GIDAN Y'AN BARIKI

Chapter 7

by @pinkyjay


*PAGE* 1️⃣3️⃣▶️1️⃣4️⃣


Suhana ta ɗaga muciya Jidda na isowa ta kai mata duka a gadon baya, su Lili ma haka sai cin uban su Farida suke Afiya saboda jangwalo masifa har Hajiya Uwani ta kaiwa duka a hannu, Suhana kuwa ta haye kan Farida sai jibagar banza takeyi, duk ƙibarta ta kasa kwatar kanta, a hannun Suhana, 

banda ihu babu abinda suke su Lili kuwa sai jibagar banza sukeyi saida suka haɗa musu jini da majina, kana suka janyosu waje kamar kayan wanki, Suhana ta kalli Hajiya Uwani tace "To tsohowar banza me halin banza, ko gobe ki kwaso wannan gayyar tsiyar kuzo kiga yadda zan lallasa muku fata.!"


Lili tace "Ai ki bar bahamagiya idan ta ƙara wannan kuskuren saina na zubar mata da haƙora!." kana suka shige ciki suka bar su Jidda na jan ƙafafuwansu da ƙyar saboda azabar duka, koda suka ƙarasa part ɗinsu Maryam ta dawo hospital, da kallo ta bisu yadda suke tafiya ga jikinsu duk ya kumbura,

lips ɗin Jidda duk ya kumbara kamar ba ita ba, Farida kuwa gaba ɗaya Suhana ta sauya mata haliltar fuska, Hajiya Uwani tace "Maryam taimaka ki duba min Ƴan Uwanki, idan waɗannacen karuwan basu halaka min su ba."

cikin mamaki Maryam tace "Me ya samesu ne Mommy.?" Nan ta kwashe komai ta gayawa Maryam dariya ce ta kwace mata kana tace "Amma wallahi Mommy bakuda hankali, ai yanzu an dena ya yin wannan shirme, amma koda yake kunyi nisa ba kwajin kira, Allah bada sa'a ko gobe ku ƙara!." 


ran Mommy ne ya ɓaci cikin taikaci tace "Wallahi Maryam ki fita idano saboda ke mayar dani sa'anki shine zaki tasani a gaba  kina gayamin magana, ni narasa abinda ya sauya ki." Jidda tace "Dukan Ya Sultan ya sauya ta ke manta lokacin da yana cikin wannan haukar ai har masu aikin gidan nan gardawa da su amma dukan tsiya yake musu,


kega ni Wallahi Mommy bazan koma bin shawarar ki ba jifa yadda ta fasa min jiki kina kallo bayan kece kika saka mu nace ki bari muyi hayar ƴan iska suzo su ya galgala ma na ita kikace ai bata da wani ƙarfi saboda bata da jiki, mun isheta, saiga shi, ta watso mu kamar shara." Farida tace "Ai mun auna arziki da Sultan baya gidan da yau sai na lahira yafi mu jindaɗi, 


saboda har yanzu ban mata marin da ya yi min ba sai da na dena gani na kwana biyu.!" Dijah ce tace "Please ku rabamu da wannan surutu Maryama duba min lafiyata kafin mijina yazo ɗaukata, ni bansan ma tsautsayin da ya kawoni gidan nan ba idan Daddyn Mu'azam ya ga hannuna me zan gaya masa.?" 


Babbar Yayarsu Zuhura tace "Ai wallahi basu dake banza ba yadda sukayi mana haka zamu rama ne amma ta wani ɓangare zamu bi yanzu muyi banza da iskancin da sukeyi." haka suka ci-gaba da tattaunawa, yadda zasu rama abinda Suhana tayi musu,  

ɓangaren su Afiya kuwa gyara paroln sukayi tas kamar babu abinda ya faru,  Kamal yazo suka koma gida, Suhana kuwa wanka tayi bayan ta idar da sallar isha'i, ta shirya cikin wata dogowar rigar abaya Black tayi mata kyau sosai, kamar balaraba, sai zuba ƙamshi takeyi, haka kawai taji tana son fita ta zaga gidan, 


fitowarta kenan saiga Sultan ya dawo, ɗaure fuska y yi kana yace "ina zakije.?" Yadda ya ɓata fuska sai ya yi mata kwarjini sosai juyar da kanta tayi tace "zaga gidan nikeson yi." Tsaki yaja kana ya barta nan tsaye,  bayansa tabi suka shige tare bedroom ɗinsa ta shiga ruwan wanka ta haɗa mai ta fito shi kuma ya tuɓe 

Ya shiga wanka  kitchen ta shiga ta haɗa mai abinci ta aje mai kan tebur  


KANO  STATE Unguwar GRA

Wannan Babban gida ne da ya amsa sunansa kaf unguwar babu gidan da yakai shi haɗuwa da tsari mai zaka ɗauka gidan shugaban ƙasa ne kutsa kaina nayi cikin wannan kai tsaye hanyar da zata sadani da parlo na nufa muryar wata mata naji kamar ana faɗa paroln na shiga wata Babbar mace na hango tsaye ita da wani Babban Mutum suna musayar yawo da shi, 

