20
by @surayyahms
2️⃣0️⃣⏯️ABUNDA KE ƁOYE/surayyams💫
maid elizabeth tafi awa biyu tana zaune cikin yanayin lura da kowani irin motsi da zai fito daga kofar zainab arifa, with few oda kitchen maids wanda time to time suna lekowa cikin sintiri a sashen kowa na fargaba tareda jiran zainab arifah din tasauko daga fushin datakeyi wanda sukansu basusan musabbabinsa ba,
babban damuwarsu kawai ta buɗe musu kofane domin kowa yay aikinsa tunkafin prof ya dawo aci taransu na rashin kulawa masa da ƴa, shiru shiru bata fito ba kuwa har suka gaji da sintiri suka hakura musmmn jin ta kunna loud music, wakar ozeba by rema na wani oron tashi a dakin tamaida gidan kamr gidan party wanda hakan yasa kowa ta hqra takoma maids station for a while...
Dagata daya bangaren kuwa wajajen 4pm na yamma ibaad ya fito daga school masjid bayan sun kammala normal lectures dinsu, dake yau din kwata kwata basuda wani private club activities kusn yau ranar hutuce ga duk wani student beginner a boyayyen club din nasu, iyaka yan assigemnt na Bio1201 da chem1241 da aka basu daga two lectures din da sukayi yau ya fito dashi wanda tun a ajin ya solving kayansa sabida he is far ahead of this basic level1 topics, already duk an kokkoya musu shi a matsayin basic introduction to medicine a club dinsu just recently inda ma ake hada musu da practical aspect na abubuwan sosai.
kasancewarsa smart guy kuma kyayyakwa dan gidan masu shi yasaka mutane dayawa daga classmates dinsa suke son suyimasa magana saidai kwarjininsa da yanayin emotionless fusknsa da kame kansa dayakeyi yasaka gabaki daya a ajinsu baida wani aboki
dan ko a seat ne shidayansa yake yawan zama batare da wani seat mate ba.
yana barin school masjid arnd 4:20pm yay gaban wata garden ya samu inuwa me sanyi ya zauna agindin wani decorative tree yana latsa wayarsa sleek champaing golden colour latest samsung galaxy me flip cover dake shi duk brand din samsung din kawai yake riƙewa bai fiye biyewa abun yayi ba.
kusan sau uku yana kirar layin maheer dan yaxo ya daukesa a mota suwuce asibiti saidai yana bugawa saiyanajin user busy da alama yabar wayarsanne a DND mode harynxu, after sitting for like 3 more mins ya tashi ya nufi gate yana tafiya anitse har Allah yasa ya kawo main gate batare da bata lokaci ba ya tsare abun hawa direct yace awuce dashi al-eeman private hospital dan ya dauko ayaanah su wuce gida.
ana saukesa a gate jikinsa a gajiye ya shiga ciki,not minding duk wani ido dake sauka akansa kai tsaye yy hanyar nurse station yadan leka ta glass windownsu daga can nesa sai baigan kowa anan ba, he stood der for a while yana daddana waya yana kiran layin anty hauwa amma duk ya kira sai yaji ba a dauka ba, can kawai sai yadawo baya wajen har reception ya samu wata nurse a tsaye yay tambaya anan aka sanar dashi cewa anty hauwan tana emergency ne saiya jirata na akalla five min yanzun nan zata fito..cikin gamsuwa da hakan yanema waje ya zauna shiru jin yunwa ta fara damunsa ga wani dan banzan tunanin yadda zaije ya tarar da fitinan ammi babba agida, duk saiyaji kmr kansa na juyawa cikin kkrin kauda wann tunanin aransa yafara kakalo tunanin gym routine dinsa da kwana biyu ya dena zuwa he was thinking of going back to gym training koda ma stress din dake jikinsa zai warware.
yana cikin wnn nazarin jim kadan wayarsa tafara kara yana dagawa kuwa yaga anty hawwan ke kiransa, cikin nitsuwa ya kai wayar kunnensa yay sallama yace mata yazo yana reception, atake anty hauwan tace masa ya karaso ciki ynxu.
..room3 ya nufa kamr yadda ta gaya masa, wajen was quiet babu motsi, ya tura kofar ahnkli da karamin sallama abakinsa jin muryanta kmr ita daya ne acikin room yakara bashi gwarin gwiwar karasowa ciki ahnkli ya turo kansa ciki yana shigowa kuwa idonsa suka sauka akan ayaana dake kwance akan gado mashak har ansaka mata ruwa
kallonta ya dingayi da mamki har ya karaso jikin gadon yagama bacci ashe takey nan suka fara gaisuwa da anty hauwa, out of curiosity yace mummy jiikintan ya tashi ne? da yanayin tausayi ta kalli fuskar ayaanahn dake kan bacci tace "mishi, ehh toh, she was just dehydrated nd weak, kaga can abincin da kuka bata da safe koda tasa abaki amansa kawai tay shine na aika aka siyo mata fruits ta samu tasha..then she dozed off for a while, tana tashi na haɗa mata ORS amma still aman bai dena ba shine kawai nasaka mata ruwa,"...kansa na kallon kasa ahnkli yace "thank you soo much mummy, kiy hakuri fa mun daura miki wahala.., tana murmushi tace "haba bakomi ibaad, amma gaskiya inaga yarinyar zata bukaci nitsuwa da kulawa, i think she needs a quiet nd peaceful environment to settle dan kamar she is grieving ne fa, ko kai bakaga hakan ba?
