KUNCIN ZUCI

Kuncin zuci

by @bintuuu

Isarsu gida suka samu Anty Amnah tazo, sunzo saboda bikin itada 'ya'yanta twins, ihun murna twins suka fara ganinsu Na'iman sai suka nufesu da gudu Na'ima na ware musu hannunta suka maqalqaleta, Nafisa na kallonsu tace "Yarannan kun gama yayi na wato" Mami da Anty Amnah dake zaune a falon sukayi dariya Anty Amnah tace "Boys babu amana" zama sukayi nan falon bayan sun gaisa Anty Amnah take tsokalan Na'ima wai tayi qiba, tayi dariya tana jin duk wani tunani da ta kwaso gidansu Laila yana washewa.
Har dare Anty Amnah na gidan sai da sukayi sallah sukayi dinner sannan ta kira driver ya maida ita gidanta dake nan Abujan wanda suke sauqa in sunzo qasar.
Daren ranan bayan Na'ima ta gama shirin bacci cikin riga da wando dogo ta saka hula akanta ta fice zuwa falon Mami sanin cewa mazan gidan basa gurinta by now, bata samu Mami a falon ba ta qarasa cikin dakin ta ganta a duqe gaban bedside drawer tana bincikawa, qarasowa cikin dakin Na'ima tayi tace "Barka da dare Mami"
Mami tadan dago tace "Habibti, bakiyi bacci ba?" Na'ima ta amsa da "Eh" ta zauna bakin gadon Mamin ta sake cewa "Abu kike nema ne Mami" sai Mami tace "Wai fa nayi ajiya ne na manta specifically inda nayi ajiyan" ta qara da "Lantana ta qara soya muku gyadan ku yananan a kitchen" Na'ima ta gyada kai tace "Har munci ma" 
Tananan zaune Mamin ta miqe ta wuce toilet sai Nafisa ta shigo tace "Nan kikayo?"  ta gyada kai, Nafisan ta zauna kan gadon itama ta zubawa Na'ima chocolates masu dan yawa akan cinyanta, ware Idanu tayi za tayi magana kenan Mami ta fito daga toilet idanunta suka sauqa kan chocolates din, Nafisa da batayi expecting ganin Mami a dakin ba ta ware idanu tace "Laaa Mami ashe kinanan, nazata kina kitchen fa"
Mami ta harareta tace "Shiyasa kika shigo da abunda na hanaku sha din kenan" Na'ima ta juya kanta dariya na taho mata, sai Nafisa ta fara dariya tace "Wallahi Mami tun safe bamu sha ba sai yanzu" Mami ta wuce gurin wardrobe zata dauki abu tace "Ya muku kyau, ku cigaba" Atare suka bata hakuri bata kulasu ba ta fita daga dakin. Nafisa ta juya ta daka duka a cinyan Na'ima, sosa gurin Naima tayi tana dariya tace "Auchh..to ai zan miki magana naga ta fito daga toilet din".

Hiransu suka zauna nan dakin Mamin sunayi, Nafisa na pressing wayanta, can tayi wani tsuka mai karfi tana kallon wayanta tace "Ni na taba kallon yarinya mara zuciya da aji irin yarinyar nan kuwa" Na'ima na kallonta tace "Me kuma ya faru?" Nafisa ta miqe zaune ta miqo mata wayan a fuska tace "Laila mana, kiga post dinda tayi a IG, ke yanzu wannan yabmiki kama da hannun Yaya Ahmad dan Allah" shiru Na'ima tayi tana kallon wayan wanda hoton hannun mace da namiji ne sarqe cikin na juna dan ba sanin hannun Ahmad din tayi ba, sai tace "Nafisa ni kuma Ina nasan yanda hannunsa yake?" Nafisa tace "Nidai ko kaffara bazanyi ba wannan ba hannunsa bane,byaushe ma ya dauki kiranta balle har ya kai da riqe hannunta" Na'ima tace "To ke me ruwanki in ma hanunsa ne, ba budurwarsa bace, meye na rantsuwan" Nafisa ta dan harareta tace "Waa? Yaya Ahmad din? lallai bakisan wannan ba, anfada miki yanada lokacinta ne...ke har matan ma in general, harkan kudade kawai yasani wannan kowama yasan haka" Na'ima tadan kyabe baki tanajin wani iri aranta batace komai ba Nafisa ta cigaba da maganan tace "Har da wani love caption, Eh lallai Laila" ta qarasa tana dan dariya ta sake miqa wayan fuskan Na'ima tace "Kiga caption din har da hashtagging din sunan Yayan fa" Na'ima ta kauda idonta daga kallon wayan jin ranta na dan baci babu dalili tace "Amfanin me kallon zemun, kinada problem wallahi Nafisa" Ta juya ta jawo blanket din kan gadon Mamin tayi kwanciyarta, ganin abunda tayin like she's not interested in the talk yasa nafisa daukan pillow ta kwada mata, fashewa da dariya Na'ima tayi tace "Allah kedin ce ai Nafee, hiran is not productive,bI don't see why kike tada jijiyan wuya" sai Nafisa ta sauqa daga gadon tace "Bazaki gane bane" ta qarasa maganan tana fita daga dakin Na'ima ta bita da kallo tana tunani aranta kan meyasa ma zataji wani abu a ranta game da hiran to, after all batada hadi da kowanne cikin mutane biyun, bata dade da fara bacci ba Nafisan ta dawo ta kwanta, nan dakin Mamin suka kwana ranan.

