. Cikin 'yan sakwanni na karance shi. Gabad'aya muka mike tsaye. Cikin nutsuwa ya tsaya yana amsa gaisuwar da muke yi masa. Ya ce." Sabbin ma'aikata ne ?" Da sauri manager da shigowarsa kenan shi ma ya ce." E, Yallabai." Ya jinjina kai yana dubanmu ta cikin farin gilashin da yake idonsa. A nutse ya furta." Kun gama dasu ne? Ina nufin kowacce ta san matsayinta." Manager Ya ce." Ranka Ya dad'e. Wad'annan daga baya suka zo. Sulaiman sha'abu ja'in ne ya turo su. Yanzu Muna buk'atar masu shara ne da goge-goge." Ya juya Yana kallon dattijuwar nan. Ya ce." Mama za ki iya aikin nan kuwa?" Da saurin gaske ta ce." Zan iya Yallabai." Ya yi murmushi a tsanake Ya sake cewa." Aikin fa ba irin na gida ba ne Mama, kin ga wurin nan da girma ba ki dai da wata lalurar ko? don ba kasafai nake d'aukar dattijai ba, ai irin wannan yana buk'atar masu lafiya da k'ananun shekaru" Ta ce." Zan iya Alhji in sha Allahu." Ya juyo yana kallonmu ni da Sahura sai ya ce." Ina fatan za ku kula sosai, idan na d'auki mutum aiki ba na son wasa, shine dalilin da ya sanya ma na fi buk'atar zawarawa ko 'yan mata, irin wad'anda ba su da uzuri na miji da yara. A dinga zuwa akan lokaci in sha Allahu ni kuma za ku same ni da kyautata muku." Ba tare da rashin kunya ba na ce." Ranka ya dad'e ni babu ni a cikin masu neman aiki, ina da abin yi, ni ma'aikaciyar gomnati ce, sannan ina sana'ar hannu, wannan 'kawata ce Sahura ita na rako." Ya ce." Okey ita tana da aure ne ko bazawara ce?" Raina ya d'an sosu da maganarsa. Na ce." Tana da aure da Yaranta uku." Na dubeta tare da cewa." Sahura ki yi bayani mana." Ta ce." Ina da aure Yallabai, yarana uku ina zaune a unguwar ja'in." Ya ce." Wannan ba zai hana a d'auke ki aiki ba muddin za ki ri'ke shi da muhimmanci, sakarci ne dai ba na so a duk sha'anina. Na san duk dokokina kun karanta a cikin form din da kuka cike ko?" Gabad'aya suka amsa. Ya ce." To, Allah Ya yi mana jagora gabad'aya." muka amsa da "Amin." Ya juya domin fita mabiya bayansa suka take masa baya. Minti biyar sai ga d'aya daga cikin escort d'insa da kudi a hannu. Ya zo dukkaninmu ya bi mu da dubu biyar biyar Yana fad'in oga ne ya ce a baku kudin mota." Ya gama raba mana sauran ya zura a cikin aljihunsa ya fice da saurin gaske... [2/13, 7:40 PM] Aunty B: 8&9 Bayan an gama komai Muka fito bakin titi muna jiran abin hawa. Na dubeta a nutse na ce." Sahura kin fahimci azancin wannan mutumin ko?" Ta d'an yi shiru daga bisani ta ce." Na fahimta sis, amma kuma ban ga lefinsa ba, idan ba hakan ya yi ba sai a samu matsala. Kin san halin mutanan mu da son zuciya. Muddin zai kyautata kamar yadda ya yi alkawari, ni kuma zan yi kokarin ganin na rike aikin da muhimmanci, ba za a samu matsala daga wurina ba." Na ce." Hakane, amma dai dole sai kin kiyaye Sahura, domin aure shi yake gaba da komai, yadda na fahimce shi kamar bashi da damuwa akan auranku hakkin mijinki da yaranku. Shi dai kawai ku fito aiki akan lokaci, hakan yana nuna duk ranar da kuka kuskure ba za ku wanye lafiya dashi ba. Gaskiya kamar akwai son zuciya a sha'aninsa." Ta yi murmushi tana cewa." Ke dai Amina tunda aka kori marigayi daga kamfaninsa ki ka tsane shi, dukda cewa jama'ar gari na shelar mutumin arziki ne, amma ke ban ta'ba jin kin fad'i alherisa ba. Kwanaki fa har zagi ki ka d'ura masa, kin ala'kanta rasuwar mijinki dashi. Allah ina tsoron kada watarana ki yi su'btar baki a gaban jama'arsa su yi miki dukan tsiya." Na ja tsaki tare da furta." Sahura kin san Allah da sanya hannun mutumin nan wurin mutuwar Ya Aminu. Abban Yusi jajurtacce ne sosai ya yi masa bauta sosai, kema kin san da haka ranga ranga aka kawo mini shi gida ciwonsa ya tashi sakamakon aikin da suka yini suna yi a kamfanin. Haka ya kwanta jinya, mutumin nan bai ta'ba zuwa duba shi ba, daga 'karshe ma sai kawai takardar sallama muka gani, wai an d'ora wani a madadinsa. Kuma babu ko sisi. Duk ranar dana tuna wannan wula'kancin sai na yi kuka. Sahura tun daga lokacin fa jikinsa ya sake rikicewa har sai da ya mutu. Ya ba zan tsane shi ba." Nasa hannu ina goge hawayen da suka zubo a kumatuna. Ta dafa kafad'ata cikin taushin harshe ta ce.'' Ki yi hakuri don Allah kin ga akan hanya muke, na yarda mutuwa d'aya ce, amma kuma tana da sanadi. Ki cigaba da yi masa addu'a. Sannan ki godewa Allah ni'imar da ya yi miki, ki tsananta da yi wa yaranki addu'a." Na ja hanci tare da furta." Sis, ba na sha'awar aure wallahi, ina jin tsoron mazan yanzu, ina ganin kamar ba zan samu mai nagartar Yaya Aminu ba. Sannan kin ga ina da yara ba kowane namiji ba ne zai yarda ya aure ni dasu ba. Ni kuma ba zan iya tafiya yawon aure na bar su a wani wuri ba." Ta tsayar mana da adaidaita sahu muka shiga. Ta ce." Kina da hujja Sis, amma fa kin san iyayenmu ba za su barki ki yi ta zama a haka ba, wand'anda suka fi ki shekaru ma suna yin aure ballanantana ke da ki ke da talatin. Kin ga a yanzu ne ki ke kan ganiyarki, amma zan yi miki uzuri idan kin ce ba za ki yi a yanzu ba sai yaranki sun girma tukkuna. Wannan kowanene zai iya duba hujjarki akan haka ." Kira ne ya shigo wayata dake cikin jaka. Na fito da ita da sauri ina dubawa sai na ga anti Yagana ce. Da sauri na daga tare da furta."Anti barka da Juma'a. Ta amsa tana fad'in." Me yasa ne yanzu ba a samun wayarki ta dadin rai, sai a yi ta kira tana katsewa. Na ce." Sai dai idan matsalar network ne anti fatan duk kuna lafiya ya yarana?" "Kowa lafiya Lou alhmdullhi dama bikin babandi ne ya tashi satin da zamu shiga za a fara, na ce bari na gaya miki tunda an yi hutun makaranta ki zo ki shiga dangi, da yawansu suna tambayarki sai ki zo ku gaisa." Na ce." Zan zo kuwa in sha Allahu anti Babandi ai mutumina na ne, in sha zan gayawa Babanmu idan na koma gida."