13
[12/23, 6:59 PM] Janafty: SADAUKARWAR SO..!!
(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)
Wattpad:@Jamilaumar315
Mallakar:Jamilaumar(Janafty)
Page1️⃣3️⃣
Shashen Hajja suka koma,Lokacin Hajja ta gama Tukama Mastur Tuwon Dayace yana so Tuwon Farar masara Tayi mai na gargajiya ba na Garin Semovita ba Da Miyar Bushashiyar Kubewa Dataji Bushashan Kifi wanda Shi Mastur din ne yazo musu da Kifin wanchan Dawowar da yayi.
Mastur yaci Tuwon nan Sosai Wanda Rabonsu Dayacii Abinci mai yawansa Har ya manta Yana Bala"in son Abincin Gargajiya Musamman kuma wanda Hannun Hajja ya Dafa Tun Lokacin Daya Tafi Hassan Gwarzo karatu Dandanon Abincin Hajja ya Wahalar Dashi kafin ya saba Hakama Dayaje Sokoto,A porthercourt kuwa Kowa ya sani ko Takeway zai bada ayimai ko Tuwon Masara ko Tuwon Shinkafa Miyar Alaiyahu,in dai aka ga yaci Shinkafa toh Babu Wadanan ne kuma yana jin yunwa bai da mafita.
Tare da Mansur sukaci Abinci kamar yadda suka Saba achan Baya ko ayanzu ma in ya Dawo Tare suke Cin Abincin Bayan sun Gama suka kara Zaman Hira Duk da Rabin Hiran Tsakanin Aiya da Mansur Sai Hajja Dake Saka musu Baki Jefi Jefi Mastur kuwa Duk da Hayaniya Lalurace garesa yau din ya Danne bai Tashi ba yana Zaune gefe Daya yana Bin Kowa da ido Baya Umh ballatana Uhm Ko Aiya ko Mansur in wani ya Sakosa Cikin Zencen baya mgana Sai dai yayi yake kawai Ya Lumshe ido basu Damu ba Sanin Hallinsa Haka kurum yake ji aransa Dama Shine Mansur fa Yana son ya zauna ya Dinga Hira da Mutane yana Sakin Jiki Dasu ammh Kwata kwata Baya iyawa ko yana so ya Daure ya Rika Shiga Cikin Mutane sai ya kasa Daya Shiga sai yajisa wani iri da an Fara Hayaniya da Surutu zai ji ya Tsani Zaman wajen Yau din ma Saboda Cikin Ahalinsa ne kuma ya Dade baya Gida Shiyasa ya Daure kawai ya Zauna yana Jinsu kuma yana Kallonsu Daya Gaji ne ya Tashi ya Shige Dakin Hajja ya kwanta,da kallon suka Bisa Sun Tabbata yayi kawaicin ne ya gaji ya Tashi ya Gujema wannan Hiran ta Mansur da Aiya wacce Duk Rabinta Gaddamane da Labaran da bai ma Shafesu ba,yana Shiga ba Dadewa Shiima Mansur ya Fita Sagir ne yazo bayan ya Fita sunyi mgana ya Dawo yace su Hajja zasu Fita da Sagir in Yaya Mastur ya Tashi Ta gayamai ba Dadewa Zai yi ba tace toh.
Mastur barci yayi akan gadon Hajja bai tashi ba sai da aka Kira Sallar La"asar kana ya Tashi ya koma Shashensu ya Dauro alwala ya Tafi masallaci Bayan ya Dawo ne ya Koma Dakinsa ya kunna System dinsa ya Fara Duba Sakonnin Muhimman Bayanan da aka Turomai ta Email Dinsa,Jefi Jefi kuma yana amsa waya Hajja ta gayamai Fitan Mansur ammh yana ta Tsumayin Dawowarsa Shuru.
