14
[12/23, 6:59 PM] Janafty: SADAUKARWAR SO..!!
(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)
Wattpad:@Jamilaumar315
Mallakar:Jamilaumar(Janafty)
Page1️⃣4️⃣
"Sun isa Doguwa Local goverment da wuri cikin maruka Sun iske Jikin Baba suLe da sauki har ya fara Fita Kofar gida haka yana ganin gari ammh baya Doguwar Tafiya.
Yaji Dadin ganinsu Baba Habibu karin Farinciki ma Har da Daddy,Haka aka Dinga ina aka Saka dasu yan"uwan Mansur kuwa haka suka Zagayesa,Mariya Dake gidan Auranta ana gayamata sai gata Maryama Daman Tana Gida Tunda auranta ya mutu,Sakina kuma ana Shirya Shiryan Auranta ne sai karamar su mardiya,da sauran yaran,Fadan da Mastur yamai yasa yaja su acikin Jikinshi Zainabu kuma tayi sanyi yanzu Tunda Goggo Ta rasu bamai goyamata baya Kuma Taga Mansur din ya Girma Allah ya Daukakashi Shike Taimakonsu Shi da Zuru"an Maryama din.
Sun Dade anan Marukan Da Zasu Tafi Dubu 100k Daddy yabama Baba sule na Hidinar Bikin Sakina Mastur kuma ya bashi 50k yace yaje asibiti a Dubashi Suka Fita waje suka Barsa Tare da Mansur su gana amtsayin D"a da Mahaifi ga Yayyin Babansa Baffanshi suna Waje suma suna Jiransa...
Mansur Shima Dubu 100k ya bama Baba Sule yace na Hidimar Gida,Mgnar kayan Dakin Sakina da komai da komai kuma ya Daukeshi yana Hannunsa,wannan kudin Daya bashi yaje asibiti sauran kuma ayi Hidiman Gida Dashi Baba Sule yana ta Godiya kamar ya kwantamai ya Shiga Dakin Zainabu yayi mata sallama ya bata Dubu 10k ya kuma ce Maryama ta Shiga makaranta Ko ta addini ne Tunda auranta ya Mutu zaman haka ba amfani Tunda sunyi sskaci basu yi karatun Boko ba,mardiya kuma in ya dawo zai tafi da ita wajen Hajja tayi karatu Zainabu ta karba Tana ta Godiya Harda kwallah Tana Tuna irin Zaman daya Gudana Tsakaninta da Maryama sai gashi yau Abunda ta Haifa ne Bangonsu.
Daya Fita suma Baffanin nashi Duk sai da ya Sallamesu 10k kana suka Rabu kan sai Bikin Sakina wanda Zatayi aure Acikin Garin Doguwa,daganan Ririwai suka yada Zango Gidan Karime Wacce kamar ta Fadi Saboda murna bakinta Kamar zai Cire Saboda Fara"a Ita a tunaninta mganar Bushara da Mastur ne ya kawosu nan da nan ta aika akira mata Bushara Daga Bakin Kasuwa inda take Saida Masara Dafaffiya,Bayan tazo Tayi mata Rada a kunni sai gashi tazo gaishe dasu Baba Tana ta wani Sunne kai wai kunyar Surukai Sai Lokacin Baba Habibu ya gayama Daddy mganar da Karime tazo Dashi Kan Bushara din Shima sai da yayi Dariya Shi ko Mansur Vidoe ya Dinga Daukanta Lokacin Datake gaishe da Ya Mastur kanta a kasa Kamar Zata mai Sujada Sai wani Sunne Kanta Take cikin Hijabi Mastur ko bi ta kanta bai yi ba ma Balle ya Fahimci wani Hali take ciki ba Ruwa Kadai suka sha agidanta Saboda sun sha Fura agidan Baba Sule Lokacin da Inna karime Taji bayanin Baba Habibu kan Ra"ayin Mastur kan Bushara sai da taji kamar Tayi kuka Har suka Tafi Bata kara Dariya ba Bayan sun ijiye mata kudi Daga Mansur har Mastur din sai bayan sun Fita ne Bushara ke Tsallen Murna Inna karimen ta Zabgamata Harara Tana gayamata yadda suka kare Dasu sai ga Bushara Har da kuka Tana Tunanin ta Samu Zankadeden Saurayi kuma sai taga samu Taga Rashi..Inna karime najinta Tana kuka Tayi mata Banza Babanta ma Dayazo Yaji Sai da yayi Dariya Daman karime bata jin mgana Sai da ya gayamata Ina Bushara Data Tashi a Kauye ina Mastur wanda Yayi gwagwamaryan ilimi ai Hadin ba Daya bane sai tace ai shima Mastur din A kauyen aka Haifeshi Duka Daya suke Dole yayi mata Shuru,Ammh Yanzu Dataji mganar Daga bakin masu yi ai sai ta bar mganar Dolenta.