yadan sosa kansa kadan yace "mumy we are still working towards dat, kawai dan ammi bata zauna bane amma in sha Allah komi zai wuce awann fannin, tace amma meya farune, why does she always cry? ko raihanatu ta mata wani abu ne
a nitse yace a'a..dama yar uwartace ta rasu few days ago kuma inaga abunda yake damunta kenan, but i assure u she will get over it, cikin yanayin tausayawa anty hauwa tace ayyah,..Allah sarki wallah tana ban tausayi sosai, duk wanda baisan zafin mutuwa ba bai faru dashi bane Allah ya jikan yar uwanta, ahnkli yace Ameen mummy...kallon bed stand din tay tace "opps gashi ruwan ma ya kare toh bari nacire mata canula sai in tasheta a bacci saiku wuce ko dan nasan hala ka gaji...karamin murmushi yay yace" a'a mumy basaima an tasheta ba is best inta samu bacci. batace komi ba ta gyada masa kai ahnkli tafara cire mata ruwan harta manna mata plaster a hannu ayaana duk bata san anyi hakan ba. after giving him few words of advices akan jikin ayaanah da irin mugun zamansu da ammi babba cikin saukar da kai yamata godiya, daga nan ya gyara zaman laptop bag dinsa snn ya dauke ayaanahn cakk ya dan rungumeta akan kafadarsa suka fito har kofar asibitin anty hauwa ta rakosu har bakin titi ya nemi abun hawa suka dawo gida.
iskan hanya yaso ya tasheta amma jin qamshin turarensa yasaka ta kara lafewa akan kirjinsa tareda nitsewa cikin baccin sosai, lokacin already karfe biyar na yamma yayi, mai adedeta ya ajesu a gate din gidansu dede gaban masallaci, he was hoping in sun shigo gidan zaizo su samu an aje musu abinci kmr yadda aka saba aje musu kullum dan ya gaji sosai baison yakara ficewa
ayaanah tana hannunsa ya shigo har main palor, wanda tun anan yaga koina yay shiru kmr babu rai aciki, very gently ya sauketa akan 3 seatter cikin kulawa ya jawo soft throw pillow ya dora kanta akai snn ya miƙe tsaye yana shirin rarumo wayarsa daga aljihunsa zaiyi kira kenan saiganan sultana ta fito, jikinta all covered dq dogon hijabi har kasa da katon math textbook a hannunta zataje lesson..
suna hade ido tabi ta rakuɓu da jikin bango tazura masa ido muryanta kasa kasa tace sannu da dawowa yaa ibaad..
kallo daya yay mata ya dauke kansa kasr wuyarsa yace mata "sannu,..shiru tay sai after few min of silence snn yace "ina mutanen gidan kuma sai yanxu ne kikaga daman zuwa lesson din? cikin saukar da kanta kasa tace "a'a yaa..yunwa fa nakeji shine yasaka ban fito da wuri ba kuma ai mummy ma ta fita batay mana abinci ba, shine naje na dafa dakaina itama saddiqa mai aikinmun batazo ba...
yace "ohh sannu newscaster! "bakowa agidan kenan sai ke, to wani shirmen kuma kika dafa?
tay shiru can kuma saitace "indomie..cikin kyabe baki yace "toh good for u. daga haka sai bai kara kulata ba yabarta da ayaanah a falorn atsaye ya haura sama dakinsa abunsa, yana shiga ya aje yar jakarsa yq tuɓe gabaki daya daga nan wajen wanka kawai ya fada kai tsaye...
sultana tabi ta mance lesson zataje ta karaso inda ayaanahn take kwance tazauna daf da ita tanata kallon kyakkwan fuskar ayaanahn tana mamakin irin sanyin kyan da Allah ya zuba mata, for almost like 30 min tana zaune tana abu daya jin karar saukowarsa yasa tacire takalminta ahnkli cikin sanda ta ruga waje da gudu ta nufi spot din math lesson inta dake bayan gidan .
..cikin nitsatsiyar takunsa me daukar hankli ya karasa saukowa wanda tun dagakan stairs kwarjininsa ke haskawa, yasaka cool marron raymond shirt paired with grizly sand colour trouser da silver agogo. wnn hadadden qamshin turarensan atake ya fara aiko sauƙo ayayin da sassnyar qamshinsa yacanza iskan gidan gabaki daya ya rikagasa isowa,
kan ayaana ya tsaya direct yana dan taɓa fukarta da cold hands dinsa tay wuf ta firgita ta farka adan tsorace ayayinda raunatun kwayar idanunta suka fada acikin hazel eyes nashi ahnkli ta lunshe ido ta bude tun kafinta budi baki tamasa magana cikin sauke ajiyan zuciya datazo mai bazata yace "ke tashi kije sama kiyi wanka, zaki ga kayanki na jiya na aje mikisu akan gadona inkinyi wankan sai ki dauka ki saka ajikin ynxun nan kafin na dawo...gyada mai kai tay tana layi layi kamr wacce baccin bai gama saketa ba..har saida yaga ta sauke kafafun ta kasa ta miƙe tsaye lafya lau snn shima yasaka kai ya fice agidan da key din mota a hannunsa..