Diza kuma Bayan La"asar ta baro Wajen aikinta Zuwa Gida Tana Dawowa Zumudin ganin Mastur yaki barinta Ko Abinci Bata iya ci ba tayi wanka tayi Sallah Tayi Shigan Wata Ubansu Jallabiya Red Colour mai kyau da ita ta yane kanta da Mayafin Jallabiyan ta Saka Wani Takalminta mai Tudu Ja Mai kyau Dashi Wayarta ta Dauka acikin Jakanta ta Haura Sama Dakin Mommy Ta isketa Tana Lissafi kusa da ita ta Zauna Tana Fadin"Mommy barka da yammah.."
Mommy Ta Dago Tana kallon yar nata Tana Fadin"Yauwa..Diza yaushe kika Dawo..?Diza tace"Ban dade da Shigowa ba..Wanka kawai nayi sai nayi sallah.."Kai ta kada Tana Fadin"Oya tashi kije Fadime ta baki abinci kici ki Huta nasan Kin gaji.."Mirmishi Tayi Tace"Mommy bana Jin yunwa Fita ma zan sake yi.."
Sai Lokacin Mommy Ta Lura da Kayan Dake Jikinta Cikin mamaki Tace"Ina kuma Zaki Daga Dawowarki ko Hutawa bakiyi ba .?ko Fita zaku yi da Mansur ne Nasanku Sarakan yawo kamar kafarku taci kafar kare.."Dariya ta saka ta Mike Tana Fadin"Kai Mommy kema Idon kika Sama na kamar yadda Aiya ta Riga ta sakamana.."
Mommy tace"ai gaskiyanta ne..Bakwa Zama waje Daya..Kune Chan kune chan Kamar wasu Sabbin Aure.."Diza ta Murmusa Tana Fadin"To ba inda Zamu Tunda an sakamana Ido..Gidan Hajja zan Leka in yi ma Yaya Mastur barka da Zuwa.."Mommy tace"Mastur.! ? Yaushe ya Dawo ? Tafada Cikin Farinciki Diza Tace"Yau da Safe Dazu mukayi waya da Mansur yake gayamin bai Shigo bane..?
Mommy Tace"A"a kila sai anjuma In Daddynki ya Dawo..In kinje kice ina mai Sannu da Zuwa Ina nan ina Jiransa Ban yi Fushi ba..Ki gaida Hajjan da Aiya.."Diza Ta Juya Tana Fadin"To Mommy Zan Fadamusu.."Daga haka ta Fice ta Sauko kasa kenan suka Hade da Mama Fadime tagaisheta ta amsa Tana Tambayanta ya aiki tace ba Dadi Tayin Abinci Tayi mata Tace Sai anjuma bari ta Shiga Gidan Hajja Mama Fadime ta Bita da adawo Lafiya.
Lokacin Data Shiga Gidan Aiya Tagaji Da Hiran Ta Shigo Ciki Tunda Ta Shiga yin Sallah Hajja ne aharaban Gidan Tana kwashe Shanyan kayan Aiya Data Wanke mata da Safe,Diza ta Duka ta gaisheta ta amsa Cikin Fara"a Tana Tambayan ta Mommy Tace Tana gaishesu ita da Aiya Mikewa Diza Tayi ta Karbi kayan Hannun Hajja Tana Fadin"Hajja Ina Aiya ne Banji Motsinta ba.."Tafada Lokaci Daya Tana kallon Motar Mastur Dake Haraban Gidan Daman tasan yana Gida in yazo garin Baya Zuwa Ko"ina Daga Gida sai kuwa in ya Shiga gaida su Mommy ko ya Leka Gidan Balaraba Gaishe da Kawu Usman.
Hajja Ta bata amsa da Fadin"Aiya Tana Ciki..Suna nan Zaune Tun Wajen azahar ita da Mansur da Babban Mutum..Babban Mutum ya Gaji da Hayaniyarsu kinsan Halinsa ya Tashi ya Shiga Ciki ya barta Ita da Mansur Shima dai ba"a Daden ba Abokinsa Sagir din yazo Suka Fita yacr bazai Dade ba Shuru dai Har yanzu..Shine Ana kiran La"asar ta Shiga Daki Tayi Sallah bata Fito ba Kila Ta Dan Kishingida ne.."
