ABUNDA KE 'BOYE...

21

by @surayyahms

⏯️2️⃣1️⃣

Abunda ke Ɓoye💫#surayyahms

Dawani irin karfin razana ammi babba ta furta nashiga uku na lalace arikice tay sauri sauri takunna main wutar dakin wajen ya kaure da haske, jikinta har na rawa rawa idonta atake yay jazurr akasa ganin yadda kwalban ruwan asirintan datake kafa kafa dashi ya fadi ya tarwaste akan tiles din yay raga raga ga ruwan maganin ya zube kafff kodis bai raguba har yana wani malala ata kafar aayanah.

in total disbelieve nd shock tarusa ma ayaanah wani irin gafalalliyar ihu me girgizarwa wanda yasa saida yarta sultana tafarka abacci a mugun gigice tabi tafado kasa dagakan gadonta timm wanda tsabar buguwar datay saida takasa miƙewa tsaye.

jikin ammi babba na rawa har kamar zatay fiffika ta rike kirjinta datakeji kamar zai kama da wuta tace "kutuman uban can, me zan gani haka..wayyo na shiga uku na..wayyo Allahna na shiga uku na lalace...

hannunta ta dora aka hartana rawa rawa kamar meijin fitsari tanaji brain inta na ringing mata million goma, million goma ya zube akasa... tadada kallon fasasshen kwalban glass din amugun raunace tace no no nooo noo nooo this cnt be happening to me, ahaukace tace...toh wallah yau za'ayi mutuwa agidan nan...dan bazan dauki asaran nan ba!!!!

da wani irin gingimmen hasala tadaga jajayen idanunta da suke nan kamar zasuyi aman wuta tsabar bacin rai takalli aayanah da already tamugun tsorata ta kangare atsaye tana hawaye sosai...

cikin daka mata wani irin hargitsatsen ihu mai tafe da zazzafar huci tace.."keeeee, Dan bura ubanki kika fasa min abuna??kinma san me kika fasa kuwa yar bura ubaa shegiya jahila walakntacciya mai kama da aljanu..¿

arazane sosai ayaana tafara komawa da baya baya sabida mugun birkicewan dataga ammi babba tay da fushi ayayinda sultana taketa kkrin miƙewa tsaye a mugun tsorace....

kagewa muryan ammi babba yay tsaban zafi da tuqiqin baqin cikin datakeji aranta musmn inta tuna cewa bayan asarar magani ga kuma biyan million goma cass da ya kamata jitayi kmr ranta aka fasa...

numfashinta na sama tana wani irin kyarma kafin kace wani abu sai zirrr hawayen baqin ciki ya fara sauko mata a idonta,...

cikin zazzafar huci da kukan baqin ciki daya faso mata abazata tahau dakawa ayaanah tsawa tanacewa wallah wallah sai na hallaka ki, in yau kikaga baki ganki a lahira ba toh babu shakka mutuwa nayi sai na kasheki na kashe banza wakantcciya kawai

kafin ayaanah ta kwaco kanta daga shock in mugun razana data shiga ammi babba ta wani irin wuff ta fixgota irin fizgowan mahaukatan nan

razanannen ihu ayaanah tafasa jin da karfin tsiya ammi babba takai mata mari, ta sake kai mata mari, sai data kifar da ita akasa. sultana tay sauri cikin tsoraccen kuka tay gudu tazo ta rusuna kusa da ayaanah zata dagata wani irin jifa da ita gefe ammi babba tay tanayin wurgi da sultanan gefe tazage karfinta ta kai ma cikin ayanaah naushi mai karfin tsiya saida ta hadata da jikin bango...

ayaanah tana ihuuuuu

sultana ma na ihuuu cikin tsananin firgici take cewa "ayaanah ki gudu ki kigudu tafara jan jan rigar mamantan a rikice mummy mummy kibarta mana mummy kidena dukanta wallah zan hadaki da babaaa mummmy meyasa kike dukanta haka metamiki dan Allah

ko jinta ammi babba batay ba dukan ayana ta dingayi da hannunta tana jajjan dogowar gashinta tana hadata da bango duk tabi ta hanata motsi atake jini yafara fita abakin ayaana sai ihu take tana kokrin kufcewa still bata hakura ba ta cakumo wuyarta ta danneta ajikin wadrobe tabi ta shakureta kamar wata saa'rta tana dura mata wasu jiga jigan ashariya tareda jin mugun zafin million gomanta da ta sata tay asararsa abanza ynxu..

