16
by @surayyahms
⏯️1️⃣6️⃣Abunda ke ɓoye!
malamin yana kammala musu bayani cikin lumshe ido da budewa ibaad yafurta alhmdullh acan kasar wuyarsa yanajin wani sanyi na ratsashi taciki ayayinda ayaana kam batasan ma me takeji aranta ba, tagumi hajy mairo tay da alaman bata wani ji dadin bayanan malamin ba, shide ya gama bayani bisa haqqin sharia da kuma nassin musulunci, agabansu akay ma ayaanar wasu yan tambayoyi game da auren wanda dakyar ta iya budan baki ta amsasu, dama ajine ko ibaad ya amshi auren agaban iyayenta da bakin sa, toh da sukaji bai amsa ba, nan aka warware duk wani kananan confusion dake tsakaninsu a shariance batare da wani dogon ɓata lokaci ba.
acikin nitsuwa da girmawa ibaad din ya tashi ya raka malamin waje, suna ficewa hajy mairo tahade rai ta juyo da bambami tanata kallon ayaana
da kmr bazatace komi ba can cikin girgiza kai da rage murya kasa kasa tace "hmmm, ke kuma yannan ai dabaki nuna musu bakison auren nan ba, wann aure ai kariya ne agareko ayaanah, duk taurin kan rayyanu yana girmama nagaba dashi hala ynzu da malamin nan yasaka mana baki ya roqesa ya amsheki a matsayin matarsa kodan kisamu kibishi binni da cikakken lasisinki, inba haka ba dayuwar mahaifinki juma zai zonan yakafa wani kwakkran dalilin da zai karbeki ahannun taawure kuma dai kinsan duk wani kalubale da zaki sha ahannun jikana rayyanu bazai kai rabin dumbin wahala da kuncin rayuwa da zaki kwasa a garin majiya a hannun ubanki juma ba.
dan shiru aayanah tay kmr bada ita hajyn ke magana ba, a mind intq gani take harma yaushe ta isa amata aure bare har ta zaɓi ta zauna da ibaad da tuntuni banda kushe lamarinta babu abunda taji yanayi. hawayen ta na zuba ahankli cikin tunani taki cewa komi, iyaka yawan surutu da lissafe lissafe da hajy mairon takeyi akan hakan saiyasa tadinga jin rauni da mugun tsoro maihade da fargaban yuwar komawarta hannun juma yanamai kare lullumeta, ahnkli wasu sabbin raunattacun hawaye suka dinga fitowa daga cikin idonta cikin rasa abunda zatace mata ta dadayin shiru tana sauke ajiyan zuciya ahankli....
karar bude kofar yasa hajy juyowa katse maganan da sauri, caraf kuwa suka hade idanu da ibaad, wani irin kallo tamasa da shirin masa masifar akan kin auren dayay saidai ganin yanayin daure fuskan daya tunkarota dashi yasaka ta sauko kasa da tempernta suka fara magana cikin hankli ayanah tana hawaye tanajinsu, yadda haj mairon take raki tana kara fahimtar dashi kalar hatsarin da rayuwar ayaanah zai shiga in suka bari hakan ya jawo ta koma kauyen majiya, da irin sharrin tsafi da mugunta dake cikin kauyen, ce masa take duk runtsi duk wuya ayaana saidai inzata zauna ahannunsa dan bazata taɓa bari aji labarin cewa baya tare da ayanah amatsayin ma'aurata ba inba haka ba juma da mukarabansa akauyen majiya zasu tsafeshi tass koma su kasheshi.
tace inma bazai riketa wajensa ba dole ne kawai ya tafi da ita birni inyaso zata gaya ma danta zaidu, ko muhammadu ko kuma surkuwanta fatima su rike mata ayanahn acan. da wani abu aran ibaad ya kalleta bayabo ba fallasa yace "hajiya duk hakan dakike fada fa bazaiyu ba, yarinya da ubanta da uwarta a raye sai ke kice akaita wani waje tay rayuwa, nidai bazan sace musu yarsu in kaita koina ba...ita kanta hjyn fada yay mata yace koda take matsayin kakarsu yakamata ta dinga tuna cewa ba alaqar jini ne ya hadata da taawure ba, taawure yar rikontace, wacce ta sameta sanadiyar aurenta na biyu, dan haka bata da wani hurumin yanke musu wann babban hukuncin akan yarsu..