Diza na Bin Bayan Hajja Zuwa Falon tace"Ayyah..Yaya Mastur din Fa Hajja..? Hajja tace"Yana Shashensu Bayan ya Dawo Sallar La"asar yace min zai Shiga yayi wani aiki ne.."Diza Ta Zauna kan Daya Daga Cikin kujerun Falon Tana Taya Hajja Ninke kayan Take Fadin"Bari na Shiga mu gaisa..Mommy ma tace nace Tana nan Tana Jiransa Batayi Fushi ba.."
Hajja na Dariya Tace"To Daman Ta ina uwa ke fushi da Danta..Zai shiga inajin Sai Zuwa Dare Lokacin Baban nashi ya Shigo da Alhaji.."Diza tace"Hakane.."Hajja Tace"Kinga Hadiza Ijiye Kayanan ki Tashi kije ku gaisa..Bana komai Zan karisa Dakaina kin Dawo Daga wajen aikin ki kin gaji bazan kara Sakaki wani aikin ba..'Diza Tace"Kai Hajja Don Allah ki barni na kusa karisawa.."Dole Hajja ta kyaleta suka Karisa Ninke kayan ita ta karbi kayan Tayi sallama Dakin Aiya Ta ganta Akan Abun Sallah Tana ta Barci Azaune Dariya ya kamata aranta Tace Dole kiyi Barci Aiya..Ko Gajiya da Surutu Bakyayi.Kan karamin gadonta ta Ijiyemata Kayan ta Fito Tace ma Hajja Bari ta Shiga ta Fito Daganan ta Fice Zuwa Shashensu Mansur din Lokaci Daya Taji gabanta na Faduwa Wanda Inda ZataTunkari inda Mastur yake Haka Zata Rika Fama da wannan Faduwar gaban,wanda in Zata Shiga Wajen Mansur bata jin irin Haka kanta Tsayr ma take Shiga Sanin Mastur din Baya nan sai Mansur din shi Kadai.!
Cikin Sanyin Jiki ta Fara Knooking a kofar Falon nasu ammh kuma Shuru Har tsawon wasu Mintina Sai kawai ta yanke Shawaran Tura kofar sai gashi ta Bude,Sai ta sawo kanta Falon da Karamar sallama abakinta Sanyin Ac Dake Falon ya Daketa Ta Lumshe kafin ta Fara Taku zuwa Cikin Falon Dakin Mastur Take kallo Data gani adan Bude Sabanin Dakin Mansur Dake Rufewa Tana Takawa Zuwa Dakin Gabanta na Faduwa kamar Ta jiya Haka takeji ammh ta kasa.
Sai da ta Tsaya akofar Dakin Tayi Sallama Cikin Siririyar Muryanta Lokaci Daya Taji Kafafunta na Rawa Lokacin Dataji Muryansa yana Fadin Ashigo Cikin Karfin Hali da Jarumta Ta saka Hannu Ta Tura Kofar ta Shiga Cikin Dakin tana karayin Wata Sallaman.
Kansa na Kasa yana ta aiki Bisa System dinsa atsakiyar gadonsa Tun Datayi sallaman Farko Yaji Muryantq ya Shaidata Ko Mutuwa yayi ya Dawo zai iya Shaida Muryan Dizan Daya gama Tantaceta Tun Shekarun Baya,lokacon Data Shigo Cikin Dakin Bai yi Saurin Dagoewa ba Duk da Yadda Zuciyarsa Tayi Tsalle Waje Daya Saboda Murna ganinta sai ya basar ya Dago kansa a Hankali yayi mata kallo Daya ya kauda kai Bayan ya amsa Sallamanta.