Aranar da suka koma kano Mansur yaso yayi ma Mastur mganar Diza sai dai kuma bai Samu Dama ba sun Dawo a agajiye kuma Shima adaran Shugaban Partysu ya Kirashi Dole ya tafi bai dawo da wuri ba Koda ya Dawo Mastur ya gaji Har ya kwanta Gari na waye kuma Karfe 8:30am na Safe Mastur yayi sallama dasu Hajja Da Baba Sule ya shiga Har wajen Daddy da Mommy yayi musu Sallama Har ya Tafi Diza bata sani ba Tana chan Tana Barci mai Cike da Tunanin Burinta ya kusa cika Lokaci yayi da Zata Bayyana ma Mastur Mtsayinsa aranta Saboda tafi Kowa sanin Halinsa in ta Zauna Tana Jiran sai ya gayamata Yana Sonta Haka Zasu yi ta zama Sai dai Tafi Kowa sanin mgana Yana masa matukar Wahala.
Shima abangaran Mastur Yaso matuka yaji wata yarinya ce Mansur din yake so bai taba gayamai ba duk yadda suka kasance abokan Sirrikan juna Wata Zuciyar tana ta wani sake sake Kada abunda take Hasasomai ya zama gaskiya in ya Lura da Statement din Mansur din sai dai baya bama Zuciyarsa Daman yadda da hakan Bai samu Lokacin da zasu zauna suyi mgana bane kuma Daya koma Porthercourt Hankalinsa ya koma kam aikinsa ko sunyi mgana da Mastur Sai dai kawai su gaisa basu samu Lokacin da zasu Tattauna ba Duk da Mansur din yana Su Tattauna mganar Domin yana so kafin Lokacin Zabensu Ayi bikinsu da Diza din Shi kuma Mastur din yace ya bari in ya samu Lokaci zai Kirasa su Tatttauna.
Diza kuwa har Titsiyeshi Tayi Tana Tambayansa wayake so..? Daman yana da wata wacce yake so ne ko Labarinta bai taba Bata ba,Kin gayamata yayi yana ganin kamar ta sani kawai jan ajin nan ne na mata ammh Shi anashi Tunanin yana Tunanin Da Zaton kamar yadda yake sonta Ba tun yau ba ita ma hakan take Sai dai ya saba Lamba Bai san Diza bashi take so ba Dan"uwansa yaya mafi Soyuwa garesa take son ya Zama Bangonta Har Abada,Kuma ma yaso ya Fahinci wani abu Lokacin Daya bata Labarin Busharan Inna karime Har da Nuna mata Vidoe Yaga Tsantsan Tashin Hankali da Damuwa Da Kishi acikin Idanuwan Diza yaso ya Fahinci wani abu ammh kuma sai bai Taba Saka Tunanin haka aransa ba sai yayi Tunanin kila Saboda Taji mganar Busharan Daga sama ne Sai da taji yace ya gayamata yadda suka kare da Inna karimen da Abunda Mastur yace ne yasa yaga Ta Sauke Numfashi Fuskarta ta Saki Daga Lokacin kuma Tatashi ta koma Gida Wuni Tayi Cikin Damuwa aranar ma Ta gwada kiran ya Mastur yafi sau goma Tana Fasawa Tana ji kamar ta Kira Mastur ta gayamai Sirrin Zuciyarta kafin wata ta Rigata Samun Zuciyar abun sonta sai dai kuma ta kaasa Tana Jin Nauyi Kuma uwa uba ba wani Sakewa ko Sabawa a tsakaninsu Tayi Tunanin ko Mansur Zata gayamawa ya gayamai Sai kuma ta Fasa Tana sakawa tana Warwarewa ammh Tabbas mganar Bushara ta girgizata Duk da Taji ance yar kauye ne ammh Kishinta ya Turniketa Diza Tana san Tana da Kishi ammh Kishinta kan Mastur Dabam ne bata kaunar ma wata taRabeshe abaya ma Datake Zaune bata Damu ba Sanin Datayi Shi Mastur Daman yake Aboki ma bashi Dashi ballatana Wata Budurwa kuma ta Tabbata inda akwai wata Tabbas Mansur zai Sanar da ita,ammh yanzu kam Lokaci yayi da Sirrin Boye zai Fito Fili itama Tana Bukatar kasancewa dashi a matsayin Matarsa.
