SADAUKARWAR SO.

12

by @jamilaumarjanafty

[12/23, 6:59 PM] Janafty: SADAUKARWAR SO..!!

(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)

Wattpad:@Jamilaumar315

Mallakar:Jamilaumar(Janafty)

Page1️⃣2️⃣

""Kwata kwata yaki Daukan Wayan Mansur Ballatana ya Sauraresa Duk kuwa da nacin Kiran da yake mai da Turamai Sakonnin ban Hakuri yayi mai Biris Abunda ke bashi Mamaki da kanin nashi Har zuwa yanzu bai iya zama ya natsu ba Ballatana ya gano Laifinsa Sai Shirmensa kawai yake in ya Tuna Haka sai yaji Dacin wani abu Ba haka yaso kanin nashi ya zama ba ammh bashi da yarda Zai yi Kullum Mansur ya Girma ne baisan ya Girma ba in yayi wani abun kamar wani yaro karami.

Ya gama gayamawa Kowa yayan nashi na Fushi Dashi..Harda Daddy Da Mommy Sai da suka Kirashi Suna Tambayan Dalili yace musu bakomai Zai kira Mansur aiki ne yamai yawa kowa ya yarda da kalaman Mastur sanin Halinsa kaifi Dayane sai ake Tausan Mansur din yayi ma yayan nashi Uzuri yanayin aikinsu ne Nan kuwa Mansur yasan waye Mastur Irin Horansa kenan kuma yana da Tabbacin Koma wani Laifi ya aikata mai Girma ya bata ran Yayan nashi da bai da kamarsa Duk Duniya Yayan Da baya son ganinsa Cikin Damuwa yayan Dayake Samin abu ya Hanawa kansa Saboda shi..Ya Tabbata Koma Miye ya Faru ya batama Mastur rai matuka Dalilin Dake Hanashi Kwanciyar Hankali kenan Ko Itama Diza tun bata Damuwa Har tazo ta Fara Damuwa ganin yadda Mansur din ya Hana kanshi Sukuni.

Daran Jumma"a ya baro Parthercourt da yammah ya iso Zaria da Safe Misalin Karfe 10:30am nasafe,Ba wanda yasan da zuwansa ko Habibu Bai gayama Ga Ranar da zai Taho ba,Kuma Shi kadai yazo Dan Rakiya Ko Daya bai Taho Dashi ba,Sai dai su Hajja suka gansa kwatsam Lokacin Tuni Baba Habibu ya Tsufa akasuwa Gogan kuwa Yana Ciki yana Barci bai ma Tashi ba Diza ma Tana Gida Bata da masaniya Ita Fita Zatayi Domin Tana da aiki Sosai Yanzu Suna samun yawan Costumer sosai arana gashi Daga ita sai Hauwa,an kawo mata Wasu mata wadanda suka samu kwarewa akan Makeup din ammh Duk basu yi mata ba Bata Daukesu ba Tana dai Cigaba da Dubawa Tun Safe tayi wanka Tashirya Bayan Tayi Taking Breakfast Daddy ya Fita kamfani sunyi baki Abokan Cinikanyasu ne,Mommy kuma Tana Sama bata Sauko Falo ba Ta Fito ta zauna Tana latsan waya Tana Jiran 11am ta cika sai ta Fita.

Shi da kansa ya Bude ma kansa get Daman basu da megadi Bayan nan kuma ya Shigo da Motarsa Cikin Haraban Gidan,Motar Mansur Daya gani yasa yaji Dadi Allah ya Taimakeshi yau ba"a Fita Gantalin Siyansa ba Sai da ya kashe Motar yaDauko Duka Wayoyinsa bai zo da kaya ba Saboda aiki zasu zame mai yana da kaya anan gidan System dinsa kawai yazo Dashi Saboda aiki ita ya Dauko Ya Taka zuwa kofar da Zata sadashi da Falon Hajja Yana Sanye da Riga da wando na Kamfanin Dkny,Black and White sai P.Cap din Dake kansa da Takalmi Booth Daya Rufe kafarsa Dashi.