kusan musu suka dingayi da kakar tashi akan wnn magann duk saikaji ka rasa waye me asalin gaskiya acikinsu...
sunq cikin musun har tawuree tasamu isowa asibitin dake taje gidan hajiya bata sameta ba, tun daga kofar dakin ta tsaya cak tanajin bayaninsu sai jikinta yayi sanyi sosai musmn data gane kmr ansamo yarta ayanah, Allah Allah take ta shigo saidai yadda taji ibaad din yake tsagewa hajy mairo gaskiya akan alakarsu matsayinta na matar kanin uba ga taawure yasa ta dan dakata kadan
yace "sam shi bazai tafi da wata ayaanah birni ba, inma kareta sukeso suyi toh ta zauna mana agaban mahaifyarta anan, hjy mairo taci kuka, tamasa zagin duniyan nan amma ko ajikinsa,
duk ta dauka tsabar baqin hali ne da ra'ayin banza yasa yake ture maganan tafiya kano da ayanahn gefe yana nuna bayaso, batason harga Allah tun jiya ya riga ya shirya yin haka aransa ba. babbn burinsa shine yajawo wata babban yarjejeniya a tsakaninsu dan ya zamana tay saurin jin maganansa akan batun dawowarta gida, in return shikuma saiyace mata zai wuce da ayanah binni. kawai de so yake yaga yadaureta da jijiyar wuyarta, dan ta amshi dukkan bukatansa, hajiya mairo tsohuwa ce mai son rikici yasan saiyay da gaske kafin ya iya rabata da kauyen nan na har abada.
suna tsaka da wann musun ahnkli taawure tabude kofar tare da musu sallama sabida bata da wani dogon lokacin batawa ya zame mata dolene taje wani waje me nisa ta ɓoye kanta nadan wani lokaci sabida aika aikan da ta rattabawa arzikin juma..
tanayin sallama kusan kallo daya ibaad yay mata jikinsa ya bashi ko ita wacece, caraf kuwa hjy mairo ta juyo baki na rawa ta ambace sunanta tana hamdala a raunace suka dan rungume juna cikin fashewa da sabon kuka tana tuhumarta ina taje
jin muryan taawure yasaka ayaanah tay firgit ta bude idanunta da suka gama jiƙkewa da ruwan hawaye dan yadda taji ibaad yanata rejecting inta yadada sawa jikinta yay sanyi bana kadan ba, sai ta dada aminta dacewa duk duniya ne aka tsaneta, ba zallan babanta da yan kauyensu ba, ita de da alama kowa ne baya son riketa.
muryan taawure dataji yasa ta kara fashewa da kukan itama ta firgita tana cewa umma umma jikinta na rawa har zata diro kasa daga gadon ibaad yay sauri ya rikota ajikinsa da karfi duk da firgicin fushi data farayi masa bai saketa ba har kafin nan taawuren ta sake hajy ta karaso wajensu ta amshe a hannunsa ta rungume yartan tsamm da wano mugun karfin shauqi ta lullumeta kamar za'a kwace mata ita dan ko kadan batay tsammanin zata zo nan ta tarar da ayanahnta ba...
sosai nauyin datakeji a zucyarta ya dan ragu data rungume ayaanah..koba komi tay riba tunda ta samu yarta Alhamdullh
dake taji duk abunda suke fada tun a kofa bata kula bayanin aayana ba har saida ta fara gode ma ibaad tanamai sakamai albarka da ya dawo mata da yarta wajen hajy mairo
kalamanta masu sanyi sosai suka ratsashi, idanunsa suka ciko da ruwan hawaye, tausayin taawuren ya hanashi furta mata komi kai kawai yake gyada mata cikin sanyin jiki har snn yay excusing dinsu ya fice waje agaggauce ya nufi motarsa ya shiga yazauna aciki tare da kifa kansa akan stiring dan yay catching breath insa...
hajy mairo batay kasa a giwa ba ibaad yana ficewa kusan tass ta kwashe labarin yadda akayi da batun auren ibaad da ayaanah tagaya ma taawure, itama taawuren bata tsaya ba tagaya mata iya abunda taje tayi ma juma acan kauyen majiya amatsayin daukar fansa wanda hakan ya razana hajy mairo sosai dan ta jima da sanin cewa taawure mace ce mai kunya da dumbin haquri.
