06
[12/23, 6:59 PM] Janafty: SADAUKARWAR SO..!!
(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)
Wattpad:@Jamilaumar315
Mallakar:Jamilaumar(Janafty)
Page6️⃣
"Ba"a Rufe Wata Biyu ba Karatun da Mallam Habibu yake ya Daukaka sosai Saboda Karatun ma Mutane Dadama magidanta suna zuwa salla masallacin Saboda karatun da Akeyi ko bakomai zaka karu kuma Zaka Taimaki kanka ka Fita Daga Sahun Jahilai.
Bangaran Mastur kuwa yaron kowa Sha"awansa yake yi,Saboda Kaifin Hazakarsa da kuma Hankalinsa kamar wani Babba Duk sanda akayi karatu kafin abar masallacin ya Dauke sa akansa Duk da wasu ya sani wasu kuma bai sani ba kamar Bangaran Qur'ani yana cikin Izifi na Arba"in ne ya kusa Sauka su Ahalari Tauhidi da Hadisai kuwa yayi Nisa Saboda Mallam Habibu Baya musu waasa yana Kokarin koyar dasu iya abunda ya sani uwa uba Suna Islamiya da Hadda Domin Taimakon kansu.
Dattajai Dadama suna Sha"awan Kaifin Basiran Mastur Banda Mansur da banda wasa da barci Babu Abunda yake yin In kaganshi agaban Wajen karatu sai in Mastur ne ya Sakashi Zama Dole Shima kafin a tashi Zai nemesa ya Rasa sai chan zai gansa abaya yana Barci kana zai Tashe shi su Tafi Gida Mastur ke zai tamai Fada Mallam Habibu kuwa sai dai yayi Mirmishi Har acikin Ransa yana Jinjina ma Baiwar Mastur ya Tabbata Ko yau bashi da Rai Mastur zai iya Zama uba kuma mai Jajircewa kan Mansur.
Alhaji Sunusi Tureta ya Dade yana Sha"wan Mastur kullum yana ganinsa bai taba Tambayan yaron waye ba sa watarana Bayan sun gama Karatu Bayan Sun Firfito Daga masallacin ya kira Mastur din Bayan yazo ya Tambayeshi Sunansa sai ya gayamai sai yace Waye Babansa ga Mamakinsa sai ya Nuna Mallam Habibu Alhaji Sunusi ya Ji mamaki Cikin Girmamawa ya isa ga Mallam Habibu ya mikamai Hannu suka gaisa Daidai Lokacin da Mastur ya Riko Hannun Mansur suka kariso kusa Dashi Cikin mamaki yake kallonsu kafin ya kalli Malam Habibu yana Fadin"Ah..Mallam Habibu kada dai kace yaranan masu Kokarin karatu da zuwa Masallaci ya"yanka ne..?
Mallam Habibu ya yi Mirmishi kafin yace"Eh Ya"ya ne Alhaji Ashe baka sani ba..?Alhaji Sunusi yace"Wlh ban sani ba ina dai ganinsu Musamman ma Mastur gashinan ina yaba Kokarin yaron sosai sai yau na Kirashi na Tambayeshi Sunansa ya gayamin kuma yace kai ne Mahaifinsa.."
Mallam Habibu yace"Allah Sarki.."Alhaji Sunusi ya Dafa kan Mansur Dake ta washe baki yana Fadin"Kai fa ya sunan ka yaro.? Da Sauri yace"Sunana Mansur Sulaiman Doguwa.."Gabadayansu suka Kalleshi Mansur akwai Surutu Alhaji Sunusi Cikin mamaki yana Fadin"Ah ba Da"n ka bane..? Naji yace Sulaiman kuma..?
Mallam Habibu yace"Eh bani na Haifeshi ba Yaron kanwatace Data Haifesa Ta rasu Mahaifiyar Mastur ta Shayar Dashi Tun yana Jaririnsa yake Hannunmu.."Alhaji Sunusi yace"Allah sarki..Masha Allah Allah ya mata Rahma..Sannun ku kunji..? Ayi takaratu Sosai Allah ya Taimaka.."Sai Lokacin Mastur yaBude baki yace Ameen Alhaji Sunusi ya bisa da kallo Lokacin Dayake Jan Hannun Mansur Daya makale ma Baba Habibu Suka kama Hanyar Gida Alhaji Sunusi ya Bisu da kallo Cikin Sha'awa kafin ya Juyo yana kallon Mallam Habibu yana Fadin"Babban bai da Sakin Jiki..Karamin kuma akwai Fara"a da mgana.."