baiy wata wata ba ya wuce cikin gari gaban wata babban fast food joint mai hade da wata katowar groceries mall ya tsaya yay parking dan shima sosai yunwan ke damunsa dan haka babu bata lokaci ya shiga ciki ya dauki basket ya siya babban goran fresh milk,da fruits salad packs,da fried rice nd chicken with cream nd salads in 4 parts dan yasan duk tsiya a agajiye maheer zai dawo anjima shima.
yana gama siyayyarsa ya dawo gida still ya samu gidan shiru nd its almost 6pm amma babu wanda ya kara shigowa banda sultana dake can baya wajen garden dinsu da lesson teacher inta, dakinsa ya nufa yasamu ayaanah har tay duka abubuwan da yace mata tay neatly, he was impressed abit da kokarinta, dan yadda yaga bata yi masa wani shirme adakin ba she seem to be a fast learner..
tasaka wankakken atamfarta na jiya ajikinta tsaf tahau kan sallayansa tanakan biyan sallolin dake kanta ahankli cikin nitsuwa. cikin sauke sihirtaccen ajiyan zuciy ya dauke ido akanta snn ya karasa kan table dinsa yabude ledojin ya hau rarraba musu abinci ya ware mata nata daban snn ya dauke nashi dana maheer yabar mata zallan natan awajen tanakan sallah tajishi daf da ita yana cewa inkin idar kizauna anan kici abincinki sabida ki samu kisha magani..
daga fadin haka ya fita da nasu abincin direct dakin maheer ya nufa ya bude kofar ya zauna akan couch jin yadda gajiya gabaki daya yarufesa, cikin bude ido da lunshewa yay bisimmilah snn ya bude zallan fruit salad din yafara ci ahnkli
bai wani jima da faraci ba kirar maheer ya shigo wayarsa, ya aje salad din akan table snn ya dauki kirar ya sanar dashi cewa harma sun dawo gida, abakin maheer din yakejin labarin cewa wai fushi ma ammi babba takeyi dasu shiyasa tabar gidan batare da tay komi na abinci ba kuma yau ta hana mei aikin su zuwa, shide ibaad baice komi ba iyaka daya sanar dashi cewa ya riga ya saya musu abinci.
within some min maheer ya dawo gidan lkcin daf ana kkrin kiran sallan magrib ya samu ibaad a dakinsa azaune, iyaka fruit salad din kawai ya iyaci daga nan bai kara taba komi ba,
shima sama sama ya zauna yaci rice nd chicken din suna dan hirarsu akan mujaheed da already ya sanar dasu cewa jiya ya tafi as fan club nawani football club dinsu acan south africa sai nextweek zai dawo.
maheer yacinye kazan duka yaci rice din kadan snn ya aje spoon ya miƙe aggauce ya shiga bathrum da niyyar watsa ruwa ajikinsa kafin nan su wuce masallaci..
yana wucewa bathrum ibaad shima ya tashi ya fita ya wuce dakinsa,yana turo kofar ya samu aayanah a tsaye duk ta rasa nayi jikinta na rawa rawa ganin aman data masa a tsakar daki gabaki daya tabata masa gogaggen floor dinsa sosai da amai.
kallonta yay tun daga bakin kofa sann ya kalle aman fusknsa a mugun harde ya karaso kmar mai aljanu "yace "Kee...waimeye kikayi min anan kenan kike nufi?
kafin ta bude baki cikin daka mata tsawa yace" kimin shiru da Allah, akan baki san hanyar bayi bane da zaki min amai anan?are u insane...
hawaye tuni ya fara sauko mata a fuskarta zirrr kamar ruwa,
acikin yanayin masifa ya fixgota tadawo gefensa ya kara kashe mata sound warning, tanata kuka batace mai komi ba har ya gama masifeta snn ya koreta tashiga bathrum din taje ta kunna sink ta fara wanke bakinta tanata kuka ahnkli.
tana fitowa tazo ta samu har ya goge wajen tass har yasaka qamshi me dadi, baice mata komi ba ransa adan bace ya wuceta yaje yay alwalansa still ya fito baiko kulata ba ya fita, jim kadan da shida maheer suka nufi masallaci, ahanyane maher yake tambyar ya jikinta wani shiru yamasa yay kamr baijishi ba dan sosai yawan kukan ayaana yafara kular dashi.
bayan sun idar da magrib ana jiran isha'i saiga nan bappa zaidu yadawo, daga haraban masallacin kofar gidansun duk suka rusuna suka gaishesa, bayan sun tattauna jikin ayaanah kadan saiya umarce maheer akan dayakai ayaanahn dakin sultana sudinga kwana acan atare. bayan nan dukan su ukun suka koma masjid domin gabatar da sallahn ishai
immidietly suna fitowa daga isha'i bappa zaidu yadauki motarsa yakara ficewa da alama can family house dinsu na rijiyar zaki zaije...
ibaad kuma har ynxu yana cikin masallaci yana amsa wayar mum dinsa, duk ta daga hankli tana so ta bar duk abunda takeyi tazo kawai fa amshi ayaanah, toh already bappa zaidu yaki mata sam yace harsai ayaanahn ta warke tass agabansa snn akai musu ita
she knows yana hakane dan kar ya bada wata dama da matarsa raihanatu zatajji aranta kamr ta kai, ko ta isa ta yanke masa wani danyen hukunci agdansa bisa akan abunda taga dama.