sai kallon bakinta take tana salati.."la ha ila ha illahu, anya taawure kina da hanklin kuwa da kikaje majiya kika aikata musu irin wann tijara da dumbin asara? toh da yanzu sun kamaki sun suka kashe ki fa ma ubam waye zakiwa asara inba yarki ba.
kusan a zuciye cikin fushi taawure tace "hajiya koda naje majiya a shirye nake, akasheni mana,dama..meye zan samu na farinciki a duniyan nan bayan juma yay wa ƴata sharrin zina ya tozartata snnn ya walaknta gawarta, yanzu inba don ahannun jikanki ayanaah ta fado inace da har na mutu bazan san inda yata take ba? hajiya, gaskya bazan iya yafe masa ba, inda ace ma nabiye wa zafin zuciyata da har lahira saina kaishi wallah, yayi kadan ya kasa..amma kinga ai bankasheshi ba, dukiyarsa da lafyarsa na rabashi dashi kuma banajin dandanasani yin haka, dan ko yanzu akace na sake masa haka wallah wallah zan iya sakewa, kaf majiya ba'a isa a walakanta ni snn a walankanta rayuwar yayana ba. ..
tana maganan ne tana kuka sosai rungume da ayaanah
ganin irin birkicewa da fushi da taawure tay yasa hajy mairo kasa cewa komi kawai ta karkada kai tana hawayen itama can dai tafara bata hakuri tana lallashinta kana ganin taawuew kasan ba acikin hayyacinta take ba dan sosai mutuwar inayah ya ruguza mata duk wani kofar tunani ya kuma saka mata baqin ciki me tsanani.
tun hajya na lallashinta har ta hakura ta kyalesu da ayaanahn dan suyi jimamin rasa inaya da sukayi atare..
jikinta a sanyaye ta basu waje tana rufe musu kofa ahnkli ta tsaya agefe tanamai share hawayenta, can kafin tafito har waje ta isa gaban motar taje ta samu ibaad ya jingine kansa da stiring motarsa idanunsa a lumshe yay shiru kamar wanda yay nitso acikin tunani
kwankwasa mai kofar motar tay ya daga kai suna hade ido ya bude motar ya sauko kasa, wani iri hajy tay da fuska kmar wacce zata masa kuka, tuni ya bi ya hade ransa, tun kafin ta fara kukan cikin katseta yakawo mata offer cewa kafin ya amince yawuce mata da ayanah can gida sai inhar zata amince tazubar da makaman neman gaskiyarta ta tattara inata inata tabar garin tudu, if not shi bazai kai ayanah ko ina ba, snn zaije kano yagaya ma su bappa zaidu da uncle moh cewa tazonan ta sato yar mutane tariketa bada cikakken izinin iyayen yarinya ba. sabuwar musu suka dingayi, kusan ince ma wayo ya mata sosai, ya nuna mata kawai bata da mafita, ai tunda aurensun ma is invalid uban kowa ma yasan labarin shi baidamu ba, inkuwa har bata amince zata bar tudu ta koma kano ba saidai abari har juman yazo tudu ya dauki yarsa kawai inyaso yaje can ya kasheta.
still suna cikin wnn musun sai ga nan taawure ta fito da sauri saurinta tana share hawayenta da suka ki tsayawa, anan ta samesu agaban motar ibaad, tana isowa ibaad ya rusuna har can kasa cikin nuna tausayi da ladabi ya gaisheta, ya mata proper gaisuwa, snn yamata ta'aziyar mutuwar yarta inayah yadan babbata hakuri shima haka tadinga bashi hakuri akan abunda ya faru dashi akan taimakon ayaanah dayi..
cikin kwantar mai da hankali tace masa babu komi itama tafahimce shi, tasan kuma gidan su babban gidane, bazata so wani abu na rashin mutunci yazo ya faru tsakaninsu da juma ba, inde bazai wuce birni da ayanan ba babu damuwa zata san yadda zatayi a rike mata ita har sai ta dawo.
