07
[12/23, 6:59 PM] Janafty: SADAUKARWAR SO..!!
(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)
Wattpad:@Jamilaumar315
Mallakar:Jamilaumar(Janafty)
Page7️⃣
"Wannan Dalilin shine zan iya cewa Mafarin Zumunci mai karfi da ya koma Tamkar yan"uwantaka ko Jini Daya Tsakanin Iyalan Alhaji Sunusi Tureta da kuma iyalan Mallam Habibu.
Domin Wata Shakuwa ce mai Girma ta Shiga Tsakanin Mansur da Diza kamar wasu yan"uwana na Jini kullum Kwanan Duniya Tana Gidansu nan take wuni suna wasa Tun ana Maidata Gida Tana kuka Har Alhaji Sunusi yace a kyaleta ta Rika kwana abun kamar wasa sai karamar mgana ta zama Baba Ya zamana Ko Dizan bata zo ba Da sun dawo makaranta Mansur ko abinci baya Tsayawa yaci zai shiga Gidansu Diza megadi baya Hanashi Saboda ya Riga ya sansa Kuma Alhaji ya bada Umarnin kada ataba Hana Iyalan Gidan Mallan Habibu Shiga Gidansa Duk sanda suke so.
Tun iyayansu na mamakin irin Shakuwar Da ke tsakaninsu Har suka Dawo suka Daina ganin Haduwar jini ce da Allah ya Hada sannan uwa uba Halayyansu yazo Daya son Surutu da kuma son wasa,Mastur ya kasance babu Ruwansa baya shiga harkansu sai dai yakan tsawatar musu suyi karatu ko sallah da Sauransu ya zamana kamar wani Babban yaya garesu Diza Tana Jin Tsoron Mastur ko mgana Yayi yanzu Zata Shiga Taitayinta ganin baya mgana kuma Baya Dariya,Bata san Haka Hallitansa take ba Balle ma Da Mansur ke Tsorata da Fadin In bata jin mgana Mastur din yana Duka ita kuma bata son Duka Shiyasa da taji mganarsa Take shiga Taitayinta sai dai baya musu da wasa Duk Jin Dadin wasan da suke da an kira sallah zasu Tashi Mastur ya Dake ma wannan Tarbiyan nasu wanda Hatta da Hajiya Asiya ta Shaida haka Domin Ko Sallah aka Kira bata Tashi ba Tana Zaune in Diza na wajen yanzu Zata kama Hannunta Tana Janta Lokaci Daya tana Fadin Tatashi Tayi sallah Kada Ya Mastur ya mata Bulala wannan abun Farinciki ne Sosai Diza bata wasa da sallah balle karatu wanda da karfi da yaji Ta shiga islamiyansu Mansur Domin in zasu Tafi sai ta Fasa kuka Tun suna barinta agida Har watarana Mastur yace Ta saka Hijabi su Tafi Tare,Jin haka yasa sai dai Suka ji an saka Diza a makarantan Islamiya Mallam Habibu ya sakata kuma Mastur yace Baba ya Dinka mata Hijabai Ta Daina yawo ba Hijabi ko Hula Diza kuma ta Rike wannan Ko Barci bata yarda Tayi saida Hula akanta ko Zamewa yayi sai tace Mommy Ya Mastur yace in ina Barin kaina abude Shedan zai Min Fitsari akaina Hajiya Asiya ssi dai Tayi Dariyan Domin ko itace Diza Ta ganta ba Dankwali Haka take ce mata Har gida Taje tayi ma su Hajja Godiya da Mastur wanda Haka kurum Natsuwarsa Take Burgeta ko Baya son mgana Haka Zatayi ta Jansa Da Hira sai dai ya kalleta ya gyada mata kai ko ya Girgiza mata kai bata Damuwa da Hakan ita dai Haka kurum Mastur din ya Shiga Ranta.