yaki sam ya bar kowa yazo inda ayaana take, duk yace musu subari sai tawarke kafin za'a kai musu ita can gida but for now dolene kawai agidan san zatay jinya, anty safeera dama bawani son rike dan wani takey har ranta ba shiyasa lamarin zuwan ayaanan bai wani darata ba iyaka ammi karama ne kawai ta damu da lamarin ayanahn sosai.
maheer ne kadai ya shiga gidan after isha, direct ya nufi dakin ibaad yana tura kofar ya samu ayaana tana kan sallah jikin ta na rawa rawa at same time tana hawaye sosai..
zama yay abakin gadon yana jiranta har ta idar tay sallama da mugun fargaban tunanin ko ibaad ne ya dawo ta juyo sai taga ashe maheer ne,suna hade ido dashi tabi ta sunkuyar dakanta can kasa tana kara tulowa da hawaye akwayar idonta.. tahowa maheer yay har inda take da sanyin murya yace "hi pretty one..kina lafya..?ya miƙa mata hannunsa yace taso muje..kin miƙa masa hanun tay tamasa shiru, yay murmushi ya zauna agabanta da muryan lallashi yace"kiyi haquri kinji??fadin hakan dayay yasa takara fashewa da kuka. dagota akasan yay cak suka koma kan kujera ya dinga lallashinta yana cewa "komi zai wuce pretty, kuma zakiji dadin zamanki anan duk abunda kikeso in sha Allah bazaki rasa ba kinji? duk yay magana bata amsashi..
tambayar duniyan nan yayi mata akan abunda ke damunta da abubuwan datake ya saya mata amma komi yace amsarta a'a ne, dakyar yazo gq rudeta da kalaman haquri har tay shiru, snn ya fito da ita har main falo ya zaunar da ita.
yana ajefan ya kara haurawa sama dauko abincin da suka ragen musu can saiga sultana tana saukowa, ganin ayaanah a zaune a falonsu ita daya yasa tay saurin isowa gareta, kallonta ta dingayi harta zauna a daf da ita, tay shiru cos she was confuse on what to say,musmn yadda ayaana ta sauke kanta can can kasa witout flinching
tay tsamamnin hala ma bataji motsin shigowrta ba, can cikin tattaro makanta ntsuwa tay gyaran murya, aikuwa a dan firgit taga ayaanah ta daga kai da sauri ta kalle direction inta,
suna hade ido for the first time hawaye me matukar sanyi ya sauka a idon ayaana dan tun da safe data kalli yanayin sultana saitaji hanklinta yaki kwanciya dan fuskarta da yanayintan sosai yake mata kama dana addanta inayah...
ganin ta zuba mata ido tana hawaye mai ban tausayi yasa sultana tay saurin tasowa ta matso kusa da ita da muryan tausayawa tace "hey, meyasa kike kuka kuma...ta dafa kafadunta kadan tace "indan mummynmu ne kike jin tsoro dan Allah kiyi hakuri kinji?suna na sultana al-mansur..kefa??
ayaanah tay kamr batasan me zatace ba tana jan jan zuciya ahnkli cikin muryan kuka tace "ayaanah".
da murmushi me sanyi sultana tace "ayaanah? oh wow nice name..toh ki dena kuka mana kinji?you nd i can be friends, i can even be ur sister...cewan hakan da sultana tay yasa taji raunattacen kuka mai yawa yazo mata itakanta bata san sqnda takara fashewa dq kukan sosai cikin tunowa da addanta inayah ba,...
gabaki daya sai sultana taji ta rude tana shirin budan baki zatay mata magana caraf sai ga ibaad yashigo ya tsaya cak daga kofa yana kallon su da wani irin murdadden murya yace "whats going on here?
da bala'in sauri sultana ta miƙe tsaye muryanta harna rawa rawa tace "nothing yaya...kawai fa magana nake mata shine naga tanata kuka..ni wlh banmata komi ba, bansan meya faru da ita ba..
fuskansa kamar na wanda bai taɓa dariya ba yace ma ayaanah "ke zo nan..da mugun sanyin jiki ta tashi tanata kkrin controling tears dinta kafin ta iso yay wuf ya jawota gabansa yace"kewai so kike na wanka miki mari ko?
a mugun tsorace ta girgiza kanta da sauri tana hawaye
yace toh uban meyasa kike son yin kuka, are u trying to sabortage ur treatment or what? kinga ina binki ahankli shine iskancinki yake dada karuwa ko?
budan baki tay cikin kukan zata bashi hqri cikin zare mata ido yace da Allah kirufa min baki, bana son ji, snn ki goge wann shegen hawayen naki kafin in fasa miki bakinki ynxun nan..
da sauri tafara goge hawayen sultana tay shiru jikinta na rawa rawa saiga nan maheer yana saukowa da robobin abinci..
kallonsu duka yayi yanamai karasowa yace meyeke faruwa anan?..pretty one are i okay..juyowa tay helplesly ta dan kallesa yace gama share hawayenki ki zoki kuci abinci da sultana saikuje daki tare kuyi bacci..