Lokacin bikin yana ta matsowa and Na'ima is not even interested in it, itadai ta dawo gida domin ta ga su Mami ne daman bawai bikin wata Salma can da bata santa ba.
Da bikin ya zama saura kwanaki kadan Meerah ta aiko musu da kayan nasu, kaya sunyi kyau har Abba saida aka nunawa
Nafisa ta kaisu salon akayi musu qunshi aka yiwa Nafisa kitso while Na'ima tace bata so aka gyara mata gashin kawai.

Cikin week din bikin Nafisa tace suje can gidan bikin Na'ima ta jijjaga kai tareda cewa "A'a bazanje ba Nafee sai ranan auren" kuma Mami ta yarda da hakan a lokacin da Nafisa ta kai qaran Na'iman wajenta.
Haka Na'ima na gani Mami suke zuwa gidan bikin tace ita sai ranar auren zata je..Ana gobe auren duk 'yan gidan sun tafi can gurin event aka bar Na'ima ita kadai da Lantana, girki suka yi bayan sun gama Na'ima ta wuce dakin Mami ta debo kayan ta na laundry sannan ta shiga dakin Nafisa ta debo nata ta wanke su tas a washing machine
Har dakin Abubakar ta shiga dake nan falon downstairs ta gyara masa ko ina, she kept herself busy sunata hira da Lantana.
Sai dare Faruk ya dawo dasu Mamin, sun shigo lokacin tana sallah a dakinta bayan ta idar ne ta tafi gurinsu nan falon Mami suna zaune, shiganta dakin Mami tace "Habibti ya zaman shiru" ta qaraso ta zauna gefen Mamin tace "Sannu da dawowa Mami" 
Mami ta amsa da Yauwa, Nafisa dake gefe azaune kan kujera itada Faruk bayan ta chanja kaya, tace "Husna tace in bakije ba gobe dakanta za tazo daukanki" Faruk yayi murmushi yace "Meyayi zafi, kamar abun dole" ya kalli Na'ima yace "Habibtin Mami kiyi zamanki ma in goben bakyason zuwan" Na'ima tayi murmushi tace "Toh Yaya" ta qarasa maganan tana dan ware Ido ma Nafisan alamun "To dai kinji" Nafisa tace "Wallahi baki isa ba sai kinje, in ban ciccibeki na kaiki ba" Mami da faruk sukayi yar dariya tace "To fah" ta juya tana kallon Na'ima tace "Habibti kinci abinci dai ko" Na'ima na dariyan Nafisan ta gyada kai tace "Eh Mami, akwai naku a dining ko a kawo muku nan" Mami tace "barshi mu huta tukunna" 
Faruk sai kallon Na'ima yake ganin she was openly herself these days, harda tsokala wanda a farkon zuwanta gidan she can go days batayi ko da murmushi ba.
Ranan ba'ayi hira a falon Abba ba, kowa ya tafi makwancinsa da wuri a huta gajiya.