Kusan kullum Hajiya Asiya na Shigowa Gidan Su Hajja kuwa sai Jefi Jefi sun kanshiga su gaisa Mansur kuma ai ya zama Dan Gida Mastur ne ya Taba Shiga Sau Daya shima Lokacin islamiya ne yayi kuma Diza taja Mansur zuwa Gidanasu sai ya Shiga ya Kirasu wannan ne Shigansa na Farko Daga Ranar kuma bai kara Shiga ba Saboda Shi mutum ne mara son Hayaniya da kuma Yawan mgana Tun Farko.
Makaranta kuwa Diza kuka ta saka ma Alhaji Sunusi kan sai an sakata makarantan da Mansur yake zuwa Tunda lokacin Mastur sun zana Jarabawan Fita Daga primary suna Jiran sakamako,Sai Mansur ne kadai ke zuwa Daman achan kaduna an sakata makaranta Tana Nursing2 Dawowarsu nan ne karatun ya Tsaya wannan Dalilin yasa Hajiya Asiyata bada Shawaran ya Sauya ma Mansur din makaranta sai ya sakasu tare da Diza haka kuwa akayi Saidai Hajiya Asiya tazo Tatafi Dashi Batare da tayi wata mgana ba taDai ce Zasu anguwa Mastur kuma baya Zaman gidan Mallam Habibu yake bi kasuwa kafin sakamakon Jarabawan nasu ya fito.
Zaria Acadamy aka kaisu akayi musu yan Tambayoyi,Tare da Sauran abubuwa Cikin Lokaci Daya akayi komai aka gama Tunda akwai kudi Diza Primary 1 aka sakata Shi kuma Mansur Primary 4 uniform da komai Da Littafai Duka makarantan ta basu Ranar chan ma suka barsu sai da suka Dawo ne Hajiya Asiya ke Fada musu Mansur suna makaranta Hajja da Aiya suka rasa bakin mgana Sai Godiya sai 4pm na yammah Ranar suka dawo Kuma Audu Sabon Direban da Alhaji Sunusi ya Dauka yaje ya Daukosu Bakin Mansur da Diza kamar Zai Tsage saboda Farinciki Mallam Habibu sai dai ya Dawo yaji Labari mai Dadi Har gida yaje ya Kara ma Alhaji Sunusi Godiya yace kada ya Damu ai sun Saba Daya yanzu.
*******
Alhaji Sunusi Tureta Mutumin Jahar Sokoto ne A wata Karamar hukuma mai suna Tureta Bashi da iyaye tun yana Gabar samartaka Allah ya yi musu Rasuwa Alhaji Sunusi yayi gwagwarmaya sosai Kafin yayi Karatu sai da ya Saida Duka Gonakin da iyayensa suka Rasu suka barmai ya samu Gurbin Shiga jami"ar Usmanu Dan Fodiyo inda yayi Digree dinsu kan kasuwanci anan ne ya Hadu da Amininsa wanda ya Zama kamar Dan"uwan garesa Alhaji Muhammed Wamako Wanda Shima Dan Wamako ne Shima Karatu ya kawosa suka Hadu nan kuma sai ya zamana abu Daya suke Karanta,Tare suka yi Digree dinsu suka kuma yi Mastes dinsu Lokacin nr suka Fara Tunanin Gudanar da waata Sana"ar Alhaji Muhammed wamako shi ya Fara kawo Shawaran su Fara Sana"ar Shigo da Motoci ba Laifi Suna yan kudade a Hannunsu Tunda bayan gama Digree dinsu sun Fara aiki a wani karamin kamfani suna samun albashinsu suna Tarawa Domin Tsayawa a kan kafafunsu.
Cikin Ikon Allah wani bawan Allah yayi musu Hanya suka Fara Sana"ar Motocin Daga kwatano,Kafin su Rufe Shekara Daya sun samu karuwa Sosai Lokacin Dukkan sun kamallah Karatasu,Alhaji Muhammed ya Riga Alhaji Sunusi Aure in da akayi mai Auran Zumunci da yar"uwarsa Farida,Anan Sokoto ya siya Gida suka zauna sai bayan Auransu da Shekara Uku kana Alhaji Sunusi yayi Aure da Asiya ita yar asalin Garin Sokoto ne kuma Tayi Karatunta anan Usman Dan Fodiyo University.