Sallama yayi da Muryansa mai Cike da Zati Aiya dake zaune ta Fara Jinsa Domin Aiya Gashi dai ta Tsufa ammh akwai son kallo Haka zata gwafe a falo Tana Dale ido,Hajja ma kallon bai Dameta ba,Bata cika Zama ba ko Tana Daki ko Tana Kitchen,Kamar a mafarki Taji Muryansa Cikin Sauri Aiya Ta Dago kai Tana Fadin"ah..ah..Muryan wa nakeji Kamar ta megidana..Lah..Wlh Shine Hajara ke fito ga yaronki Da Safe haka Maraba Maraba da Zuwa..!

Take Fada Cikin Fara"a Kamar bakinta Zai yage Saboda Murna Mirmishi ya saki Har Hakoransa Farare suka Bayyana Dukawa Yayi ya cire Takalmin Kafarsa kana ya kariso Cikin Falon kasa ya Zauna Daidai kafafun Aiya ya ijiye abunda ke Hannunsa yace"Aiya na same ku lafiya..?

Ya Fada yana kallonta Kansa ta Shafa tana Fadin"Lafiya Megidana Dan albarka..Zuwa Haka ba Sanarwa.."Kansa na kasa yace"Saboda yanayin aiki ne Aiya..Kada nace gani zuwa kuma ban samu zuwa ba..! Ina Hajja da Baba..?

Yafada Yana Kara gyara Zama Cikim Fara"a Tace"Eh hakane kam..Hajja tana ciki Habibu kuma ya fita kasuwa Ke Hajara..Ki Fito ga Mastur ya Dawo.."Tafada da dan karfi Hajja Dake Cikin Dakimta Tana Gyaran kayanta Taji kamar Muryan Aiya Dayake ta Kunna Radio ga kuma karan Tibi baisa Taji ba Fitowa Tayi Tana Fadin"Aiya naji..."Mganarta Ta makale ne ganin Mastur zaune yana kallonta Baki ta Washe Tana Fadin"A"a Babban Mutum ne..? saukar yaushe..?

Tafada Cikin Farinciki Tana karisawa Kusa Dashi kansa Ya maida kasa ya Danrankwafa yana Fadin"Ina kwana Hajja..? Yanzu na iso.."Cikin Fara"a ganin Dan nata take amsa mai Lokaci Daya Tana Tambayansa Wajen aikinsa yace Alhamdulillah Mikewa Tayi bayan Aiya tace"Ke Hajara Kawo mai abun kari mana..Kin barsa Zaune kuma kinsan Tafiyar Safe yayi.."Shi dai kawai Mirmishi yayi bai yi mgana ba Hajja Ta Shiga Kitchen Ta Zubomai Soyayyan Dankalin Da Suka karya Dashi Dama na Mansur ne ta Diban mai da kwai sai Fulas din Ruwan Zafi da kayan Tea ta Fito Dauke da Faranti Da Sauri ya Mike ya karba yana Fadin"Sannu Hajja..Da baki Dauki ba da kin Kirani na Dauka Dakaina.."

Yafada yana Ijiyewa nan Saman Cafet Din Daya Malale a tsakar Falon,Hajja Tayi Mirmishi Tana kallon yaron nata Daya kara Sauyawa Tace"ai ka girma da wannan aikin Babban Mutum.."Yana Zama gaban kayan Karyawan yace"A"a Hajja Kin Taba gani ko Jin inda D'a ya girma da yima iyayansa aiki..?

Dariya Tayi Tana kara Godema Allah Daya bata D'a kamar Mastur in yayi mgana ko Baba Habibu albarka,Tea ya fara Hadawa ya Fara kurba Aiya na Gefe Tace"Hala Habibu bai son da Zuwanka bane..? Hajara ko Zaki Kirashi ne ki gayamai..?

Da Sauri ya Girgiza kai yana Fadin"A"a Aiya a kyaleshi ai ina nan ba yau zan koma ba sai Gobe in Allah ya kaimu.."Hajja Tace"Gobe goben nan Babban Mutum..? Kallonta yayi yana Fadin"Eh Hajja..Monday akwai aiki fa..Zuwan Daman Domin na ganku ne..Na kuma Bata ma Mansur rai."Aiya tace"Aifa Koda naji yana ta Sambatun nan nasan wani abu yayi.? mansur sai Shirin Allah ni Habibu ma yayi mai aure ko Zai yi Hankali.."