hajy mairo da ba akasa da ita ba, nan ta tuma ta cafe zancen tace sam sam bata aminta da wann hukucin ba, inde har zata kwashe inata inata tabar tudu r yadda yakeso, saidan inshi ibaad din zai amince ya zama guardian in ayanaah, snn ya wuce da ita cikin kano ayau ta zauna agaban fatima kafin itama tagama parking din tadawo ta samesu acan.
ibaad yay shiru yaki cewa komi ba, duk rakin da hajy mairo tayi, taawure tace musu ita zata wuce wani kauye acan jigawa dan batason matasan garin majiya susan me tay bare azo a dauketa anan tudu aje kasheta a majiya. dan haka zataje can yankin jigawan dama tana da yan uwan mahaifyarta awajen, su irin fulanin tashin nn ne suna yawan zuwa kiwo zata nemesu tazauna awajensu kafin komi ya lafa...
haka sukasha kukan rabuwarsu agabansa da hajya mairo har gwanin ban tausayi...duk kudin ajiya dana jinya dake wajenta hajy mairo tace mata ta rikesu kawai halak malak taje tanemi tsira.
jikin taawure amatukar raunane ta juya, da shirin komawa cikin asibitin dan tay sallama da aayanah, ibaad yana gama shanye hawayensa daya kusa zubo masa ya bi bayanta anatse ya tsareta, saida suka koma can gefe inda babu idon mutane akansu ya tabbata she feel safe with him, snn ya mata bayanin duka duka manufarsa akan hajiya da kuma ayaanah, sosai ya zage ya nuna mata cewa ya fahinceta ya gane halin datake ciki kuma karta damu, yay mata alkwari zai tsaya mata akan yarta har tasamu tay karatun, he will be her quide, snn ya ciro wallet dinsa duk ya rasa inda zaisamu paper, sai ya rubuta mata number wayarsa kawai ajikin sabon dubu daya, snn ya kara fitowa da sabbi sabbin 1k notes din masu yawa baima kirgasu ba ya damka mata su duka ahannunta batare da ya sake hannuntan ba yace mata "Dan Allah kartace masa a'a, tay amfani da kudin duka tay kudin mota dashi, taje duk inda zataje tanemi tsira daga juma snn duk abunda takeso kawai ta kirasa he promised her dat yarta will be in safe hands with him in sha Allahu..
yana maganan nan kawai kuka taawure take masa kamar zata cire ranta, dan bata taɓa samun wani wanda ya iya karantar duka turirin damuwa da baqin cikin dake yawo aranta ba kamar shi..yaro ne, amma gashinan da hankali da tausayi da halin manya atattare dashi.
cikin nuna mata tausayi da girmamawa ya tausasata da kalamai masu sanyi ya kuma lallabeta har saida ta amshi
kudin, fadin irin albarka da godiyan data masa ranar bazai kiyascu ba, ganin lokaci na tafiya yasa tay marmaza ta karasa ciki dan tay sallama da ayaanah
babu wani bata lokaci
tadagota suka rungume juna ta masa nasiha masu ratsa jiki tare da jadadda mata cewa mutuwar inayah ba shine karshen rayuwarsu ba, su hada hannu sucika manyan burikan su, tay mata hakan, dan tasan inayah zatafi jindadi in rayuwarsu tay kyau ba muni ba,
..,snn umarni tabata akan da tay ma ibaad biyayya, ta kallesa a a matsayin dan uwanta kuma yayanta karta saɓa masa..tare damata alkwarin wata rana inkomai ya lafa zatazo har kanon ta nemesu...
gabaki daya ayaanah ta raunana sai tanajii kamr magangnun sun mata tsauri da mugun nauyi dan bama ganewa take ba dan bakaramin kukan rabuwa da mamantan taci ba, haka kuwa tana kallo taawure tabar asibitin taje waje tasamu ko magana ibaad basuyi da hajy mairo ba.
sai fushi take dashi wai yaki karban ayaanah, taawuren tana zuwa ibaad ya mata sallama sukayi bankwana sai yawuce ciki yabarta da hajiya.
anan ne ta sanar da hajiya duk yadda sukayi dashi tabi ta nuna mata kudin daya bata, duk mamaki saiya rufe hjya, suna hawaye ta rakota har waje ta tsare mata abun hawa har saida taga tay nisa snn ta dawo.