*******
Bayan Wata Daya..
University of Lagos Da Misalin karfe 12:30pm na ranar Jumma"a
Alhamdullillah su Rumana sun kamallah Jarabawansu ta Karshe Aranar Sun Firfito Kowanne kagani Fuskarsa Cikin Fara"a da Farinciki mazan su da matansu suma sanye da Farar Lapcoat ne,Suna ta Daukan Hotuna Cikin Murna mara Misaltuwa Ruma gefe ta koma Ta Dauki wayarta ta kunnata Wanda Tunda suka Fara Jarabawan ta kasheta Karatu kadai ta saka agaba,ba kama Hannun yaro bata kira ba"a kiranta Umma ta kira Tana Dagawa Cikin Farinciki tace"Umma Mun fito Last paper dinmu yanzu.."
Umma Dagachan Bangaran Tace"Masha..Allahu Ruma..Allah yasa abunda kika karanta albarka Allah yasa kiga sakamako mai kyau.."Cikin Farinciki Rumana ke amsawa Da"Ameen Umma..Nayi kewarku keda Abba..Ina Goggo Jummai da juma..? Umma tace"Kowa lafiya..Abbanki ya Fita yana kamfani Goggo Jummai na Daki ta kwanta Kafarta na matsa mata Juma kuma tana Kitchen..Muna kewarki Rumata yaushe Zaki Dawo..?
Ruma tace"Allah sarki..Ki gaishemin da goggo ta Umma..Zan Dawo sai Next week.Zan tsaya in yi Clearence,sai kuma akwai Dinner da muka Haada In kuma gama Sai na Dawo gida,in sakamako ya Fito da kuma in sunkiramu Indection..'Umma tace"Shikenan Allah yayi Jagora Ruma..Ki kira Abbanki Ya Damu kullum sai yayi Zencenki.."
Rumana Tace"Zankira shi yanzu Umma.."Da haka suka yanke kiran Abba ta Kira Cikin Farinciki ya Daga wayar,yayi murna da Farinciki Da Rumana tace sun gama jarabawa yayi mata addu"a sosai ya Tambayeta yaushe zata dawo tamai Bayanin da tayi ma Umma ya Fahimta suka Rabu bayan ya Tambayeta ko tana Bukatar Wani abu tace A"a bata Bukatar komai da haka sukayi sallama ko Cikin makaranta Bata bari ba zuwa Hostel Taga Sakon 100k Daga Abba ya Turo mata Murna da Farimciki ya Cikata Har Abada tasan ita yar Gatace.