kai tsaye cikin iko ibaad yace "she is not eating!! bacci kawai zataje tay yanxun nan...ya kalle sultana a dakile snn yace" take the food for yourself, nd take her with you. inta sake bare baki kizo ki gayamin, saina mata shegen duka.. very stupid girl, uban waya yace miki anason jin kukanki...
yana fadin hakan ya haura sama yana jan tsaki..
wani hawayen taji ya kara sauko mata maheer baice komi ba ya mikawa sultana abincin snn ya bi bayan ibaad din da mugun sauri, ibaad na shiga dakinsa ko zama baiy ba saiga maheer din ya shigo fuskarsa adan dore yace"kaikuma meye haka zakana ma yarinya karama tsawa kana tsoratata"..and why wud u say she is not eating ahakan ne zata warke maka kafin sati biyu???
da bacin rai ibaad ya kallesa yace "you dont get it do you??maheer wallah am tired, nagaji, tun jiya yarinyar nan take bani ciwon kai while i was busy tolerating her amma batagani, daga tamin fitsari a atsakr daki sai takicin abinci, in kuma aka tursasata taci haka zata yi amai ta ɓata koina da kazanta, wai ciwon hauka ne? nifa kaga banason iskanci da sakalcin banza, yanxu fisabillah me ake mata datake yawan yima mutane koke koke
cikin lumshe ido da budewa maheer yace "dude she is just a child, just take it easy on her ko kaine akace sistrnka ta mutu snn qaddara ya raba ka da mum dinka rana tsaka wallahi bazakaji dadi ba bare wnn yar yarinya karama...
a mugun dakile ya kalle maheer din cikin jan tsaki yace "okay naji, ynxu sai a tsaya knn ana kallonta tana duk abunda taga dama?see...guy inkai zaka iya hakan fine, nide i won't tolerate that. i know is hard for her and she is sick, amma wnn dabiun datakeyi na koke koken nan bafa zai taimaka mata wajen warkewa a both side of her health nd grieve ba, dolene fa sai anbude mata ido if not babu abunda zai canza a condition na ciwonta saidai ma ta dada lalacewa..kaga ni, am soo tired wallah, bacci nakeji cos i have 2 more classes tmorw...kaje kawai kayi abunda ya dameka.
yana fadin hakan ya nemi waje ya zauna akan gadonsa yay shiru yanajiran maheer din ya fita ya bashi waje, for good five mins maheer baice komi ba, he was just trying to understand his point of view, cikin kyabe baki ahnkli yace"wann zafin zuciyar naka ai da soja kaje ba medicine ba,anyhow sha..i will see you tmrw.
kan ibaad na kallon gefe yace "naji, gudnite,..maheer ya gyada masa kai snn ya fita.
falon ya dawo, ya samu wajen shiru har sultana ta lallaba ayaanahn sun haura can sama izuwa dakinta atare. ya kama hanya zai je duba su kenan sai ga ammi babba ta shigo riki riki da wani leda datake kaffa kaffa dashi a hannu.,
kasar wuyansa ya amsa sallamarta yana kallon agogo almost 8.30 na dare ta dawo..
fuskansa ba asake ba cikin dauriya yace ina wuni mummy...
tsaki me kara taja mtcheww cikin watsa masa harara me zafi tace"aikin banza,.. daban wuni lafiya ba ai da bazaka ganni ba..and where is sultana
metaci yau?...ko ubankun bai kira farkansa ta ciyar masa daku bane wato ana jirana nazo nay muku girki ga boyi boyinku ko?..
shiru yay mata
wani tsakin ta kara jaaa zata haura sama dayan sashen domin taje taduba sultanan maheer yay saurin tsareta da cewa "mummy she is not upstairs..ibaad yanakan mata assignmt acan sashen baba.
tana juyowa tace "karya kakeyi munafiki...wani sashen baban naka?? toh yanxun nan mukay waya da safeera tace min ga babanka cann yaje can gidan sunakan tattaunawa a falonta da dan uwansa muhammad,
maheer ya dan sosa kai yace" ai dama bance yana nan ba, i just told u abt sultana dan karki bata lokcnki kije sama, dats all i know..maybe kafin ya tafine ya barsu acan
cikin katsesa da masifa tace "yabarsu acan? see..dont u stand here..go over der now, kadena barin min yata da katon namiji sukadai da sunan yana koya mata karatu...inku kun aminta da ibaad din naku nifa ban aminta da shi ba karyaje ya danne min yata ya cuce ni ehee just go up der nowww ka duba min lafyar yata..
da sauri yace yess maa.
hawa yay yadan buya awani waje yana ganinta tafasa zuwa dakin sultanan, tana wucewa sama sashenta ya sauke wani makudan ajiyan zuciya tareda jin reliev aransa dan yasan muddin tasan cewa ayaanah zata kwana a dakin sultana wani sabuwar rikici zaa balo da daddaren nan...