Mallam Habibu yace"Mastur ai Miskili ne arana bazaka Taba Kirga maganarsa ba..Mansur kuma Yaro ne mai surutu da kuma Shiga Jama"a da waasa.."Alhaji Sunusi yace"Madallah Allah ya rayasu..Zan gayama Iyalina ta Shiga su gaisa da Iyalanka Sai DIZA ta samu abokan wasa barin ma Mansur tasu Zata zo Daya Domin itama akwai Son wasa Sosai.."Mallam Habibu yace"Naji kunya Alhaji..Wlh Nace Mamansu din ta Shigo bata samu Lokaci bane..Ammh Zata Shiga su gaisa Tunda Ita ya kamata ta Fara Shiga su gaisa.."Alhaji Sunusi yace"Bakomai kada kadamu..Mallam Habibu mungode kwarai muna karuwa da Karatu Allah ya bada lada.."Ya amsa da Ameen suka Rabu Cikin karammawa Mallam Habibu yajuya ya Nufi Gida Alhaji Sunusi kuma ya Shiga Cikin Gida.
Da Mallam Habibu ya koma Gida ya Iske Mastur nayi ma Mansur Fada kan Surutun da ba"a Tambayesa ba Aiya na Tayasa Dariya yayi yana kallon Mastur yace"Kaga Babban Mutum ka kyalesa..yarintan kenan Watarana sai Labari..""Da haka ya kashe mganar Ammh Aiya itama Dataji Surutun da Mansur din yayi sai da tayi ta Fada Hajja kuma Tana Shigar ma yaronta Shi kuwa sai Tura baki yake yi Halittansa ne baya iya Daina Surutu Haka sukayi Shirin makaranta Mansur na kunci ammh Kuma Mastur na Lallashinsa ya saki Ransa Shiyasa Sau Tauri bamai Shiga Tsakaninsu Domin wata kaunace Wanda Allah ne kadai yasan iyakarta a Tsakaninsu.
Kamar yadda Alhaji Sunusi yayi alkawarin Ranar da yammah Ta kama alhamis ne ba makarantan Islamiya Dukkansu Suna Tsakar Gida Hajja na Zaune kan kujera yar Tsuggo Tana wanke wanke Mansur na Gefenta yana mata Dauraya Aiya kuma Nadaga gefe Tana Tankadan garin Tuwo Mastur ke Zaune Kofar Dakinsu yana Dauke da Littafi yana karatu Domin suna gabda Zana Jarabawar Common ce Baya wasa da Karatu ammh Lokaci bayan Lokaci yakan Dakata da Karatun ya Shiga Madafi yana Iza ma Hajja Wutan Murhu Data kada Miya ta Dora Tuwo.
Hira suke yi Sama sama da Aiya da Hajja Mansur kuma yana ta Dauraya Rabi kuma yana wasa da Ruwa Duk ya Jika Jikinsa Mastur na gefe Tunda ya zauna kala bai Bude baki yace ba sai dai Lokaci Bayan Lokaci yakan Dago ya kallesu basu wani Damu ba Sanin Halinsa Hajja Tuni ta sakamai Suna Miskili kafi Mahaukaci Ban Haushi.
Aiya ce Dake Tankaden Garin Masara Ta kalli Mansur Dake wasa da Ruwa tace"Mansur baka Jin mgana kalli yadda ka jika Jikinka da Ruwa.."Sai Lokacin Hajja ta lura da aikin Daya keyi Fuska ta bata Tana Fadin"Tashi kaje Nagode Dan barka..Kalli yadda kajika Jikinka daRuwa in sanyi ya kamaka ka Fara Mura ko Zazzabi fa..? Baka jin mgana ko Allah zan Fara Dukan ka fa Mansur.."Tafada Cikin Fada Tashi yayi yana Fadin"Hajja kiyi Hakuri.."Mirmishi Ta saki kafin Tace"Nayi Dan albarka..Maza Ka shiga Daki ka cire kayan nan ka Sauya wasu..Sai ka Fito da wannan Ka shanya su sha iska kaji ko..?