Abba kuwa Farimcikinsa Daya Rumana ta gama karatu zata Dawo gabansa,Yana son Ruma Tayi aure yaga Jikokinsa Ita kadai ya Haifa aduniyar nan yana Bukatar ganin Tsatsaon Ruma kafin ya bar Gidan Duniya Ko da Farko bai so ta Fara Karatu bai aurar da ita ba Sunsha mgana da Alhaji Sunusi kan hakan Shiya ya Dinga Bashi Shawaran ya barta ta Cika Burinta,Nayi karatu Allah barshi In Allah ya kawo mata Mijin ko Tana cikin yin ne sai aurar da ita sai ta Cigaba da karatunta adakinta da wannan Shawaran ya Tsaya mata Har ta Cimma Burinta Sai dai abu Daya na Damunsa na ganin Rumana bai Taba gani ko Jin Labari wani Saurayinta ba Har Umma ya Tambaya tace Batajin Rumana Nada wani Saurayi ammh dai bata sani ba,Hakan yasa Hankalinsa ya tashi yana so Rumana Tayi aure yana son yaga ya'yanta.
Alhaji Sunusi ya kira yagamai Abun Farinciki Shima ya Tayashi Murna sosai ya kuma ce in Lokscin Indaction dinsu ya Tashi ya sanar dashi Shida Mommy Har da Diza zasu je mata Har Lagos Abba yaji Dadi Sosai yace insha Allahu,Daganan suka gangaro kamar mganar kasuwancinsu Da haka suka Rabu,Daddy yana Dawowa yake gayamawa Mommy Lokacin suna Falon Sama Har da Diza Mommy ta kalli Diza Tana Fadin"Diza Zaki ma yar"uwarki Lagos ko..?ki tayata Murna ta Zama likita.."
Diza na Faman latsa wayarta Tace"In bani da wani aiki Mommy..zani insha Allahu.."Daddy yace"In bata da Lokaci ki kyaleta Asiya..Ni Dake sai muje.."Mommy tace"A"a da ita zamu je..Haka zasu ta zama basu san juna ba..? Tun suna Yara ba Rabonsu da juna.."Daddy yace"Zasu san juna mana..Ai Rumanan ta Dawo Gida ko Daga baya Sai taje Tayi musu ko Kwana Biyu ne suga juna.."Mommy tace"ai shikenan.."Diza na jinsu bata tankasu ba,Bata jin ma Zata samu Zuwa bata kaunar Tafiya mai Nisa kuma in Tatafi wazata bar ma aikinta,Sai dai in kafin Lokacin ta samu wacce Zata rika Taimakonta Tana nan dai tana Dubawa bata son ta Dauki Shirmanmu ne,So take ta samu Kamar Hauwa wacce Take da kokari kan aikinta.
******
Ranar lahadi ta kama Weekend ne Tun Safe Mastur na Apartment dinsa bai Fita ya gaji Shiyasa yasha Barcinsa Sallar Azahar ma acikin Gida yayita sai da ya idar ya Daga waya ya Kira Sargent Inuwa yace yazo Gida yana Nemansa ba Dadewa sai gashi yazo kudi ya bashi yace yace yayimai Takeway din Tuwon Shinkafa miyar agushi da Nama ba Dadewa ya Dawo ya kawomai,ya Sallameshi cikin Gidan ya Dawo yaje kitchen ya Dauko Filet ya Juye ya Zauna yaci ya koshi ya Dora da Ruwa Dayake shan Lemukan Turawa basu Dameahi ba Nan Falon ya Zauna kan Daya Daga Cikin kujerun Falon yana Hutawa,Sai Tunanin Mansur ya Fadomai kan mganar Dayace zasu yi Tashi yayi ya koma Cikin Bedroom dinsa ya Dauko Wayarsa Wacce Sai personal mutane yake kira dashi kamar su Hajja Daddy da Sauransu Yana Dawowa yaje ya Dauko Karamin Kofi na Tangaran ya Zubo Coffea Daya Dafa da Safe yazo ya zauna yana kurba yana Laluban Wayar mansur din sai yaji wayar tana Ringing bai Daga ba sai ya Juya akalan kiran ga Baba Habibu suka gaisa yana kasuwa sai ya Kashe ya Kira Hajja suka Dade suna mgana Har ta bama Aiya sukayi mgana Daganan ya Kira Umma da Abba dake Sokoto suka gaisa nan ne ma Abba ke gayamai Gama Karatun Rumana Gobe ma Zata Hau jirgi ta Dawo Gida ya Tayata Murna kwarai yace zai Kirata Daganan sai ya Kira Wayar Daddy bayan sun gaisa Daddy ya karamai mganar da sukayi Dayazo Kan mganar Aure ya kuma ce yakamata Tunda Mansur yace Yana da wacce yake so shima yasan Abunda yake Ciki Dahaka suka Rabu da Daddy Duk sai Mastur yaji ya Damu ba wai bai Tashi Aure bane baisan Ta Ina zai Fara ba yaso sai sun samu Daidata da Fahimtar juna Tsskaninsa da Diza kafin komai ya Biyo baya,Shi bai san ta ina zai Fara ba kwata kwata bai da wani sani kan Harkan Soyayyah ba Shiyasa ya kasa yin wani yinkuri,Abunda ke Damunsa ma Rashin Sakewar da bashi Dashi Tsskaninsa da ita.
