Chapter 10
by @pinkyjay
P 19&20
Ya Sha wahala sosai saboda yafi wata ɗaya a hospital bayan an dawo dashi gida Hajiya Uwani taso kashe sa amma da taji zancen dukiyarsa da Mahaifiyarsa tabar masa gado,sai ta ta ƙirƙiro da maganar ayi mai aure,a haɗa shi da Farida ɗiyar Yayarta, Daddy baya musu da duk abinda ta faɗa,
ya kira Sultan ya sanar da shi amma be yarda ba, saboda haka ta taje wurin malaman ta da bokaye aka saka shi dole ya amince da auren Farida ga kuɗaɗen da Uwani ke karɓa wurinsa wai na hidamar biki, saida aka zo zancen ɗaurin aure tace a nan gidan za'a ɗaura ko a masallaci, haka Daddy ya but maganarta,
Alhaji Abubakar shine waliyin Sultan, Daddy waliyin Farida haka akayi shagalin biki babu dangin uban Farida, saboda bata da Uba wurin yawon bariki aka samu cikinta, sunyi iya yinsu wurin zubar da cikin amma abin beyi ba dole suka haƙura har aka haife Farida, bayan nan uwarta ta samu wani mai kuɗi ta aure yanzu haka tana Nijar,
Kuma batasan waye uban Farida ba, saida akayi kwana biyu da ɗaura aure kana Farida ta tare bayan sun jiƙata da kayan tsisbace-tsisbace-tsisbace, saida sam Sultan baya sha'awar ta, nan ma saida sukayi da gaske ya fara kusantar ta, nan fa ya haukace akanta dukiyarsa ya zuba mata sai yadda taga dama,
Saidai yanzu ba iya kuɗi kawai suke so ba takardun kadarorinsa suke buƙatar ya mallakawa Farida amma sun kasa samun wannan damar, sunyi iya yinsu wurin Malamai amma a banza, Farida ta kasa haƙuri, watarana suna kwance, take tambayarsa inda yake aje takardun kadarorinsa,
yace mata ai shi sam baya aje wani abu mai daraja, a Najeriya ƙasar waje ya adana komai nasa, kuɗine kawai yake ajewa duk inda ya ga dama, shine ta matasa mai wace ƙasa yake ajeye abubuwan, ya ce mata duk inda ya ga dama, ba haka taso ba bayan ta koma bedroom ɗinta,
takira Mahaifiyarta, ta sanar da ita halin da ake ciki, washegari da safe, Sultan ya shirya ya samu Farida parlonta yace yana son fita, ya zaga gari bata hana shi ba, saboda yau tana son fita zuwa wurin wani sabon Malami, yana fitowa gidanmu yazo kusan wata shida zuwa bakwai da aurensa,
baya zuwa ko ina, ko naje Uwani bata bari na gansa ita da Farida haka Ummana dole muka haƙura sai dai Addu'a mukeyi mai, Uwani ta saka aka koreni Company nin Sultan shine dalilin da ya saka na fara ɗinkin tela, ina zuwa gidan Ƴan Bariki, har na haɗu da ku,
yana zuwa gidan Umma gaba ɗaya ya rame ya yi baƙi kamar ba Sultan haɗadɗen gaye maiji da kyau ga kuɗi, amma duk ya zama wani iri, kamar a tsorace yake, Umma na ganinsa ta fahimci halin da yake ciki ruwa ta ɗibo a ƙofi, ta karnta mai fatiha 7 falaƙi7 nasi7 ikilas7 kafirun 7 ayatul kulsiyu 7 tayi mai rufi cikin ruwan ta bashi
ba musu ya karɓa ya sha, ya rage saura ta sakani na shafe mai jikinsa, ya kwanta sai bacci, wannan da ku ka ji na faɗa anayinsu ne idan akayiwa wani asiri, ko baya da lafiya anyi magani ba dace ba, da izinin Allah komai zai zo karshe musamman asiri, tsawon sati ɗaya akeyi ba'a ƙetare rana,
UMMA tace min Kamal yaron nan asiri ne a jikinsa dole sai yayi sati yana shan wannan tofin, nace mata kawai ta rabuda shi, ya zauna nan gidanmu, saboda bada tare da direba yazo ba, haka kuwa akayi be falka ba sai ƙarfe huɗu tare muje masallaci mukayi sallah, kana muka dawo gida,