Da Sauri ya Gyada mata kai Lokaci Daya ya kwashi Gudu Zuwa Dakin Aiya ta rakasa da Allah ya Shirya Hajja na Dariya Tana Fadin"Aiya na lura kina son Dan albarkana kina akai kasuwa.."Aiya ta tabe baki Tana Fadin"Bana son Raggon Miji bai iya komai ba sai Waasa..Gwara Mijina Mastur wanda ko komai akwai Jarumta ga Maida Hankali a Karatu.."Hajja na Dariya ta waiga Tana kallon Mastur Tana Fadin"Aifa..Ammh kina Hakuri da wannan Miskilin Megidan naki kalli fa Tunda ya Fito Bai Bude baki yayi mgana ba Wlh har ce ma Baban Mansur nake ko wani Cuta ke Damun Mastur ne bamu sani ba yace Ba ko Daya Tsabar Miskilancin sa ne na Hallitta.."
Aiya na Dariya tace"Shi wai ko Bakinsa baya wari ne..? Hajja ta Tsintsire da Dariya ita da Mansur Daya Fito Daga Daki ya Sauya kaya Jikakkun na Hannunsa Duk Dariyan da sukeyi yana Jinsu ammh bai Dago ba sai ya Nuna bai san ma me suke mgana ba Mansur ne ya Tabashi yana Fadin"Yaya Kaji Aiya na cema ka mai warin baki ko..?
Dago Idanuwansa yayi Cikin Sanyin Murya yana Fadin"Najita kyaleta..Ina Karatu ne kaima kaje ka Shanya kayanka kazo ka Dauko naka Littafin ka karanta.."Tuni Annurin Mansur ya Dauke ya Bata rai ganin haka yasa Mastur yace"Tafi kaje kayi wasanka..Kada kamin kuka.."Ai sai ya saka Dariya ya wuce da Sauri Kai kawai Mastur ya Girgiza kafin yayi Mirmishi ya Cigaba da Karatunsa,Hajja da Aiya na Ta Dariyan Murnan da Mansur yake yi Jin ance yaje ya Cigaba da wasansa.
Kamar Daga sama sukaji Sallama Daga saman kansu Kusan alokaci Daya Hajja da Aiya suka Juyo zuwa ga Kofar Shigowa gidan suna kallom mai Sallama Idanuwansu ya sauka kan Wata Mata kyakyawa Fara yar Duma Duma Da ita bata da Tsawo kuma ba Gajera ba mai Fadin Fuska Tana Sanye da wani Leshi Daga ganinsa kasan bana kananan kudi bane sai Babban Mayafin Data saba akanta Kafarta Fara cikin wani Takalmi baki mai Tudu Fuskarta Cike da Fara"a Hannunta kuma rike da wata karamar Farar yarinya ce Jajir kamar atabata Jini ya Fito mai kama da Matar sai dai ita yarinya Doguwar Fuska gareta kuma bata da kiba Lange lange Take kamar ta Balle Tana Sanye Cikin Bulawis din yara Doguwar Riga Ja Iyakarta Gwiwanta kafanta sanye da Sandal na yara mai kyau Harda Safa mai kyau sai kanta da akayi mata Kitso Chuku Wanda aka Tufke mata Daga Tsakiyar kan da wasu Ribhon masu kyau Hannunta kuma na Dauke da wata katuwar Teddy Mai kyau ta Yar Bby kamar Tayi mgana itama an Chaba mata ado Kamar yadda Yarinya taci ado kamar Zata Gasan kyawawan mata.