Yana cikin wannan Tunanin Wayar Mansur ta Shigomai bayan ya Dauka sun gaisa Mastur yace ina ya shiga ya Kira bai Daga ba Mansur yace"Ina Daki Ya Mastur..Na kwanta ne nagaji banga kiranka ba.."Mastur yace"Ina Fatan kayi sallah ko..?
Mansur yace"Yanzu na tashi..Nayi yaya ya aikin..?Mastur yace'Aiki Lafiya lau..Ya Siyasar taku..? Mansur na Dariya yace"Siyarku dai Ya Mastur..Kai ma ai yayan Dan Siyasan ne.."Mastur Mirmishi kadai yayi bai yi mgana ba Mansur yace"Yaya Mastur kun kara mgana Da Daddy kan Mganar nan ne..?
Mastur ya lumshe idi yana kara kwantar da kansa Saman kujera yace"Eh yanzu ma da mukayi waya sai da yamin mganar.."Mansur ya mike Zaune yana Fadin"To yaya kai kana da wacce kake so ne..? Ni dai nasan baka Dashi..Baka iyama Hira da Namiji Dan"uwanka ballatana Mace..? Ya fada yana yar Dariya Mastur yayi Shuru kafin yace"Kai ma ka sani ashe..? Ni na rasa ta ina Zan Fara ne Ammh Tunda ka iya Zan zo ka Koyamin Honourable.."Dariya ta kama Mansur yace"Nima ban Fara Gwajin bafa Yaya Mastur.."Mastur ya gyada kai yana Fadin"Meyasa..?bakace aleady kana da wacce kake so ba.."?
Mansur ya mike Tsaye yana Shafa kansa yace"Ai ban taba gayamata Sirrin Zuciyata ba ya Mastur..Ina sonta Tun ban san kaina ba na Fara sonta Tun Ranar Farko Dana Fara ganinta a Lokacin kuruciyarta..Ban Fahimci hakam ba sai da na Fara mallakan Hankalin kaina na Fahimci itace komai nawa ya Mastur.."Mastur Dayaji kalaman Mansur kamar dashi yake yasa yaji Jikinsa yayi sanyi Zuciyarsa ta Fara Tsalle waje Daya kada yazo Suna Tarayyah Shi da Dan"uwansa wajen son Abu Daya Bai ma samu Zarafin mgana ba yaji Mansur na fadin"Duka Tsarin Rayuwata Burinta ne ya Mastur...Duk da ban gayamata ba na tabbata itama Tana Sona kamar yadda nake sonta.."Mastur Dayaji Kamar Wutar Lantarki yajashi ya Mike tsaye rike da Kofin Coffea din Dake hannunsa Cikin Bushewar baki yace"Waccece..ita Mansur.."?
Mansur yayi Mirmishi yace'"Nasan zakayi mamaki ya Mastur..Yar gida ce...DIZA ce...!! Dam! Dam! Dam! Mastur yaji gabansa ya Fadi kansa yayi wami Mugun Saramai,Hannunsa da Jikinsa na rawa Lokaci Daya Kofin Hannunsa ya Sulale ya Fadi ji kake Tus ya Fashe Tsakar Dakin Saman Cafet din Dake Falon,Wayar ma Dake Hannunsa sai ta Sabule ta Fadi Saman Cafet din Jikinsa Jallabiya ce ammh Haka yake gumi da Zufa Har yana Tsiyaya Har kuwa da A.C dake Falon da Fanka wacce ke Gudu Tana bada iska.