Ata fannin zainab arifah kuwa ranar gabaki daya bata sauko kasa ba kuwa har saida mahaifinta prof zayyanu ya dawo gidan da yamma..
yana zuwa kuwa kamr yaji jikinsa cewa babu lafiya sam yaki zama yahau bori yace ma maids marmaza suje akira masa yarsa ta sauko yana son ganin kyakkwan fuskarta..
koda maids sukaje duk taki ta kulasu, har saida mum dinta hajya hamida taje dakanta ta dinga buga mata kofar tana lallaminta jin ance babanta ne yake son ganinta yasa ta sauko sanye da pink dior riga da wando daya matseta kanta babu dan kwali tabaza sumanta har wuyanta ta taho kasan cikin daure fuska da kukkuni..
suna haɗa ido da babanta da gudu taje ta fada ajikinsa tanamai sake masa kuka mao cikke da shagwaba da sakalci
wani irin yagalgalata ya dingayi yana tambayarta abunda yake damunta ,dakyar ta dena kukan tafara gaya masa ai wata ce tazo da irin jakarta makranta ita gaskiya ko acanza mata wani jakan wanda babu wanda zai iya sayan irinsa ko acire ta kawai a school din amaida wani...
cikin tsantsan nuna mataso da gata prof zayyanu yace matsalarki kenan princess
tace mishi ehh..yace toh shikenan..let me do sumting abt it ryt now..ciro wayarsa yay ya daddana ya bude dollar acct dinsa atake yay mata transfer $80k dollars..yace princess ga kudi ki saya duk jakar makarnta
daya miki..ita kuma yarinyar i will asked for her to be removed banason ana bata miki ranki kinji ko?? wani irin rungumarsa tay da karfi tana murna kamar ba itace ta dinga masa kuka yanxu ba..thank u soi much daddy..i love you i love you soo much...ure the besssssttt
wani irin fari zuciyarsa tay ganin ta tana murna sai yaji dadi aransa sosai, yay kissing inta a forehead so lovingly da murna tace "let me go nd oder it...and dad gobe zan rakaka 5 days conference dinka a paris..i wanna be by ur side..
cikin tsabar murna yace "as u wish my princess..
kissing dinsa tay agefen kuncinsa tace i love u daddy
..nn ta wuce sama tana wani irin murna sosai haka ya dinga kallonta yana murmushi harta bace ma ganinsa..
hajiya hamida taja wata kalar tsaki"haba alhaji yanxu akan jaka shine tay wann abun kuma ko scolding inta bazakayi ba ka sake daukan maqudan kudi ka bata tasaya wani? wann fa almubazaranci kake koya mata
yace keee? dagata min haba da Allah, kinfara kananan magana nan naki kenan ko. yata kenan mini fa in duk duniya tace tanaso wallahi saina bata bare kuma wani jakar banza
hajy hamida tace nifa ban hanaka bata abunda take so amma 80k$ alhaj yay yawa mana..stop making her a careless spender..ohon maka ai yarka ce..
yace "yeah yeah nd u stay out of it..zainab arifah is so sooo fascinating, jinina ne ajikinta, ke bakiga ma yadda taketa kkrin shiga harkan business dina tun yanxu ba?she is confident nd smart, she have potential to be a good ceo in d future nd i will make sure she is better than me .
cikin kyabe baki hajy hamida tace" kaidai akwai son zuga yarka..but, anyway she loves to impress you more than anything in her life..hala shiyasa tke kkrin koyan abubuwan dakake yi na business tun yanxu..
yana murmushi yace "i am soo proud of her.. tay murmushi tare da rage murya kasa kasa tace "is good ma da zata bika paris din dan dazu mukay waya da safeera tace min wann shegen mayen yaron data kwallafa shi arantan ya dawo...
atake mood din prof ya canza yace "really? to kema kiy shoru kartaji tafasa tafiyar nan cos i dont want her near him for now
Allah ma yasani wallah na tsane shi...banda darajar ubansa danake gani da ko mutuwa zaiy wallah bazai zo kusa da yata ba
hajy hamida tace hmmmm lets just keep quiet kasan zainab arifah da laɓe karma tanajin mu, ka tashi muje kayi wanka na hada maka special ruwan wanka..murmushi yay tare da ko waist dinta suna dariya ahaka suka haura sama atare.
fannin zainab arifah kuwa tana zuwa dakinta dama she already have this long purchase history with the LVs, dan haka atake ta kira private client consierge insu na can paris tay odering black colour rarest limited taiga leather special oder edition na LV bag pack, costing abt $79k (114million in naira) za'a kawo mata jakan in 5 days time can a hotel din da zasu sauka sa babanta in sunje. hqr saida tay hakan sann taji hankalinta ya kwanta sosai ta dau waya ta kira elizabeth ta hada mata ruwan wanka, tay wanka masu mata massage suka mata snn ta sauko kasa taci abinci ta koma dakinta taje ta zauna tanata karatu har saida tay bacci...she rarely pray sabida batama fara islamiya ba tukuna just few ayoyin sallah kawai ta sani guda uku falak da nasi da qul huwa as she was tougth by her father..
dagata dayan bangaren kuwa ammi babba tana zuwa dakinta tay sauri ta kulle kofarta kirif harda saka masa key snn ta aje babban ledar data shigo dashi din akan gado, jikinta harna rawa rawa kmr wata marar gaskiya ta bude ledan tasaka hannu aciki, one after the oda tahau fitowa da shu'uman magangunan mata da akeyisun da laƙanin shirka da sihiri da suka karbo wajen zinariyar mace.