Lokacin Daya kalleta kamar TaKafafunta Zasu kadata Saboda wani irin yam Dataji ya Tsirgamata Tundaga Kafarta Har saman kanta Dakyar ta iya Zare Takalmin Kafarta Ta Fara Taku Har Cikin Dakin Gefen Gadon Ta samu matsunguuni Ta Dofana Duwawunta Tana Gaisheshi ya amsa batare daya Dago ba,Sai da Tagama gaishesa ya Dago yana kallonta Kasa kasa ganin Ta wani Zauna kamar Ana Koranta kuma ta wani Sunkuyar Dakai yana mamakin Yadda yarinyar take mai Girman kai ko don Yana mata Fada ne in tayi ba Dadai ba Ko kuma Saboda Baya musu wasa Tun Baya Daga ita Har Mansur din.
Cikin Dakakkiyar Muryansa yace"Ki zauna Dakyau mana.."Jin Abunda yace ne yasa ta Dan gyara Zamanta Taa Dan Muskuta Tana Fadin"Mommy Tace tana gaisheka..Kuma wai Tana nan Tana Jiranka batayi Fushi ba.."Kamar bazai Tankata ba Sai da ta Saci kallonsa Taga yana Dan Mirmishin nan nashi mai Tsada Chan Taji muryansa Cikin Kasaita yace"Zan shiga anjuma in Daddy ya Dawo.."Daga haka bai kara mgana ba itama Sai ta Dauke kanta Kamar bata kallonsa Tana ta wasa da wayarta Dake Hannunta.
Shuru na wani Lokaci ita Tana Zaune kanta a kasa Bata kara mgana ba ammh Zamansu a waje Daya yana kara Sakata Cikin Natsuwa bataki su Dauwama ahaka ba Har Abada ba,Shi kuma yana auna Yadda Dizan ta koma ne yanzu yana mamakin Inya gansu Tare da Mansur Wani bayama wani Fada ammh In suka Hadu kamar Salaha take komamai Sai yake Danganta Haka da Girman kai takemai ko kuma wani Shariyace bai sani ba..
Wayarta ake ta Kira Tana kin Dagawa yana jinta karan Wayarce ta Dameshi Da wani Zafin Zuciya yana Tunanin kada ace wani Namiji ke kiranta Cikin Muryansa Ta Dakiya yace"Ki Daga wannan wayar taki..Kararta na Damuna..".
Da sauri tace"Hauwa ce ke kirana..Wacce ke taimakamin Bangaran Office dina na Makeup.."Bai kara mgana ba ya Dai kalleta ta gefen ido Ganin Ta Daga Kiran Tana Fadin"Ya akayi ne Hauwa..?
Baisan me ake ce mata ba Daga Karshe dai tace"Hauwa kiyi ma wadanda sukayi Bukking na Gobe..Kuma ina Gayamiki bana sin zari..Kada ki Cikamana Mutane Mutane Goma sun isa in kuma kika Cika Wlh ke zan bari da aiki Am Telling u.."Dagachan Bangaran Hauwa na Dariya tace"Bakomai Madam.."Daga haka ta yanke Kiran Duk yana Jinta ita kuma Sai Ta gama wayar ta gano Laifinta da Sauri Tace"Kayi Hakuri..Zan yi waya ban Fita ba Allah sa Hayaniyata bai Dameka ba..'
Bai tankata ba Har ta Cire rai Sai Taji yace"Kin fi jin Dadin wannan Sana"ar taki da Cigaban Karatunki Khadija..?
Yafada yana Kafeta da Idanuwansa masu Firgitata da Sauri ta Sadda kai ta kasa Mgana Ba Tun yau ba yasha mata mganar Cigaban Karatunta Dama Dama ace Zata iya Karatun Datayi Saboda Cikama Mastur Burinsa Sai Dai kuma Bazata iya Juran Wahalhaun Karatun ba kuma Ba Ra"ayinta bane yin Karatu bai Zurfi Hakan tafi jin Dadin Rayuwarta So Simple.
