09
SADAUKARWAR SO..!!
(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)
Wattpad:@Jamilaumar315
Mallakar:Jamilaumar(Janafty)
Page9️⃣
Zaria..
Hanwanfulani
Kofar Dakinta Ta Turo ta Fito Zuwa Falon kasa Lokaci Daya Tana Mika da Mitsike ido Domin Barcin bai isheta ba,Hamma ta saki bayan ta saka Bayan Hannunta Ta Rufe bakin,kan Daya Daga Cikin manyan Royal Chairs Din da sukayi ma Falon kwanya Ta zauna Tana Dora kafarta Kan kujeran dayan kuma Tana kara Mutsiketa kan Tattausan Cafet din Dake malale a tsakar Katon Falon Dayaji kayan More Rayuwa.
Doguwar macece Fara mai Dauke da Doguwar Fuska Da karan Hanci Dogo,Bata da kiba Lange Lange Take har yanzu bata Sauya ba sai dai ta Kara Murjewan Girma da kuma Hutu da wayewa,Farar Fuskarta kamar na Mahaifiyarta Hajiya Asiya Take sai dai Tswon kafan na Alhaji Sunusi ta Debo da karan Hancinsa,Rayuwa da kuma Girma sun Sauyata ammh Barkwancinta da Surutunta suna nan Kama Daga yadda take wani Motsi da bakinta Kamar Tana so Tayi mgana kuma ba Mganar take yi ba Hankalinta dai kacokan ta maida kan wayarta Daga gani Abu take yi mai muhimmaci kuma ya Dauke mata Hankali
Khadija Sunusi Tureta kenan Wacce akafi Sani Diza.
Wayarta Kirar iphone12 ce a hannunta Tana Sanye da kayan Barci Riga da wando Farare masu Taushi kanta da irin Hulanan mai Taushi na Barci mai Boye Duka kan Mutum aciki ,Gabadaya Hankalinta ya tafi kan Mutanen Dake son Oder Cake da Donut Duk ayau Diza Tayi suna ta Shahara Tana Harka da masu kudi da masu Mulki da masu garin Dayake tasan kan aikinta kuma ta kware akai Shiyasa Duk wanda Tayi ma aiki Sai ya kara Nemanta Tana Harka da Social Media Sosai Saboda Tanan take Dora Duka Harkokinta kuma Tana samun kasuwa Ba Laifi Duk da achan Catering din nata Tana da ma"ikata mata masu kular mata da wajen da masu aikin Bata Cika Zuwa ta Tube Tayi aiki ba sai ya zama Dole,ammh Takan je Lokaci bayan Lokaci Duba mike Faruwa, duk suna mgana Dasu ta waya, Musamman Bangaran Makeup dinta Wanda Daga ita Hauwa ce wata Ma"ikaciyarta masu kula da Wajen so in ayi Buking Makeup ma Tafi yawan zuwa Bangaran Domin yima wadanda sukayi Buking Din Makeup din bata Zuwa Gida In kuma Bukatar Hakan Tataso sai dai Hauwa Taje.
Diza Ta tara kudi da bata san iyakarasu ba Bayan Kudin Aikinta Daddy Duk wata yana Tura mata Kudi acikin Bankinta,Tmai mgana ya bari yace Hakkinsa ne,Diza bata sin Takura Ballatana wani abunda zai zama Takura gareta Shiyasa Taki Karatu Tafi son social Life Dinta kuma Iyayanta sun mara Mata Baya,Arayuwarta Babu Abunda Ta Nema ta rasa komai Tana samunsa Daidai Gwargwado.
Abu Dayane Bata samu ba Har yau Abunda Take kwana Dashi Aranta Tana Tashi..Shima Din ta Dangantanshi da Lokaci ne bai yi ba ammh Tabbss In Lokaci yayi Zata mallaki Abunda Take so,Duk yadda suka Shaku Da Mansur Bata Taba gayamai wannan Sirrin Zuciyar nata ba Bata san Dalili ba Gashi Dai baimai yawan Fara"a bane gareta bamai yawan Dariya bane gareta ba,bamai yawan Mata Wasa bane Bata ganin Sakin fuskarsa bane Ballatana Sakin Jiki Da Mutane Haka Allah yayi sa Kuma ahakan Take jin sonsa Aranta Kamar tama fi sonsa akan karan kanta Wanda Gashi dai ba wata Shakuwa sai Tsakanin Girmamawa Ta yaya da kanwa Ammh kuma Batasan ya akayi ba Itadai ta wayi Gari da Soyayarsa wacce kullum Take Huda Duka Gabobinta Tana kara Ninkaya acikin Zuciyarta.