dawowarta kenan tazo ta samu har ibaad ya gama biyan kudin jinya da duk wani abu da ake binsu ita sai tawuce ta dauko ayanahn suka fito, tun da suka kama hanya, basuyi wani magana ba har saida suka isa gidanta nan ma sharesu yayi ya hada ruwan zafi a heater yayi wanka yazo ya samu hajya ta sa anhado masa break fast mai nauyi yazauna yana ci itakuma ayaana aka kaita wajen wanka
hawaye duk yaki tsayawa a idonta dan duk inda ta zaga a gidan saitaga kamar zataga addanta da mamanta, she was seriously ill, nd grieving. gabaki daya memories dinsu yanata dawowa mata kai...
dakyar ta shirya adayan dakin hajy mairo ta sakata dan dole taci abinci snn aka kawo mata riga da zani brown colour na coté d' ivoiré kayan yama mata oversized ma amma haka ta saka tana gama cin abincin bacci me nauyi ya dauketa awajen..
tsakanin ibaad da hajiya mairo dakyar suka sauko sukafara magana musmmn data fara tsokanoshi da batun alherin da yay ma taawure, ya hade ransa tamau, yace mata aidqma can ta daukesa mugu ne shiyasa bata yadda dashi ba, dan haka karta damesa kawai tunda zai wuce kano da yarinya ta gaya masa exct ranar da zata gama tattarawa ta dawo gida itama.
badon son ranta ba hakanan suka warware maganan, aka sa ranar, 14days lissafin ranar da zata gama parking da kudin sallamar wasu wokers intan, da wanda zata basu incharge dan su cigaba da mata sana'ar abincin anan tudu dan akwai katon gidan almajirai datake ciyar dasu atunaninta inhar tabar tudu gabaki daya wazaina ciyar da yaran nan. duk suka gama lisasafi, taso ya bata tsawon wata guda amma ibaad yace sam sati biyun kawai ya isheta tunda tana case da yan ta'adda. shi zai gaya ma bappa zaidu da uncle moh ranar tahowarta inyaso za'a kawo mota kawai azo a dauketa da tarkacenta gabaki daya.
ganin babu yadda ta iya dashi yasata kyaleshi, ibaad ne kawai yake iya mata haka tayi shiru saboda sosai take kaunar sa aranta duk dama koyaushe acikin fada zaka same su, jim kadan bayan sun yi hirar karatun sa yace mata shi zaiwuce kano yanxu sabida zai kai ayanahn asibiti adubata acan
wajajen karfe 10:30am saura nasafiya aayanah ta farka duk baccin bai wani isheta ba, haka haj. mairo ta sakata agaba tay mata nasiha mai shiga jiki, duk kusan irin abunda taawure ta gaya mata ne dazu akan tay ma ibaad din biyayya sann ta sani cewa mutuwar inaya ba shine karshen rayuwarta ba, nn ta hadata da ibaad din ta musu atare akan suy hakuri su zauna lafiya tunda qaddara ne ya hadasu. shide baice komiba harta gama surutun ta within few minutes ya fita yabarsu, yagoge motarsa tsaf, yana shigowa yadau jakarsa yace mata kawai su tashi shizai tafi yana da practicals karfe 2 na rana..
daga ayanahn har hjy mairo kuka sukeyi rungume da juna tazo tasakata a mota harda sakamata seatbelt yana sallamar kakansa ko kallo daya bai kara ma ayanah yasa kai ya kunna motar suka kama hanyar kano.
tafiyar kurame sukayi banda kukan da ayanah takeyi babu abunda kakeji, baison yace mata tay mai shiru ba dan yariga yasan abunda takeji is alot to carry, ga zafin mutuwa gana abunda yake faruwa da su, iyaka da abun ya ishehi ya kunna karatun qur'ani ya dan kure musu volume tun tana cigaba da kukan har zuciyanta yay sanyi tafarabin sautin karatun da zuciyarta tana tuna addanta inayah, her fav thing in this world was qur'an ..sai kuka mai zafi take tana tuna irin murnan da sukayi ranar da inayahn tay sauka har bacci me nauyi ya kara daukarta.
ABUNDA KE ƁOYE
SURAYYAHMS
***
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
AREWABOOKS
@SURAYYAHMS
WATTAPAD @SURAYYAHMS
WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025