Fuskar Mata ta washe da Fara"a ganin su Hajja Aiya ce ta amsa Sallaman Tana mata maraba Hakoranta ta Bude Farare Har da Hakorin makkanta wanda ya karaa mata kyau da kwarjini,Hajja ta Tsame Hannunta Daga wanke wanken Datake yi Ta Mike Tana Mata Maraba Dukkansu suna mata kallon Rashin Sani Daki Hajja ta Shiga ta Dauko karamar Tabaarma ta Shinfida mata Lokaci Daya tana mata Maraba Takalminta ta Cire ta zauna Tana Zaunar da yarinyar agefenta wacce take ta kalle Kalle Lokaci Daya tana ta wasa da Teddy ta Mansur Dake Tsaye gabadaya Hankalinsa na kan yarinyar da yar gunkin Bby Dake Hannunta gabadaya Tatafi Dashi Sabanin Mastur da Tunda suka Shigo Sau Daya ya Dago kai ya kallesu ya maida kansa yana Cigaba da karatunsa bai kara Dago kansa ba.
Hajja ta zauna gefenta Tana Fadin"Sannu da zuwa.."Lokaci Daya tana ijiye mata ruwa awani kofin Silba Mai kyau Amsa mata tayi Cikin Fara"a Lokaci Daya tana gaisheta kana ta Juya suna gaisawa da Aiya Ganin kamar suna mata kallon Rashin Sani yasa tace"Sunana Hajiya Asiya..Wannan yata ce Khadija muna kiranta da Diza..Daga nan gidan makotan ku da muka Tare kwanaki.."
Daga Hajja Har Aiya sai suka washe Baki Aiya tace"Allah Sarki..Sannu da zuwa.."Hajiya Asiya ta amsa Tana kallon Mansur Daya tsaya yana kallonsu Hannu ta Mikamai Tana Fadin"Sannu Boy..Taho mai sunanka..? Da sauri Mansur ya isa gareta Lokaci Daya yana gayamata sunansa Mansur Sulaoman Doguwa Dariya Hajiya Asiya Tayi tana Fadin"Wow...primary nawa kake..? Kai ya daga yana kallon Mastur Dake Zabga masa Harara sai Hajiya Asiya ta Daga kanta suka Hada ido da Mastur da Sauri ya kauda kai Cikin Sanyin Muryansa yace"Ina wuni Hajiya..? Mirmishi ta saki kafin tace"Lafiya lau..Ammh ni ba Hajiya sunana ba Inda Zaka kirani da Mommy kamar da yadda Diza Take Kirana Danaji Dadi.."Mamakinta ya kama su Aiya basu samu Zarafin mgana Ba Mansur yace"Mommy Mommy.."Har sau Biyu kumatunsa Ta shafa Tana Fadin"Eh..Daz my Boy..Mansur.."Tafada Cikin Fara"a Diza ce ta Tureshi Tana Fadin"Ba Mommy ka bace..Is my Mom.."Hajiya Asiya na Dariya Tace"Ke Diza abokin ki ne..Na yi muku Abota ko baki son Abokin wasa..? Da sauri ta Daga kai Tana Washe baki Kallon Mansur Hajiya Asiya Tayi Tana Fadin"Yauwa toh kaima ga kawa nayi maka Daman Halin ku yazo Daya...Diza itama akwai mgana Sosai kamar aku.."Hajja tayi Dariya Tana Fadin"Kice Zamu ce ta Tatar da muje mu..Mansur Surutunsa Har ya baci da son wasa.."Hajiya Asiya tace"Itama Hakan take..Diza akwai som wasa Sosai barin ma in taga yara Dayake Sokoto da muka Fara zama muna zuwa Gidajen Yan"uwa tana samun abokan wasa Buh Tunda muka Dawo kaduna Sai ta zama sai ita kadai Daga Sch sai gida gata da son wasa fa Toh nan din ma Hakane naji Dadi Dana Shigo naga kuma da yara Diza Taji Dadi sosai.."
Daga Aiya har Hajja Mirmishi Sukayi Hajja Tace"Allah Sarki.."Shuru ya Biyo baya kafin Aiya tace"Hajiya baki sha Ruwan ba.."Hajiya Asiya tayi Dariya kafin tace"Wlh nasha Ruwa Daga gida..Ammh bari nasha ko Kadan ne.."Lokaci Daya Tana Daukan Ruwan ba kyama bakomai Tasha kadan ta Ijiye Daidai Lokacin da Mastur ya Mike Dauke da Littafinsa ya Shiga Ciki Ta bisa da kallo kafin ta Dawo da kallonta kan Hajja Tana Fadin"wacece Matar Mallam Habibun mai mana karatu..?Nima Daga cikin gida ina Karuwa sosai Alhaji ma nata Godiya yace akara muku Godiya Allah ya saka.."