Sai da Ta gama Duba Duka Sakon nin Dake Cikin wayarta,Hauwa ta Kira sukayi mgana kan Wadanda sukayi Buking din kwalliya sun Rabu kan Zata Shigo Zuwa anjuma Merry ta kira sukayi mgana kan Gidan Sarki suna Bukatar oder Cake,Wajen Spicess 3000,Daman ta Sanar dasu Ta kara kira ne Taji komai na Tafiya Daidai Merry Ta Tabbatar mata da nan da Zuwa 1pm komai zai kamallah Sai da suka gama wayar ne ta kalli agogon wayarta pass 10,Cikinta ta Shafa Domin Tana jin Yunwa Tashi Tayi Tana wani naka naka da Fuska Tana kallon Upstairs Baki Ta Tura gaba Ta Nufi Hanyar Kitchen bayan ta Cillar da wayarta kan kujera kamar ta Wurgan da wani abun banza.
Da Sallama ta Shiga Kitchen din Ganin Fadime Datake kira Mama wacce ta Manyanta yanzu Kimamin Shekaru 54 aduniiya Fadime Ta Dago Tana Washe baki tace"A"a Uwar Dakina Har kin tashi..?
Diza Ta Daka Tsalle ta Dane kan Kitchen Cabinet Tana Fadin"Na tashi Mama..Na Fito Ma ko"ina is To Booring Daddy da Mommy basu Sauko ba.."Ta Fada Tana Tura Baki irin na Shagwabbun yaranan da suka samu gata.
Fadime na Soya kwai Daya Cika Kamshin Kitchen din Tace"Zasu Sauko yanzu ai Uwar Dakina.."
Diza TaRausayar dakai Tana Fadin"Ina kwana Mama Fadime.. ? Tana Saka kwan Cikin wani Filet take Fadin"Lafiya lau UwarDakina ya gajiya..? Saukowa Tayi Daga kan Cabinet din Tana Fadin"Ba wata gajiya fa Mama..Ni yau bana jin cin irin wannan Breakafsat din naku Mama bari na Leka wajen Hajja Allah sa Kunu da Kosai Tayi Mana.."
Mama Fadime na Dariya Tace"Hanzarta Domin Kisan Bata Kiyuwan yin kosai Hajja.."Diza ta Fice tana Dariya Fita Tayi Ta koma katayyacen Dakinta kamar Dakin Wata Matar Aure Saboda yadda yaji kayan alatun Rayuwa Babban Wardrope dinta ta Bude ta Dauki Wata Abayarta ta Zura bayan ta Cire kayan Barcin Jikinta Sai ta Dauki Bakin gyalen Abayan ta Yane kanta Dashi,Ta Fito Falo Bayan ta Sauya takalmin kafarta Direct Fita Tayi zuwa Falo ta Dauki Wayarta kana ta fita zuwa Haraban Gidan inda Tsala Tsalan Motoci guda uku suke Fake a Wajen Daya nata ne Daya kuma na Hajiya Asiya ne Dayan ce Ta Alhaji Sunusi.
Gaisawa Sukayi da Baba megadi kana ya bude mata karamar kofa ta Fice Tana Fita Taga matasa Da yawa akofar gidansu Hajja Mirmishin Saman Lebe Tayi Domin tasan mai girma Honourable suke jira Dama Jiya ya gayama ta yau zasu yi Taro da Shugaban Jamiya anan Zaria Bata kula kowa ba duk da wasu sun santa aido Suna ta mata barka da Fitowa Bata tankasu ba Ta Tura Get din Gidan Baba Habibu daya Dawo na Zamani mai Dauke da Sashe Biyu.
Shashen Farkon na Su Hajja ne Shashen Ciki kuma na Mansur da Mastur wanda ke Dauke da Babban Falo sai Kitchen sai Bedroom guda Biyu Daya na Mansur Daya na Mastur ne Gabadaya Gidan kamar bashi ba Bambamacinsa Dana su Diza kawai Bene,Ammh Shima gidan sun kashemai kudi wajen Tsarashi Filin Dake kusa dasu suka Siye sukaHadeshi da Gidansu Shiyasa Filin ya wadata Har aka samu ma"adanar Motoci da Dan Haraban Gidan da suka Fitar ma Get.