saiga kiran Farida Umma tace ya sanar da ita tafiya ta kama shi, yanzu haka, jirgi tashi zaiyi, sai nan da sati mai zuwa zai dawo haka ya sanar da Farida ta rufe sa da masifa kamar wani ya ronta, amma taji daɗin tafiyar ta shi saboda tana wurin Malamin da taje yace sai yayi sati ɗaya yana kwanciya da ita,
zata samu biyan buƙatar da takeso, cikin kwana biyu Sultan ya fara wankewa kamr ba shi ba, haskensa ya dawo, saboda yana samun kulawa wurin Umma sosai, ranar da ya cika sati, ɗaya, komai ya dawo mai sabo ya gayama Umma shi besan yadda akayi ya aure Farida ba yanzu gida zaije sakinta zaiyi,
Umma ta lallashisa tace ya kwanatar da hankalinsa, yabi komai a sannu kar ya nuna musu ya dawo cikin hankalinsa, har sai ya gano abinda suke shiryawa, kana ya riƙe addu'a da yawan ibada kar ya yi a gaban Farida saboda zata iya hana shi da wannan shawarar ya koma gida ya riga Farida dawowa, ya shige bedroom ɗinsa ya kwanta,
saboda bacci yakeji, amma ya kasa yi, sai juyi yakeyi kan bed yana tunanin halin da Su Hajiya Uwani suka saka shi, muryar Farida yaji itada Hajiya Uwani cikin parlo, suna magana , akan wurin Malamin da Farida Hajiya Uwani tace ai shine ya yi mata asirin Daddy ya aureta ya walaƙanta Mommy suna wannan magana Saiga Umman Farida ta shigo nan suka baje suna hirar abubuwan da sukayiwa Mommy har zuwa haɗa aurensa da Farida,
akan dukiyarsa, yanzu shirin su na gaba su kashe sa shine kawai, Farida tace gaskiya tana son sa adai yi mai wani abu da ban amma banda ƙisa, da farko basu yarda ba sai da tayi ƙaryar tana da ciki wata biyu a bari idan ta haihu dole dukiyarsa ta dawo hannunta, da wannan shawara suka aje,
sai maganin da zata saka mai cikin abinci ya cigaba da yi mata biyayya, suna wannan zance Sultan ya fito jikinsa har rawa yake, gaba dayan su sun firgita da ganinsa, sai da suka tashi tsaye, wani murmushi ya yi wanda yafi kuka ciyo yacewa Farida ya saketa saki biyu, su fita su bar mai part,
ko ya halaka su, haka suka fito jiki a mace, babu wanda yake magana, Sultan kuwa Umma ya kira ya sanar da ita duk abinda ya faru bayan dawowarsa, tace ya cigaba da addu'a saboda ba rabuwa da shi zasuyi, haka kuwa akayi wurin Malam suka koma ya basu wani garin magani yace su zuba akan hanyar da Sultan yake bi,
yana taka shi, aljanu zasu samu damar shiga jikinsa su barkita mai tunani, sumayar da shi mahaukaci ranar suka zuba maganin yana fitowa sallar magrib yana taka shi sai wani ihu sukaji, na Sultan, securityn gidan suka taso duk wanda ya matso inda yake, to sai ya karya mai hannu ko ƙafa,
wani masifar ƙarfi ne ya shiga jikinsa, ranar duk wanda ke gidan yaji jiki, abin ban mamaki part Hajiya Uwani ya shiga parlo ya same su,
sai dariyar mugunta sukeyi na halin da suka jefa shi ai kuwa sun sha duka don saida ya karya mata hannu, Farida kuwa ya sauya mata fuska da jiki aka duka, har su Maryam, an kira Daddy aka sanar da shi saboda baya ƙasar yana London, sai da aka samo gardawa masu ji da ƙarfi suka fito da Sultan suka dannesa akayi mai allurar Bacci,
suka saka shi part ɗinsa, kusu sun sha wahala, saboda duk ƙaton da ya kaiwa naushi ya zuɓe ƙasa, abu kamr filim ɗin indiya, haka suka mayar da Sultan Mahaukacin ƙarfi da yaji, banda allurar Bacci babu abinda Daddy kesa anayi mai ya fi wata uku a haka watarana naje gidan su Hajiya Uwani sun fita,