Dagachan Bangaran Mansur yaji karan Faduwan abu Tus..Rike wayar yayi yana Fadin"Hello Ya Mastur..Kana jina..? Hello..? Yaji Shuru Domi Mastur yana jin Hello din Mansur ammh Jikinsa ya Daskare waje Daya ba zai iya Daga Hannunsa ba Ballatana har ya Duka ya Dauki Wayar kansa yana wani Saramai Lokaci Daya yana jin Amsa kuwan Mansur na Fadin Diza ce Zabinsa itace wacce yake so Tun tana Lokacin kuruciyarta Kenan Sun Fara son Diza Shi da Mansur alokaci Daya kenan..? Hasbunallahi wani"mal wakeel.."Yafada Lokaci Daya yana Dafe kansa Dayaji kamar zai Cire lokaci Daya yaji yayi yaraf ya Fadi na saman Cafet din Har hannunsa yana Dafa Glass din Daya fashe na Kofin,jini ya fara zuba ammh bai takai ba Halin da Zuciyarsa take ciki yafi Jinin Dayake Zuba Mansur kuwa gajiya yayi ya yanke wayar yana Tunanin Network ne sai dai kuma ya kara Kiran Wayar Mastur naji ammh ya kasa ma kallon Wayar Balle ya Dagata Har ta karaci Ringing dinta bai iya wani Motsin Kirki ba.
Kansa ya Dafe da Hannun Bibbiyu Jinin Daya bata Hannunsa Dashi yasa ya Dafe kansa Dashi Bai damu ba Cikin Wani irin Fuzgar Numfashi yake yi Domin Yanajin kamar Numfashinsa zai bar gangar Jikinsa Numfashi ya Fara saki Daya Bayan Daya Lokaci Daya yana Jawo Numfashin nashi kafin yaji ya dawo Daidai,Maida kansa ya jingina jikin kujera yana Jin kamar ya Rusa ihu,Ajiyar Numfashi kadai yake Saukewa yana jin Wayarsa nata Neman agaji yama kasa Tashi ganin kamar zai iya Shiga wani Hali yasa ya fara Kiran Sunan Allah,Cikin ikon Allah sai yaji shi ya Fara dawowa Cikin Hayyacinsa har ya iya Rarrafawa ya Mike Tsaye kan kafafunsa,Allah ya Taimakeshi bai Taka kwalban ba ya Tsallake komai Harda Wayarsa ya Fada Bedroom dinsa yana Rangaji kamar zai Fadi ya Fada kan Katifarsa Kamar wani matacce Yana so ne yaji ya yi kuka ko Radadin Dake zuciyarsa Zata Ragu gabadaya Jijiyoyin kansa sun mike Radau kamar mai wani Cuta Haka yake jin gabansa na wani Rugurugu kamar ajalinsa yazo Innalillahi wani'inna Illaihirraju"un wannan wani irin al'amarin ne Taya sukayi Tarayyah wajen son Abu Daya da Dan"uwansa..?meyasa ma bai Taba Tunanin Soyayyah Tsakanin Mansur din Diza ba..? Yake kallon haka kamar Shakuwa ce..?kuma itama Tana sonsa..Bazai Taba zama Sanadin Shiga Tsakanin Abunda Dan"uwansa yafi so akan kowa ba ko da Soyayyar Diza zai Kasheshi ya Zama Dole ya Binne wannan Soyayyar har Abada ya Cireta aransa Ta zama wani mafarki na Dabam Ya zama Dole yayi SADAUKARWAR SO ga Dan"uwansa Mansur Dagashi sai Allah suka san yana kaunar DizaDaga Rana mai kama ta yau bazai Taba bari wani ko wata yasan wannan mganar ba Ballatana Mansur ko Dizan susan da wannan labarin ba,kansa yaTura cikin Filo yana so yayi kuka ko zai ji sanyi ammh kuma abun akasan Ransa yake sukansa abu kamar waasa sai ga ciwom kai da Zazzabi mai Zafi har ya RufeShi Har yamma yana cikin wannan HALIN Har akayi Sallar La"asar bai iya Tashi ba yanaji Zuciyarsa ta Saukar ma da Jikinsa wani Nauyi,har aka Kira Mangariba ya kasa Tashi Sargent Inuwa ne yaga anyi Sallar La"asar ba Yallabai anyi mangariba ma Shuru yadda kowa yayi Shedansa baya wasa da Sallah akwai mtsala Shi yazo Gidan Ya Duba Tundaga Falo ya Tsorata ganin Fashashen glass ga Jini Sai daiHalin Daya samu Mastur aciki yafi Firgitashi Cikin Firgici yaje ya Kira Sauran Sargent din suka Tarairayesa zuwa mota Sai wani private Hospital,suna kaisa Sanin matsayinsa yasa nan da nan aka karbesa aka fara bashi Taimakon gaggawa,basu samu sukuni ba sai da suka Tabbatar da an kaisa Daki na musamman Bayan an sakamai Drip an mai alluran barci.