Tana Shigowa Haraban gidan da bai Cika Girma ba sosai Taga Mashin din Baba Habiba Domin Yaki yarda Mastur ya siya masa Mota yace su dai su hau shi Mashin dinsa itace Daidai Dashi,Dole suka kyalesa ammh Sun Sauyamai da Roba Roba mai kyau ta Zamani,Sai Motar Mansur kirar Matric Baka,Tana gani ta gane dukkansu basu Fita ba kenan kai Tsaye kofar da sadata da Babban Falon Gidan ta Nufa ta Tura da Sallama Cikin Siririyar Muryanta ta Shiga.
Aiya ce ke Zaune kan Daya Daga Cikin kujerun katon Falon Tana kallo Duk da Tsufa ya kara kamata ammh Jin dadi sun sauka Har yanzu da karfinta sai dai Ciwociwo na Tsoffafi wadanda ba"a rabasu Dashi Tana jin muryan Diza Ta Dago Cikin Fara"a Tana Fadin"Muryan wa nake kamar ta Hadizatu..?
Tafada Cikin muryan Tsufa Wanda Daman kanta Duk ya Cika da Furfura,Diza data kariso ta zauna agefenta Tace cikin Tura baki "Ni fa Aiya ba sunana Hadizatu ba suna Khadija ko kice min Diza.."Tabe baki Aiya Tayi Tana Fadin"Kwaji Dashi dai..Ku yaran zamanin nan akwai Sanabe..Sunanki suna ne mai Daraja sunan matar ma"aki Sallallahu alaihi wasallam Kuma itace mace ta Farko Data Fara Karban kalmar Shahada a mata kuma ta bada Rabin Dukiyanta wajen yima addinin Allah Hidima ammh Shine kike wasa da sunanki kina maidashi wani wai Dizza.."Ta fada Cikin bayanna Takaichinta Dariya ta kama Diza ta Fara kyakyatawa Sai ga Hajja ta Fito Daga Cikin kitchen din Dake Falon Ta kara zama Babban Mace,Ta kara kyau Domin yazu Rayuwa tayi musu Daidai Tana Fadin"Aiya ke da wa kuma..?
Sai kuma Taga Diza Baki ta Washe Tana Fadin"Diza ashe kece..?ni danaji mgar Aiya ma na Zata Dan albarkan nanne yazo yana Tsokarnata Mansur.."Diza ta Sauko Daga kan kujera ta Duka tana gaida Hajja ta amsa Cikin Fara"a Tana Tambayanta iyayaanta tace suna Lafiya,Kafin tatashi ta koma ta zauna Tana Fadin"Hajja ina Baba..?baifito bane..?
Hajja Tace"Yanzu zai Fito..Na barsa yana wanka ne Dazu.."Diza tace"Ok..Allah sa Koko da kosai kikayi mana Hajja Shi nazo sha nagaji da cin Kwai da Tea wlh.."Hajja na Dariya tace"Kamar kin sani..Yau Daga Baban Mansur Har Mansur din Shi sukace suna son su karya Dashi..Sha kurumakin yanzu zan karisa Toyan kosan.."Tsalle Diza taBuga Tana Fadin"Yauwa..Hajjanmu Har naji Dadi wlh..Muje na Tayaki Soyan Kosan.."
Hajja Tayi Saurin Fadin"a"a barshi..Kwaskon Karshe ya Ragemin Zan karisa aikina Kinji Diza.."Diza ta bata rai Zatayi mgana Hajja tace"kar ki damu Maza Tashi ki leka Abokin naki Yanzu ya bar nan Naji yana Fadin suna da Taro kilama yana chan yana yana Shiriritarsa na Fama.."Mirmishi Diza Tayi ta Mike Tana Fadin"Shikeman Hajja Tunda kin Hanani Tayaki aikin..Bari na lekasa na Dawo.."
Hajja Tace"Yauwa kafin ku Dawo na Gama komai Diyata.."Dariya Diza Tayi Aiya Dake Zaune Tatabe baki Tana Fadin"Katon Saurayi ammh Har yau bai bar Shiririta ba ni bansa ma ya akayi aka Zabe wannan Talasurin ba wlh..Allah sarki Megidana Mastur Namijin Duniya Dan Sanda mai ma kasar sa Hidima.."Daga Hajja Har Diza Dariya suka saka Diza na Ficewa Take Fadin"Zaki maimaita agabansa.."Tana Fada ta Fice ta Fita Zuwa Shashen su Mansur din.