ayaahna na kukan fitar rai tana kkrin fighting dan ta gudu itakuma ammi babba ta damke ta gam gam tana huci hawayenta na zuba tanata zage zage da bala'in karfi..

wanda ihun datake ma kadai ya isa ya gigita su, sai cewa take wallah wallah wallah saina kasheki dan baki isa kimin wann uban asarar na kyaleki ba, ke waye? waya aiko ki kixo kiga bayana? toh kijje kice musu wallah kunyi kadan kun kasa dake dasu duk baku isa kuga bayana ba. ..

a mugun tsorace sultana take rawan ɗari dari musmmn dataga muryan ayaana ya dena fita tsabar shakure mata wuya da ammi babba tay idonta saida ya juya yay fari solll tana neman numfashi dakyar..

sultana ta zube kasa ba acikin hayyacinta ba tadinga neman abunda zata gwada ma mum dintan amma batasamu ba, bakaramin razana sultanan tay ba tanata rabza firgitaccen kuka

tanayi tana ihu ma mummyn nata amma inaaa, data ga kmr haikan zata kashe ayaana a 360 ta tashi fice da gudu kamr mai aljanu tabar dakin tanata kuka maikara duk gidan saida ya dauka da muryanta...

tsabar ta razana batama san sanda ta isa sashen ibaad ba

duka daya tay ma kofarsa ya budu tafado cikin dakin arazane tana kuka tana haqi tana kiran sunansa da karfi yaaa ibaaad... yaa ibaaad.. yaaa ibaad

ganin babu kowa a dakin yasa tasharo kwana ayanayin datake

dawani irin speed ta sauko kasa daga nan tay kofar waje babu takalmi tana wani irin ihun razana tanamai kwala sunan ibaad da karfi kaman zatay fitsari a jiki.

atake security da sukaji ihun ta suka fiffito lkcin an fito daga sallahn fajr knn bappa zaidu na baya, maheer da ibaad na gaba sultana ta wuce securities pheewww da mugun gudu daf zata bude main gate ta fita can waje kenan taci karo dasu duka ukun abakin kofar, she was shaking, crying nd panicking at same time...

in total shock suka tsaya kallonta idonta a rufe cikin numfashi take nuna hanya tana cewa "yaaa ibaad, yaaa ibaad..baba.. baba...yaa ibaadd.."maheer yay saurin rikota jikinsa da karfi yana cewa sultana sultana meyafaru? da tashin hankli bappa zaidu ya kwacota jikinsa yace "calm down sultana kigaya mana meyafaru???wayo koroki haka...

cikin kara fashewa da matsanancin kuka tace "baba mummy ne.....

..mummy ne kawai tazo dakinmu ta dinga dukan ayaanah tanata duknta kuma tace wai ai zata kasheta kuma ta matse mata wuya ta shakure mata wuya da karfiiiin tsiya sai dukanta take kanyi acikinta

..kusan a rude maheer yace what???? wani irin jan zuciya sultana tay sai luiii ta fado jikin bappa zaidu ya riketa jikinshi harna rawa rawa kusan atare sukacewa innalillahi wa inna ilaih rajiun.

ibaad bai kara scnds daya awajen ba jin kirjinsa na bugawa da mugn karfi kamar zai faso waje da saurin dayay kama da gudu ya shiga gidan idonsa kusan a rufe nan ma maheer yafara binsa a baya direct suka wuce sashen sultanan har suna rige rigen isa...

lokcin she was just bullying the girl tabi ta shakureta babu imani tana gaya mata irin yadda ta tsaneta da kuma dumbin asarar data mata ynxu wanda tace wallh sai ta kashe akai babu makawa...

kusan atare suka fado dakin kamar anjefosu, da gudu maheer yazo ya damketa ibaad kuma ya fara kokarin raba hannunta da wuyar ayaana wani irin birkicewa tay taturje musu tana ihu tana zage zage tana cewa "kubarni na kasheta,

..wallah saina kashe ta...ku kunsan asarar datamin ne.. wallah babu wanda ya isa yahana ni kasheki anan gidan shegiya kawai mayya walakantacciya