Mastur Farkawa kawai yayi Washegari ya gansa a asibiti sai alokacin abunda ya Faru ya Dawomai wannan Nauyin kan nashi yana nan har yanzu,Ba zai iya Tuna Rabonsa da Ciwo mai Zafi irin haka ba tun wani Ciwon Typiod Daya Taba yi yana Hassan Gwarzo har sai aka Dawo Dashi gida a Tearm din bayan Lokaci bazai iya Tuna wani DogonCiwo Dayayi ba ma sai dai irin Ciwon kai haka da Ciwon Gabobi na gajiya,ya takura azaman asibiti sannan kuma shi ba Ragon Namiji bane Jarumi ne Tsayayye bazai Taba zama saboda mace ya zama haka ba Dole ya gagice yana cema Likita ya bashi Sallama ya samu Lafiya sai dai bai Saurareshi ba Domin ya gayamai Jininsa ne ya Hau Lokaci Daya bai yi mamaki ba Domin yanayin Daya shi ga Ya zata ma Mutuwa zai yi.
Ransa bai kara baci ba sai da Sargent inuwa yazo ya kawo mai wayarsa da Jallabiyansa da Boxers Dayaje gida ya Daukomai Shine yake gayamai yaga wayar nan yashe afalo Shine ya Dauko mai yana Hanya Mansur ya kira ya Daga yagamai Yana asibiti bashi da Lafiya Ran Mastur ya baci kamar ya kwada ma Sargent Inuwa Mari,Haka ya karbi Wayar bai iya amsa Wayoyinsu Baba da Daddy da suke ta Kiransa ba Yariga ya sani Mansur ya gaya musu Bashi da lafiya,kuma shi yanzu bai san me zai ce musu ba shiyasa ma ko Taba wayar bai yi ba Duk da yaga Tarin Kiransa da akayi tayi kuma baya Raba Daya Biyun Kiran Duk na Mansur ne.
Sai da ya kwana Biyu Likita ya sallameshi da mganguna da kuma Gargadi mai girma kan kada ya saka ma kansa Tunanin Daya fi karfinsa Saboda Kada ya Kamu da Hawan jini Shi kuwa aransa yacr na nawa kuma ai yama kamani Tunda na Rasa Diza da toh kawai ya amsa bayan ya karbi Duka mgangunan Sargant Inuwa ya Tukasa Zuwa gida a Daya Daga Cikin Motocin Heaquater nasu Kudin asibitin ma da komai su suka Dauki Nauyin komai.