Hajja na Dariya Tace"Ai ya isa Auran Aiya.."Aiya ta Tabe baki Tace"Ahakan..? Ammh Irinsa Mashiririciya irin yarinyar nan Hadiza ko..? Daman sun Dace da juna a aura musu juna suje Chan su karata bamai ma wani Fada.."Yana kurban Tea ne Aiya ta Fadi haka Sai da yaji Ruwan Zafi ya kasa Shiga Cikinsa ya Tsaya Cak Makogwaronsa Sai kuma Numfashinsa ya Fara sama Sama nan da nan ya Kware ya Fara Tari Hajja da Aiya suka Rude suna mai Sannu nan da nan sai ga Tea din na Biyo Hancinsa Ruwa Hajja ta Ruga Kitchen ta Debomai na sama wanda Take Tarawa a kofi Ta Bashi ya karba ya kafa kai yasha Sosai kana ya Dire Kofin ya Koma yana Jingina da kujera yana Maida Numfashi Su kuma suna aukin Jeramai Sannu.

Ya Dade yana kai da kawo Tsakaninsa da Zuciyarsa da kalaman Aiya kafin ya Iya Daidatuwa Dakyar ya iya Bude Idanuwansa da sukayi Jajir Dasu Kamar Garwashi,ya Muskuta yana Kallon Hajja da Aiya da suka Kwabe Fuska kamar Suyi kuka Mirmishi ya saki kafin yace"Kada ku damu..Bakomai Hajja.."Yafada Lokaci Daya yana Mikewa Domin Gabadaya Cikinsa ya Cushe ne Duk da rabonsa da wani abu Tun Daya Bar Porthercourt ya taho yana mararin abincin Hajja ammh Kalaman Aiya sun saka komai ya Fita kansa.

Ganin ya Mike yasa Aiya Tace"Ah ya haka..?baka karisa karyawan ba Ka tashi..?

P.cap dinsa yadan Ja baya ya Shafa Goshinsa yana Fadin"Sai anjuma Aiya.."Yana Fadin haka ya Duka ya Kwashi Wayoyinsa da System dinsa ya dago yana Kallon Hajja Datayi wani iri kafin yayi mgana Ta Rigasa da Cewa"Kana dai Lafiya ko..,?

Mirmishi yayi mata kafin ya gyada kai yana Fadin"Eh..Hajja bari naje nayi wanka.."Da Sauri tace"Dan"uwanka na nan bai Tashi ba.."jinjina kai yayi bai yi mgana ba ya Fara Takawa zai Fita Tace"Me zan Dafa maka da Rana..?

Yana jin Haka ya waiwayo yana kallonta kafin yayi Mirmishi yace"Nayi kewar Tuwonnki Hajjanmu.."Farinciki ya kamata da Sauri tace"Angama Babban Mutum..Yau zakaci Tuwon Hajja Har ka Koshi.."Kai ya gyada kafin ya Duka ya Zura Takalminsa Ya Dago Hajja Ta Juya Zata Shiga Kitchen da Tiren kayan karyawan Data kawomai yace"Hajja Inna Karime ta Kirani...!

Waigowa Tayi Tace"Yaya karime.? Lafiya..? Cikin Sigan Tambaya Juyawa yayi yana Fadin"Sai na Fito Zamu Tattauna.."Ajiyar rai ta Sauke Tadanyi Mirmishi kafin Tace"Afito Lafiya..'Ranta ba Dadi Domin tasan mganar kenan Yaya karime bata bar mganar Hada Auran Babban Mutum da Yar wajenta Bushira ba,ta Ina Rayuwar Bushara da mastur ta Dace in da ace Zai yi Na"am Datafi kowa Murnan ammh kuma hakan akwai karuwa ga wanda yayi Karatun Boko mai Zurfi ya Rayu a Wayewan waje a Hadashi da wacce ko Hanyar makaranta Bata sani ba Ta Tabbata Mansur bazai karbi Bushara ba Ballatana Babban Mutum.