Dawani irin zuciya ibaad ya mata damka daya tareda finceke hannunta a wuyan ayaanah agarin zai riko ayaanah jikinsa yabi ya tureta akasa timmm ta fado taci da baki akan fasashen kwalban maganin tafadi ta buga bakinta da kanta wanda atake suka fara jini, maheer yay sauri yabi ya danneta akai yana kokarin janta baya suna kokawa a rikice, haka fasashen gwalaben nan yabi ya yayyanka mata jiki da hannunta sosai sai ya zamo kamar yayanka da reza akai..

da ihu take cewa zanci ubanka maheer inba ka sakeni ba, maheer ka sakeni, maheer kasake ni nace maka wai ina wasa dakai ne...??? ka tashi min ajikina, idan ka sake na tashi sai na maka dan bura uban duka maheerrrrrr ure hurting meee...

Da tsawa yace "mummy bazan sake ki ba, kina haukane..suka fara kokawa kamar ba uwarsa ba dakyar ta turesa ya buga kansa da jikin gado...ta miƙe da sauri ganin yadda ayaanah ta kankame ibaad tanata numfashi sama sama tana rabza kuka yasa tay kukan kura itama zata fincikota ajikinsa ba acikin hayyacinsa ba ya kara tureta tana miƙewa kuwa ta wanka masa wani gawurtaccen mari a fuskansa saida iskan wajen ya dauke cakkk

baice mata komi ba ya kara boye ayaanah datake sheka kuka sosai ata bayansa ta rike rigarsa gam gam tabi ta mannu dashi cikin matsanancin kuka da tsorata jin yabi ya tantameta da hannunsa kamar wacce zai mayar da ita cikinsa...

rada rada hannunta ya fito a fuskansa, sai ihu take tana cewa wallah sai anbiyata kudinta snn ta zata kyale yarinyr nan tana yi tana kai ma ibaad duka yana kaucewa...

ayanah gabaki daya ta rude dan kamar ita aka mara haka taji zafin marin da ammi tamaa ibaad din a fuskansa ta kara tantamesa tanata kuka..

ganin ciwonta yana neman ya tashi ibaad yafara yunkurin fitar da ita adakin, ammi babba tay babakere tace sam bazai fita da ayaana a dakin ba har sai anbiyata kudinta da aka mata asara idan ba haka ba sai ta kasheta

atake maheer ya shiga tsakaninsu, cacar baki ya kaure tsakaninsa da mamansan tana fada yana fada kamar zasu daga dakin da surutu, kowa yay zuciya.. suna cikin haka caraf sai ga bappa zaidu ya shigo rike da hannun sultana da itama din dakyar ta farfado, she had a mild nervous breakdown sabida tsabar tarazana saida yay da gaske snn ta dawo hayyacinta snn suka samu suka iso...

yana shigowa cuwon ayaaanah ya tashi with full speed tafara zufa tana numfashi sama sama ibaad ya rirrketa yana kkrin kareta daga ammi babba at the same time yana hura mata iska abaki..

kuka takey ahankli tana rirrikeshi, badon tsabar wahalan da ammi babba ta bata ba saidan marin dataga anmasa akanta wanda sosai yadaga mata hankli batare da tasan dalilin hakan ba..

haka ya tsuguna kasa da ita yana kkrin bata emergency help acikin hayaniyan nan in oder to make her stay counsious abit kafin su wuce asibiti agaggauce

bala'i ne ya kaure tsakanin maheer da babansa da mamansa..

itace da lefi dumu dumu amma ta fisu daga jijiyar wuya duk da tasha maruka hudu ahannun bappa zaidu ammma haka takiyin shirun tana kuka tama zage zage...

duk ta kasa gaya musu asalin meyene ayaanah ta fasa mata take wann dan uban borin, ran bappa zaidu ya mugun baci, haka nan tasa zuciya ya debesa ya fatattakota har waje daga ita sai doguwar gown in nitynta kafarta babu ko takalmi "yace ta fice masa agidansa taje gidan ubanta har saiya nemeta...ko takalmi bai kyaleta ta dauka ba dama kuma ashe tun tale tale bata zo gidansan da komi ba.

kuka ta dingay security dingidan suka zagayeta da bindiga tanata bori tana cewa wai ita aka cuta,wallah wallah bazata yafe musu ba, fuskanta gabaki daya ya kumbura daga marin datasha ahannun mijin ta, kaga jikinta zaka dauka tay fada da damisane duk maheer ya kwarzana mata jiki da fashashen kwalba tafin hannuntu har yana tsitda jini.