Ganin ta kasa Mgana yasa ya kada kai yana Fadin"Is ok..Tashi kije..Tunda haka kika zaban ma kanki..Ammh ki Sani akwai Watarana da Zatazo kina son Kiyi Karatun..Ammh kuma Lokaci ya Riga ya Kure Miki.."Yafada yana Jin wani Takaichi acikin Ransa Kamar akan kaya take ta Mike da Sauri Ta Juya ta Fara taku Zata Fita yayi Galala yana Binta da kallon Soyayyah Muradi Sha"awa da Kauna Ta Har abada Sai gaahi ta waigo Sun Hada ido Irin kallon Dataga yana mata yasa ta Saka takalminta da Sauri ta Fice Ta Rufomai Kofan tana Sauke Numfashi Dakyar ta iya Jan Kafa ta Fice Daga Shashen Saboda Halin Datake Ciki Ko Shashen su Hajja bata koma ba ta Fice Daga Gidan Zuwa Gida Gabadaya Soyayyar Mastur Data Binneta acikin Ranta Taji Tana ta Fitowa Daya Bayan Daya,Har ta Shiga Cikin gida Jikinta bai bar Rawa ba Dakinta Ta Fada ta Rufo Kofa Ta Dire kan gado Tana Haki kafim Lokaci Daya kuma wasu Hawaye suka Fara Zubomata kanta Ta Dafe Tana Fadin"Ya zan yi ya gane ina Matukar Sonsa..?me zan yi Nima ya Soni Kamar yadda Nake sonsa..?
Haka take ta Fada kafin ta Sulale kan gadon ta Fashe da wani marayan kuka wanda yake Fitowa Daga Karkashin Zuciyarta.
Shikuwa abagaran Mastur yayi kokarin Zama Namijin Duniya Bayan Fitan Diza bakinsa ya Cija yana Kada kai Har sai yaushe ne zai iya gayamata Yana Sonta..? Watarana ne zai gayamata Ya Fara sonta ne Tun bata mallaki Hankalin kanta ba..? WaniDare zai Tabbata Dare mai Albarka da Tarihi a garesu..?shima bai sani ba ammh Tabbas in ya Cigaba da Zama ahaka yarinyar Zata kasheshi Lokacinsa bai yi ba.
Sai dakyar ya iya yakice Tunaninta ya Cigaba da aikinsa Har Mansur ya Dawo Dole ya Ijiye aikin ya Cigaba da yima Mansur din Fada da lallashi yana kara Nunamai Muhimmancin Iyaye da kuma yan'uwa Har Mansur din ya gamsu yace mai insha Allahu Hakan bazata kara Faruwa ba,Da haka suka Cigaba da Hiransu Rabin Hiran Duk Mansur ne yana Bashi Labarin Siyarsu da Halin da ake Ciki Sjidai yana jinsu wani wajen yayi Mirmishi wani wajen kuma Dayaga yana da ta cewa sai ya Tofa albaarkacin Bakinsa Har aka Kira Sallar mangariba suka Fita Zuwa masallaci Mastur bai bari sun Dawo ba sai da suka Tsaya akayi Sallar Isha"i wanda Tare da Daddy da Baba Habibu akayi ta Sai Bayan an Idar da Sallan ne suka ga Mastur wanda ya Duka yana Gaishesu Daddy ya amsa Cikin Farinciki ya Dagosa yana Shafa kansa Basu Tsaya wata mgana ba Su Mansur da Baba Habibu suka Nufi Gida Bayan Mastur din yace Zai Shigo kafin ya kwanta.