Bayan sun yi aure suka Hada kan Matansu Waje Daya suna Zaune Lafiya gefe Daya kuma Suna Cigaba da Kasuwancinsu Duk da Shuru basu samu Haihuwa ba Ammh basu Damu ba Suna Cigaba da addu"ansu Cikin Lokaci kadan Allah ya sama Abun albarka shekara Goma da suka shude har kowa ya mallaki katon Gida da Motar hawa sunje sun sauke Farali su da matansu kuma Har sun kai wasu Daga Cikin Danginsu,kana sun Bude wani karamin ma"aikata Da suka saka ma suna WAMAKO AND SONS MOTORS LIMITED..!,Cikin Lokaci Daya sukayi suna suka kuma Shahara Ajahar Sokoto har zuwa Lokacin kuma Allah bai basu Haihuwa ba.
Farida ita ta fara Haihuwar yarta mace wacce taci sunan Mahaifiyar Alhaji Muhammed Wato RUMANA,sai bayan Haihuwan Rumana da Shekaru Uku kana Hajiya Asiya ta Haifi Diza wacce kamar bazatayi rai ba wajen Haihuwarta ba dakyar aka samu kanta,Tun kuma Daga ita bata kara Haihuwa ba haka itama Farida sai ya kasance sun Rumgumi Abunda Allah ya basu Sun gode ma Allah.
Komawar Alhaji Sunusi kaduna kasuwancinsu ne ya Bunkasa Har Kaduna da Sauran Jahohi sun Hada Hannun Jari da wani Kamfani Dake Shigo da Motoci Daga kasashen Waje Dalilin Dayasa ya Dawo Kaduna da zama kenan Hajiya Asiya taji kewa Sosai Domin Sun Saba da Hajiya Farida Tamkar wasu yan"uwa ga Diza da ta saba da Rumana ammh basu da yarda Zasuyi yanayin kasuwancin ne Shekararsu Duka Duka Biyu ne a Kaduna suka Dawo Zaria da Zama Saboda Bude wannan Rishen da sukayi anan,sun Riga sun Raba abun Kamfaninsu na chan Sokoto Takardun da sunan ciki na Alhaji Muhammad Wamako ne na nan Zaria kuma sai ya zama na Alhaji Sunusi Tureta ne sun Raba abun saboda Halin Rayuwa sai dai,Sauran Hannayen Jarinsu Dake wasu kamfanonin Dake makwafta dasu.
Dawowarsu nan Zaria yan"uwan Hajiya Asiya suna zuwa Sosai Lokaci bayan Lokaci hakama Hajiya Farida Tazo ssu Biyu Ita da Alhaji Muhammed Domin Lokacin da suka Tare basu samu zuwa ba Rumana na makaranta ammh bayan sun samu Hutu sun zo sun kwana Biyu yaje yaga wajen sosai yaji Dadin ganin yadda abubuwa suka Tafi Daidai kamar yadda suka Tsara.
*****
Mansur da Diza suna Cigaba da Zuwa Zaria Acadmy,Ayayinda Mastur ke zaman Jiran samakonsa kwatsam Sai gashi ta Fito kuma Daman ya Cike makarantar kwana ne Harda Hassan Gwarzo,kuma Alhamdulillah yasamu da Farko Hajja taso taki yarda yaje makarantar kwana ammh sai Mastur din ya nuna yana so kuma yana Bukata Sai Mallam Habibu ya maramai baya Hajiya Asiya ne Data Shigo Taji Aiya na Fada Taje ta gayama Alhaji Sunusi Shi kuma ya samu Mallam Habibi yace ya kawomai Takardun Makaran nashi,haka kuwa akayi ya Dauko ya bashi ba"a Rufe wata Daya ba Komai ya kamallah Mastur ya samu Gurbin karatu a makaranta Hassan gwarzo Duka abubuwan da suka Biyo baya Alhaji Sunusi yayi komai Harda Provison dinsa da komai da komai yace baya Bukatar Mallam Habibu yace komai Mastur kamar D'a yake garesa bashi da bakin Godiya sai dai yacigaba da mai addu'an Allah yasa ya gama Lafiya.