Wannan karon Aiya ce tace"Gata nan Hajara sunanta Ya'yanta na kiranta Hajja..'Ta fada Tana nuna Hajja Lokaci Daya tacigaba da Fadin"Ni kakarsu ce Danake Zaune dasu Aiya suke Kirana Daga Doguwa ta kano muka Dawo nan da zama Shekaru Biyar da suka gabata.."Hajiya Asiya tace"Allah Sarki..Haka Alhaji yace ku Mutanen kano ne ni kuma haifaffiyar garin Sokoto ce Mijina ma Haka sai dai shi Dan Tureta ne Dake Sokoto.."
Aiya Tace"Masha Allah Tureta ai babban gari ne.."Hajiya Asiya tace"Sosai ma Aiya garin nata samun Cigaba.."Aiya ta karkace Zama tama bar Tankaden Datakeyi Tana Fadin"Wannan yarinyar ita kadai ce Diyarki kenan Hajiya..? Hajiya Asiya ta juya Tana kallon Diza da Mansur Dake wasa da Teddy kamar sun Shekara tare Ta Murmusa kafin tace"Ita kadai gareni Aiya..Shekararmu Goma sha Biyar da Aure sannan Allah ya bamu ita Nasha Wahala wajen Haihuwarta kamar ban yi Rai ba..Sai kuma Allah ya Takaita abun Mahaifta ta samu Mtsala Tun lokacin aka Ciremin ita Diza ita kadai ce yarmu kuma Sanyin Idaniyanmu.."Aiya da Hajja Fuskarsu ta Nuna Jimani suka Hada baki wajen Fadin"Allah sarki..Allah ya rayata.."Ta amsa da Ameem kafin Ta kalli Hajja tana Fadin"Wanchan Daya shiga Dakin chan shima Da'n ki ne..?
Da Sauri Aiya tace"Itama Shi kadai ne D'anta Data Haifa..Itama kamar kece Tana da mtsala a Mahaifinta Tun wani bari Datayi Likitoci achan Doguwa sukace da wuya ta kara Haihuwa.."Hajja ta Sunkuyar Dakai bata so So Aiya ta Fadi haka ba ganin ai yau suka Taba Haduwa da Hajiyar Cikin Wani Jimami Hajiya Asiya tace"Kai..Allah ka bamu Ikon cin wannan Jarabawan..Shi Mansur fa..?
Tafada Tana Nuna Mansur da suke ta waasa da Diza da Sauri Hajja Ta tare Aiya Tana Fadin"Shima kamar D"a yake garemu..Maryama kanwar Mallam ita ta Haifesa bata ga ma abunda ta Haifa ba ta bar Gidan Duniya Ni na Shayar dashi Nice kamar makwafin Mahaifiyarsa.."Hajiya Asiya tace"Wayyo..Allah ya Jikanta..Aikuwa uwa kike garesa Domin Nonon Uwa Tankar wani Sinadarin Soyayyane Tsakanin uwa da Abunda ta Haifa Allah ya Raya mana su..Ammh Shi wanchan din sam bai da mgana ne..?
Aiya tace"Mastur kenan..Baban Mutum..Baya mgana kuma bata Dameshi ba Kirarinsa kenan Miskili kafi mahaukaci ban Haushi..Wlh sai yaron chan ya wuni bai cema kowa Kanzil ba Shi dai barsa ina zashi karatu ina ya Fito karatu kamar wani Baturen Ingila.."Hajiya Asiya da Hajja sukayi Dariya kai ta kada kafin tace"Allah sarki..Daman haka Allah ke Hallitan wasu Mutanen sam zaki ga mgana bata Damunsu.."