Suna komawa suka Hadu anan Falon Hajja,Baba Habibu nata Tambayan Mastur wajen aikinsa yana amasa mai,shi kuma Mansur yana Kitchen Wajen Hajja sai gasu sun kawo Abinci Shinkafa da Miya da Salat,Sai Tuwon da Mastur yace a Dumamai Shi zai ce,Baba Habibu na gani yacr Hajja Tayi Sonkai Shima Tuwon yake so Mastur yace Bari ya wanko Hannu sai suji Tare Mansur na jin Haka yace Shima Dashi Za"aci,Haka kuwa akayi su uku suka Taru suna ci Tuwon Cikin Farinciki Bayan sun gama ne Mansur da Baba Habibu suka Kara da Shinkafa Shi kuma Mastur yana gefe yace ya Koshi Yaje Kitchen ya wanko Hannu yazo ya zauna yana Kallon Baba Habibu ganin haka yasa ya gyara Zama yana Fadin"Babban Mutum ya akayi ne..?
Mastur yace"Baba kan mganar Zuwa Maruka Duba Baba Sule..Gobe zamu Tafi da Mansur in Zaka samu zuwa sai mu Tafi Tare ."Baba Habibu yace"Ba Mtsala Allah ya kaimu..Kayi Tunani kwarai kuma ina Fatan kayi mai Fadan Sakacin da yake yi da Iyayansa da yan"uwansa."Mastur ya gyada kai yana Fadin"Namai Fada Baba.."Mansur ya Tura Baki yana Fadin"Ni wai Baba sai kayi ta cewa amin Fada.."Aiya Dake gefe tace"Kana jin mgana ne..? Tun kana yaronka kake Laifi.."Hararanta Yayi yana Fadin"Kefa Daman yar saka Ido ne Aiyan nan.."Yafada yana wani Mele mata baki Ta Jefeshi da Murfin kula Tana Fadin"Kada kamin Rashin kunya..Ga megidana akusa in saka ya sakayamin kai.."Dariya ta kama su Baba Habibu Mastur ma sai da ya Murmusa.
Hajja ce ta kalli Baba Habibu Tana Fadin"Kaji ashe ya karime ta Kira Babban Mutum..? Baba Habibu Dake sakacen Hakori ya Kalleta yana Fadin"Topha..Me tace mai..?kardai kan mganar Busharan ne..?
Hajja na kallon Mastur tace"Bansani bai gayamin komai ba ammh ina Zaton akanta ne.."Baba Habibu zai yi mgana Mansur yace"Wata Busharan kuma Hajja..?Kafin suyi mgana Aiya tayi karaf Tace"Busharan Karime mana..Wai Saboda Shirmenta Taga Megidana ya zama Ubansu Take so ta Hadashi da Bushara yarta.."Mansur ya waro ido Yana Fadin"Wai ya tafi da ita Porthercourt tayi mai aiki..?
Dariya Ta kama Mastur Sai da ya Murmusa Allah ya Shiryi Mansur Baba Habibu ne yamai Dakuwa yana Fadin"Kaga naka nan Mansur..Ko Zai dauki yar aiki mai Zai Hadasa da Daukan mace Kuma ma yar"uwansa.."Mansur yace"Ah Baba in ba yar aiki ba Bushara fa..!wlh a yar aikin ma xai Taimaka mata ne.."Aiya Tace"Kai Sakarai waye yace maka yar aiki ce..? Wai fa ya Aureta..?
Mansur ya Zaro Ido Kamar yaji Mugun Abu yace"Au...? Na shiga Uku ni Mansur Sulaiman Doguwa..Ammh Inna karime Ta Gama da Ya Mastur wannan Bakauyan yarinya Kazama da wani katon Bakinta kamar Dankalin Kasa ne Zata Auri Yayana Son kowa kin Yarinyar Data Rasa..? chab wlh da Sake wannan ma Allah Yaya in ya kalleta ayyada yake zai iya yin amai.."Hajja ce Dake kusa Dashi Ta Sakarmai Dundu Tana Fadin"Zan ci Mutumcinka fa Mansur.."Yana Dariya ya Tashi Da Gudu Zuwa Bayan Mastur yana Fadin"Wlh Yaya kada ka yarda..Uhm.Wlh ka yarda ka Aurta achan Wajen aiki Sai an Daina ganin Girmanka.."Hajja ta Sake Dakamai Tsawa Aiya tace"Ke Hajara ki kyaleshi mana..Karya ya Fada..? Kamar yadda Karime take yaya gareki Ni Uwa nake gareta ammh fa Bana Goyon bayan Karya da Cuta Kin gani nan."