"Wallahi Hajiya Binta idan ki ka koma yi maganar mai sunan Mama a bakin aurenki yarinyar da ta tozarta ni a idon duniya, ta walaƙanta ni wallahi keji na rantse duk lokacin da ta dawo wannan gida sai na kaita gidan mijinta, sai dai ta haɗe zuciya ta mutu yarinyar banza!." Wacce ya kira da Hajiya Binta idanunta cike da hawaye,


tace "Naji bazan koma yima maganar ta ba amma wallahi Alhaji bazaka kashe min ƴa ba a banza ko ta dawo bazan taɓa bari ta zauna da Buhari ba, yaron da kowa ya sani ɗan shaye-shaye da neman matan banza! na roƙe Allah ya sa duk inda Zainab take tayi aure zanga yacce zakayi da auren da kasa aka ɗaura mata." 

"Yanzu Hajiya BINTA a gaban Alhaji ki ke kiran ɗan Yayarsa ɗan biyar mata mazimaci!.?" Wata mata ce ta ida maganar tana sauka kan step." Hajiya BINTA tace " To tsohowar munafuka hatsabibiya na faɗa idan ke isa ki hana ni kwana a gidan nan komai nisan jifa kisani ƙasa zai dawo sannu bata hana zuwa sai dai a daɗe ba'aje ba."


Alhaji ne yace "Kuluwa rabuda ita, duk wannan haukar da takeyi bazai hana ni kai Mai sunan mama gida Buhari ba." Wata dariya Hajiya BINTA tayi kana tace "Ai duk wannan abin dake faruwa kece sanadin komai ta Allah ba taki ba." Tana gama faɗar haka ta haura sama, ta barsu nan  Alhaji fita ya yi ita kuma kuluwa,


sama ta hau bedroom ɗinta ta shiga waya ta ɗauka tare da kiran wata number ringing ɗaya aka ɗaga tace "Hello Hajiya Ruky wallahi akwai matsala gaba ɗaya BINTA ta haukace akan neman ƴarta babban tashin hankalina yanzu ta dena shakkar gaya min magana yaznu inaso ki koma wurin Malam na bakin Rafe ya ƙara nisanta


Yarinyar daga gida idan nan kusa take ya saka aljana mantau ta shafe mata tunanin gida gaba ɗaya kar mata tayi tunanin dawowa." Ɗayan ɓangaren Ruky tace "Karki damuwa Kulawa kunama me mugun harbi, zuwa gobe zanje wurinsa duk abinda akayi zan sanar dake yanzu dai ki turo kuɗin shan fetur." Kuluwa tace karki damu yanzu zan turo miki." Ta katse kiran, 

tana faɗin "Dani kike zancen BINTA keda ƴarki saida a lahira ko a falki, sannu a hankali sai na fitar dake gidan nan gaba ɗaya." Ta ƙarasa maganar tana wani kaɗa ƙafa,  Hajiya BINTA kuwa tana shiga bedroom ɗinta alwala ta ɗora ta gabatar da sallar nafila kana ta buɗe Alkur'ani mai girma tana karatu bayan ta kammala addu'a tayi sosai Allah ya bayyana mata tilon ƴarta da ta haifa, 


Allah yasa tayi aure saboda tasan halin Alhaji, da masifar taurin kai,



SOKOTO STATE

Washegari da safe Suhana tacewa Sultan tana so ya taimaka su Afiya su dawo gidan da zama saboda gudun matsala Jamal zai iya lalata komai yace zai kira Kamal ya ɗauko su, part ɗin kusa da Hajiya Uwani zasu zauna, haka kuwa da yamma sai ga su Afiya Kamal ya ɗauko tare da kayansu, tsabar iskanci, da neman magana,


suna gama saka kayansu ciki kiɗa suka kunna, sai tiƙar rawa suke gaba ɗaya har part ɗin Hajiya Uwani ana jin ƙarar kiɗan, Suhana kuwa ta zage sai rawa takeyi ita da Afiya, Lili kuwa ta gaji zama tayi tana kallon su, Hajiya Uwani da ta fita Unguwa dawowarta kenan taji kiɗa na tashi part ɗin ta shiga don ganin su waye a ciki, 


wani burki taja bakin ƙofa tana ƙare musu kallo, kafin ta shiga ciki babu wanda ya ankara da shigowarta kiɗan ta kashe sai lokacin hankalinsu ya kai ga reta, Afiya tace"Kutumar uba waye ya baki damar shigo muna part har da kashe mana kiɗa kamar daga gidan tshonki mukazo dasu!.?" Lili tace "Bar tsohowar banza,

idan bata fitar muna part ba yanzu jiki zaiyi tsami." Cikin ɓacin rai Hajiya Uwani tace "Na baku nan da mintuna goma ku tattara ku fitar min a gida kafin na saka ayimin waje daku karuwan banza kawai andai yi asara an baro gidan iyaye anayon ta zubar ana rabawa Maza gindi lungu da saƙo." Tana ida maganar ta juya ta fita,


sosai zagin ya shigesu, amma suka basar  Hajiya Uwani kuwa security gidan ta kira tace su fito mata da su Afiya, nan suka sanar da ita Sultan ya basu damar zama a gidan bazasu iya taɓa su ba har sai idan Sultan ne ya bada umurni, ranta ya yi masifar ɓaci part ɗinta ta shiga, sama ta haura, bedroom ta shiga gefen bed ta zauna,


kana ta ɗauko wayarta wata number ta kira, bugu biyu aka ɗaga tace "Hello Hajiya Rabi." Ɗayan ɓangaren akace"Ya akayi kaska uwar haɗi da ganin wannan kiran nasan akwai magana.?" Hajiya Uwani tace"Sosai ko ƙawata." Nan ta kwashe duk abinda ya faru ta gayamata Hajiya Rabi tace 