she was sooo convinced cewa karshen matsalar ta da mijinta yazo kenan, wani shu'uman ruwane aciki ta fito dashi daga kwalba tana kakkafa kaffa dashi dan kuwa ruwan dake cikin kwalban shine jagoran aiki,
zinariya ta riga ta gaya mata in har babu ruwan nan toh duka sauran concotion din data bata bazasuyi aiki ba, garin magani ne kala kala har guda uku da wani busashen jini anyi shi yawani kangare kamar konannen kilishi
zinariyar mace tace "har saita zuba ruwan kwalban nan a regular herbal tea dinda bappa zaidu yake yawan sha da safe while ruwan yana tafasa, snn ta tabbata yasha sosai kafiin nan sai tafara masa barbaden garin maganin akowani abinci da zata bashi har sai ya kare, shikuma busashen jinin a miya kawai zatana yankawa tana sawa har sai ya narke sann taje tabashi yaci.
zinariya tace mata muddin tay wnn abun daga ranar bappa zaidu zai mance fatima snn zaina jin magananta sosai kamarma itata haifesa haka zai dawo yana mata biyayya har akan gado, haka kuma still zai bude mata bakin aljihunsa, sai abunda taga daman deba daga kudinsa, ta tabbatar mata da cewa ko duka ribar busneses dinsa da salarynsa tace ya dauka ya bata duka haka zaidinga batasu batare da yacire ko asi aciki ba..
tsabar zinariya ta ci alwashi da wann hadin yauko sisinsu bata karba akan wann maganin ba,cewa tay suje sai sun gwada in aikin yaci snn sukawo mata kudinta 10million naira ne in cash. inkuma suka lalata aikin da kansu still zasu biya ta dan bata daukar asara.
ammi babba was very careful wasu abubuwn ma awayarta ta rubuta dan karta manta, abu daya ne ya rage mata dan tariga tasaba in sun samu matsala da mijinta irin haka batakai masa abun karyawa da safe, yadda tay masa borin hauka yau gani take kmr intakai mai shayin gobe da kanta bazaisha ba..
shiyasa tun ahanya ta gama lailaya hakan aranta kusan ma abunda yasa take neman sultana kenan, tattara duka magunguna tay ta aje su a very safe place acikin drawerta ta kulle da key, iyaka kwalba me dauke da muhimmin ruwan ne ta bari akan table, daga nan cire kayan jikinta tay tasss tafada wanka tafito ta kalkale jikinta da gyara snn ta saka wata shegiyr doguwar silk nity green colour irinna manyan mata...
lokacin already karfe goma saura ya karato zama tay agaban madubinta tana karewa kanta kallo tana baza wata irin shu'uumar murmushi da tunanin yadda zata baza baqar mulkinta akan bappa zaidu inhar maganin nan yaci. daga kan ibaad, har ayaanah duk ta sakasu a list din wayanda zata saka bappa zaidu ya walaknta su yaci musu mutunci kafiin ya musu korar kare a gida.
atake tafarajin wani farin ciki aranta tanajin cewa zuwa next week by now gidan nan daga ita sai y'ayanta babu wasu bare.
tajima tana zaune acikin wann tunanin har saida ta jira12pm yay yadda tasan duk tsiya mijinta ya dawo gida kuma kowa yaje dakinsa by now ya kwanta...
atafannin su sultana kuwa tunda takai ayaanah dakinta bisa umarnin ibaad gabaki daya ta kasa gane kan yarinyar, dan daga ta zauna sai kagata takure kanta agefe daya tayita kuka ahnkli har tana jan sheshheka me zafi, like sumtin is really eating her up nd paining her duk saika rasa meke asalin yawo akwalwalr ayanaah.
magiya da rarrashin duniya sultana tay mata amma takiyin shiru, kuma ko ta mata magana batacewa komi sai dai kuka, abun dik ya dame sultana har saida tafara cemata zataje ta kira yaa ibaad yazo kafin wani abun ya ragu har suka kwanta.
ahakama taki tasaka nity da sultana ta bata da kayan jikinta ta rakube agefen gadon tay lumui cikin takura jikinta waje daya...
bayan ta nitsu dakin was dead silent for a bit haka sultana tabar mata wutar bedside lamp din gefenta a kunne dan kar taji tsoro daganan hartay bacci ayaanah bata saka ranar runtse ido ba
12pm na dare na cikawa ammi babba ta fito cikin sanda gashi gidan yay wani irin shiru banda karar aircones babu abunda kakeji koina ya dau qamshi da sanyi sosai...
babban kitchen ta nufa tabude spicess scrolls, ta debo zallan herbal spices na hada tea din da mijin nata yafiso tahau shirya komi in d ryt quentity ta zubasu duka a empty tea maker snn tarufe shi witout adding any water da zimman da safe sultana inta tashi zatay masa tea din, sai ita takai masa tasan inde yarsace takai masa tea da safen dolene yasha.
wucewa tay dakin sultanan danta tasheta a bacci snn ta jadadda mata hakan, snn tace mata idan zatafara tafasawa ta kirata ita tazo ta sama mata ruwan, wai ahakan wayo tay dan tasan lokcin ne perfect time da zata iya zuba maganinta acikin sauki batare da ciwon kai ba
kai tsaye ta kulle kitchen ta fara tafiya har takai dakin sultanan tabude ahnkli ta shigo da mamaki taga bedside lamp daya a kunne, itakuwa ayanah tanajin motsin shigowar mutum tay maza ta rufe idonta tay kamar bacci takeyi
cikin sauri ammi babba ta kunna general wuta tana ganin mutum biyu ne akan gadon yartan babu jira ta isa wajen da zafin nama tawani irin janye bargon kasa, tana ganin ayaanah kusa da yarta akan gadon sai taji ranta ya harzuka yay baqi qirin....da har ta miqa hannu zata jawota kasa tay wurgi da ita sai ta tuna cewa she dont have time for creating a scene dat may cause her attention tafiso ne kawai tay focusing akan maganin nan.