ganin ayaanah ta dan fara farfadowa kadan yasaka maheer ya karaso kansu hanklinsa amugun tashe yakai hannu zai tabata ta firgita ta danna masa cizo ahannunsa ba acikin hayyacinta ba takoma jikin ibaaad ta bi ga kankamesa amugun razane tana kuka sosai

daukarta ibaad din yay cak idanunsa yay jaa sosai yace ma maheer ya rakasa suje asibitin he will try to keep her breathing harsu isa

babu bata lokaci maheer ya share hawayensa suka fito da sauri sauri ibaad yana rike da ita

daf lokacin anata tuka tuwon rigima da bala'i da ammi babba da security a tsakar compound bappa zaidu kam tuni ya kyaleta da securities din yashige ciki da sultana abunsa ransa yau bakaramin baci yay ba...he was soo tempted to write a full blown divorce for her har ya dauki paper da pen a desk dinsa amma daya tuna cewa babu kyau yanke hukunci irin wannan acikin fushi sai bai rubuta sakin ba

suna shiga motar ibaad ya zauna da ayaanah agidan baya maheer ya shiga driver seat.

wani dan uban waina motar yay da mugun karfi yazo da gudu kamar zai kaɗe ammi babba ta ruga a guje tay waje tana ihu security sukay maza maza suka tsareta acan..

dura ma maheer din ashar ta dingayi harsaida sukayi nisa snn ta hakura ta kama hanyar gida...

6.54 am sharp suka isa harabar al-eeman privte hospital maheer ne ya tsaya a reception yay cike cike, tru transfer ya biya kudi while ibaad ya wuce emergency da ita direct aka fara bata taimakon gaggawa.

ciwon sosai ya tashi mata har aka fara tunanin akaita ICU ranar sosai ibaad yaga tashin hankalin da bai y tsammanin zai gani ba, duk suka tsaya a kofar emergency gwanin tausayi hawaye na zuba a idon maheer yanabi yana sharewa cos he dosnt even knw what he is feeling abt his own mother ryt now, dan sam bai san wata irin mahaukciyar mata bace ta kawosa duniya..

daga bangaren bappa zaidu ya dau lokaci yana tambayar sultana abunda ya asalin faru, toh dake itama ba duka tasan manufar mamantan ba iyakan abunda tasanin kawai ta gaggaya masa, word to word abunda ta dinga ce ma ayanah, har da zuwanta dakinsun jiya datay da daddre ta mata maganan tea,da komi daya faru saida ta fada ma babanta dalla dalla..

lallabarta yay yamata nasiha har saida ta dawo hayyacinta snn yace mata taje tay sallah tay shirin schll yau shizai kaita dakansa ba driver ba..

tana ficewa ya kira su ibaad a asibiti bayan sun gama wayar atake ya kira waliyyin ammi babba, dake ransa har yanxu a bace yake babu wani boye boye ya kai kararta tareda cewa gaskiya shi zai saketa dan yagaji da tijara da abun kunyar da take masa agida..bata barshi ba, bata bar yayansa, bata bar danginsa ba, bare baki, ransa a mugun bace yace gaskiya azauna ayi magana idan ba haka ba saki uku zai mata ya kawo wacce zata rike masa yayansa dakyau cos raihanatu is no more setting any good motherly exmple to his children ..

jikin waliyyin nata bakaramin sanyin yay ba dan bappa zaidu bai taɓa kiransa ya gaggaya masa magana masu tsauri da nauyi haka ba...tun awayan ya babbashi hakuri amma yay shiru bai amsa ba har ya katse wayarsa yanajan tsaki..

shikuwa waliyyintan baiy ƙasa a giwa ba ya kira mahafinta ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, wasu maganganun ma awajen matarsa yakeji na yadda ake gulman yadda raihanatu take zuba rashin mutunci agidan mijintan tunba yau ba ..

yace ma babanta gaskiya suyi zama da yarsu adau mataki akanta dan yaga da Alama wnn karon kamar dagaske bappa zaidu yakeyi zai saketa kuma baya tsanmanin saki daya ko biyu zai mata tunda ya kawo batun karo aure.