"Keyi kuskure sosai wallahi yaza'ayi ki bari Sultan ya ƙara aure baki sanar dani kesan yaron da taurin kai, ko bokayen da ke aiki a kansa sai sun sha wahala, yanzu dai ya ya kikeso ayi.?" Hajiya Uwani tace"so nike ayi mai abinda zai sake wannan shaiɗaniyar yarinya, hankalinsa ya dawo kan Farida."


Rabi tace "To shikenan zuwa gobe zan zo duk yadda mukayi zan gayamiki." Suka yi sallama, 


Sultan kuwa bedawo gidan sai ƙarfe goma da rabi na dare, lokacin Suhana ta dawo part ɗinta, wanka tayi ta sha wasu ƙananan kaya riga ce iya cinya, ta tsaya, duk net ce da ita da babu duk ɗaya, parlon sama ta.zauna tana jiran dawowarsa, bata jima da zama ba ya dawo, ta shi tayi ta rungume shi janye jikinsa ya yi,

yace "Please ki dena bana so a waje kawai nace kiyi min haka banda cikin gida!." "Okey kawai tace mai bedroom ɗinsa ya shige, ita kuma ɗauke wayarta ta saka tsohon layinta, kai tsaye Jamal ta kira, har ta katse bai ɗaga, ta koma kiran numbersa kenan Sultan ya fito, cikin izza yace "Kije ki haɗa min ruwan wanka."

bata ɗago ta kallesa ba ta ce "Kamanta bamuyi yar jejeniyar har ruwan wanka zan riƙa haɗama ba, aikina iya waje ne kawai banda cikin gida." Dai-dai lokacin Jamal ya ɗaya wayar "Heeee haaa hello Hana...!" Gaba ɗaya ya rikice jikinsa har rawa yake, Suhana tace "Babyna ykk." Wata ajiyar zuciya ya sauke! 

tare da fashewa da kuka, yace "Hana ina kika tafi kika barni, Please Hana ki dawo muyi aure.!" Wani tausayinsa ne ya kamata har idanunta sun ciko.da kwallah cikin muryar lallashi tace "cam down, Baby in sha Allah nan da wata biyu zuwa uku zan dawo muyi aure kaji my honey!."  Jin tayi an karɓe wayar 




Daga hanunta  an jifar da ita ƙasa, ɗagowa tayi suka haɗa idanu sai da ƙirjinta ya buga da ƙarfi, ganin yadda yanayin Sultan ya sauya kamar ba shi ba cikin wata irin murya ya ce "Ke ashe Mahaukaciya ce ban saniba, Jahila, saboda bakida ilimi iskanci kawai kika saka a gaba,

da aurena a kanki ki ke waya da wani kwarto a gabana saboda ke mara kunya ce to wallahi daga yau haka ta koma faruwa duk abinda ya faru dake hammm!." Ya bar parlon gaba ɗaya,  Suhana kuwa gaba ɗaya ta tsorata da yanayinsa ta window ta parlon ta duba wurin aje motoci. Ta hangosa 

Cikin wata ƙaramar  mota. Ya shiga ya fita da gudun tsiya, hankalinta ne ya tashi, ɗauko wayar tayi ta ɗan fashe ba sosai ba, number Kamal ta kira tayi sa'a bugu ɗaya ya ɗauka tace "Don Allah Ya Kamal ka taimaka Sultan ya fita da gudu a mota kuma ransa a ɓace yake ban san abinda zai faru da shi ba." 


Kamal yace "Hana ki kwanatar da hankalinki nasan inda ya dosa yanzu zan je wurin idan ya iso zan sanar dake." Ta ce to Sultan kuwa yana fita  Shukura hotel ya wuce ya dama yana da ɗaki cikin hotel ɗin kuɗin shekara ya biya, zama yayi gefen bed tare da janyo shi-sha ya haɗa kana ya fara zuƙa, yana tura hannunsa cikin sumar kansa da ta sha gyara,  

sautin muryar Suhana na dawo mai cikin kunne ' Honey zan dawo muyi aure!' da ƙarfi yace "No no hakan bazai taɓa faruwa ba kima dena lilsafin fita gidana bazan taɓa bari ki aure kowa ba" shiru ya yi yaci gaba da zuƙar shi-sha,  bayan mituna goma kamar wani zautatce ya fara magana, shi kaɗai,


Writer ✍️*bye PINKY DARLING MRS JAY*