Koda ya koma gida ya iske har an Tsabtace Falon kuma yasan ba kowa bane sai Sargent inuwa bai ce komai ba ya Shiga Ciki ya Bisa da kayansa da magungunansa kafim ya saramai ya Fice Bai iya wani Tunani ba Domin Tun Daga Lokacin da Mansur ya gayamai Diza yake so ya rasa Duka wani Tunaninsa wanka yayi Ya zo ya saka Saukakkun kaya Saboda Jikinsa ba karfi,Lokacin an kira Sallar azahar Sai kawai yayi Sallarsa sai ya Dauko Wayarsa yaga Tarin Misseds na su Baba,Hajja,Mansur Daddy,Mommy Harda Diza abun mamaki Da kamar zai kyalesu sai yayi wani Tunanin kada suji Shuru su Zata ba Lafiya su Dauko Hanya Mansur ya Taba zuwa Har Cikin Apartment dinsa kuma ya Tabbatar da zai iya cewa Su Taho wannan Tunanin Da yayi yasa ya Lalubi Lambar Baba Habibu ya Kirashi wanda ya Daga da Gaggawa yana Tambayansa Lafiyansa..!
Cikin Dauriya Mastur yace"na samu sauki Baba har na Dawo Gida..likita ne ya Hanani Daga waya Shiyasa kukajini shuru.."Baba Habibu Dake kasuwa yayi ajiyar Zuciya yana Fadin"Alhamdulillah..Ai mu hankulanmu ya tashi..tunda Mansur yazo yagayamana Sargent dinka ya gayamai baka da Lafiya kana asibiti Muke ta kiran wayarka Shuru baka Daga ba Hankulanmu sun Tashi har ma Zuwa gobe Babanka da Mansur din sukace zasu bi jirgi Suzo nan Porthercourt din su Dubaka Ko lafiya..!?
Mastur yace"Basai sun zo ba..Suyi Zamansu Baba na samu Lafiya.."Baba Habibu yace"Shikenan Allah kara Lafiya."Mastur yace"Ameen..Ka gayamusu Baba basai sun zo ba..Zan kwanta ne nasha mgani zuwa anjuma zan kirasu.."Baba Habibu yace"Shikenan..Allah kara lafiya.."Daga haka suka katse kiran Mansur Baba Habibu ya kira ya gayamai sunyi waya da Mastur ga Abunda yace sai Lokacin Hankalinsa ya kwanta ya gayama su Hajja kowa yaji Natsuwa jin yana Lafiya,Daddy kuma Mastur din ya Kirashi da kansa ya gayamai sun Dade suna mgana yana mai Fadan ya Rika kula da kansa.
******
Bayan kwana Biyu Mastur ya gyagije ya Fara Fita Office ba wai Domin Zuciyarsa ta warke ba ya mike ne Tsaye ga Kakafunsa Saboda kada Gyambon da Raunin Dake Cikin Zuciyarsa ya shafi gangan Jikinsa alhalin ya Riga yayi ma kansa alkawarin Sadaukar da Soyayyar Diza zuwa ga Dan"uwansa Mansur.
Kowa ya kirashi a waya yamai ya jiki,Hatta da Abba da Umma Dake sokoto sun ji Labari kuma sun Kirashi Daddy ya gayamasu Rumana ma ta Kirashi Har sau Biyu Tayi mai Sannu da Jiki kuma Text dinta yana Shigowa Wayarsa Lokaci bayan Lokaci na kulawa Gareshi bai taba bi takai ba,Diza ma ta kirashi ammh bai Daga ba,Domin bashi da wannan kwarin gwiwan kwana yake baya Barci Sallah kawai yake yana Rokon Allah ya bashi Juriya ya kuma yaye mishi Soyayyar Diza acikin Ransa ya bashi Ikon kauda kai da Sadaukarwa Gashi nan ne dai kamar yana Tsaye ammh Cikin Lokaci kadan Ramarsa Ta Bayyana wanda yake Daga Cikin Zuciyarsa ne Lalle Soyayyar Bala"i ce Tana Azabatar da masu yinta bai Taba Zaton Soyayyar Diza Zata iya maidashi haka ba sai gashi Cikin kwanaki Kadan Rayuwarsa ta Fara Sauya kwana yake da Mugun Ciwon kai,kuma yana shan mgangunan da likita ya Bashi Sai dai baya kiyayewa da yawan Tunani Mansur bai kara Tadamai mganar ba ganin Halin Dayake Ciki Shima bai yarda sun kara Tattauna mganar ba kada wannan karon Mansur ya Fahinci wani abu Wanda baya Fatan Hakan Ta Faru..!