na samu damar shiga part ɗinsa na tarar da shi, cikin wannan hali cikin masu tsaron lafiyarsa wani ya bani labarin abinda ya faru da Sultan, nan na yanke shawarar ɗakarsa na tafi dashi gida, saida Umma tayiwa Sultan Kuka, duk wani mai tausayi da imani sai ya tausayawa Sultan,
wanka nayi mai na saka mai kayana duk allurar baccin bata sake shi, yana tashi zai fara bige -bige yana ganin Umma ya zauna sai ya fashe da kuka, Limamin Unguwar mu Umma ta kira, shi ya yiwa Sultan ruƙiya, da ƙyar aljanun suka fita jikinsa, saboda ba iya waɗan da aka turo bane wasu na jikinsa, da jimawa,
bayan sun fita, ya bashi magani, da wasu addu'o'i Umma nayi mai da ruwan zan zam, da zuma, yana sha,
Uwani kuwa batasan wainar da ake toyawa, sai da safe Dr dake zuwa yimasa allura yaje amma be gansa ba, haka sukayi ta nemansa amma shiru tana komawa wurin Malam yace musu zai dawo ai ba nesa ya yi da gida ba, kuma yana nan cikin hauka, da wannan bayani, suka gamsu,
suka dawo gida bayan sati ɗaya, Umma taje ƙauye wurin ƴan Uwanta a chan ta samowa Sultan tsarin jiki yadda asiri be saurin kama jikinsa idan ma ya samu shiga to bazaiyi tasiri, ba a jikinsa, zai fita,
sai da ya yi sati biyu, ya dawo Sultan ɗinsa, ya mayar dani Company matsayin MD muka wuce gidansu, Su Hajiya Uwani sun girgiza da ganinsa, duk sun sha jinin jikinsu, tun da ga lokacin Sultan ya sauya ya zame musu tantirin ɗan iska a gidan maganar kowa baya ji, duk abinda ya ga dama shi yake yi, idan Hajiya Uwani ta shiga sabgrsa,
ya yi mata rashin mutunci, ya zageta tas, ko Daddy ya taɓasa baya haƙura, dole suka shiga shakkarsa, gashi suna yawon wurin Malamai amma a banza kamar ƙarawa wuta fetur sukuyi, saboda har ƴaƴanta mata idan sukayi mai kallon banza dukan tsiya yake yi musu, wannan shine Labarin Sultan nayi ta yi mai magana,
yaje wurin dangin Mommy tun da ta sanar da shi inda zai samesu, amma yace bazai je, saboda su guje Mahaifiyarsa me zaiyi wurinsu." Kamal ya ƙarasa maganar yana shafe kwallar da ta zubo mai a fuska, su Afiya kuwa kuka sukeyi na tausayin Sultan,
kiran sallar magrib ne ya tayar dasu komai yace da ga masallaci zai wuce gida Suhana ta haɗo turamen atamfa da turaruka tace ya kaiwa Umma idan Sultan ya dawo zasu zo, shima kuɗi ta bashi tace ya sha fetur, bayan sun idar da Sallah Lili tace "Gaskiya Hana karki yarda ki rabuda Sultan, ki zauna tare dashi,
kiyi iya yinki har Allah ya saka mai sonki ku cigaba da rayuwar aurenku maganar idan buƙatarsa ta biya zaku rabu ki ajiyeta gife ki saka a ranki zaman aure kika zo Allah zai dafa miki cikin lamuranki." Afiya tace "Nima abinda zan gayama ta kenan, wallahi ko ban aure Daddyn Sultan ba sai munci uban wannan shegiyar mata."
Suhana tace "Aini wallahi yanzu ma naji inason zama da Sultan yanzu Faridar nike jiran zuwanta saina saka mata ciyon zuciya, ta mutu." Haka dai suka cigaba da tattaunawa yadda zasu gara Hajiya Uwani a gidan, zuwa ƙarfe tara suka wuce part ɗinsu, Suhana kuwa wani tayi ta gabatar da sallar isha tayi addu'o'i,
saboda akwai yawan ibada da addu'a, kana ta kira wayar Sultan har sau biyu be ɗauke ba, har ta kwanta saiga kiransa, ya shigo
Writer ✍️ Bey *PINKY DARLING MRS JAY*