Ranar da Mastur zai tafi makaranta Mansur haka yake kuka kamar ransa zai Fita haka Diza ma ganin Mansur na kuka sai itama ta kama Ranar itace Rana ta Farko Daya Taba Rike Hannuwan Diza yana bata Hakuri ya Hadasu ita da Mansur din yayi musu Fadan su maida Hankali a karatu Don Allah banda wasa sukayi mai alkawarin Insha Allahu Zasu yi karatu kamar yadda yake so,Hajja ita kanta sai da Tayi Hawaye Hakama Aiya Ga Tsufa Sai kuka Tana Fadin ina zai Tafi ya barta Shi kansa Domin yana Namijin Duniya ne bai yi kuka Haka suka Shiga Mota dashi da Alhaji Sunusi da Mallam Habibu Audu Direba zai kaisu su Hajja na waje suna Daga musu Hannu.
Tabbas Sabo wani abu ne..Ranar Mansur da Diza wuni sukayi wasu sukusuku dasu Kamar basu da lakka Barin na Mansur Dayafi Kowa Shakuwa Dashi Haka Aiya da Hajja su kansu Sunji Dabam yau koda Mastur baya Yawan mgana Ai Sabo wani abu sai dai sun Ji Dadi da su Mallam Habibu suka Dawo suna sanar dasu makaranta ce mai kyau inda Mastur din ya zaba kuma Insha Allahu zai samu karatun Dayake Fata kuma in anyi Hutu zai Dinga Zuwa ganin gida da Haka suka samu suka Saki Ransu Kowa yacigaba da Harkokinsa...
Tafiyar Mastur Kano Shi ya kara Saka Karatun Diza da Mansur kara Lalacewa makarantan Kadai suke zuwa da sun Dawo ba mganar su dauko Littafansu su Duba sai wasa,islamiya kuwa sai sun ga dama suke zuwa Daman Mastur ke matsa musu ko mallam Habibu shi kuma yana kasuwa Mastur kuma baya nan Hajja Ko tayi musu mgana Sau Daya bata karawa Ballatana Aiya,Hajiya Asiya kuwa Tana da i don"t Care kuma bata som mtsama yara In tayi musu mgana Sau Daya suka Nuna basason zuwa kyalesu Take yi Alhaji Sunusi kuma Baya zama yana Kamfani inda yake da Office dinsa sai Dare yake Dawowa ba wanda ya Fahimci karatunsu ya Fara Rauni Ballatana ya kwaba musu.
Dawowar Hutun Mastur na Farko ya Fahimci Sai a Hankali Karatun Bokon suna Zuwa Dole na addinin kuwa Duk sun watsar wanda suka sani a baya sun manta Dashi yayi Musu Fada Sosai suka nuna sun ji Zasu gyara a hutun da yayi sun Dage saboda yana mtsa musu ammh Da Zarar ya koma Shikenan sai ungulu ta koma Gidanta na Tsamiya kuma Laifin Duk na Mansur ne Shine Babba Im ya ce Diza tayi abu bata Tsallake mganarsa toh shima ba son karatun yake ba sai Su wuni agidan su Diza suna kallo ko suna Buga Game Hajiya Asiya bata da wata Damuwa balle Har ta kwaba musu.
Zuwa Lokacin Zumunci mai karfi ne ya Shiga Tsakanin Gidajen Biyu,Alhaji Sunusi ya Dauki Mallam Habibu kamar Dan"uwasa kaninsa baya Zartar da komai sai da Shawaransa wani Zakka ne im zai Fitar shi zai samu kan mganar Alhaji Sunusi Duk wata kamar yadda zai Siya kayan abinci agidansa haka zai aika Dashi Gidan Mallam Habibu komai na Rayuwar nan babu abunda suka Nema suka rasa Tun Mallan Habibu na Jin Nauyin Alhaji Sunusi har ya Daina Dalilin Haka yasa Shima in ya samu alherin yake ma Mutane irin su Usman Tunda ko bakomai bazai manta da karamincin Usman garesa ba.