Washegari da sassafen Mami ta tafi gidan bikin ta barsu suna bacci, Na'ima bata tashi ba sai almost nine shima yunwa ce ta tada ita ta sauqa yin breakfast sanye cikin purple color din kayan bacci mai laushi kamar cutton a jikinta, hularta tayi baya kwantaccen gashin goshinta duk ya bayyana, kitchen ta shiga tana tsaye bakin fridge Nafisa ta shigo itama da kayan baccin ajikinta tana miqa alamun itama tashinta daga bacci kenan, zuba madara Na'ima tayi a cup ta miqa mata, Nafisa ta karba tana kaiwa baki tace "Yaushe zamu shirya mu tafi, Husna called me" Na'ima tayi hanyar fita daga kichen din hannunta riqe da kofin madaran tana cewa "Nafee mu dan bari anjima mana, it's too early" Nafisa ta bita suka fita tace "Kinsan fa za muje wurin makeup dinnan" zama sukayi a nan dining zasuci abincin.

Basuyi nisa da fara cin abincin ba Faruk ya shigo, on a normal circumstances Na'ima ba wani damuwa tayi ba dan babu hijab a jikinta sanin cewa tana zama da normal kaya ko a gabansa ne dan kamar Yaya na jini ta dauki Faruk kuma shima bai damu ba, Amma ganin wanda ke biye dashine yasa ta daskare a wurin ta kasa kai cokalin abincin bakin ta aranta tana cewa "Yau kuma me wannan mutumin yazo yi da safe haka" because tunda ta fara rayuwa a gidan bata taba ganinsa ba sai kwanannan. 

Qarasowa dining din Ahmad yayi yana dan kauda idonshi daga kallonta ganin yanayin kayan jikinta.
Sanye yake cikin white polo shirt da blue jean shima in a casual way, ganinsu yasa nafisa cewa "Yaya, good morning" Ahmad ya zauna yace "Nafisa, kin tashi lafiya" Nafisa ta amsa tareda gaisheda Faruk sannan ta miqe ta fara serving dinsu abincin, sai Na'ima ta ajiye cokalin hannunta ta dan fara gyara hulanta da jelan gashinta masu tsayi suka qi komawa duka, tace "Ina kwananku" Faruk dake kallonta ganin how cute she looks, yace "Lafiya Na'ima, I thought kun tafi gidan bikin fa" Na'ima ta dan jijjaga kai tace "Sai anjima" Ahmad ya kasa jurewa sai da ya dago ya kalleta amma Na'ima taqi kallon gefensa,  murmushinsa na yau saida ya dan bayyana ganin still dai she can't look at him kuma baisan meyasa ba yake bidan ta kalleshin . 
Hira sukeyi sama sama suna cin abincin, Nafisa tace "Yaya anan ka kwana ne?" Ya dan jijjaga kai hankalinsa na kan abincin da yake ci kadan kadan, anutse yace "A'a can gidana na kwana" Faruk yace "Gidan baba was crowded i don't know how Yaya Adam is cooping" Ahmad ya dan gyada kafada yace "Wannan jama'a basa damun baccinsa ai" Nafisa da faruk suka danyi dariya. 
Na'ima dake jinta so uncomfortable under his Eyes yasa tun dazun idonta ke kan plate din gabanta bata dago ba aranta tana ayyana meyasa wannan bawan Allahn ke sa mata rashin nutsuwa ne, samun kanta tayi da dan dagowa tana kallon hannunsa hoton rannan da Nafisa ta nuna mata yana fado mata arai. 
Koda su Na'iman suka gama yin breakfast din bata tashi ba har seda Ahmad ya tashi suka nufi falon Abba sannan ta miqe tafara taya Nafisa tattare wajen.