Knooking Ta Farayi Daga Kofar Falon Mansur Daya Ke cikin Dakinsa yana Kokarin Saka Links dinsa na rigar Blue din Shaddan Dake Jikinsa yayi Tsai da Rai sai kuma ya kara,jin Knooking din Cikin Tunanin ko waye ya Fito Daga Bedroom dinsa yana Kokarin saka Links Din Kofar Falon ya isa ya Zare Key din Jiki Bayan ya Bude sai ga Diza ta Bayyana Tana Tsaye Tana kallonsa Shima Idon ya kafeta Dashi kamar zai Cinyeta.
Aduniya in akwai Hallitan Da Baya gajiya da kallo Diza ce..Ita ce wacce ke jan Ragamar Rayuwarsa Gabadaya,Ko Bata gabansa ya Riga ya gama Zana Duka Hotonta acikin Zuciyarsa ko Bata Tare Dashi Da Zarar ya kadaice ita yake gani kuma yaji Har ya samu Sukuni Duk Duniya Bayan Iyayansa da Yayansa Mastur bai Taba son Abu kamar Ransa Kamar yadda yake son Diza ba zai iya Mutuwa Duk Ranar Daya Rasata,
Wani kallon kauna da Muradi mai Girma yake Jifanta Dashi cikin Matsakaitan Idanuwansa Mansur ya Sauya ya Kara Girma Da Cikar mazantaka,Kallo Daya zakamai kaga kamar Hoton Maryama ce saboda Tsabar yadda kamminsu ya Bayyana Mansur Dogo ne,Sai dai ba Sosai ba Bai kama Kafar Tsawon Mastur ba A kafadan Mastur yake in suka Jera da juna,Mansur yana da Haske sosai Har yafi ma Mastur sai dai Shi Fuskarsa Mai Yalwar Fara"a ce da Barkwanci mai wasa da Dariya da Dadin Zama,Mansur ya zama Cikakken Mutum da Cikar Zati da kamala a Shekarunsa Daya Taka Matakin Rayuwa mai Cike da Nasara da Sa"a Mutane Dadama suna mamakin ganinsa yaro Matashi Ya samu Sa"ar Rayuwa har yake amsa sunan Honourable Mansur Sulaiman Doguwa.
Diza ce Taga ya Shagala da kallonta sai ta Saka Gefen Mayafinta Ta Daki Fuskarsa Tana Fadin"Wannan kallon fa My Honourable,ko baka Taba ganina bane..? Daman haka take Kiransa Shi kuma sai yace mata My Firstlady
Sai Lokacin Mansur ya Dawo Daga Cikin Hayyacinsa Ya saki ajiyar rai bai ce mata komai ba ya Bata Hanya yana Fadin"Bismillah My First lady.."Tayi Dariya kawai Ta Shige Shikuma yamaida kofar ya Rufe yaBiyo bayanta yana Fadin"Kamar kin sani yanzu nake Shirin Kiranki..'"
Tana Zama kan Daya Daga Cikin kujerun Falon Take Fadin"Gani nazo..Ai kasan ko baka nemeni ba Duk inda aka ga gwamna sai anga Firstlady dinsa.."Ta karishe Tana Dagamai Gira Dariya yayi yana Karisa Saka Links Dinsa yace"Nagode My Firstlady.."
Tana Mirmishi ta Kalleshi Sama da kasa Tana Dariya Shima sai yabi kansa da kallo yana Fadin"Ya akayi ne..? Ko Kayan basu yi bane na Sauya su..?
Kai ta Girgiza Tana Fadin"A"a..Kayi kyau My Honourable na..kayan sun maka kyau sosai..Ammh pass 8 fa kada ka makara wajen Taron.."Tafada Tana kallonsa agogon Azurfan Dake Hannunsa ya kai Duba kafin ya dan Yamutsa Fuska yana Fadin"Sai10am za"a Fara Taron..Bari na je na Dauko Hulata da wayata da key din Motata muje Shashen Hajja mu karya kafin na wuce ko..? Zaki fita yau ne ko zakimin Rakiya ne..?
Diza Tace"Eh zan je Office Anjuma akwai wadanda sukayi Bukking din kwalliya..kuma Hauwa Zataje House Service ni kadai ce.."