Hajja Tace"Shi kam Mastur abun nashi kamar cuta..Ka wuni Shuru baka mgana.."Tafada Cikin bayanna Jimaminta Hajiya Asiya tace"Ba fa Cuta bane..Haka suke irinsu Nature su ne haka.."Daganan sai Hira ta tsinke a tsakaninsu har Hajja tatashi tayi Talge,ta Dawo suka Cigaba da Hiransu sai ana gabd da kiran mangariba Tayi Shirin Tafiya Diza kuma tace bazata Bita ba Taga abokin waasa ganin haka yasa Hajiya Asiya ta kalli Hajja Tana Fadin"Hajja bari na barta Wajen Mansur..anjuma zan aiko Fadime mai aikina Tatafi da ita.."
Hajja Tace"Bakomai Hajiya.."Ta saka Takalminta Lokaci Daya Tana gyara zaman mayafinta Tana Fadin"Sai anjuman ku..Ammh fa Aiya zaku sha Fama da ita Bata jin mgana Ku kwabata kada tayi muku Barna.."Aiya tace"Ai muna da irinta Shima wannan da kike ganin ba jin mgana yake yi ba.."Dariya sukayi gabadayansu Har Kofar gida Hajja ta Rakata Tana Gayamata sai sun shigo Kafin ta Dawo Ta samu Aiya na kallon su Mansur Dake ta waasa Diza akwai baki sai Bashi Labarin Kaduna take da makarantansu da Daddyta dinta yayi mata kaza yayi mata kaza Hajja ta Dauki Sauran garin Tuwonta Tana Fadin"Gaskiya Daga Megidan har Matan gidan suna da Kirki..Jifa bamu shiga ba ita ta Shigo mana.."
Aiya Tace"Nima Zencen da nake yi kenan araina..Matar ta Burgeni ba Ruwanta Kalli yarinyar mana ki gani Daga gani bata da bakunta ballatana kyama ace wacce ke Rayuwa awannan gidan ne zaune anan Gidan Tana wasa cikin kasa.."Hajja Tace'"Irin Mansur ne ba Ruwansu..Ba irin megidan ki ba mai Tsoron mutane ba Yana jin anyi baki zai Shige Ciki yaki Fitowa kamar za"a yanka sa..Ka Fito Bakuwar Tatafi.."Ta Karishe Fada Tana Daga Murya Aiya na gefe Tana Dariya.
Yana Daga Cikin Dakin yana Jinta bai Fito ba sai da ya Kimta Littafan karatunsa waje Daya kana ya Fito Aiya ta Kallesa Tana Fadin"Har an fito Megidana..? Kai ya gyada mata bai yi mgana ba Mansur yake kallo da Diza Dake wasa kafin ya Isa bakin Rijiya ya isa ya saka Guga ya jawo Ruwa ya Ciccika Butoci Da Ruwa ya Dauki Daya ya kai ma Aiya Har gabanta ta karba tana sakamai albarka kallon Hajja yayi yana Fadin"Hajja ga ruwa nan in zaki yi alwala.."Zata Shiga Madafa da Garin Masara a Faranti tace"Tom Babban Mutum.."
Mirmishi yayi kafin ya Dauki Butan Dake da Ruwa ya Fada Makewayi Bai Dade ba ya Fito yana Tsugunnawa Lokaci Daya yana kallon Mansur yace Cikin Kakkuran murya kamar wani Babba"Mansur kabar wasan nan Baka ji an kira sallah bane..?
Dagowa yayi yana kallonsa bai basa Daman mgana ba ganin Diza Itama ta waigo Tana kallonsa Kansa ya Kada kawai yace"Kai da ita Duk ku zo ku Dauki Buta kuyi alwala.."Ayadda yake mgana kamar wani Babba Hatta Aiya Dake gefe sai da ta kara Jinjina ma Jarumtan Mastur Hajja na Madafi kuwa Sai da taMurmusa Miskilin Dan nata Jajirtattace ne Sosai kamar Ubansa.