Mansur ya Daga mata Hannu yana Fadin"Yauwa Aiya..Ko kefa..Zan yi meneji Dake in na zama gwamna ko Shugaban Tsoffin mata na baki.."Baki ta Washe Tana Fadin"Haba Honorobul ko dai Mukamin Fisladi din.."Gabadaya Su Baba Habibu suka saka Dariya Mansur Har yana Tuntsirawa Ya Dago yana Fadin"Aiya bafa Honorobul ba Honourble akace..Ba kuma Fisladi ba Firstlady akace mtsalan ba Turanci.."Mastur ne ya Murdemai kunni yana Fadin"Baakajin mgana ko..? Ihu ya Fara yana Fadin"Na bari Yaya kunnina..Srry.."sakinsa yayi yana Mirmishi Aiya kuma Rai Ta Bata Tana Fadin"Koma miye..dai nadai Fada Daidai ehe..Dakace cewa ba Turanci kafi ni iya Fada ne..?
Mastur ne yace"Bai fi ki ba Aiyata..'Baki ta Washe Tana Fadin"Yauwa Megidana na kaina.."Baba Habibu ne yayi gyaran Murya yana Fadin"Babban Mutum me kace game da mganar Kariman..? Abunda ka yanke Shine Daidai Tunda Kaine keda Wuka Da Nama..?
Shuru yayi bai yi mgana ba Mansur yayi karaf yace"Baba Allah baya sonta baz.."kallon da Mastur ya bishi Dashi ne yasa yayi Shuru yana Sosa keya Kai Mastur yadan gyada kafin yace"Baba nifa ba yanzu zanyi Aure ba..Ta aurar da ita in ta samu Miji nayi mata alkawarin Bata Dukkan wani Taimako in Hskan Tataso.."Aiya tace"Shikenan Fakat.kagama mgana.."Baba Habibu yace"Hakane kayi mgana..Ammh mganar ba yanzu Zakayi aure ba ai Shirme ne Babban Mutum kafa Girma ga Mansur Dukkanku kun Isa Aura Shi yama sani Lokacin Daya samu Kujeran kansila ya samu Tawaye kan Rashin Auransa ba Domin Alhaji ya Shiga ya Fita da bai Samu Ba..Yau da yake neman kujeran Chairman Bamai Zaban sa bai da mata Shima ya sani Ballatana kai da Kake gaba Dashi.."Hajja da Aiya suka Hada Baki wajen Fadin"Gaskiya ne.."Shuru Daga Mastur Har Mansur sukayi Mansur yana so yayi mgana ammh kuma yana Tsoro ganin Mastur bai ce komai ba.
Mikewa Baba Habibu yayi yana Fadin"Ku tashi kuje ku gaida Babanku..Shima nasan mganar zai yi muku Domin Ya Dade Daman yana tuntubata kan mganar.."Batare da Mastur yace komai ba ya Mike yana Fadin"Sai da safen ku.."Mansur ma ya Mike Hajja da Aiya sukayi ma sai da Safe sukuma suka Bisu da Allah ya tashemu Lafiya Domin Daga Gidan Daddy Shashensu zasu wuce.
Har suka shiga Gidan Daddy Ba wanda yayi mgana Mansur yana so yayi mgana kuma ganin Mastur ya Hade rai yasa ya kama Bakinsa Afalon kasa suka Zauna Mama Fadime ta Haura Sama Ta gayama Mommy,Diza na Cikin Dakinta Tun Bayan kukan Datasha bata Fito ba Wanka ta Sakeyi ta Saka Kayan Barci Riga da wando masu Taushi,Ta Fita Kitchen ta Hado Tea ta koma Daki Tana Sha Tana Duba Sakonnin Da aka Turomata Duk Ranta ba Dadi Mommy Data lekota sai tace Batajin Dadi.