wayarna kunnensa tun baisauke ba yaji sallamarta da sassafen ta shigo gidansu da kuka

mahaifiyrta dake daure mata gindi ita tafara fitowa da uban carbi a ahnnunta suna haɗe ido tay salati tafara tambayarta ko lpya taganta haka ahujajam babu mayafi bare takalmi?

wani dan uban kuka ammi babba ta kara fashewa da shi mamantan ta riketa da tashin hankli

dede ta budi zata fara magana kenan sai ga babanta ya fito fuuu kmar iska daga falonsa dawani makaken wayar wuta irin cable dinnan bai wani tsayajin me zatace ba amugun harzuke ya cakumota ya hau chauda mata cable din ajikinta yana cewa tunda ke kin nuna ma duniya ke karamar yarinyace zakisan cewa kuwa baki karfin duka agidan nan ba..

wani dan uban ihu takey tafadi kasa agigice tana murkusus tana cewa wayyo Allah na baba dan Allah kay hakuri wallah ni aka cuta..baba nice me gaskiya

gashi dogon nity ne ajikinta mai tsantsi kamr satin innan ya dan kame dirin jikinta sai feywww fewww taji duka na shiga jikinta kota ina tsabar zafin datakeji

kamar zata suma haka take birgima ya hadata har da uwartan ya masifesu yace mata tay waje tunda ta iyayin rashin mutunci da hauka wa mijinta toh badai ta zauna masa agidnsa ba saidai tafita taje pyschtri wajen yan uwanta mahaukata tacigaba da rayuwa.

duk surutu da borin da mamanta tay bai kulasu ba...haka kuwa ya mata rashin mutunci ya koreta agidan yasa aka kulle masa gate dinsa..

karshe gidan kawunta wanda shine waliyyinta dayake da mugun zafin ta wuce wanda kafin ta isama zazzabi me mugun zafi ya rufeta, badon da taimakon saka bakin matarsa ba nan ma da korarta zaiyi dan wncn karon ma datay yaji shine yaje har gida ya bawa bappa zaidun haquri aka maidata...

abun duniya ya taru ya mata yawa, saida aka kira nurse tazo gidan tasaka mata ruwa, duk iyayenta maza suka dau zafi sosai...matan ne suke zaune tare da ita...

wanda yake matsayin shine mahaifinta yace muddin ta bari mijinta ya saketa saiya tsineta mata dan haka tafa san yadda zatay tashawo kansa tun basu kai ruwa rana ba.

kawuntan kuma yace abarta agidansa har sai ya garata kafin asan me zai faru agaba. tunda ta kwanta a dakin kuka kawai takey tana dan danasanin faruwar komi gashi tabar wayoyinta duka a gida batasan taya zata kira aminiyarta ta gaya mata kalar iftila in daya fado mata ayau ba. ita ba magani ba, ga asarar million goma ga mijinta da yayansa sun dau zafi akanta sosai..

bangeren su ibaad kuwa har angama shirya ayaana za aikata ICU a dorata da ggawa akan oxygen sai kuma condition in nata yay subsiding miracously numfashinta ya dawo daidai..

dede lokcin bappa zaidu ya aje sultana a school, kafin nan yazo asibitin ya samesu nan aka sanar da shi duk abunda yake faruwa, after much talk with the doctor ya biya kudi for exra heart specialist consultancy da za'a iya samu agaggauce..

bayan bappa zaidu ya gama abunda zaiyi anty hauwa ce ta rakosa har waje snn ya wuce office abunsa dan gaba daya jiyake kamar he is not in mood for everthyn yau.

anan asibiti su ibaad suka zauna harsaida akai yan kwaje kwaje aka tabbar da komi lafya snn aka bata private room akan asibiti zasu riƙeta anan for some days for further observations.

sai wajajen 10:30 kafin komi ya lafa, maheer ya fita yaje ya siyo musu breakfast wanda kwata kwata ma dan kadan sukaci suka kyautar da saura, can sai ibaad ya tashi yafice da wayarsa a hannu ya kyale maheer din yana zaune akan kujera kusa da ayaanah datake kan bacci baiko gama karasawa reception ba suka ci karo da mahaifiyarsa...

#SURAYYAHMS

idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata

AREWABOOKS

@SURAYYAHMS

WATTAPAD @SURAYYAHMS

WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER *** TO BE ADDED

#SURAYYAHMS

#COMEBACK SERIES

2024/2025