Bayan Fitansa ne Zata Shige Kitchen Din Dake Falon Taji mganar Aiya Tana Fadin"Uhm..aini Laifin Habibu nagani da bai Takama Karime Burgi ba..Ina Bushara Ina Megidana..! Ai ko Mansur dai Da ba wani Hankali ya Cika ba bana so ya aureta ba Tsakani ga Allah da akwai Cutuwa.."Mirmishi kawai Hajja TayiSanin Halin Aiya Tunda karimen Ta Tako da kanta Tazo Da mganar Aiya ta Kushe Tace bazata Sabu ba Baba Habibu kuma Daman bamai mgana bane yace mgana tana Hannun Mastur Inya amince Shi bai da Ta cewa Mansur kuwa ba wanda ya gayamai mganar ansan Bakinsa Kamar Sikat kada ya gayama Mastur sai gashi Ta Kirashi Da kanta kuma Tunda yace Ta Kirashi Aranta Tasan mganar ne.

Cikin Sanyi jiki da wani Raunin Zuciya ya Cigaba da Takawa Zuwa Shashen nasu,Gabadaya Zuciyarsa ta Shiga wani Sake sake na Daban kodai kodai Soyayyah suke yi ne..? Tunanin haka sai da Yaji Gabansa ya yanke ya Fadi Da Sauri ya karyata mganar bayan ya Girgiza kansa Acikin Zuciyarsa yana Fadin Da ace suna Soyayyah Tabbas da Mansur ya Fadamai baya Taba Boye masa komai,Tabbas da akwai Wani abu a Tsakaninsu Dashi ne zai Fara jin Labari Yin wannan Tunanin yasa yaji Hankalinsa ya kwanta har ma ya Karisa Shiga Shashen nasu Dayake Shuru Kamar ba Kowa.

Kamar zai wuce Bedroom Dinsa sai kuma ya Fasa ya Karkata Zuwa Dakin Mansur din ya Tura sai yaji a bude sai ya Tura ya Shiga gogan na kwance Baje Baje akan gado yana Barci Dagashi Sai Gajeren wando Dakin kaca kacs Daga gani ya Dade bai ga gyara ba Chan kaya Chan waya chan System Chan Takardu Takarce dai Gasunan.

Kai ya Dafe Cikin mamakin yaushe Kanin nashi Zai Sauya ne..?wata zuciyar tace mai kila sai Ranar da yayi aure ya zama magidanci.."Tuna Haka da yayi yasa ya Murmusa kamar zai Juya ya Fita sai kuma ya Fasa ya Fara Taku Zuwa Gaban makeken Gadon da Mansur Yake kai yana Sharar Barcinsa,Ya Dade Tsaye yana kallonsa kafin ya Duka yayi amfani da Hannunsa Guda Daya ya Murdemai kunninsa da karfi wanda yana Cikin Barci yaji kamar an Rike masa Kunnuwa sai yayi Tunanin mafarki ne,Sai ya kara Juyawa zai kara Bajewa Mastur ya kara Damke Kunnuwansa da karfi Wanda ba Shiri yasa Mansur ya Bude Idanuwansa da suka kankance Saboda Barci ganin wanda ke gabansa yasa ya Zabura ya Mike Zaune yana Mitsike ido Cikin Muryan Barci yace"Yaya Mastur na u..?

Bai ce mai komai ba Illah gyara Tsayuwa kawai da yayi yana dan Hararansa ganin haka yasa ya Sauko da Sauri Daga kan gadon ya Daka Tsalle ya Rumgume Yayan nashi yana ihun Murna da Faman Tambayansa yaushe ya Dawo bai sani ba Yana jinsa yayi masa Shuru bai tankamai ba bai Damu ba ya Dago yana Fadin"Yaya me nayi kake Fushi Dani..?

Yafada a Shagwabe kamar zai yi kuka Sai Lokacin Mastur ya kallesa yace"AU baka ma sani ba ko..?

Shuru Mansur yayi kafin yace"Allah Yaya duk iya Tunanina na kasa Tunawa..'Kunnensa Daya ya Murde yana Fadin"Ka manta da wayar da mukayi Dakai ta karshe..? Me nace maka..?ka Rainani ko Mansur yanzu ka Daina Jin mganata baka saka Komai agaba ba sai wannan Shanshancin Siyasan ko Daya maida kai wani kazami ko kanka Baka iya gyarawa,ji kanka Ka Tara suma ba aski ba gyara Kalli Dakinka kamar na Mahaukata bazaka iya gyarawa ba..? Whta Wrong With u ka Fara Hauka ne..?