Kamar wasa taji muryan Daddy da Mommy a Falon kasa alhalin Tasan basu cika zama ba sai Falon Sama batare da Tayi Tunanin Yafa komai ba ta Fito Ko Dankwali Bata Dashi Kitson Kalaban da Hauwa Tayi mata sun Bazu a Kafadanta Dayake Tana da gashi Wadanda ta gani Zaune saman Cafet gaban Daddy da Mommy ne suka Sakata Ta kasa Karisowa Jikinta sai ya kama Rawa Mastur Da yayi mata kallo Daya ya kauda kai Yana Jin Bugun Zuciya da wani Sanyi Sanyi na Shigarsa Mansur kuwa Kura mata ido Yayi Cikin Soyayyah da Muradi..
Mommy ce ta Ganta Sai ta kalli Daddy Tana Fadin"Ga wata ma Gandamemiyar Budurwan ka manta da ita Alhaji..Itama Diza ya kamata in sun Fito da matan Aure itama kce ta Fitar da Miji mu Aurar da ita mu Huta Tunda ba Karatu take ba.."Ta Fada Tana Nunata
Jin Abunda Mommy tace ne yasa Diza ta Zaro Ido Lokaci Daya ta juya ta koma Cikin Dakinta Gabanta na Faduwa Ta Fito da Mijin Aure..? Suma su Ya Mastur mganar Matan Auran Daddy ke musu..? Wani Mirmishi Ta saki kafin tace"Inaga Lokaci ne yazo..!
Achan Falo kuwa Diza na Shigewa Mansur ya Juyi yana kallon Daddy Cikin Sosa kai yace"Ai ni Daddy ta kwana Gidan Sauki..Daman Lokaci nake jira da kuma Yaya Mastur kada ace nayi gaggawa.."Daddy da Mommy Harda Mastur suka Kafeshi da ido Daddy yace"Gaggwan me Honourble..?
Mansur na sosa kai Duk kunya ta kamashi yace"INA DA WACCE NAKE SO TUN TUNI..!
Gaban Mastur ya Fadi Ras..Ya kara Ware ido yana kallon Mansur Daddy da Mommy suka Washe baki suna Fadin"Masha Allah Abu yayi kyau.."Mommy tace"Yar ina ce Surukar tawa..?
Kan Mansur na kasa yace"Mommy Yaya Mastur zai gaya muku zan Fadamai Daga baya.."Daddy na Dariya yace"Ba Damuwa muna Jira..Kai kuma Babban yaya kaima ka Kokarta a Duba dai zaman haka Bai Dace ba Shekaru nata Tafiya.."Mastur Dayaji Jikinsa yayi sanyi Cikin Ladabi yace"Insha Allahu.."Daganan sukacigaba da Hira Rabin Hiran Ta Bangaran aikin Mastur Ne shiyasa Saboda Daddy nema yake Bude baki yana Bashi amsa,anan ne ma yake Fadamai Tafiyansu Maruka Gobe Daddy yace Shima zai Bisu Goben Daman bazai Fita Kamfani ba,Basu bar Gidan ba sai 11saura na Dare kana suka yi musu Sallama suka Tafi Diza kuwa Farinciki yasa tuni tayi Barci da Wuri batasan Tafiyarsu ba...
Suna Shiga suka Kulle get din suka Nufi Shashensu Ranar Mansur Dakin Mastur ya Tattaro ya kwana ganin Dare yayi ga Gajiyasa yasa bai mai mganar Diza ba ya bari sai Gobe to Gari na Wayewa Karyawa kadai sukayi suka Dauki Hanyan maruka su Hudu Daddy,Baba Habibu ,Mansur da Mastur a Motar Mansur sukayi Tafiyan Kuma Mansur ke jan Motan.