Bayan sunyi wanka suke shirya cikin simple attire, Nafisa ta saka musu kayansu cikin bag suka wuce gurin makeup din.
Sunyi kyau sosai bayan angama make up din barinma Na'ima kamar ka sace ta, ankon daya kasance na lace ba qaramin haskata yayi ba.
Isarsu gidan bikin bayan sun gaisa da mutanen da suka idda a main falon gidan sai suka wuce part din Mamma dan Nafisa tasan acan zasu samu Mami, aikuwa ta na zaune tareda wasu yan'uwansu manyan mata, bayan sun gaisa dasu, Nafisa ta jasu dakin Salma 
suka samu 'yan mata a dakin kowacce na yauqin ta isa, Husna da Salma basa dakin sai Laila da qawayenta sun hakimce kan gadon Salman, Nafisa na kallonta tace "Sannunku..Laila Ina Husna?" ta amsa dakyar "Bansani ba" zama suka yi kan tsabtacaccen carpet din dake shimfide a dakin, Na'ima daman bata kulasu ba tayi zamanta ko kallonsu batayi ba.
Laila ta kallate sannan tace da Nafisa "Yar zaman gidan naku bata tafi ba kenan" Nafisa ta juyo tana dan hararanta tace "Bangane ba, what do you mean?" sai Laila ta kyabe baki tace "Wannan ta kusa da ke din mana" Nafisa tace "First of all sunanta Na'ima and secondly, I'm in good spirits yau dinnan Laila karki batamin rai dan banida lokacinki" kafin Lailan ta amsa Luba dake zaune gefenta tace "Ha'a taga bare a cikinku ai dole tayi magana" a fusace Nafisa tace "Sannu Lubabatu, sannu 'yar'uwarmu ta jini, kinga idan ina magana ta hankali ki daina tsomamun baki, ke asuwa?" sanin masifan Nafisa yasa Luba juyawa tana tsuka me qarfi, cike da tsiwa Laila tace "An fada din bare, dan wannan farin nata ba ta inda kuka hada jini da ita" Nafisa ta miqe Na'ima tayi saurin riqo gyalenta, ranta ya sosu da wannan maganar da suka fada har hakan saida ya nuna akan fuskanta amma ta danne tace da Nafisa "Mu fita Nafee" ganin yanda bacin ranta ya fito fili yasa Nafisa batayi musu ba ta jira miqewan Na'iman suka nufi hanyar fita daga dakin, 'yan matan dakin da suka tsaya kallon draman suka bisu da kallo, Laila tayi tsuka tace "Gwara ku fitan dan nima banida lokacinku" wata qawarsu tace "To ke Laila me farar yarinyar ta miki?" Laila ta kalleta a fusace tace "Babu ruwanki".

Haka na'ima tayi wunin gidan bikin ranta duk babu dadi dan Nafisa ta zage itada Husna sai bidirinsu sukeyi, Na'ima ta qi binsu haraban gidan da ake taro ta na zaune a main falon gidan riqe da yarinyar Anty Fatima immediate sistern Ahmad, sai wasa yarinyar take da dankunnen Na'iman.

Bayan ankai amarya tare dasu can gidanta dake cikin wata shahararriyar unguwa cikin Abujan, suna zaune cikin Mini falon amaryan Na'ima tace "Nafisa ki tashi mu tafi" Husna tace "A'a ku bari ango suzo mana" sai Na'ima ta dan bata rai sai kuma a hankali tace "Har sai mun jirasu?" kafin Husna tayi magana Nafisa tace mata "Kinsan jaraban Na'ima kuwa, muje naji anty Amnah tace zasu tafi yanzu dan har ta kira za'a zo  daukansu" Miqewa Na'ima tayi jin haka dan duk a taqure take a gidan gashi ta gaji, gurin su Anty Amnah Nafisa ta kaita, Anty amnah tace "Gaskiyarki Na'ima bari mutafi tare, barsu su gama rawan kansu" Nafisa tayi dariya tace da Na'ima "To sai na dawo" da haka ta koma upstairs.
Sunanan zaune aka kira Anty Amnah, bayan tabgama magana dana dayan bangaren ta kashe wayan tace "Tashi muje Na'ima mai daukanmu yazo" ta qarasa tana fadawa wata mace dake gefenta, miqewa sukayi Anty Amnah ta sake cewa "bari muyi sallama da amarya" sannan suka wuce upstairs, Hanyan waje Na'ima ta nufa akan zata jirasu can gurin motan, fitanta ta hango wata black mota a haraban gidan ga light dinta a kunne, qarasawa tayi tadan tsaya ba daf da motan ba, nacikin motan ya bude ya fito yana kallonta, dan riqe numfashinta tayi kadan ganin Ahmad.