Yafada Cikin Husky Vioce dinsa ammh Cikin Fada Saboda Bacin Ran abunda Mansur din ya aikata Mansur Zafi ya Isheshi Domin da Zafi ya Rikemai kunnin kuma yaki Saki,kara ya Saki yayi kasa da kansa yana Fadin"Wayyo yaya..Wlh kunnina Zafi ka Sakeni Plz...'Kara Matse kunnin yayi Da Karfi Har sai Da Mansur yaji kamar yayi kwallah Mastur yace"Yanzu ka Tuna Laifinka ko baka Tuna ba..?

Da Sauri yace"Na Tuna..Na Tuna..Wlh na Tuna yi hakuri Yaya bazan kara ba.."Sai Lokacin ya Sakeshi Lokaci Daya ya juya yana Barin Dakin yace"Ok..Kafin mu Fara Ainihin Fadan namu kafim ka Fito u Bettrr Clean dis Room ka gyara komai In bahaka ba Ranka sai yafi haka baci.."Da Sauri Mansur yace"Yes Sir...!Fita yayi yana Kyafci bai yi mgana ba yana Fita Mansur ya koma yana Rike kunnunsa Lokaci Daya yana Fadin"Wlh Ya Mastur yasan Lagon mugunta..Allah ma ya Taimakeni ya Daina kolo akai..Ai da naci Ubana yau.."Yafada yana yar Dariya Lokaci Daya Yana Tuna mganarsu ta karshen kan Gidansu ne Da auran kanwarsa Sakina Dayace yaje Chan Maruka ya gaida Baba Sule ya kuma Yi musu abunda ya kamata ammh Sam ya Manta Kansa ya Dafe kawai bai da ta Cewa Karamin Tsaki yaja jin ana ta Kiran Wayoyinsa Kamar Zai yi kuka ya Mike ya Fara Tattara Kayan daya watsar a kasa ko Ta kan wayoyin Dake Zube kan gado suna neman agaji bai bi ya Fara gyaran Dakin Sanin Da yayi in yayi wasaa Mastur ya Dawo bai gyara Dakin ba Yasan Sauran..

Diza kuwa Batasan Mastur ya Dawo ba 11am nayi ta HauraSama Tayi ma Mommy Sallama ta Hau Motarta ta Fice taso ta Shiga su gaisa da Hajja da Aiya Mansur kuma tasan bai Tashi ba yana Barcin gajiya Sai kawai ta wuce Tunda ana Jiranta Hauwa sai waya take mata tace in ta Dawo sai ta Shiga Ta isa wajen keman ba Dadewa ta Fara aikinta Sagir Abokin Mansur ya Kirata Tare sukayi Makaranta anan ABU,Shi bai samu aiki bane har yanzu sai Yake bin Mansur din yana Taimakamai Kamar dai P.A dinsa Shine ya Kirata yana Fadin yayi ta Kiran Wayar Mansur bai Daga ba Tace bata Gida Ammh bari ta Kirashi Taji itama Dai Kamar Sagir din ne Domin bai Daga kiranta ba sai ta Kira Sagir din Tace Kada ya Damu kila bai Tashi bane ya Bari zuwa anjuma ya Sameshi agida yace mata Shikenan ya gode da Haka suka yanke kiran..