Kai ya gyadaa mata yana Fadin"Ok..Bari na shiga na Fito.."Yafada yana wucewa Ciki ita kuma sai ta sauke idonta kan Karamin Frime din Dake kan Tv Stand din dake Falon Hoton Mastur ne da Mansur Mastur da Uniforms dinsa ajikinsa Ranar da aka bashi Rank din Zama Dcp ne,Abuja Mansur din yaje mai shine Sukayi Hoton Sun yi Bala'in kyau Mastur yana Rike da Kafadan Mansur Dukkansu Suna Dariya,Fararan Hakoransu a waje in ga gansu Zaka Fahimci Tsantsan kaunar juna atsakaninsu.
Hoton ta kurama Ido ko Kiftawa batayi Gabadaya Hankalinta ya tafi kan Mastur shi take kallo Lokaci Daya Tana Sakin Mirmishi Wani Shauki da muradi mai girma yana kara Shiga Zuciyarta Bata ma san Mansur ya Fito ba sai da Taji mganarsa sama sama yana cewa Tatashi su tafi Kasalance ta Mike tana gyara Mayafin kanta Kallonta yayi kafin ya Dan Dakata yana Fadin"Kash..Nayi mantuwa.."
Kallonsa Tayi Tana Fadin"Ai daman baka Rabo da mantuwa..me kuma ka manta..? Wayarsa yake Dannawa Loksci Daya yana Fadin"Ban kira Ya Mastur ba Diza..Kuma Duk Safiya Bayan su Baba dashi nake Fara mgana kafin na Fita.."Komawa Tayi ta zauna Ranta na mata Fari yau zataji muryansa Data kwana Tana Marari ba wata Shakuwa Tsakaninsu Shiyasa Take jin kunyar kiransa ammh Lokaci Bayan Lokaci suna Waya Dashi ta wayar Mansur,Abunda ke bata mamaki Kusan kullum sai ya Kira Daddy ko Mommy ta Ammh Ita bai Taba kiranta ba Ko Da sau Daya itama Bata Kiransa ba Saboda Bata san Tana ina Zata Fara ba.
Mansur ta kura ma Ido ganin ya kara bata rai Ido ta waro mai Tana Fadin"Ya ya dai..? Yana zama gefenta yace"Bai Daga kiran ba.."Ta rausayar dakai Tana Fadin"Kila yana Aiki ne..Kasan fa baya Hada aikinsa da komai Gwamna na ."
Bai samu Zarafin mgana ba Dayar wayarsa Kiran Samsung wacce Mastur ya siya musu iri Daya, ta fara Tsuwwa Ya Daga yana mgana Yan Siyasansu ne ya Dade yana mgama kafin ya katse Kiran Daidai Lokacin da Dayan wayar tasa Ta Dauki Neman agaji Tare da Shi Da Diza suka kai kallonsu kan Wayar sunan wanda suka gani ne ya saka kowannensu Sauke Boyayyiyar ajiyar Zuciya
Ya Mastur ne Baro baro yake Kiran Wayar Mansur da Sauri ya Dauki wayan ya Daga Cikin Shagwaba kamar karamin yaro yace"Nayi fushi ya Mastur..Ban kiraka ba kuma baka kirani ba Tun Safe..Na kuma kiraka baka Dauki kirana ba Mansur ne fa Mansur dinka Wanda baka da kamarsa.."
Yafada yana Tura baki,Diza kallonsa kawai take Tana yar Dariya sanin Halin Mansur Shi Haka yake Rayuwarsa mai Sauki ce,Hulan kansa Zanna Bukar ya Tura gefe Lokaci Daya ya saka wayar Speaker Daidai Lokacin da Mastur yayi Mirmishi Cikin Kayattaciyar Muryansa yace"Honourable Mansur Sulaiman Doguwa..Am Sorry Sir.."
Yanayin yadda yayi mganar sai da ta saka Diza Taji bugun Zuciya Mansur kuwa Baki ya washe yana Fadin"Kai ne Sir ai Yaya..Ya aikin..? Ka tashi lafiya..?kaci abinci..?kana wajen aiki ne..? Mirmishi kawai yayi Lokaci Daya yana Sagala wayar a kunnuwansa da Hannu Daya Dayan Hannun kuma yana Danna System dinsa Sargent Inuwa na Tsaye agefensa yana Jiran Umarni.
Cikin Sanyin sa yace"Oh..Wata Tambaya zan Fara amsaka Daga Ciki. ?