Ganin yayi mganan ba wasa yasa Mansur din ya Mike yana kallon Diza yace"kawo Yar bebin nakai Dakin Hajja..In mun Yi sallah sai mu Cigaba da wasan.."Make abunta Tayi taki basa ganin haka yasa yace Mata"kina son ya Mastur ya Dake ki..? Sai ta girgiza kai Kamar Zatayi kuka Da Sauri yace"Toh kaima Aiya ta ijiye Miki Kizo muyi alwala."Ba musu Tatafi ta kaima Aiya Datagama Alwala Zata Shiga Ta karba Tana Fadin"Maza kiyo alwala Kizo muyi sallah kawata.."Baki ta washe mata ta amsa da Toh Tatafi ta koma Wajen Mansur Lokacin Har Mastur ya idar da alwalansa Sai Mansur ya mika mata wata karamar Buta Shima ya Dauki Nashi Suka Fara alwala In Tayi Kuskure sai ya gyara Mata Har suka Idar Mastur na Gefe yana Kallonsu suna Idarwa Hajja na Fitowa Daga Madafa Mastur yace"Hajja ki kaita Tayi sallah zamu tafi masallaci. ".
Daga Haka yaja Hannun Mansur suka Fice wanda ke tta waiwayanta Har yana mata Bye Bye.
Hajja Ta kaita Dakin Aiya ta Bata wani karamin Gyale ta yafa mata Sukayi sallah Tare da Aiya suna idarwa Ta zauna tana Motsi da baki ganin Aiya na Addu"a itama Sai ta Fara Motsi da baki Aiya na kallonta yarinya sai ta Burgenta Sunanan Su Mansur suka Dawo Daga masallacin saboda Sauri Baya yabar Mastur ya Rugo Zuwa Gida ya Fada Dakin Aiya yana Kiran Diza Tana ganinsa ta Mike Tana Murna Aiya ta Dauko Musu Bebin suka Cigaba da wasansu,Mastur kuwa yana Dawowa ya koma Daki ya Cigabq da Karatunsa.
Har Hajja ta tuka Tuwo taje Tayi Salla ta Dawo ta kwashe ta saka Ruwan Zafi na wanka Tazo ta Zubama Aiya nata ta sakama Diza nata Duk da bata da Tabbacin Zataci,Sai Mansur yace ta Hada musu sai ta sakama Mastur nashi Dabam Kamar yadda suka saba Ta Shinfida katuwar Tabarma suka Zauna Abunda ya bama Aiya da Hajja mamaki yadda Diza taci Tuwo Harda kari ita da Mansur Suna gama cin Tuwon kenan aka Kira salla wannan karon ma Mastur ya tasa Mansur suka Tafi masallaci itama Dizan sukayi sallah Tare da Aiya Sun idar kenan sun Fito su Mansur suka Dawo suka kara Murna Diza da Mansur Har Hajja da Aiya na mamaki koda yake wasa ne ya Hadu da wasa ne.
Mallam Habibu ya Dawo ya iske Diza yarinyan Sam bata da Bakunta ta saki Jikinta Ya siyi ma Mansur Sweet sai aka Raba Musu Aiya ce ke koramai Bayanin Shigowar Hajiya Asiya da Abunda ya wakana Cikin Fara"a yace"Allah sarki..Mutanen Kirki ne Allah ya bar Zumunci.."Yana cikin Cin Tuwo Sai ga Wata yar Matashiyar yarinya Wacce bata Wuce Shekaru 30 ba ta Shigo da sallama bayan sun gaisa dasu Hajja tace sunanta Fadime yar aikin Gidan Hajiya Asiya an ce Tazo Tatafi da Diza Dizan na ganinta ma ta Fara Kiran sunata alamun sani Data Fahimci Tafiya da ita za"ayi sai ta Fara kuka Dakyar da Lallashi Ta yarda tabi Fadime Mansur din kansa Kamar zai yi kuka Ranar da Wuri yayi barci haka itama Dizan Daga bangaranta..
Washegari Karfe 9am Sai ga Fadime ta kawo Diza sai dai Su Mansur suna makaranta Fadime take Fadin tun Safe Take kukan sai an kawota Wajen Mansur Hajja ta karbeta tace sun Tafi makaranta ammh sun kusa Dawowa zata zauna..? Diza tace eh sai Fadime tatabi ta barta Wajem Hajja Aiya ta Fito Tajata Daki Suna ta Hira kamar Wata babba Duk da yarinya ce ta Fahimci yar gatace Diza ta gaba da baya.