Mastur kuwa yana Shiga Bedroom Dinsa yagansa Tsaf Dashi,Duk da ba haka ya barsa ba Daga gani an kara gyarashi kuma ba kowa bane ya gyara sai Hajja Mirmishi kawai ya Saki yana Jin Kaunar Mahaifiyar Tashi acikin Ransa Kayan Hannunsa ya Zube kan Katuwar Katifar Dake Shimfide adakin Wacce Taji Shinfidun alfarman Mastur Bai Cika son Gado ba Shiysa sai makeken Wardropr dinsa Dake Shake da kayansa Bai Tsaya wani Bata Lokaci ba yaTura Kofar Tiolet Din Dake Dakin ya Shiga wanka Yayi ya Fito Daure da Babban Towel Gaban Madubin Dake Dakin ya isa yaShafa mai kansa SayeSaye da gashi kadan Kadan Domin Mastur ya Tsani Tara Gashi Duk Sati yake Zuwa aski,In yaga Mansur ya Tara Gashi Ya Dinga mai Fada kenan Tun ba yau ba ammh bayajin mgana sam Har yau ya girma ammh bai San ya Girma ya Daina aikin Yarinta ba Shi yana mamakin yadds Har ya Fito Siyasa Partyn Dayake Ciki Ta karbeshi Sai dai kuma Bai da ja Mansur Mutun ne mai Dadin Zama Barkwanci da Son Mutane ya Tabbata Duk inda ya zauna Ko na awa Biyu ne sai sun ji suna kaunarasa Sau Tari In gayansa ya Shige Cikin su Hajja yana ta Hira sai ya Rika Bashi Sha"awa Domin shi bazai iya ba Mgana da Hayaniya kamar Lalura suka zamemai.

Jallibiya ya Zura Kawai ya Samu waje ya kwanta Domin ya gaji Tafiye ce fa ba Kadan ba Daga Porthercourt Zuwa Zaria Bai saba ba Domin Sau Daya suka Taba Tafiyan Mota kuma alokacin bashi ya Tuko Motar ba Sargent Inuwa ne,Ko takan Wayoyinsa bai bi ba daman suna Kashe ne ya Kwanta Yana Lumshe ido Saboda gajiya bai Dade ba barci ya kwashe Sai dai Mansur ya Shigo ya gansa yana Barci sai ya Fita ya Rufomai Kofa Ya Fice Daga Shashen Bayan yayi wanka ya Saka kananun kaya Na kamfanin Armani Shashen iyayen nasu ya Shiga suka gaisa da Hajja da Aiya suka Fara Diraman nasu ta Fama Hajja Tace Ina Mastur yace mata yana Ciki yana Barci ya Dade anan Shashen su Hajja kafin ya koma Barayinsu ya Dauko Wayoyinsa Kira ya Samu ba adadi Kiran Diza Shi yafi Muhimmanci ita ya Kira Take gayamai Kiranta da Sagir yayi.

Karamin Tsaki yaja yana Fadin"Kyalesa..Nifa yau ba Inda Zani..ina Fita Zan kara Laifi Wajen Ya Mastur..!Da Sauri Diza tace"Bangane ba..? Kunyi waya ne..? Da sauri yace"Ai Diran makiya yayimin Firstlday ta...Tun Safe ya Shigo..Kinga yadda ina barci ya Murdemin kunni Kamar zanyi kuka..Yana Dakinsa yana Barci yanzu Kafin ya Tashi Barci na karbi Hukuncina.."Farinciki Daya Cika Zuciyar Diza Yaushe Rabon Da Taga Abun Sonta Wannan Labarin yayi mata Dadi.

Cikin Farinciki tace"Ka gano Laifinka kenan My Honourable..?yana shafa kansa yace"Eh..Kanmganar zuwa Maruka ne.."Kai ta gyada Tana Fadin"Uhm..Ai na sani.Mansur Allah ya Shiryeka.."Yana Dariya ya amsa mata sun dan Taba Hira Yacr yaushe Zata Dawo Tace Sai ta gama Sallaman Mutane Zuwa La"asar Zata Dawo kana suka Katse Kiran Diza Taji kamar an sakata a ajannah Tana aiki Tana Mirmishi ita kadai Har Hauwa sai Da ta kalleta Tana fadin"Madam kamar an biya miki Kujeran makka..?

Diza tayi dariya Tana Fadin"Kai hauwa saka ido ko..? Ai wannan Farincikin nawa yafi Biyamin Kujeran maakka."Tana Dariya Tace"Allah Madam..?

Bata kara mgana ba ganin basu kadai bane Ashagon akwai masu Jiran kwalliya da wadanda akeyimawa ammh Ranar Duk wanda yaga Diza Sai ya Fahimci Fara"anta ya Karu Sauri Sauri Take tana son Ta gama Komai Ta koma Gida Ta Sakashi acikin Idanuwanta.