Mansur yace"Duka yaya Nidai.."Yafada yana Dariya yana kallon Diza Datayi Kasake Tana Sauraran Muryan da Bata gajiya da Sauraranta ko Jinta Mastur kuma Dagachan Bangaran Bai yi Dariya ba sai dai ya saki Fuskansa Cikin Dakiya yace"Komai Lafiya..Mansur Fatan kaima haka..? Yafada Kamar an sashi Dole Sargent Inuwa na Gefe aransa yana ayyana Duk Duniya banda wannan Dan"uwan yallabai bai mai sakashi mgana takai Goma Arana Ko da su bai taba gani ba ammh yasha jin wayarsu Yanajin yadda Mansur din ke yawan saka Ogan nasu mgana ko bai so ba
Mansur kuwa Daga Chan Bangaran ya tsike da Zuba yana gayamai Taron da zasu yi da Irin kayan da ya saka ya Karishe da Fadin"Yaya Mastur Shaddan fa Dana Tura maka Hotonta nasakafa..Diza tace nayi kyau Sosaifa ko nayi maka Hoto ne kagani..? Zamu yi Vidoe callne..?
Kansa ya Dafe kawai yana Dan Jizan Lebensa jingina yayi da Jikin Kujeran Dayake kai bayan ya Ture Computer din gabansa Da Hannu ya Nuna ma Sargent Inuwa Fayel din gabansa Har ya gane me yake Nufi da Sauri ya kame mai Lokaci Daya ya Dauki Fayel din ya Fice sai Lokacin Mastur yayi mgana yana Jan Numfashi saboda kiran Sunan Diza da Mansur yayi sai da Zuciyarsa ta amsa.
Cikin Sanyin Murya yace"A"a ina aiki ne Mansur..ammh nasan kanina mai kyau ne..Kowani kaya ya saka suna mai kyau.."Yafada yana Dan Mirmishi Mansur yace"Daz my Yaya ni kadai..Yaya when zaka zo ne..? Wlh muna kewarka Hajja Baba Aiya Mommy,Daddy Har da Diza Gata agefena.."
Mastur yaji gabansa ya Fadi Cikin Taushin Murya yace"Ok..Tare zaku Tafi Taron kenan..? Mansur ka Daina Zuwa da yarinyar nan cikin Taron maza fa Ita macece ka kiyaye Abunda nake gayamaka.."Ya karishe Kamar Kamar Zuciyarsa Zata Fito Saboda Takaichi da Kishi Sanin Halin Mansur din Da Diza yawo kamar sun ci kafar kare Last Month yaje Zaria bai kwana ba ko da yaje basa nan wai Suna Catering din Dizan Tun Safe Dagachan Mansur din zai je Taron su na Siyasa Zata Rakashi Saboda Takaichi ko Jiransu bai yi ba shi da Tawagarsa suka Dauki Hanyar Porthercourt Daman Abuja suka zo Sunyi Meeting da IGP na kasa.
Mansur ya kalli Diza itama Ta kallesa Tana Tura baki Abunda na Cimata Tuwo a kwarya Intaga yadda Mastur bai Damu da ita ba Ballatana Lamarinta Sai dai bai Chanza ba yana nan da Fadansa da Tsare Gidansa Data Sanshi Dashi Tuntuni.
Mansur yace"Ni ba Tare zamu ba..Catering dinta zata tafi Tana da aiki...Gata ma ku gaisa.."Yafada yana Tura mata Wayar gabanta Mastur yayi Saurin Bude idanuaansa jin Sallamar Diza Cikin Siririyar Muryanta Bai amsa mata Sai da ya Fara Kokuwa da Numfashinsa kafin yace"Kina lafiya..?
Daman ai gaisuwansa bata wuce haka tace"Lafiyata kalau ya aiki..? Kamar baya som mganar yace"Alhamdulillah.'Daga nan bai kara mgana ba sai Kokuwa yake da Numfashinsa itama sai ta kasa mgana Karban Wayar Mansur yayi yana Fadin"Wai Yaya Mastur Ita har yau Diza Bata Saki Jiki Dakai ba..Tsoronka Take ji Tun Lokacin ina ce mata kana Duka.."Yafada yana Dariya Mastur bai biye masa ba yace"Ka tashi ka tafi kada ka makara..Ka tuna ka girma yanzu kai ba yaro bane..Mansur din Baya Bashi bane na yanzu Honourable ne wanda Hakkin Jama"a Dadama ke kansa.."