Doguwa kuwa sau Daya suka Taba zuwa sanda karime ta Haihu Yayar Hajja sun je Dukkansu sun kwana Biyu sun Dawo Lokacin Mastur na makaranta da Mansur suka Tafi Da Diza wacce tace sai taje suka Tafi da Ita a zuwan da sukayi ne Sule mahaifin Mansur yazo ya Roki Mallam Habibu kan zai Tafi da Mansur chan maruka yan"uwan su gansa Shima ya gansa Mallam Habibu bai yi Gaddama ba ya amince sai dai Diza tace itama da ita za"a je sai yace ya Tafi dasu Dukkansu Lokacin da Goggo da Zainabu suka ga Mansur sunyi mamakin ganin girmansa da yanayinsa Lalle ya samu Chanjin Rayuwa Ballatana Sauran yan"uwan nashi Duk ya Fita Dabam Dasu Goggo Kasa Boye Bakincikinta Tayi balle da suka ga Diza Sulen yace musu da ita suka zo Daga Zaria yar makotansu ne sun ganta yar gayu Kuma Daga ganinta Sun ga Jinin Kudi da Jin Dadi,Da sule yaso su kwana ne ammh Diza ta saka,kuka Dole acikin Daran ya Dawo Dasu Doguwa Gari na waye suka koma Saboda makaranta kuma Daman Audu Direba ne ya Taho Dasu kuma yazo ya koma Dasu.
Jin Dadin Rayuwa Sai dai su mallam Habibu su bama wasu labari,Suna Cikin Rufin asirin Allah,Mansur kuma ya zama Dan gata Domin komai Tare da Diza ake musu Mastur kuma Duk wata Alhaji Sunusi na Turamai Kudi ta Hannun Wani malami amakaranta lokacin da suka kaisa ya karbi Lambarsa Shi yake Turama kudin yayi mai Siyayyah Shima baya Cikin Wata Wahalan Rayuwa in sukayi Hutu ya Dawo yayi kiba ya kara Haske sai da Ramar Makaranta da kuma Chanjin Rayuwa Hajiya Asiya da Hajja sun zama kamar kawaye ko nace yan"uwa basa iya Boye ma Juna Komai Hajiya Farida Tasha Zuwa sukan Shigo Tare da hajiya Asiya su gaisa da Hajja Har ma suyi ta Hira Sau Daya dai suka Taba zuwa da Rumana itama kamar mastur Take bata da Hayaniya Ballatana yawan mgana sai dai ta zauna Tayi Shuru Tana kallon Diza da Mansur suna abunsu.
Tun Mastur na Dawowa Hutu yana Matsama Su Mansur da Karatu har yagaji ya saka musu Ido ganin sun yi Nisa basa Jin Kiran sai kawai ya Fita batunsu ammh bai Fasa yi musu Fada ba sai su nuna kamar sun ji da sun Fara kwana Biyu sai su Bari,Bawai basa Karatun bane suna yi ammh basa maida Hankali Har gwara ma na Bokon Dole sukeyi ammh na Addini kuwa Har suna manta na Baya Diza kuwa Daman Karatu ba Damunta yayi ba Tafi son waasa Data Fara wayau kuwa Game da kuma Kallo Sai Shima Mansur yake Biye mata ba wanda zai iya ma wani Fada acikinsu.
******
Tafe Tafe Rayuwa haka tacigaba da Gangaragarawa Cikin Kudiran Ubangiji Gashi Har Mastur ya zana Jarabawar Fita aji 6 ya dawo gida yana Jiran Sakamako Lokacin yana da Shekara 19 aduniya ne,ayayin da Mansur ke da Shekara 15 aduniya yana SS1 ita kuma Diza Tana da Shekara 11 aduniya Tana kuma JSS1 ne,Dukkansu sun Girma sun Fara mallakan Hankalin kansu.