tsaki me kauri taja ta dauke idonta akan ayaanah snn ta koma gefen sultanan ta zauna daf da ita gently frailing her soft hair da fingers dinta tana shafa mata fuska harsaida ta farkan da ita...
suna hade ido acikin gigin bacci sultana tace "mummy? ammi babba tay murmushin yake tace "yes my baby.. na tasheki ko?? sultana tanakan mutsuka ido tace "yess amma yaushe kika dawo gidan mumy shine kika tafi ko abinci baki ajiye min ba., jawota jikinta tay tana peting inta tace "toh sorry..keee ni ba wann maganan nazo miki da shi bama. kinaji na? sultana tace eh" jawota jikinta ta dada yi snn tace" autana inaso ne gobe da sassafe kije kitchen zakiga na hada miki komi a tea maker saikiyi ma dadynki tea dinsa ki kaimasa har sashensa ki aje. toh zakiga bansaka ruwa ba, daga kinfito just come nd call me first, zanzo nasaka miki ruwan ke saiki dafa ki zuba a flask dinsq kikai masa snn karfa kice masa nina taimaka miki kikay tea din kinji?
da mamaki a idon sultana tace "toh..toh mummy amma inyace meyasa nakawo masa faa..yafa san ban iya tea din ba.
cikin zare mata ido tace "kedallah bazai fadi haka ba kefa yar autarsa ce. bakiga wai fushi dani yakeyi bane. i just want to be good to him, shiyasa nakeso ke kikai masa tea dinsa na safen yasha kinsan dai inbe sha ba bayajin dadin jikinsa ko wai so kike kiga yana yawan ciwo da tari??? da yaranta ayanayin sultana ta girgiza kai tace "aa..dan shafa kanta ammi babba tay tace toh yawwa autana na..sai naganki goben ko?akasale tace tohh mummy gudnite...
tana miƙewa ta kashe musu wutan dakin yay wani irin duhu snn ta fita ta laɓe kofar after like 10min data tabbata sultana tay bacci sai ta dawo cikin dakin da sanda tanufi wajen ayaanah direct tawani irin jawota akan gadon ta direta akasa with strong hatred nd hostility
mummunan bugawa zuciyar ayaana yay da tsoro ta bude baki arazane zatay kuka acikin duhun ammi babba tace"sai inci ubanki kika bude min baki har ke waye da zaki kwanta akan gadon yata shegiya kawai jahila walakantacciya...
maza kwanta anan akasa dan ubanki..anan zaki kwana babu wani bargon rufuwa da zaki samu tunda ba ubanki bane ya siya mata...
hawaye masu zafi na sauka a idon ayanaah jikinta na matsanancin rawa ta sulale kasa akan cold floor din ta kwanta a mugun rakube tana hawaye sosai..
tsaye ammi baba tay akanta harsaida taji tay shiru ta kwanta akasan snn ta kama hanya tay waje.
the house was quite for a while kowa na bacci a dakinsa, washe gari kiran sallan farko alarm na sallan fajrr yay buzzling amma sultana bata farka ba, sanyin asubuh yasa ayaanah was soo soo cold gabaki daya sai taji fitsari na damunta
miƙewa tay akasan ta shiga bayin da lalube jin bayin da dumi yasaka bata fito da wuri ba, datay fitsarin kawai ta nemi waje ta zauna a rakube tanata jira akira sallahn fajr din saitay alwalanta mai gaba daya saita fito..
tsabar zumudi yasa ammi babba farkawa ana daf zaa shiga masallaci, dake she is damn sure ibaad shine maijansu sallah a anguwar tasan duk da wuri mazajen gidan nata suke fita masallaci
it was the perfect time for her to strike,saida ta bari duk mazan sun fice masjid, snn ta sauko marmaza ta bude drawer ta dauko kwalban maganin datake kafa kafa dashi kamr kwai, not forgeting dat ance inhar tay wasa da wann ruwan dake cikin kwalbar tokomi da aka bata ya lalace kenan. with immense care ta rikosa a hannunta tayo hanyar dakin sultana dan ta tasheta a bacci tun kafin kowa ya dawo.
tana bude kofar dake dakin da duhu lokacin kuma ayaanah tay alwala cikin lalume ta fito acikin duhun batama ganin gabanta sai dada zulmuwa cikin duhun takeyi tana lalaume tanamai neman inda zata kunna switch
wani gamuwar kicibis sukayi da ammi babba jin sun riko hannun juna cikin mugun tsorata ammi babba tadaka wani ihu cikin tsilla wata uban tsallen bazata a mugun mugun tsorace ta sake kwalban maganin kasa sai faasssss faassss ya fashe ruwan maganin ya zuba yana malala agaban aayanah ....
DAN ALLAH ATAYANI SHARE..
COMENT HEAVILY SO THAT WE CAN POST AT NIGHT
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025