Cikim kwamciyar Hankali yake mganar wanda duk wanda yaji Sai Muryan ta sakamai Natsuwa Mansur yace'Insha Allahu Yayana.."Mastur yace"Ina aiki ne..U took Later..Kada ka manta ka Kira Baba Sule ka gaishesa bana son in kara maka mgana Mansur ok..?
Da sauri yace"Allah zankirasa yaya.."Gud..yace Lokaci Daya yana katse Kiran.
Diza Datayi wani Sanyi da ita ya kallah yana Fadin"Bari na Kira Baba Sule kamar yadda yaya yace..kije ganin nan zuwa.."Bata yi musu ba ta mike Dauke da wayarta Sanin Da Tayi bazaiTaba waya da Mahaifinsa agabanta ba Bata san meyasa Mansur ba wata Jituwa ko Shakuwa Tsakaninsa da Yan"uwansa ta Bangaran Uba ba Duk ko da yadda Baba Sule ke yawan zuwa abaya ganin mansur din Yanzu ne ma ya Rage zuwa Saboda Shekarin sun ja,iyalai sun kara yawa da wasu matsalolin Rayuwa Har Mastur da Ba D'ansa ba yana Kiransa aka kai suna gaisawa,Shi haka yake kowa sai dai kaji yana yabonsa Haka Abba da Umma na Sokoto Suna ji da Mastur kamar Dan su na Cikinsu Kullun sai ya Kirasu sungaisa Yana da Kyawawan Hallayan Ga ita ne kadai bashi da kyawawan mu"amala.
Tana Fita ya Kira Baba Sulen suka gaisa Bashi da lafiya ne Typiod bai ma sani ba Mastur din ya Kirashi ya gayamai Baba Sule yace ma Mansur yaushe zaizo yace sai ya samu Lokaci nan yake gayamai Bikin kanwarsa Sakina ya taso..Kuma Auran Yayarsa Maryama ya kare Tana Gida Mansur yace sai ya samu Lokaci zai zo Insha Allahu Daganan suka Rabu ba wata Shakuwa Ballatana Fahimtar juna Baba sule Koda yaushe in ya Tuna sai yayi Hawaye Ba kowa bane Silan komai sai goggo Da yau Mansur a wajensa ya tashi Daya Tabbata Ya Fahimci acikin ya"yansa shi na Dabam ne.
Chan Shashen Su Hajja ya iske Diza Baba Habibu ya Fito,Daman sungaisa Tun Safe Zaman karyawa sukayi Dukkansu Aiya sai Tsokanarsa Take yana Ramawa ko Hajja Ta Tare mai Baba Dai na jinsu yana Dariya Yana gama karyawa yayi musu Sallama ya Fice Zuwa kasuwa Mansur ma bai jima ba ya Fita Domin Samarin anguwan da matasa sun Cika kofar Gidan Suna Jiransa Dakyar ya samu ya Fitar da Motarsa Saida ya sallamesu kana suka Raka Motarsa da sai kayi Gwamna Honourable Mansur Har Bakin Titi.
Diza kuwa Nan ta kai Har 12 suna Hira dasu Hajja kana ta baro Gidan Zuwa gidansu ta iske Daddy ya Fita sai Mommy Da Tayi bakuwa kawarta Hajiya Baraka wacce suke Business Tare,suna Zaune ne afalon Mommy na sama chan ta shiga suka gaisa kana taSauko ta Fada Dakinta wanka Tayi ta Shirya Cikin Doguwar Jallabiya ta yane kanta da Vail din Rigar Daman ita Duk kayanta Jallabiya ne Saboda Tana sonsu sosai,Takalminta ta saka ta Dauko karamar Jakarta ta Fito Ta Shiga Kitchen ta samu Mama Fadime na Girki tayi mata sallama Tace Zata wajen aiki,Daganan ta Haura sama Tayi ma Mommy Sallama ta kuma Karbi key din Motarta tace yau da ita Zata Fita.
Daga Gidan Direct Dogarawa ta wuce Tanayi Tana Duba agogon Fatan Dake Hannunta Bata so Tayi african Time koda ta ta samu Mutum Biyu na Jiranta,Rigar aikinta kawai ta Dora a saman Kayanta ta Fara aiki Daman sunyi mgana da Hauwa Ta wuce,So take tagama Ta Leka Cikin Catering Taga Abubuwan Dake wakana anan wajen