Mastur da zuwa Lokacin ya riga zama Babba sai abubuwansa su ka Karu manyace Rashin mgana da Rashin son Hayaniya sai da ma ya Girma kana Miskilancinsa ya kara Bayyana,,Mansur kuma Rashin ji sai abunda yayi gaba Sarutu kuwa kamar yamai yawa,Diza ma Haka sai dai ita bata kai Mansur Surutu ba sai dai tafi kalkali da Mgana,Mastur yana Shan Takaichi in yaga Sakamakon su na Jarabawa Basa wani karatu sai wasa yagaji da mgana ya kyalesu sai kallo sai game Dayake ma Nan din ma Alhaji Sunusi ya saka musu kayan kallo,wuni suke abu Daya basa ko Gajiya In suna Buga game kuwa Su cika gidan da Hayaniya kuma in ya Fito yayi musu mgana sai suyi kamar sun Daina yana komawa Daki zasu Lallaba su Fice su koma Gidan su Diza su Dasa Daga Inda suka Tsaya Tun yana mamakinsu har ya Daina Shi dai karatu yana da Dadi Kuma Amfanin wanda ya Tsaya yayi ne,shi har yau har gobe bai Daina Karatu ba a makaranta kuwa ya karishe sauke alqur"ani Ya Fara sauran Littafai yanzu ko daya Dawo Gida da mallam Habibu Suke karatu bayan Sallar Isha"i Mansur kuwa yana Daki yana kallo ko kuma yana Gidansu Diza ya Saka musu ido ne,ya bari Har watarana su gane Illar Abunda suka zaba ma kansau.
Sakamakon Jarabawan Mastur ta Fito kuma komai yayi Kyau Alhaji Sunusi ya Tambayeshi Wata makaranta yake so yace Jami"ar Dan Fodiyo kuma Shi Dan Sanda yake so ya zama Alhaji Sunusi yaji Dadin Hakan Sosai nan da man ya Fara Nema mai Jami"ar ta Hannun Alhaji Muhammed wamako Cikin Nasara kuma Mastur ya samu Gurbin Karatu a jami"ar zai karanta chemical engerneering Domin yaso ya sama mai makarantan Horarwa ta yan sanda ne sai Alhaji Muhammed wamako ya bada Shawaran Ya farayin Digree Tukunnah in yagama saiya Tafi police Staff Collage yayi Short Service da wannan Shawaran yayi amfani har komai ya kamallah kuma Alhaji Muhammed yace Mastur yazo Gidansa ya zauna Har ya kamallah karatunsa.
Haka kuwa akayi Mastur bai kara wani Zama ba ya Tattara ya Tafi Sokoto ya samu Tarba Sosai Wajen Hajiya Farida wacce Rumana ke kira da Umma,Rumana ta girma Domin Shekaranta 14 kenan aduniya Tana Jss3 zata Ss1 yarinya ce mai kwazo da son karatu ga Kokari da kuma Natsuwa bata da Hayaniya,Shuru Shuru da ita ga Naci kan karatu Gabadaya Daga Boko har islamiya na Daya take zuwa Mastur Farkon zuwansa Gidan yarinyar tayi ta Burgesa yayi ta cewa aransa Dama Diza ce Dama Mansur ne Domin yana son yaga yaro mai kokari da mai da kai a Karatu ammh Sam su ba wannan ne agabansu ba sai Shirmen banza.
Farkon zamansa agidan bata sake Dashi ba sai daga baya Ganin ko abu ne ya Shige mata Duhu Data Nuna ma Alhaji Muhammeda Datake kira Abba sai yace takai ma Yayanta Mastur Tun Tana Nokewa Har Ta fara sakin Jiki ganin Komai ta kaimai zai koyamata Dallah Dallah Yadda zata Fahimci Komai sai gashi Cikin Lokaci Rumana ta kara zama mai Kokari Sosai Fiye da Baya saboda Mastur na Taimakonta Abba da Umma suna Jin Dadi saosai Har sai da sukayi waya da Alhaji Sunusi yana gayamai irin Kokarin Mastur shi dai ba mai Hayaniya bane ammh kuma Yana da Hankali Da Natsuwa.