Mastur bai Tashi ba sai Bayan Azahar Ya tashi da bacin ran Barci yasa bai samu sallah ba agurguje ya Fada Tiolet yayi alwala ya Fito ya Shimfida Darduma yayi sallah yana Zaune yana Addu"a Mansur ya Shigo Dakin sai ya gansa ya Tashi Cikin Fara"ansa ya isa Kusa Dashi ya zauna yana Fadin"Ashe ka tashi..?daman yanzu nake Shirin Zuwa na Tasheka Har munyi sallah

Baice komai ba sai da yagama addu"an kana ya waigo yana kallinsa Fuska ya Hade yana Fadin"Kasan Girman Matsayin Mahaifi Kuwa Mansur..?

Ganin irin kallon Dayake mai Da kuma yanayim Muryansa yasa ya gane ba wasa kai ya Dukar yana Fadin"Nasani yaya..Kayi Hakuri abubuwa ne..!

"Har akwai wani abin da zai hanaka zuwa ganin mahaifinka bai da lafiya..? Mansur ka bani kunya Bantaba Zaton Haka ka koma Da bana nan ba..Ka baci Sam yanzu baka da Tsausayi.."Mansur kamar zai yi kuka yana son mgana ya Hanashi Mikewa Mastur yayi yana Nimke Darduman Dake Hannunsa yace",Ko ka Dawo Cikin Hayyacika ko kuma na Dakatar da wannan Takaran naka na Dauke ka na maidaka makaranta ka Cigaba da Masters Dinka..Tunda naga Siyarsace ke Sakaka kana Raina mganata Data Baba kuma kana Banzatar da Mahaifinka da yan"uwanka.."

Yafada Lokaci Daya yana wucewa ya barsa a wajen Wajen Wayoyinsa ya isa ya Dauka Yana kunnawa Bayan ya Zauna da Rarrafe Mansur ya Kariso gabansa Hannunayensa Saman kunnnuwansa yana Fadin"Afuwan Yaya..Bazan karaba Insha Allahu.."Kamar bazai kallesa ba ganin ya Isheshi Da magiya ne yasa ya Sauke mai Hannuwan yana Fadin"Is ok..Ya wuce..Ammh ka Shiga Hankalinka.?

Da sauri Mansur yace"Nama shiga..Na Dade da Shiga Yaya Mastur.."Mganar sai tabama Mastur Dariya Sai da ya Murmusa yana Saka Hannu ya Dago Mansur din suka Mike Tsaye ya Rumgumesa Mansur Shima yaRumgumesa yana Murna Cikin Bubbuga Bayansa Mastur yace"Ba ina maka Fada bane..Ko ina so in ta kuraamaka ba..No..Nafi kowa Son kanina da kuma somganin Rayuwarsa ta Inganta.."

Hawaye suka Cika Idon Mansur ya Dago yana Kallon Yayanshi yace"Na yarda da Yayana..Yau ko Bayan Raina na Tabbata bazan yi kuka Rashin mai Zama Bangon na ba data ahalinmu ba."Hararansa yayi yana Fadin"Ka Shirya gobe ma muje marukan tare..Sai na Koma Jibi."Tsalle ya saka yana Fadin''Yauwa.."Mirmishi kawai yayi mai ya Dauko wayoyinsa yana Fadin "Muje Shashen su Hajja..Nasan yanzu Tagama min Tuwona.."

Mansur yace"Au daman wai kai take ma Girki.? Lalle Hajja son kai.."Mastur bai kulasa ba ya Fice yana Fadin"Ai daman kai kanka ka sani.Kullum haka kake Fadi.Alhalin kai kana Gida Ni kuma sai Lokaci Bayan Lokaci nake Zuwa.."

Mansur nabin Bayansa yace"Uhm..Ba wani nan Yaya Allah Hajja yanzu tafi sonka.."Yafada yana wani Tura baki Tsayawa Mastur yayi har yazo Suka Jera Suna Dafe da kafadun Juna kamar wasu yara In kagansu alokacin sai ka kara kallonsu Domin zasu Burgeka da ganin Irin Shakuwar Dake Tsskaninsu.