Nan gidan yake Zaune sai dai in suna da Karatu ya shiga Cikin makaranta ko kuma in zai yi Karatu baya waasa da abunda ya kaisa In ya Dawo yana Daki yana Karatu,in ba Karatu ba yana Barci Saboda ya samu Hutu Rumana ma bata wuni agida sai 4 take Dawowa makaranta da Tadawo sai Islamiya sai Dare take zama agida kuma bata Wani kallo ko Game da zai Dauke mata Hankali da anyi sallar Isha"i taci abinci Zata kawo ma Mastur ya koyama Math Sosai take son Taga ta zama Wata kwaruwa akan Math Shiyasa ta Dake mai in ya koya mata Daganan Zataje tayi Homework dimta Data gama sai Shirin kwanciya Saboda makaranta da Safe
Mastur har acikin Ransa yake Sha"awar Rayuwar Rumana kuma yake jinta Tamkar wata kanwarsa ta Jini Haka itama ya Fara Burgeta da Dabi"unsa da Hallayansa ya zama na kowani Lokaci Tun Tana kankanuwarta Tayi Ta Tunaninsa Shikuma Mastur ba wacce yake Fama da Tunaninta irin Diza yana so tayi Karatu ta Daina wasa yana so Ta Mori iliminta watarana yanaji aransa Dama Rumana Diza ce Dayafi KowaFarinciki Saboda Takaichin su ita da Mansur ko Hutu suka samu zamansa yake asokoto yaci Hutunsa,ko waya ya kira Mansur din ya Karba yana mai Magiyan yazo sai yace wani abu yaTsayayi,Dayake Alhaji Sunusi ya Siyama Mastur wayan Hannu Saboda Karatu da kuma Kiran Gida a koda yaushe sukayi mgana Dasu awaya sai yayi musu Fadan su Daina Biye ma Kalle kallen Banza su maida Hankali Da Karatu Zasu ce mai Toh ammh Abun ya zama Jinin Jikinsu akwai wani Hutu Daya koma lokacin Mansur na Shirin zama Jarabawar su ta Fita,Diza kuma Zata Shiga SS1,yana musu Fadan Maida kai a karatu Bude bakin Mansur sai yace mai shi Siyasa fa zai yi yana so ya zama gwamna,Diza na gefenta ta kada kai tace"Wlh daka Biyani..Domin inason na Auri Dan Siyasa Haka kurum suke Burgeni.."
Mastur ya Dade yana kallonta wani abu na Shiga Ransa Mansur kuwa Tunda yaji Diza ta Fadi Haka yaji Ra"ayin Abun ya Shiga Ransa sosai abaya Kawai Shirmensa yake yi na zai yi Siyasa ammh yau da Diza ta Furta Haka yaji Duk Duniya Bai da Buru Face Cikama Diza Burinta,Shi kuwa Mastur Jikinsa ne yayi sanyi Domin Diza ta nuna Daga Secondary Bazata Cigaba ba bata da Burin yin Karatu mai Zurfi Dukkansu bai matsama kowannen acikin su ba,yadai yi musu Fatan alheri ya sallamesu ya Dade yana Tunanin Abunda Diza ta Fada yaji acikin Ransa Kamar shima yaShiga Siyasa saboda ita Saboda a yan kwanakin nan yana Jinta Sosai acikin Ransa Wanda yake jin zai iya komai sabida ganin Cikar Burinta sai dai me Yana da Burin zama D'an Sanda Ko Domin Taimakama kasarsa Bazai kara mtsama musu ba,Abunda suka zama Rayuwarsu shine daidai zai musu addu"an Allah ya cika ma kowanensu Burinshi.